← Book details auren shehu Part 2 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 17 OF 34

Sashe 17

auren shehu Part 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Jiki na rawa ta kara dawowa ga saniyar, sai sannan ta gane wannan farin abun mai yauki yauki ba komai ba ne fyace dan saniya ne ke kokarin fiitowa, Saniyar nan dai nakuda ta ke. Hankali Zainab ba karamin tashi yayi ba musammam yanda ta ga wajan na kara budawa duk sanda Saniyar ta dan tsaya tare da durkusar da kafafun ta na baya, haka kuma ta dan tasa sai ta cigaba da takawa, da ke dabba dabba ce ciwan da take be hana ta cin ciyawa ba duk sanda ta gifta ta gaban sa.

Kamar yanda Saniyar ke kuka haka Zainab ke taya ta, haka kuma ita ma ba ta fasa safa da marwa ba ta na mai bin sahun Saniyar. Usman tafe tun kafin ya iso gidan gonar ya ke jiyo kukan Saniyar, tsoran kar ta cutar da Zainab ya sa shi karasawa da gudu.

Sa kafar sa gidan yayi daidai da lokacin da saniyar ta durkusar da kafafun ta na baya, kamar mai Shirin zama kasa ta sullubo yar saniyar ta akan idanun Zainab. Idanun Usman kan Zainab, tashin hankalin da ta ke ciki be boye kyawun halittar ta ba, dan kuwa Usamn zai iya rantsewa tun da ya zo duniya be taba ganin bafulanar da kayan saki ya mata kyau ba kamar yanda yayiwa Zainab, rigar ya saukar mata har ciki, abun ku da mai hips sai zanin ya zauna mata a kugu ya mata cif cif.
"Abu..."
Usman ya kira sunan ta cikin wani irin yanayi, hakan ya sa Zainab juyowa da sauri dan sam ba ta lura da shigowar sa ba saboda idanun ta na kan saniyar nan da ke kokarin lashe abin da ta haifa. Ganin sa da gudu ta nufe shi, cikin kuka ta shige jikin sa hakan ya sanya Usman runtse idanun sa, kan ta bisa kirjin sa yayinda ta ruke sa gam ta ke fadin

"Haihuwa ta yi, a gaba na ta haihu! Wallahi ta haihu!"

Usman na mai shafa bayan ta cikin rarrashi yayi karfin halin furta

"Yi shiru bar kuka Abu, kin ga baki da lafiya, ai ta riga ta haihu ni ma kin ga wata rana haka za ki haifo min diya mai kama da ke....."

Cikin sauri ta zare jikin ta daga nashi, cike da tsiwa ta furta

"Allah ya sauwake na haihu da kai gwara...."

Cike da danasanin furucin sa da ya ja masa rage jin dadi ya furta

"Don Allah kar ki karasa! Kin ga dai muna da mai jego be kamata mu na hayaniya gaban yar jinjira ba! Bari na taimaka mu su"

"Mtswww"

Amsar da Zainab ta bashi kenan yayinda ya wuce ta ya na mata dariyar kyeta. Sai da ya cire rigar sakin sa da rawani ya rage daga shi sai dogon wando sannan ya shiga taimakawa saniya. Bini bini sai ya kama Zainab wacce ke zaune bisa kujerar tsakar gida daga gefe ta na satar kallan sa, daga sun hada ido ta yi saurin kau da kai gefe.
Cikin ranta mamakin kyau da kyan sura irin na Usman ta ke, lalle Usman ya isa wannan kalmar ta "Man" dan kuwa da a ce wayayye ne da Zainab ta yi alfahari da shi, duk abin da ta ke mafarki na kyawun da namiji Usman na da shi, gaba daya sai ya dishashe mata duk wani kyan Sudais da ta ke gani, sai dai Usman kauyenci ya masa kan ta.

"Ina ma a dauki wayewar Sudais a bawa Usman"

Cewar Zainab cikin ran ta, gaba daya ta shagala cikin tunani sai tsuntar idanun ta tayi cikin na Usman, hakan ya sa ta kawar da kai cike da jin kunya. Usman na murmushin jin dadin yanda matar ta sa ke satar kallan sa ya ce

"Babu komai Abu ki kalle ni da kyau, ai ni mijin ki ne lillahi warasulihi! Jira na ke ki shirya na fara biyan bashin sadakin da na mora!"

Cike da jin kunyar ya kamata a karo na farko Zainab ta nemi amsar da za ta bashi ta rasa, ta tsinci kan ta tana mai tambayar

"Mace ce ko namji?"

Cikin rashin fahimtar abin da ta ke tambaya ya ce

"Me fa?"

"Abin da ta haifa, mace ce ko namji"

"Oh mace ce"

Ya bata amsa a taikaice yayinda ya ke duban yar jinjirar saniyar, har lokacin saniyar na lasar abar ta.

"Wani suna za a sa mata?

Zainab ta kara tambaya zuciyar ta daya. Usman na mai darawa ya bata amsa da

"Har wani suna na musammam ake sakawa dabba? Kai wani abun sai yan birni, toh wani suna ki ke so a saka mata?"

"Halitta!"

Cewar Zainab kai tsaye. Yanda ta fada da iya gaskiyar ta da kuma yanda ta yi mirsisi da fuska ne ya sanya Usman fashewa da dariya mai karfi har yana jefa kai baya. Yanda ya ke dariyar ya sa Zainab saka dariya. Sai ga su duka biyun suna dariya har Usman ya kare ta sa dariyar Zainab ba ta dena ba tsabagen na ta na muguntar ta ga yar saniyar ta mata kama da kanwar ta ta Halitta.

Tsayawa Usman yayi ya na kallan ta cike da sha'awar yanda fara'a ke yiwa Zainab kyau, tun da ya ke be taba ganin ta cikin annushuwa haka ba. Ko da ta ankare da kallan da ya ke mata nan ta ke ta tsuke fuska, Usman na murmushi ya ce

"Fara'a na mi ki kyau Abu, MashaAllah ki na da kyau"

Shiru ne ya biyo baya na dan wani lokaci, kafin daga bisani yayi gyara muryar ya ce

"Allah sarki Halitta, mace ce ta gari mai tsoran Allah....."

Wani irin bakin kishi ya taso ya tukare kirjin Zainab musammam da ta ji Usman ya kara da

"Darajar ta ya wuce a saka ma saniya sunan ta, ki bari idan ki ka haifar min diya a saka mata Halitta...."

"Aikin banza aikin wofi! Toh da ka san ita ka ke so ai da ka fadawa Daddy da be yi kuskuran aura maka macen da ba ta gari ba! Ka ga ita ba ma sai ka sato ba! Amma ka yi kum aka daura min auren masifa! Ka rabo ni da uwa ta, da yan uwa na! Da wayewa! Da makaranta ka kawo ni duhun daji bayan ka san natsane ka! Ran da na fara ganin ka na tsane ka! Har wata mace ta gari! Me ya sa ba ka aure ta ba! Allah ya isa wallahi!"

Ta wuce jiki da suri gudun kar hawayen da ke idanun ta su kunyata ta su zubo gaban Usman. Cike da mamakin me ya fada har ya tunzura ta haka ya bi ta da kallo dan sam be kawo a ran sa kishi ba ne. Zainab kuwa zubewa ta yi bisa tabarma ta sha kukan ta, wato ko a kauyen ma sai Halitta ta daga mata hankali, ta na can Saudia tare da na ta mijin amma ga Usman nan sai yaban ta ya ke.
Usman kuwa nan ya yi zaman sa sai da ya killace saniyar sa tsaf, har ya samu karamar ta fara shan nono, sannan ya nufi bukkar dauke da damammiyar furar da aka aiko masa da shi bayan Zainab ta shige ciki.

Ko da ya shiga ya aje kwaryar yayi gefe ba tare da ya tanka mata ba, yana kokarin saka riga ya ga ta ja kwaryar da kan ta, ta bude ta fara shan furar. Cike da mamaki ya ce

"Yau kuma yunwa ake ji Abu?"

"Na ga alamar so ka ke ka kashe ni, gwara na ci na koshi ko na sami damar yakar ka"

Cewar Zainab yayinda ta ke hadiyar furar da ko sukar babu, ta karfi da yaji ta ke sha. Be bata amsa ba sai da ya sanya rigar sa tsaf, ya zo ya zauna kusa da ita, hakan ya sanya Zainab matsawa da sauri gudun kar su hada jiki. Sai a sannan ya lura da idanun ta da yayi jajur, da alama kuka ta sha. Be tambaye ta dalili ba, Hannu ya kai goshin ta domin ya ji ko zabin da jikin ta ya kara raguwa dan dazu da ta rungume shi be ji zafin sosai ba. Da sauri ta buge hannun ta na mai kokarin kwada masa lodayi, ya janye hannun tare da fadin

"Na zaci mutuwar ki ke so ki yi ai? Me m ki ka ce? "
Ya fada cikin kokarin tuno kalaman Zainab, ya kara da

"Yauwa ka kashe ni ko na kashe kai na...."

Zainab ta masa banza ta cigaba da shan furar ta, har ya fitar da ran za ta kara tankawa sai ji yayi ta ce

"Wannan wani irin rayuwa ne a ce babu asibiti? Yanzu wannan dabba ce ta haihu fa, ina ga mutum?"

"Mu na da unguwar zoma"

Ya bata amsa a taikaice. Cikin rashin gamsuwa Zainab ta furta

"Idan kuma haihuwar ta zo da tangarda fa? Unguwar zoma ta iya tiyata ne? Sauran rashin lafiyar ina ake duba mutum bare a san cutar da ke damun shi a bashi magani?"

Shiru Usman ya mata yayinda ya ke tuno haihuwar Cangwai da ya zo da tangarda har ta kai ga rasa ran ta, haka ma na wasu dirgaggu da ba zai iya mantawa ba. Daga bisani ya furta

"Abu?"
"Uhum"
Ta bashi amsa baki cike da fura.

"Ya jikin ki?"

"Da sauki, wannan maganin da bani ya taimaka min"

Usman na gyada kai ya ce

"Kenan muna da magani mai kyau ko? Muna shiga dawa mu samo Allah ya mu ilimin, sarrafa su kamar yanda yan birni su ke sarrafa shi ne ba mu iya ba, shi ya sa na ke mana kwadayin sayasar tallfin ruga da shugaban kasa ke san kawowa"

"Ruga settlement policy?"

Zainab ta tambaya. Ya girgiza kai tare da fadin
Chapter 17 · 0% Book details