Sashe 3
Zuciya Da Kuna Part 1 Complete Hausa Novel · about 5 min read
Washegari Fatima na zaune a gefen falon tana riƙe da jaririn da ya yi bacci a jikinta, fuskar ta ɗan samu natsuwa bayan dogon kuka da wahala, hannunta na shafa kansa a hankali kamar tana jin tsoron wani ya zo ya kwace shi, Dada na zaune kusa da ita tana kallonta cikin tausayi, amma daga ɗayan ɓangaren falon Zeynab na tsaye tana kallon su da wani irin ido mai cike da rashin jituwa, zuciyarta ba ta kwanta ba tun da aka ce Fatima ce zata riƙe yaron, duk da murmushin da take yi a gaban mutane, a cikin ranta akwai wata wuta mai zafi, tana jin kamar an ƙwace mata wani abu da ya kamata nata ne, sai ta juya ta nufi inda Fatima take zaune, mutane suka ɗan yi shiru suna kallon ta, saboda sun riga sun lura da yanayinta, ta tsaya a gabanta tana kallon jaririn sannan ta ce cikin murya mai ɗan sanyi amma mai tsini, “So… yanzu ke ce uwarsa kenan?” Fatima ta ɗago idanunta a hankali, ba ta amsa ba, sai ta ƙara rungume jaririn, hakan ya ƙara ɓata ran Zeynab, ta ɗan yi dariya kaɗan tana cewa, “Interesting… very interesting… mace da ba ta taɓa haihuwa ba suddenly ta zama mother overnight,” wasu daga cikin matan suka fara kallon juna, Dada ta ɗan motsa amma bata yi magana ba tukuna, Fatima ta sauke idanunta tana ƙoƙarin kaucewa rikici, amma Zeynab ba ta tsaya ba, ta ƙara matsowa kusa da ita, “You think it’s easy? Kina ganin raino wasa ne? Do you even know what you’re doing?” muryarta ta ƙara ƙarfi kaɗan, mutane suka fara jin abin da take faɗa, wasu suka fara girgiza kai, Fatima ta ji kalmomin suna shiga zuciyarta kamar wuka, amma ta yi shiru, sai hawaye suka fara taruwa a idonta, Zeynab ta ci gaba, “Wannan yaron yana buƙatar wanda ya san responsibility, ba wanda kawai yake emotional saboda ba shi da haihuwa,” kalmar ta fito da tsauri, wannan karon Fatima ta ɗago kai, idanunta sun cika da hawaye, “Please Zeynab…” ta faɗa a hankali, amma hakan bai sa Zeynab ta tsaya ba, sai ta ɗan sunkuya kusa da ita tana faɗin cikin harshen Turanci mai tsini, “Let’s be honest… you’re just trying to fill a void… right?” wannan kalma ta karya zuciyar Fatima gaba ɗaya, hawaye suka zubo da sauri, jikinta ya fara rawa, ta ƙara rungume jaririn kamar yana kare ta daga duniya, “Stop it…” ta faɗa cikin muryar kuka, amma Zeynab ta sake cewa, “You’re not his mother… and you will never be,” wannan kalmar ita ce ta ƙarshe da ta karya komai, Fatima ta fashe da kuka sosai, kuka mai ƙarfi wanda ya sa kowa a falon ya yi shiru, wasu mata suka fara cewa “Haba…” Dada ta ɗaga hannu tare da ɗaga murya cikin ƙarfi, “Zeynab” amma kafin wani abu ya faru, ƙofar falon ta buɗe da ƙarfi, Haroon ya shigo, idanunsa sun sauka kai tsaye a kan Fatima da ke kuka da kuma Zeynab da ke tsaye a gabanta, ya tsaya na ɗan lokaci yana kallon scene ɗin, zuciyarsa ta ɗan buga, sannan cikin murya mai ƙarfi ya ce, “What is going on here?” shiru ya sauka, babu wanda ya amsa, Fatima ta ci gaba da kuka, hakan ya ishe shi fahimta, ya juya ya kalli Zeynab, idanunsa sun canza, “Zeynab… what did you say to her?” ta ɗan ɗaga kai tana ƙoƙarin nuna ƙarfi, “I was just telling the truth” kafin ta gama magana, ya matsa kusa da ita cikin sauri, hannunsa ya ɗaga slap! sautin ya cika falon, mutane suka yi shiru gaba ɗaya, Zeynab ta dafe kunci cikin mamaki, ba ta taɓa tsammanin hakan ba, idonta ya cika da hawaye, amma ba saboda ciwo ba… saboda kunya, Haroon ya nuna mata hannu cikin fushi, “Don’t you ever… ever talk to my wife like that again!” muryarsa ta girgiza falon, “Do you hear me?” ta kasa magana, ta ɗaga kai kawai, hawaye na sauka, “You crossed the line, Zeynab… you went too far,” ya juya ya kalli mutane, “From today… you stay away from my wife and my son… do you understand?” kalmar my son ta fito da ƙarfi, ya jaddada ta da nufi, Dada ta ɗan lumshe idanu tana jin daɗin yadda ya tsaya tsayin daka, wasu daga cikin mutanen suka girgiza kai suna goyon baya, Zeynab ta juya da sauri ta fita daga falon cikin kuka, tana jin kamar duniya ta rushe mata, Haroon ya juya ya nufi Fatima, ya zauna kusa da ita, ya riƙe hannunta, “Hey… look at me…” amma ta kasa ɗaga kai, kuka ya rufe ta gaba ɗaya, ya ɗan matsa kusa da ita ya rungume ta, “I’m here… nobody will hurt you… not anymore,” ya ɗan ɗago fuskarta da hannunsa, hawaye sun ɓata mata fuska, “You are his mother… and nobody… nobody will take that from you,” ta kalle shi cikin rauni, “Really?” ya ɗaga mata kai, “Yes… I promise you,” ta ƙara rungume shi, kuka yana raguwa a hankali, jaririn a hannunta ya motsa kaɗan kamar yana jin yanayin, Dada ta matsa kusa da su tana cewa cikin nutsuwa, “Komai ya wuce… ki kwantar da hankalinki,” falon ya fara dawowa da hayaniya a hankali, amma wannan karon kowa ya san wani abu ya canza, wani layi ya ja… wanda ba za a sake ketarawa ba, kuma a cikin wannan dare, Fatima ta fahimci abu ɗaya ba kowa ne ke son farin cikinta ba… kuma ba kowa ne zai iya tausayinka acikin yanayin da kake ciki ba don haka dole tasan cewa ba kowa bane abun yarda...
_Sau da dama namiji kan taka rawar gani wajen shamakance iyalansa ga wata aibantawa daga wajen yan uwansa don gina mutuntakarsu a zuciyarsu, shin kuna ganin abinda HAROON yai yayi daidai kuwa?_
BZ2026
08081005693
07040402435.
ZUCIYA DA ƘUNA
By Billy S. Fari & Nana Hadiza
@nanadiso10 | Arewabook
PAGE 3.
_Sau da dama namiji kan taka rawar gani wajen shamakance iyalansa ga wata aibantawa daga wajen yan uwansa don gina mutuntakarsu a zuciyarsu, shin kuna ganin abinda HAROON yai yayi daidai kuwa?_
BZ2026
08081005693
07040402435.
ZUCIYA DA ƘUNA
By Billy S. Fari & Nana Hadiza
@nanadiso10 | Arewabook
PAGE 3.