← Book details Zuciya Da Kuna Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 7 OF 17

Sashe 7

Zuciya Da Kuna Part 1 Complete Hausa Novel · about 7 min read

A cikin family ɗin Haroon kuwa… ba kowa ne ke farin ciki da wannan ba. Didi kakar Haroon tun farko bata son Fatima, tana yi mata kallon da bai dace ba, amma daga baya, ganin yadda Haroon ya tsaya tsayin daka a kanta, sai ta ja baya, ta rage tsangwama, amma hakan bai nufin ta amince ba. Meme kuwa… mahaifiyar Zeynab… bata ɓoye ra’ayinta.
A gare ta, Fatima black magic tayiwa haroon. Zeynab ma tana ci gaba da nuna ƙiyayya a ɓoye. Lokacin da aka yi aurenta ya mutu, ta so ta zauna a gidan Haroon, tana cewa “I’ll stay there…” amma Aslam ya katse ta “No… you stay with your mother” saboda ya san manufarta ta je ta ƙara musu damuwa.
A hankali, family ɗin ya rabu gida biyu waɗanda ke tare da Fatima da waɗanda ke kallonta da hassada Dalili kuwa guda ɗaya ne. Arzikin Haroon Duk inda aka je, sunansa yana ƙara ɗaukaka. Projects dinsa suna bunƙasa. Investments dinsa suna ninka.
Har ma a cikin estate ɗin da suke ciki, gidansa ya fi na kowa kyau, ya fi girma, ya fi tsari. Kowa yana son wani abu daga gare shi.
Amma… sai da yardar Fatima ake samu.
Hakan ya ƙara musu haushinta sosai Makiyanta suka ƙaru.Wasu har suna cewa suke a ɓoye “Ta yi masa black magic…”
Amma babu wanda ya isa ya faɗa a fili.
Rayyan kuwa…rayuwarsa tana tafiya cikin tsari. Fatima ce ke kai shi school. Fatima ce ke ɗaukar sa. Ko da akwai drivers, ko da akwai ma’aikata…ita ke son yin komai da kanta. Islamic school dinsa ma ta kula sosai da shi, ta sa ya shiga sosai cikin ilimi da tarbiyya, cikin ikon Allah, kwakwalwarsa ta buɗe, ya zama exceptional student, duk wani exam first position, duk wani competition shi ne a gaba. Teachers suna cewa “He’s brilliant”
Students suna girmama shi. Amma hakan ya ƙara tada ƙiyayya a cikin family. Har ma Uncle Usman…wanda a baya yana kusa da su…
ya fara canzawa. Saboda ganin irin nasarar da Haroon ya samu. Rayyan ya zama matashi mai hangen nesa. Wata rana ya zauna kusa da Fatima ya ce, “Mom… I want to join the army.” Ta ɗaga kai ta kalle shi.Idonta ya nuna tsoro. “No.” Kalma guda.Ya yi shiru. Bai ƙara magana ba. Saboda a wurinsa duk abin da Mom take so… shi yake so. Daga baya, ita ce ta zaɓa masa course Business Administration
“Zaka gaji Dad… you need to understand business.” Ya ɗaga kai. “I will.” Haroon ya yi alfahari da shi. Ya fara koya masa harkokin kasuwanci. Fatima kuma ta buɗe masa wata ƙaramar gonar da ta gada daga mahaifinta, a wani wuri mai kyau kusa da Île-de-France countryside, wuri mai cike da natsuwa da iska mai tsafta. Rayyan ya shiga cikin aikin. Da safe school. Da yamma farm. Cikin kankanin lokaci…ya nuna ƙwazo. Harvest na farko da suka yi… ya zama babba. Haroon ya ƙara musu kayan aiki, machines, support.“Good job,” ya faɗa yana kallon sa da alfahari.
Amma duk wannan nasara…ba ta kai girman soyayyar da yake yi wa Fatima ba.Idan ka gan shi a waje tare da ita yake. Idan ba school ba tare da ita yake. Idan ta yi tari kaɗan “Mom we need to go to the hospital.”
Idan ta yi shiru “Are you okay?” Wata rana ma ya ce, “I can’t lose you…” ta ɗan yi dariya. “Nothing will happen to me…” amma a zuciyarta… ta san wannan soyayya ba ƙarama ba ce

ZK2026
08081005693
07040402435.
ZUCIYA DA ƘUNA

By Billy S. Fari & Nana Hadiza
@nanadiso10 | Arewabook

PAGE 5.

Cikin wannan lokaci ne gidan Haroon Kareem ya sauya gaba ɗaya zuwa wani sabon yanayi na farin ciki da nasara,kasuwancinsa ya bunƙasa sosai, sunansa ya shiga cikin jerin manyan attajiran da ake girmamawa a birnin, kamfanoninsa suna aiki a fannoni daban-daban real estate, importation, luxury investments duk inda aka ambaci Haroon Kareem, ana magana ne da girmamawa, ana kallonsa a matsayin mutum mai hankali da hangen nesa, amma duk da wannan arziki da daukaka, akwai abu guda ɗaya da ya fi komai muhimmanci a gare shi iyalinsa. Rayyan… wanda aka haifa cikin hawaye, ya girma cikin soyayya.
Tun yana ƙarami, Fatima bata taɓa barinsa ya ji wani irin rashi ba, duk abin da yake buƙata tana nan, amma ba kaya ba ne kawai, ba abinci ba ne kawai soyayya ce, kulawa ce, da wani irin attachment da ya wuce misali, duk wanda ya ga yadda take mu’amala da shi zai rantse cewa ita ce ta haife shi, tana kiran sa “My Rayyan…” yana amsa da “Mom…” cikin wani irin laushi da ke sa zuciya ta narke.
Da safe, kafin ya tafi makaranta, Fatima ce ke shirya masa komai, uniform dinsa mai kyau, shoes dinsa masu tsabta, tana gyara masa gashi a hankali tana cewa “Stand still… you’re always moving” shi kuma yana dariya yana rungumeta “Mom you worry too much…” Haroon na tsaye a gefe yana kallon su da murmushi, yana jin wani irin cikar zuciya.
Rayyan ya zama yaro mai hankali sosai, a makaranta yana daga cikin top students, teachers suna yabonsa, abokai suna girmama shi, yana da nutsuwa amma yana da confidence, yana magana cikin ladabi amma akwai wani irin ƙarfi a cikinsa da ke fitowa lokaci zuwa lokaci, kamar yana ɗauke da wani abu daga baya da bai sani ba.
Ranar wani school event, aka kira iyaye domin ganin yadda yara ke gabatar da ayyukansu, Fatima da Haroon suka halarta, suna zaune a cikin hall mai kyau, yara suna gabatarwa ɗaya bayan ɗaya, sai aka kira suna “Rayyan Haroon” ya tashi cikin nutsuwa, ya hau stage, ya fara magana cikin English mai kyau, confidence dinsa ya fito fili, kowa ya kalleshi, Fatima ta dafe zuciyarta tana murmushi da hawaye a lokaci guda, “That’s my son…” ta faɗa a hankali, Haroon ya kalleta ya ɗan riƙe hannunta “He’s doing great…”
Bayan an gama, mutane da yawa sun zo suna gaishe su, suna yaba Rayyan, suna cewa “You raised him well” Fatima ta ji zuciyarta ta cika da alfahari, ba ta san lokacin da ta rungume shi ta sumbace shi ba “I’m so proud of you…” shi kuma ya ce “I did it for you Mom…” kalmar ta shiga zuciyarta sosai.
A gida kuwa, Rayyan ba ya rabuwa da Haroon, suna yawan fita tare sometimes business meetings, sometimes just drive around the city, Haroon yana koya masa abubuwa, yana nuna masa yadda rayuwa take, yadda ake yanke hukunci, yadda ake zama mutum mai daraja, Rayyan yana sauraro da nutsuwa, yana ɗaukar komai a hankali. Wata rana suna zaune a office dinsa mai girma, gilashi a ko’ina, ana kallon Paris daga sama, Haroon ya kalli Rayyan yana cewa “One day… all this will be yours” Rayyan ya kalle shi cikin mamaki “Really?” ya ɗaga masa kai “Yes… but you have to earn it” ya ɗan murmusa “I will” Amma a bayan wannan farin ciki, akwai wasu idanu da ke kallon su da wani irin yanayi, Zeynab ba ta taɓa mantawa da abin da ya faru ba, a duk lokacin da ta ga Rayyan tare da Fatima, zuciyarta na cika da wani irin abu, wani abu da ya haɗa hassada da ƙiyayya, tana jin kamar an ƙwace mata wani abu da ya kamata nata ne, sauran family ma ba duka ne suka amince da wannan haɗin ba, wasu suna yin gulma a ɓoye.

Amma duk wannan bai shafi Rayyan ba.
Shi rayuwarsa guda biyu ce kawai Mom da Dad A wurinsa, Fatima ita ce komai, ita ce duniya, ita ce zuciyarsa, yana son ta ba tare da shakka ba, yana kare ta kamar yadda yaro zai iya kare uwa.

A daren wani rana mai sanyi, bayan Rayyan ya kwanta, Haroon da Fatima suna zaune a balcony, suna kallon hasken Paris, iska mai laushi na kadawa, Fatima ta jingina da shi a hankali “Look at him… he’s grown so fast…” Haroon ya ɗan rungumeta “Because you gave him everything…” ta ɗan yi murmushi “No… we did” Ya ɗan jawo ta kusa da shi “I couldn’t have done this without you…” ta kalli idanunsa “And I couldn’t live without him…” ya ɗan murmusa “Or me?” ta ɗan yi dariya “You too…”Ya sumbaci goshinta a hankali.
Chapter 7 · 0% Book details