← Book details auren shehu Part 2 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 14 OF 34

Sashe 14

auren shehu Part 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read

"Toh ki saurara da kyau ki ji, mutum kamar Shehu sai fa kin masa bita da kulle dukan kabarin kishiya! Ni ba zance mi ki ga hanya daya da zan iya taimaka mi ki da shi ba matukar ba surkulle za mu yi ba, Usman kuwa babu surkullen da zai ci shi, ko siriki na ya buga ya bar shi...."

"Wani sirikin na ki? Ba kin ce ya rasu ba?"

Zainab ta tambaya cikin rashin fahimta, hakan ya sanya Rahila saurin gyara maganar na ta

"Ina nufin kafin ya rasu, eh kafin ya rasu din, toh dai abin da na ke nufi za mu ta gwadawa ne ko Allah ya sa a dace, yanzu dai ki fara da wannan shawarar da zan baki, ki saka wannan ki tai har fadar Shehu, na san matukar manya su ka gan ki da wannan shiga dole Usman ya ji kunya da kishi, kin ga a dole ya mayar da ke gun iyayen ki"

Zainab na mai tunanin ya aka yi wannan azancin be zo mata tun da ba ta amsa ma Rahila da toh.

"Anjima zan zo in je in wanke miki"

Rahila tace kafin ta fice tana barin zainab da auno kalar azabar da za ta sa a ma Shehu in ta isa gida. Ita kuwa Rahila tunanin yanda za ta isarwa mijin ta da wannan kyakkyawan labarin, dan ta san halin Usman duk hakurin shi matukar aka kai shi bango ya kan yanke hukunci mai tsauri, ko shakka babu idan har hakin ta ya cimma ruwa ya kori Zainab, mijin ta ya sami nama har gida, tsaf kame ta zai yi yayi gaba ko ba komai sa dan farfado.

Bayan fitowar Rahila Hansai ke tambayar ta dalilin dadewar ta a bukkar, tare da mata kashedi ta ce dai baki ta saki baki ta na ma Kado zance da Hausa ba, in haka ne ta kuka da kan ta. Cikin nuna kyamkayami ta ce

"Tir Allah wadar na ka ya lalace! Ina ni ina Kado maras daraja kamar wannan dai?"

Hansai na jinjina kai ta ce

"Gwara dai, babu ruwan ki da ita"

Zainab kuwa Raliya na fita ta aikata shawarar da aka bata. Shudin rigar ta damammiya ta saka, tare da bumshort din ta shi ma shudi, komai ya fitu zanzan duk da ramar da ta yi. Dan mitsitsin mayafi daya daga cikin doguwar rigar ta ta daura, dan shi kadai ya rage mata sauran duk tayi tutu akai.

Cikin annushuwan abin da ta ke shirin yi ta sa kai ta fito, wato ba Hansai da sauran jama'ar gidan ba, hatta Rahila da ta bata shawarar sai da ta bude baki cikin al'ajabi.

*Khadija Sidi*
Auren Shehu 2

8

Yanda kowa ya ke kallan ta ya sanya Zainab shakkar irin shigan da ta yi a kara na farko. Matan sun yi tsit in da masa yara ke kokarin rufe idanun yaran su gudun kar su ga tsairaici.

'Mata da yara kenan su ka shiga dimuwa saboda shigar da ta yi ina ga maza matasa da dattija da ke zaune fadar Shehu? Lalle babu maras daraja kamar wanga Kado'

Cewar Rahila cikin ran ta tana mai adduar Allah ya sa Zainab ta tabbata ballagaza ta taka har fada. Ganin Zainab ta dauki kafa tinkis tinkis ta na shirin fita Iyalle da ta kasa jurewa ta sha gaban ta cikin tsawa ta furta

"Waiyazubillah! Ina za ki fita haka tsurara? Wannan wani irin rashin daraja ne!"

Tafa hannu Zainab ta ke jin hausa radau bakin Iyalle wacce dimuwar ganin Zainab ya sa ta manta ta yiwa Zainab hausa.

"Ikon Allah da kin iya hausa shi ne da ki ka min kunne uwar shegu?"

Sai a sannan daga Iyallen har sauran matan gidan su ka ankare da subul da bakan da Iyalle ta yi. Cikin wayencewa ta na mai sosa kyeya ta karya harshe ta koma fulatanci. Hakan ne ya batawa Zainab rai ba tare da ta yi la'akari da shekarun Iyalle ba ta furta

"Dakin uwar ki zani! Na san kin ji wannan ma!"

Kuka Iyalle ta sa, ta na mai tafa hannu in da sauran matan gidan su ka shiga bata baki, Rahila ce mai ruko Hansai wacce ta ke kokarin damko Zainab da niyar bata kashi.

Cikin wannan hali ta sa kai ta fice daga gidan. Kamar yanda shigar Zainab ya girgiza ahalin gidan Shehu, haka ma sauran jama'ar Rugur, musammam maza domin kuwa shiga irin ta Zainab ko da wasa ba su taba ganin irin ta ba, dan a wajen su ba ta da maraba da tsirara. Babban abin da ya ke jan hankalin jama'ar rugur kuwa jikin Zainab ne, dan kuwa Rugar Shehu kaf babu mai irin shi, yawanci yara mata da sun fara dirgen dangin, mama ya dan tasa a kirjin su ake mu su aure, haka kuma maman ba ya zuwa koina daga sun haihuwa daya sun shayar sai ya zube sharkaf, dan haka akasalin Rugar daga wanda na su ya dan fara tasawa haka kuma duka an mu su baiko, sai na matan aure da ya zama silifas.
Wasu matasa da su ka kasa hakuri bin ta su ka ke yi a baya, Zainab kuwa ba ta fasa nufar Fadar Shehu ba. Bello wanda ya baro fadar kenan da niyar kai sako gidan Shehu ne ya fara ganin ta, ganin haka yayi ba shiri ya juya da saurin sa domin yiwa Usman gargadin masifar da ta dumfaro shi.

Cikin tashin hankali Usman ya bar fadar, abin ku da dogo nan da nan ya cimma Zainab tun kafin ta karasa fadar.
Ganin yanda ya tunkaro ta kamar zakin da ya shekara dari be ci abinci ba ya sanya matasa juyawa da sauri, ita kan ta sai da gaban ta ya fadi, Amma hakan be sa ta fasa tunkarar sa ba. Wani irin damka ya kai wa hannun ta har sai da ta saki kara, be kula ba haka kuma be iya duban ta ba gudun abin da zai iya aikatawa nan bainar jama'a matukar be danne zuciyar shi ba, ya soma jan ta kamar leda ba tare da ya ce mata uffan ba.

Duk yanda ta so ta cije ta ki bin sa abin ya gagara, ta na ji ta na gani haka su ka wuce sashin Shehu da sauran bukkoki, Zainab na waige waige cikin neman doki amma ganin yanda kowa ke dauke kai sanadiyar fushin Shehu ya sa Zainab saduda ta mai jiran tsammani. Ganin ya kutsa da ita dokar daji ya sa Zainab farin ciki, hakin ta ya cimma ruwa Usman yayi fushi gashi zai fitar da ita hanya.....wata boyayyar bukkar da ta hanga ne ya sanya murnar ta komawa ciki, musammam da ta ga sun nufi bukkar bilhakki. Cikin kokarin kwatar kan ta Zainab ta ke fadin

"Dallah malam ka sake ni! Ka sake ni! Ina ka ke ja na!"

Idan Usman ya tankawa Zainab toh dutse ma ya tanka. Bukka ce kwallin kwal sai garken Shanu wanda tsayawa fadar adadin su ma bata lokaci ne. Daga dayan gefen kuma yar karamar gona ce, sai kuma bishiyon kayan marmari da su ka hada da mangoro, leman tsaki, ayaba, fasadabur da dai sauran su.
Maimakom kufar karar da ta saba gani, kofa garwa ce jikin bukkar wanda duka daya Usman ya mata da kafadar sa ta bude, ya na mai jan Zainab su ka shige bukar sannan ya sake ta ta fadi kasa. Juyawa yayi ya jawo kofar ya rufe ta hanyar sanya mukulli da kwado ya datse.

Cikin faduwar gaba Zainab ta ke duban kofar, kafin daga bisani ta bi bukkar da kallo, bukkar na da girma sosai dan ta ma fi bukkar Shehu girma kadan, Amma idan aka dauke tabarmar kaba da ke shimfide tsakar dakin babu komai ciki. Da sauri Zainab ta tashi ta na mai fadin

"Da ka kawo ni nan uban me za ka...."

Yanda Usman ya juyo ya sanya ta zuke zancen ta, idanun ta cikin na sa da su ka yi jajur tamkar garwashi Zainab ta ja da baya a hankali ta na mai fadin

"Usman......"

Hannu biyu ya sa ya cire rawanin kan sa a saukake, karo na farko da ya bayyana mata fuskar shi hakan me ya sanya Zainab ruke numfashin ta. Ta sha ji ana cewa kyawu kamar mutum shi yayi kan sa, kokuwa ace kyawu kamar aljan ba ta taba gasgata akwai irin wannan kyawun ba sai a yau. Lokaci guda Usman ya rikide mata ya koma mata tamkar balarabe.

Ta san Usman fari ne, haka kuma ko ina ta ga manyan idanun Usman da kuma bakin gashin gira da na idanun sa za ta gane Usman din ne, haka kuma tun asali ba ta rena tsayin hancin sa ba, bakin lallausar gashi da ya taho tun daga kan sa, ya bi layin saje haka kuma ya sauka ta bakin sa ya na mai zagaye bakin ne ya kara kawata fuskar shi, ta zaci duk duniya babu gemu da shaje da zai kai na Sudais mijin Halitta kyau ba, ashe ba a banza Usman ya ke boye fuskar shi ba.
Ganin Usman ya sa hannu ya cire rigar jikin sa, yayinda faffadar kirjin sa wanda ke rufe ruf ruf da lallausar gashi ya bayyana, ga kuma kaunji nan duka hannayen sa ya sanya Zainab ja da baya. Yanayin bacin ran da ya ke ciki, wanda ya hadu da kyawun sa ya mayar da shi tamkar hatsabibi mai hatsabibin kyau.

"Usman.....me ka ke yi?"

Cewar Zainab cikin rawar murya ta na mai fitar da idanu.

"Hakkin ki zan baki Abu! Na ga kin fara fita hayyacin ki har ki na fitowa tsirara nema na...."

Cewar Usman yayinda ya nufota ya na kokarin kwance tazuge. Ganin haka haka Zainab ta fara ja da baya tana fadin

"Kar ka zo kusa da ni! Wallahi kar ka zo kusa da ni! Da na hada jiki da kai gwara na hada da kare! Kar ka zo...!"
Chapter 14 · 0% Book details