BABI NA GOMA SHA BIYU.
Uwa Uwa Ce Part 2 Complete Hausa Novel · about 19 min read
Wata sallamar tayi ta kutsa kai cikin dakin da sanyinsa ya busa har kasusuwanta. A take taji kwarin gwiwarta ya dadu. Sai da ta shiga daga inda yake zaune ya danna remote kwayayen fitilu uku suka kama. Haske ya gauraye dakin da zaka rantse ba namiji ke gyara kayansa ba. Komai tsaf ga kamshi ga kyau.
"Ke da waye?" Ya tambayeta yayinda ta kai ido inda Qibdiyya take bacci.
"Asabe. Tana kasa."
Shiru suka yi na dan lokaci suna yiwa juna kallon kallo. Ita tana ganin wautarta na rashin kusantar kanin nata tun da dewa. Shi kuwa abubuwa da dama ne suka cunkushe kirjinsa. Zazzabi yake ji da matsanancin ciwon kai.
"Na san abin da ya kawoki Uwani zan kuma baki domin ki taimaki Qibdiyya. Sai dai abu daya ne ba zan miki ba..."
Idanunsu suka sarke da juna. Magana yake yi mata ba da wasa ba. Bata jin ma banda gaisuwa sun taba yin wata doguwar magana dashi banda yanzu. Idanun nasa sai suka zame mata tamkar masu wadanda ke huda sassan jikinta. Gabadaya sai ta tsargu ta kasa sakewa. Don ma tana da baki ne ta ce,
"Ban gane ka san me ya kawoni ba? Daga zuwa taimako sai ka soma fada min magana saboda raini."
Dan murmushi ya yi cikin son nuna burgarta bata je masa ko ina ba. Ya dora maganarsa ba tare da ya damu da bata amsar ma
ganarta ba.
"Kamar yadda na ce zan biya ki dubata amma ko kwandala ba zan baki ba domin ki bar maganar nan a matsayin sirri."
"Me yasa?" Ta fara cewa tana zaro ido sai kuma tayi saurin gyara zancen "yaushe na ce maka idan baka biya ba zan tona maka asiri?"
Mikewa ya yi kansa na cigaba da sarawa ya matso da Qibdiyya bakin gadon yana cewa,
"Baki fi kowa so da damuwa dani ba Uwani amma sai gaki ke kadai a gidana a wannan lokacin. Ina Innayo ina su Zara? Me yasa baki fada musu kun fito tare ba?"
Hade rai tayi na borin kunya ta saka safar hannu.
"Saboda irin wannan abin ba abu bane da ake so ayi ta yamadidi dashi ba."
Wani dan murmushi ya yi mai sauti
"Qibdiyya dai 'yarki ce, tonon asirinta naki ne. Kuma magana dole zata fito idan aka tsinci tsinannen da ya yi mata wannan abin da rai ko babu."
Fita ya yi yaja kofar dakin ya barta da tunanin kalamansa. Taji zafin maganganun duk da gaskiya ce ziryan bai mata sharri ba.
Qibdiyyan ta tasa a hankali don kada yarinyar ta firgita idan taji ana tabata cikin bacci.
Cikin yan uwan mahaifinta Uwani tana sahun gaba na wadanda bata saba dasu ba kuma suke bata tsoro. A firgice take kallonta amma Uwani bata fahimta ba saboda sabgar yara ba tata bace.
A hankali dai take yi mata magana domin ta kwantar da hankalinta.
"Yi kwanciyarki dubaki zanyi."
Tana kai hannu zata cire mata pant, Qibdiyya ta runtse ido yadda ta yiwa Asabe.
"Kema hannu zaki saka min a nan? Idan an saka wannan safar ba zai min zafi ba?"
Hannuwan Uwani sai suka fara rawa ta kasa cire pant din. Wannan wadanne irin maganganu ne suke fita daga bakin karamar yarinya irin wannan?
Tana can tana tunani caraf idanun Qibdiyya akan alluran dake cikin first aid box din. Jikinta ya kama rawa ta soma kuka.
Munzali yana jin kukan ya bude kofar. Sai dai yaci karo da abinda yasa shi jin ina ma bai zo duniya ba. Qibdiyya ce take cewa,
"Don Allah kada kiyi min allura wallahi ba zan fadawa Daddy ba. Abin nan ne bana so ki tura min da karfi yana min ciwo kinji" kallon da taga tana yi mata ta kasa cewa uffan ne ya bata damar tashi zaune don ko kadan bata so ayi mata "Kwanta ni inyi miki. Nima na iya."
Tsigar jikinsa har tashi take yaji kansa kamar k'wari suna yawo. Da dan allinsa ya nunata yana daga murya ba tare da ya sani ba.
"Me kika iya? Me zaki yi? Qibidiyya waye ya koya miki wannan abin?"
Baiwar Allah a gigice ta tashi idanunta suna zubar da hawaye. Idan da abin da yafi komai daga mata hankali bai wuce shi ko Abbati su sani ba. Uncle Daddy alkawarin kisa ya yi musu. Zai yanka mata su irin yadda aka yi a bidiyon da ya nuna mata.
A zafafe Munzali ya sake cewa "nace waye ya koya miki? Da wa kuke yi? Innalillahi wa inna ilaihi raji'un." Ya rike kansa "Uwani kin ji abin da tace kuwa?"
Qibdiyya dai ba abin da take sai kuka. Haka ma Munzali wanda ya dubkule hannu yana dukan bango. Yatsunsa har kara suke amma bai daina ba. Uwani kanta ta kidime. Sai a lokacin taji wani girma ya sauko mata. Idan bata tari abin da yake faruwa ba da uban da 'yarsa duka zasu shiga wani hali. Hannunta ta kama ta zaunar da ita a kan cinyarta.
"Daina kuka Qibdiyya ki fada min waye yake saka miki hannu a cikin pant."
Cikin faduwar gaba Qibdiyya ta kalli Daddy dinta ta girgiza kai.
Wata irin tsawa ya yi mata wadda har Uwanin sai da taji cikinta ya kada. Kaiwa da kawowa kawai yake a dakin jikinsa na tsuma. So yake ya samu wani abu ya matse ko ya yi ta duka har sai kuzarinsa ya kare.
A lokacin azal ta fada kan wanda bai ji ba bai gani ba. Hakika Allah ba azzalumin Sarki bane. Sai dai kuma Yana nuna ishara ko aya akan wasu domin ya zama gargadi ga majibintansu.
"Uncle Lilu"
Amon muryarta ya fito lokaci guda da kiran sallan da Ladanin masallacin kusa dasu ya soma na Magariba.
Yawun bakinsa kafewa ya yi ya kasa hada harufan da zai kira sunan Lilu. Ga wani abu mai daci yana bin busasshen wuyansa yana saukar masa a ciki. Zuciyarsa kuwa tamkar farantin tangaran haka yaji tayi rugu rugu.
A karamar kwakwalwar Mariyatul Qibdiyya kuwa, tayi tunanin kama sunan Lilu tsira ne gareta da iyayenta. Shi yana da kirki ba zai yanka su ba. Uncle Daddy da yace yana ganinta duk inda take yanzu ba zai mata komai ba.
(Ba da niyya Munzali ya taka muhimmiyar rawa wurin janyowa Lilu laifin da ba nasa ba. Yarinya ce wadda aka tsorata tun lokacin da ake batawa rayuwa. Yanzu kuma an sake firgita ta da fada da tsawa. Wannan kadai ya isheta dalilin yin shiru ko ta kira sunan wani daban. Da wane mataki aka fi saurin samun bayyanar gaskiya a irin wannan yanayin da ba a fata? Rarrashi da laluma musamman ga kananun yara. Idan sun kama suna iyaye a bincika a sake bincikawa. Yara ma suna karya! Wani domin kwatar kai, wani kuma domin maslahar da yake ganin canja gaskiyar zai kawo.)
Washegari bakwai a hanya ta yiwa iyalan Alh. Tahir. Ana sallame sallar Asuba suka shirya. Lilu da Mardiyya ma ko wanka basu yi ba saboda iyayen sun matsu su tafi. Awa biyu ta kaisu gida. Shi Alh. Tahir kai tsaye office ya wuce. Yana shiga ya shiga dube dube yana daga abubuwa. Wannan wayar da yake kiran 'yan matansa yake nema ido rufe. Fatansa kada ta fada hannun da asirinsa zai tono. Da ya gaji da neman sai ya kira direbansa da masinja.
Shi direban umarnin kai mota wanki ya bashi. Ya ce a cire duka kujerun a duba masa wayar. Masinja kuma ya kira masu shara a fitar da komai na cikin office din a duba masa. Amma fa koda ya bayar da wannan aikin yana da tabbaci dari bisa dari bai barta a office ba. Motar yafi zargi. Kawai dai ya yi amfani da karin maganar bahaushe da ake cewa idan kana neman rakuminka ka duba har cikin allura.
Dakin da suke meeting ya shiga ya zauna yana jin zuciyarsa tana wani irin bugu. Ya rasa me yake damunsa tun wayewar garin yau. Ransa a jagule yake ga fargabar da bai san dalilinta ba. Ya san dai yana matukar tsoron wayar nan ta fada hannun wani a cikin gidansa. Mutumcinsa ne zai zube wanwar. Matansa sun san komai amma ba zai so su gani kamar yadda suka ga sakon Yumna ba. Amma 'ya'yansa fa? Wanda Farha ta gani ya ishe shi jin kunya har ya mutu. Tunanin Yumna da ya yi sai ya sake kad'a shi wata duniyar. Rabonsa da ita tun ranar da wayarsa ta bata. Kamar sauran 'yan matansa ita ba bata da numbar kowane layi sai na wannan wayar. Yadda take babu hankalin nan yana tsoron kar ta zo gidan ta ce tana nemansa.
Wuni ya yi yana ta tufka da warwara har aka gama ayyukan da ya saka ba a ga wayar ba. Bai iya tabuka komai ba ya tafi gida.
Kurar da bata taka kara ta karya ba a dakinsa ya fara karkadewa kafin ya shiga wanka. Idan bai yi da kansa ba ya san Mami ba za ta bar Sauda ko Mardiyya suyi masa ba. Musamman da yake daga tafiya suka dawo za ta ce suma sun gaji.
Yana gama shiryawa ya dare gado zai yi ramuwar bacci sai ya bige da chatting. Hirar kwallon kafa ce suka kusa yin awa guda suna fafata musu shi da abokansa a group dinsu. Daga kwance sai da ya koma ya zauna. Can aka turo hoton jerin wasannin da suke magana a kai da sakamakon. Lilu bai san lokacin da ya yi ihun murna ba. Club dinsu ne suka yi nasara kamar yadda suka fada. Sun cinye musun. Yana cikin murnarsa Suhaib ya shigo sanye da wandon bacci da singileti. Da gani shi ma wanka ya sake yi zai kwanta.
"Ka fa hanani bacci da ihu."
Lilu ya daga hannuwa irin na masu saranda yana murmushi.
"Takawarka lafiya dan rigimar Mami yanzu nima zan kwanta."
Suhaib bashi da zabin da ya wuce yin murmushi.
"Kai kuma Dan-ta-kife din Mami ko?"
"Kada ka dora min sunan da ba halina ba."
Suhaib ya gyara tsayuwa gami da yin kwafa "ni rigimar halina ce kenan?"
"Banda rigima tun dazu me ya hanaka bacci sai yanzu daga yin ihuna za ka fito?"
Tsuke baki Suhaib ya yi ya juya yana murmushi. Me kuwa ya hana shi bacci sama da tunanin yarinyar da ya gani tare da makaniken nan? Haushinta ya kamata yaji a ganinsa. Sai aka yi rashin sa a ta cike tunaninsa da wasu abubuwa da bai saba kai kansa garesu ba. Wai yau shi ne yake tunanin wace makarantar gaba da sakandire ce za ta fi kusa da gidansa (Alh. Tahir ya mallaka musu filaye shi da Lilu wadanda ake kan aikin ginawa) idan matarsa iyakarta sakandire kafin auren.
Dariya ya kama yiwa kansa na yadda aka yi daga haduwar rana daya ya san cewa iyakarta sakandire. Koda ya koma daki maimakon ya kwanta kamar yadda ya yi niyya sai ya zura jallabiya ya nufi bangaren Jiddo.
A dakin Lilu bayan fitar Suhaib da karewar musun nasu sai ya soma hamma. Gajiyar biki da ta tafiya tayi masa rubdugu lokaci guda. Mikewa ya yi ya nufi gaban socket din da yake saka chaji. A nan yaga chajarsa da bakuwar waya. Tsorata ya yi don bai ga ta inda za a ce wayar ta shigo dakinsa ta jona kanta ba. Yan uwansa kuma duka ya san babu mai irinta. Kamar ya tafi kiran Suhaib sai ya fasa. Yanzu kowa zai kara raina shi ace bai iya komai ba duk bakinsa. Ya daure zuciyarsa ya daga hannuwansa ya karanta musu Ayatul Kursiyyu ya tottofe.
"Kun dai san nan dakina ne amma duk da haka ban ji haushi don kun jona chaji da chajata ba" ya rage murya da salon rokon arziki "ina neman izini in cire in saka tawa ko rabin awa ne?"
'dillll'
Yana rufe bakinsa text ya shigo wayar. Hanjinsa gabadaya ya kanannade saboda tsoro ya koma kan gadonsa ya haye har kafafunsa.
"Daga magana sai ku turo min text? Indai chaji ne na hakura har abada." Ya zuro kafarsa yana kallon kofa gabansa na faduwa "don Allah zan fita inje dakin yayana. In je?"
'dillll'
Wani text din ya kuma shigowa. Dole ya fasa fita yana fadawa kansa cewa gargadi ne ake yi masa. Ya koma yana mika hannu yana janyewa duk a tsorace
"Bari in duba don kada ace nayi rashin kunya. Ni din banza in ja daku? Ku da ake cewa sai kun shekara dari kuke fara samartaka...."
'dillll'
"Naji. Naji!
Ya dauki wayar sai dai a kulle take. Abinka da fitinannen matashin zamani. Ya manta da tsoron da yake ji ya koma kokarin gano pattern din budeta. Bai sha wata wahala ba ya samu bayan yan dabaru. Abin da ya daure masa kai bai wuce ganin pattern din sak irin na Abbansu ba. Kai tsaye wurin messages ya shiga. Ya tarar da sakonni sun tasarma dari. Kuma wani abin al'ajabi na layin basu fi a kirga ba. Sauran kuwa harrufa ne wasu D, V, J, gasu nan dai. Na sama saman da suka yi alamar sune aka yi yanzu ya bude. Harafin dake jiki Y ne.
(Naji labarin tafiya kayi da tsofaffin matanka. Shi ne ka kasa daukar wayata saboda kana jin tsoronsu? Anyways an tabbatar min yau ka dawo. Na baka zuwa azahar idan baka kirani ba zan zo har gidan ai ba bakona bane. Aure ne dai ko ana so ko ba a so sai na amsa sunan matar Alh. Tahir)
"Abba?" Ya ambata a raunane, hawaye na zubo masa. Duk wani kuzarinsa ya kau sai zafin kirji.
Tarin tambayoyi ne a kansa na son sanin yadda aka kwana a ragaya. Neman amsa ya shiga yi ta hanyar bin text din yana maimaitawa. Bai samo amsar komai ba sama da haddace mummunan sakon. A kasan ransa kuma sai tunanin me zai fi dacewa ya yiwa wannan mai tsautsayin da ta iya shafawa idonta toka ta turo wannan sakon. Cikin sauri ya koma baya ya soma bin sauran harrufan da aka adana sunan mutane dasu ya bude nasu sakonnin. Sannan ne kuma jikinsa ya yi mugun sanyi. Hira ce tsakanin Abbansu da 'HARUFFA' daban daban ta rashin da'a. A haka ma ya kula amsoshin Abban basu da tsayi sosai. Wannan kuma dama ya yi ne domin tsira daga forwarding chat ko screenshot da ake yi a whatsapp. Dena binsu ya yi ya koma saman wanda suka yi musaya da Y. Nata da yawa korafi ne akan rashin zuwansa da maganganun aure. Har tana cewa mahaifinta ya ce idan bai zo ba a satin zasu fasa bashi ita.
Ko kadan Lilu bai damu ba idan Abban aure zai yi. Salon hirar ce tafi daga masa hankali domin alamu sun nuna cewa ba a hira aka tsaya ba. Yaci karo da inda aka yi zancen hotel da guest house. Da kuma godiyar 'yan matan akan tarin kudaden da ya basu. Whatsapp yaso dubawa sai dai babu shi akan wayar.
Yana nan kansa ya rarrabu wurin fassara abubuwan da ya gani yaji shigowar wani sakon. Y din ce dai. Kamar dama jiranta yake yana shigowa ya bude.
(Kaga fa ina tunanin ciki ne ma dani. Zan yi test a gida idan positive ne zan turawa Farha hoton ta whatsapp. Sai a yiwa tsofaffin gwangwanye albishir sun kusa samun karuwa.)
Kuka Lilu yake tamkar yaron goye. Karshen sakon ma da kyar ya iya karantawa saboda cikar hawaye. Nambar ya kwashe ya zuba a wayarsa. Tunda ya kai nambobi shidan farko sunaye masu shigen nambar suka dinga raguwa. Yana saka ta bakwai sai ya rage suna daya.
YA YUMNA kamar yadda suke kiranta shi dasu Sauda a matsayinta na aminyar yayarsu.
Kin tsayawa ya yi sai da ya rubuce ta duka ya tabbatar da sunan da ya gani. Yana jin lokacin da zazzabi ya rufe shi hade da wani irin sanyin jiki. Bashi da hujjar karyatawa saboda harafin da ya gani a wayar Alh. Tahir ya kara bashi tabbaci.
"La haula wala quwwata illa billa. Abba? Ya Yumna?"
A gigice ya mike da ya tuna ma'anar sakon karshe. Indai Yumna ciki ne da ita kenan komai ma ya faru tsakaninsu. Zuciyarsa a take ta tashi saboda kyamar hakan da yaji. Ya fada bandaki ya amayar da duk abin da ke cikinsa. Baki kawai ya kuskure bayan ya gama ya fita daga dakin.
Duk gidan Alh. Tahir babu wanda Jiddo ta tsana a tsukin kwanakin nan kamar Suhaib. Da can da baya shiga shirginta mantawa ma take dashi. Iyakarsu da juna idan zasu wuce kuma suna kusa taji sautin tsakinsa. Tsakin da tun aurenta da ubansa take ji kuma bai taba damunta ba. Ba kuma wani abu ne ya janyo yake yi mata shi ba sai kamasu da aka yi a daki wanda shi ma yaje wurin.
Abubuwan da suka biyo baya da auren nasu sun taimaka kwarai wurin dasa masa tsanarta. Sai gashi bayan shekaru sun shude ta sake bude kofar sabunta zarginta a zuciyarsa. Alal hakika bai yi wani mamaki ba lokacin da yaga tana shirin barin wurin dinner da makaniken nan. Sanannen abu ne cewa indai bawa ya kulla aminci da zina to ba makawa sai ta kawo masa ziyara watarana. Mahaifinsu yace yaji ya gani wurin sabon Allah. Dolensa kuwa ya girbi shukar da yayi ko ba dade ko ba jima. Shi dai adduarsa kullum bata wuce Allah Ya tsare masa mahaifiyarsa da kannensa.
Sallama hade da kwankwasa kofa ya yi da ya isa bangarenta. Mai'aikinta ce ta amsa ta bude masa. A hakimce kan two-seater yaganta tana waya. Ganinsa a tsakar falonta ya mugun firgitata. Lafiya ko rashinta basu taba kawo shi inda take ba. Yau da yazo ta san lallai akwai matsala. Wayar faduwa tayi daga hannunta ta kuma gyara zama ba shiri.
"Nambar makaniken nan zaki bani." Cewar Suhaib, fuska babu annuri.
Jiddo sai ta daburce duk saboda gudun tonon asiri. A haka ta cije ta harare shi.
"Rashin kunyarka ta isheni Suhaib. Idan ban ci darajar shekaruna ba ai ya kamata in ci na matsayina a gidan nan."
Surutunta bashi da gurbi a kwakwalwarsa balle yaci darajar neman ta maimaita domin ya fahimta.
"Zan samu ko in tafi?"
Rainin wayonsa ya sake bata haushi. Wato ma bai ji abin da tace ba bare ta san ran zai yi aiki dashi. Yatsina fuska tayi ita a dole bata san me yake nufi ba ta ce,
"Wane makaniken?"
Wannan karon Suhaib ne ya hango rainin wayonta. Sai da ya dage girarsa daya sama ya murmusa. Harsashi zai hada mata a wurin Alh. Tahir don ranar tada bom din bata zo ba. Wannan ba aikinsa bane. Lokaci da talalar Ubangiji ga bawan da ya dage akan aikin sabo zai cimmata wataran.
Wata irin murya ya yi amfani da ita sai a rantse sangartaccen da ne a gaban mahaifiyarsa yana zuba shagwaba.
"Don Allah ki bani Anti Jiddo."
Ita kanta da taji muryar sai da ta kara tsorata fiye da farkon zuwansa. Ta san dole akwai abin da yake nufi da haka. Ba dai ta zata maigidan ne da kansa ya shigo falon ba tare da ta kula ba sai yanzu.
Ran Alh. Tahir fari kal kamar takarda yau ga Suhaib a bangaren Jiddo. Yadda yake magana ya nuna masa sun jima da daidaitawa. Ya dinga zuba murmushi kamar sakarai har yana mantawa da halin da yake ciki.
"Wato kin saka danki a daki yana ta shagwaba aka rasa wanda zai amsa min sallama ko? Wai ma mene ne yake faruwa zan yi alkalanci."
Suhaib ya yi saurin bashi amsa kafin ta sami damar juya zancen.
"Nambar makanikenta na Kano nake so Abba shi ne taki bani wai sai na yarda gobe zan rakata shopping"
Wohohooo. Alh. Tahir da shi ma ba wani samun hira daga Suhaib din yake ba duk irin son da yake masa sai yaji kansa ya yi gingirin. Murmushi yaki yankewa a fuskarsa.
"To ai sai ka amince dan Jiddo"
'I reject it! Tuff, tuff' cewar Suhaib a zuci yana jin tsigar jikinsa na tashi saboda an kira shi dan Jiddo.
"Na amince. Don Allah ki bani"
Tsabar mamaki sai ta kasa cewa komai banda kai da take gyadawa kamar kadangaruwa taga manja. Sunan Danliti ta lalubo tunda Alh. Tahir ya musu karan tsaye yaki tafiya. Dama al'adarsa ce shiga bangaren kowa idan zai fita ko ya dawo.
Bayan Suhaib ya kwafe nambar ne Alh. Tahir yake tambayarsa me zai hada shi da makanike a Kano.
"Wani case ne babba ya taso tsakaninmu dashi."
Alh. Tahir ya dan bata fuska
"Ban gane ba? Wani abu ya yi maka?"
Suhaib ya yi hanyar kofa yana cewa "a'a, motar Anti Jiddo yaso lalatawa ba don Allah Ya kaini wurin da suke ba da wuri."
Sautin cikin Jiddo har kunnuwansu saboda tsoro. Suhaib kuwa ya fice yana jin Alh. Tahir na tambayarta me ya sami motar har aka nemo makanike shi bai sani ba. Rantse rantsenta kadai ya jiyo ya kara gaba don bashi da lokacin jin karairayin da zata yi.
Lilu kuma da ya fito bai zame ko ina ba sai bangarenta Mami Khadija. Ya yi zaton samunta ta kwanta ko shirin kwanciyar kamar kowa sai yaga sabanin haka. Laptop ce a gabanta ga tulin takardu ta soma barbazawa tana aiki. Gaban table din da aka yi mata musamman saboda aikinta yaje ya mika mata wayar.
"Ga wayar mijinki idan ya dawo ki bashi."
Tun shigowarsa take kallonsa amma furucinsa yasa ta koma yi masa firgitaccen kallo.
"Mijina? Mijina fa ka ce Lilu. Ko dai nice ban ji ba da kyau?" Ta furta a sanyaye.
Lilu ya cije lebe cikin bacin ran tuna abubuwan da ya gani.
"Mijinki maigidan nan nake nufi."
Laptop din ta tura gefe ta tashi tsaye tana dubansa.
"Ko agolanci nazo da kai gidan nan bana tunanin za ka iya budar baki ka kira wanda nake aure Mijina."
Duk shashancin Lilu bai taba zina ba. Mami Khadija ta dasa musu tsananin kyamar wannan laifin tun basu san kawunansu ba. Yafi kowa fitina a gidan amma akwai iyakokin da ko a mafarki bai hango kansa da ketaresu ba.
Kalaman Mamin murmushi suka saka shi.
"Mamina kinfi karfin haka a wajena. Wallahi indai mai mutumci wanda ya san darajar kansa data iyalinsa kika aura ni mai tayaki yi masa biyayya ne."
Da ya gama maganar ya dora wayar a kusa da tata ya fice da sauri. Zama a gabanta karyar masa da zuciya zai sake yi ya kaishi ga kuka. Tausayinta yake ji sai dai kuma jikinsa ya bashi ta jima da sani. A hanyar zuwa dakin ya dinga tuno irin nasihunta da fada da suna yara har kawo ga yanzu. Kusan komai yafi ta'allaka akan zina.
'Ba halinsa bane!' shi ne abin da Mami Khadija ta fara fadawa kanta a lokacin da taji kamar ta kwashe shi da mari. Kwalla ce ta taho mata saboda jikinta yana bata da wuya idan ba sirrin boye ne ya fito fili a wurinsa ba. Yadda Farha ta sani bayan Suhaib gashi yau shi ma ya sani. A ranta ta dinga tsarkake Mulkin Ubangijin da ya haramta zina. Hakika wannan kaba'ira tana zubar da mutumcin mai mutumci. Yau Lilu da bakinsa yake kiran mahaifinsa da wani suna ba Abba ba.
Kallon wayar tayi sau daya ta kawar da kanta. Alh. Tahir na shigowa bangarenta daga wurin Jiddo ta damka masa wayar daga bakin kofar da ta tare don kada ya shigo ciki.
"Lilu ne ya kawo"
Gumi a take ya tsatstsafo akan goshinsa.
"Ya ce wani abu ne?"
Mami Khadija ta kalle shi ido cikin ido ta ce "ya ce ga wayar mijina na bashi idan ya dawo"
Alh. Tahir ya karkata gefen fuskarshi gareta yana son tabbatar da abin da ta ce.
"Mijinki? Dani yake?"
Cikin ko in kula ta ce "a iya sani na ba."
Daga haka ta rufe kofarta ta barshi a wurin yana jinjina girman abin da yake samunsa a tsukin nan.
"Ke da waye?" Ya tambayeta yayinda ta kai ido inda Qibdiyya take bacci.
"Asabe. Tana kasa."
Shiru suka yi na dan lokaci suna yiwa juna kallon kallo. Ita tana ganin wautarta na rashin kusantar kanin nata tun da dewa. Shi kuwa abubuwa da dama ne suka cunkushe kirjinsa. Zazzabi yake ji da matsanancin ciwon kai.
"Na san abin da ya kawoki Uwani zan kuma baki domin ki taimaki Qibdiyya. Sai dai abu daya ne ba zan miki ba..."
Idanunsu suka sarke da juna. Magana yake yi mata ba da wasa ba. Bata jin ma banda gaisuwa sun taba yin wata doguwar magana dashi banda yanzu. Idanun nasa sai suka zame mata tamkar masu wadanda ke huda sassan jikinta. Gabadaya sai ta tsargu ta kasa sakewa. Don ma tana da baki ne ta ce,
"Ban gane ka san me ya kawoni ba? Daga zuwa taimako sai ka soma fada min magana saboda raini."
Dan murmushi ya yi cikin son nuna burgarta bata je masa ko ina ba. Ya dora maganarsa ba tare da ya damu da bata amsar ma
ganarta ba.
"Kamar yadda na ce zan biya ki dubata amma ko kwandala ba zan baki ba domin ki bar maganar nan a matsayin sirri."
"Me yasa?" Ta fara cewa tana zaro ido sai kuma tayi saurin gyara zancen "yaushe na ce maka idan baka biya ba zan tona maka asiri?"
Mikewa ya yi kansa na cigaba da sarawa ya matso da Qibdiyya bakin gadon yana cewa,
"Baki fi kowa so da damuwa dani ba Uwani amma sai gaki ke kadai a gidana a wannan lokacin. Ina Innayo ina su Zara? Me yasa baki fada musu kun fito tare ba?"
Hade rai tayi na borin kunya ta saka safar hannu.
"Saboda irin wannan abin ba abu bane da ake so ayi ta yamadidi dashi ba."
Wani dan murmushi ya yi mai sauti
"Qibdiyya dai 'yarki ce, tonon asirinta naki ne. Kuma magana dole zata fito idan aka tsinci tsinannen da ya yi mata wannan abin da rai ko babu."
Fita ya yi yaja kofar dakin ya barta da tunanin kalamansa. Taji zafin maganganun duk da gaskiya ce ziryan bai mata sharri ba.
Qibdiyyan ta tasa a hankali don kada yarinyar ta firgita idan taji ana tabata cikin bacci.
Cikin yan uwan mahaifinta Uwani tana sahun gaba na wadanda bata saba dasu ba kuma suke bata tsoro. A firgice take kallonta amma Uwani bata fahimta ba saboda sabgar yara ba tata bace.
A hankali dai take yi mata magana domin ta kwantar da hankalinta.
"Yi kwanciyarki dubaki zanyi."
Tana kai hannu zata cire mata pant, Qibdiyya ta runtse ido yadda ta yiwa Asabe.
"Kema hannu zaki saka min a nan? Idan an saka wannan safar ba zai min zafi ba?"
Hannuwan Uwani sai suka fara rawa ta kasa cire pant din. Wannan wadanne irin maganganu ne suke fita daga bakin karamar yarinya irin wannan?
Tana can tana tunani caraf idanun Qibdiyya akan alluran dake cikin first aid box din. Jikinta ya kama rawa ta soma kuka.
Munzali yana jin kukan ya bude kofar. Sai dai yaci karo da abinda yasa shi jin ina ma bai zo duniya ba. Qibdiyya ce take cewa,
"Don Allah kada kiyi min allura wallahi ba zan fadawa Daddy ba. Abin nan ne bana so ki tura min da karfi yana min ciwo kinji" kallon da taga tana yi mata ta kasa cewa uffan ne ya bata damar tashi zaune don ko kadan bata so ayi mata "Kwanta ni inyi miki. Nima na iya."
Tsigar jikinsa har tashi take yaji kansa kamar k'wari suna yawo. Da dan allinsa ya nunata yana daga murya ba tare da ya sani ba.
"Me kika iya? Me zaki yi? Qibidiyya waye ya koya miki wannan abin?"
Baiwar Allah a gigice ta tashi idanunta suna zubar da hawaye. Idan da abin da yafi komai daga mata hankali bai wuce shi ko Abbati su sani ba. Uncle Daddy alkawarin kisa ya yi musu. Zai yanka mata su irin yadda aka yi a bidiyon da ya nuna mata.
A zafafe Munzali ya sake cewa "nace waye ya koya miki? Da wa kuke yi? Innalillahi wa inna ilaihi raji'un." Ya rike kansa "Uwani kin ji abin da tace kuwa?"
Qibdiyya dai ba abin da take sai kuka. Haka ma Munzali wanda ya dubkule hannu yana dukan bango. Yatsunsa har kara suke amma bai daina ba. Uwani kanta ta kidime. Sai a lokacin taji wani girma ya sauko mata. Idan bata tari abin da yake faruwa ba da uban da 'yarsa duka zasu shiga wani hali. Hannunta ta kama ta zaunar da ita a kan cinyarta.
"Daina kuka Qibdiyya ki fada min waye yake saka miki hannu a cikin pant."
Cikin faduwar gaba Qibdiyya ta kalli Daddy dinta ta girgiza kai.
Wata irin tsawa ya yi mata wadda har Uwanin sai da taji cikinta ya kada. Kaiwa da kawowa kawai yake a dakin jikinsa na tsuma. So yake ya samu wani abu ya matse ko ya yi ta duka har sai kuzarinsa ya kare.
A lokacin azal ta fada kan wanda bai ji ba bai gani ba. Hakika Allah ba azzalumin Sarki bane. Sai dai kuma Yana nuna ishara ko aya akan wasu domin ya zama gargadi ga majibintansu.
"Uncle Lilu"
Amon muryarta ya fito lokaci guda da kiran sallan da Ladanin masallacin kusa dasu ya soma na Magariba.
Yawun bakinsa kafewa ya yi ya kasa hada harufan da zai kira sunan Lilu. Ga wani abu mai daci yana bin busasshen wuyansa yana saukar masa a ciki. Zuciyarsa kuwa tamkar farantin tangaran haka yaji tayi rugu rugu.
A karamar kwakwalwar Mariyatul Qibdiyya kuwa, tayi tunanin kama sunan Lilu tsira ne gareta da iyayenta. Shi yana da kirki ba zai yanka su ba. Uncle Daddy da yace yana ganinta duk inda take yanzu ba zai mata komai ba.
(Ba da niyya Munzali ya taka muhimmiyar rawa wurin janyowa Lilu laifin da ba nasa ba. Yarinya ce wadda aka tsorata tun lokacin da ake batawa rayuwa. Yanzu kuma an sake firgita ta da fada da tsawa. Wannan kadai ya isheta dalilin yin shiru ko ta kira sunan wani daban. Da wane mataki aka fi saurin samun bayyanar gaskiya a irin wannan yanayin da ba a fata? Rarrashi da laluma musamman ga kananun yara. Idan sun kama suna iyaye a bincika a sake bincikawa. Yara ma suna karya! Wani domin kwatar kai, wani kuma domin maslahar da yake ganin canja gaskiyar zai kawo.)
Washegari bakwai a hanya ta yiwa iyalan Alh. Tahir. Ana sallame sallar Asuba suka shirya. Lilu da Mardiyya ma ko wanka basu yi ba saboda iyayen sun matsu su tafi. Awa biyu ta kaisu gida. Shi Alh. Tahir kai tsaye office ya wuce. Yana shiga ya shiga dube dube yana daga abubuwa. Wannan wayar da yake kiran 'yan matansa yake nema ido rufe. Fatansa kada ta fada hannun da asirinsa zai tono. Da ya gaji da neman sai ya kira direbansa da masinja.
Shi direban umarnin kai mota wanki ya bashi. Ya ce a cire duka kujerun a duba masa wayar. Masinja kuma ya kira masu shara a fitar da komai na cikin office din a duba masa. Amma fa koda ya bayar da wannan aikin yana da tabbaci dari bisa dari bai barta a office ba. Motar yafi zargi. Kawai dai ya yi amfani da karin maganar bahaushe da ake cewa idan kana neman rakuminka ka duba har cikin allura.
Dakin da suke meeting ya shiga ya zauna yana jin zuciyarsa tana wani irin bugu. Ya rasa me yake damunsa tun wayewar garin yau. Ransa a jagule yake ga fargabar da bai san dalilinta ba. Ya san dai yana matukar tsoron wayar nan ta fada hannun wani a cikin gidansa. Mutumcinsa ne zai zube wanwar. Matansa sun san komai amma ba zai so su gani kamar yadda suka ga sakon Yumna ba. Amma 'ya'yansa fa? Wanda Farha ta gani ya ishe shi jin kunya har ya mutu. Tunanin Yumna da ya yi sai ya sake kad'a shi wata duniyar. Rabonsa da ita tun ranar da wayarsa ta bata. Kamar sauran 'yan matansa ita ba bata da numbar kowane layi sai na wannan wayar. Yadda take babu hankalin nan yana tsoron kar ta zo gidan ta ce tana nemansa.
Wuni ya yi yana ta tufka da warwara har aka gama ayyukan da ya saka ba a ga wayar ba. Bai iya tabuka komai ba ya tafi gida.
Kurar da bata taka kara ta karya ba a dakinsa ya fara karkadewa kafin ya shiga wanka. Idan bai yi da kansa ba ya san Mami ba za ta bar Sauda ko Mardiyya suyi masa ba. Musamman da yake daga tafiya suka dawo za ta ce suma sun gaji.
Yana gama shiryawa ya dare gado zai yi ramuwar bacci sai ya bige da chatting. Hirar kwallon kafa ce suka kusa yin awa guda suna fafata musu shi da abokansa a group dinsu. Daga kwance sai da ya koma ya zauna. Can aka turo hoton jerin wasannin da suke magana a kai da sakamakon. Lilu bai san lokacin da ya yi ihun murna ba. Club dinsu ne suka yi nasara kamar yadda suka fada. Sun cinye musun. Yana cikin murnarsa Suhaib ya shigo sanye da wandon bacci da singileti. Da gani shi ma wanka ya sake yi zai kwanta.
"Ka fa hanani bacci da ihu."
Lilu ya daga hannuwa irin na masu saranda yana murmushi.
"Takawarka lafiya dan rigimar Mami yanzu nima zan kwanta."
Suhaib bashi da zabin da ya wuce yin murmushi.
"Kai kuma Dan-ta-kife din Mami ko?"
"Kada ka dora min sunan da ba halina ba."
Suhaib ya gyara tsayuwa gami da yin kwafa "ni rigimar halina ce kenan?"
"Banda rigima tun dazu me ya hanaka bacci sai yanzu daga yin ihuna za ka fito?"
Tsuke baki Suhaib ya yi ya juya yana murmushi. Me kuwa ya hana shi bacci sama da tunanin yarinyar da ya gani tare da makaniken nan? Haushinta ya kamata yaji a ganinsa. Sai aka yi rashin sa a ta cike tunaninsa da wasu abubuwa da bai saba kai kansa garesu ba. Wai yau shi ne yake tunanin wace makarantar gaba da sakandire ce za ta fi kusa da gidansa (Alh. Tahir ya mallaka musu filaye shi da Lilu wadanda ake kan aikin ginawa) idan matarsa iyakarta sakandire kafin auren.
Dariya ya kama yiwa kansa na yadda aka yi daga haduwar rana daya ya san cewa iyakarta sakandire. Koda ya koma daki maimakon ya kwanta kamar yadda ya yi niyya sai ya zura jallabiya ya nufi bangaren Jiddo.
A dakin Lilu bayan fitar Suhaib da karewar musun nasu sai ya soma hamma. Gajiyar biki da ta tafiya tayi masa rubdugu lokaci guda. Mikewa ya yi ya nufi gaban socket din da yake saka chaji. A nan yaga chajarsa da bakuwar waya. Tsorata ya yi don bai ga ta inda za a ce wayar ta shigo dakinsa ta jona kanta ba. Yan uwansa kuma duka ya san babu mai irinta. Kamar ya tafi kiran Suhaib sai ya fasa. Yanzu kowa zai kara raina shi ace bai iya komai ba duk bakinsa. Ya daure zuciyarsa ya daga hannuwansa ya karanta musu Ayatul Kursiyyu ya tottofe.
"Kun dai san nan dakina ne amma duk da haka ban ji haushi don kun jona chaji da chajata ba" ya rage murya da salon rokon arziki "ina neman izini in cire in saka tawa ko rabin awa ne?"
'dillll'
Yana rufe bakinsa text ya shigo wayar. Hanjinsa gabadaya ya kanannade saboda tsoro ya koma kan gadonsa ya haye har kafafunsa.
"Daga magana sai ku turo min text? Indai chaji ne na hakura har abada." Ya zuro kafarsa yana kallon kofa gabansa na faduwa "don Allah zan fita inje dakin yayana. In je?"
'dillll'
Wani text din ya kuma shigowa. Dole ya fasa fita yana fadawa kansa cewa gargadi ne ake yi masa. Ya koma yana mika hannu yana janyewa duk a tsorace
"Bari in duba don kada ace nayi rashin kunya. Ni din banza in ja daku? Ku da ake cewa sai kun shekara dari kuke fara samartaka...."
'dillll'
"Naji. Naji!
Ya dauki wayar sai dai a kulle take. Abinka da fitinannen matashin zamani. Ya manta da tsoron da yake ji ya koma kokarin gano pattern din budeta. Bai sha wata wahala ba ya samu bayan yan dabaru. Abin da ya daure masa kai bai wuce ganin pattern din sak irin na Abbansu ba. Kai tsaye wurin messages ya shiga. Ya tarar da sakonni sun tasarma dari. Kuma wani abin al'ajabi na layin basu fi a kirga ba. Sauran kuwa harrufa ne wasu D, V, J, gasu nan dai. Na sama saman da suka yi alamar sune aka yi yanzu ya bude. Harafin dake jiki Y ne.
(Naji labarin tafiya kayi da tsofaffin matanka. Shi ne ka kasa daukar wayata saboda kana jin tsoronsu? Anyways an tabbatar min yau ka dawo. Na baka zuwa azahar idan baka kirani ba zan zo har gidan ai ba bakona bane. Aure ne dai ko ana so ko ba a so sai na amsa sunan matar Alh. Tahir)
"Abba?" Ya ambata a raunane, hawaye na zubo masa. Duk wani kuzarinsa ya kau sai zafin kirji.
Tarin tambayoyi ne a kansa na son sanin yadda aka kwana a ragaya. Neman amsa ya shiga yi ta hanyar bin text din yana maimaitawa. Bai samo amsar komai ba sama da haddace mummunan sakon. A kasan ransa kuma sai tunanin me zai fi dacewa ya yiwa wannan mai tsautsayin da ta iya shafawa idonta toka ta turo wannan sakon. Cikin sauri ya koma baya ya soma bin sauran harrufan da aka adana sunan mutane dasu ya bude nasu sakonnin. Sannan ne kuma jikinsa ya yi mugun sanyi. Hira ce tsakanin Abbansu da 'HARUFFA' daban daban ta rashin da'a. A haka ma ya kula amsoshin Abban basu da tsayi sosai. Wannan kuma dama ya yi ne domin tsira daga forwarding chat ko screenshot da ake yi a whatsapp. Dena binsu ya yi ya koma saman wanda suka yi musaya da Y. Nata da yawa korafi ne akan rashin zuwansa da maganganun aure. Har tana cewa mahaifinta ya ce idan bai zo ba a satin zasu fasa bashi ita.
Ko kadan Lilu bai damu ba idan Abban aure zai yi. Salon hirar ce tafi daga masa hankali domin alamu sun nuna cewa ba a hira aka tsaya ba. Yaci karo da inda aka yi zancen hotel da guest house. Da kuma godiyar 'yan matan akan tarin kudaden da ya basu. Whatsapp yaso dubawa sai dai babu shi akan wayar.
Yana nan kansa ya rarrabu wurin fassara abubuwan da ya gani yaji shigowar wani sakon. Y din ce dai. Kamar dama jiranta yake yana shigowa ya bude.
(Kaga fa ina tunanin ciki ne ma dani. Zan yi test a gida idan positive ne zan turawa Farha hoton ta whatsapp. Sai a yiwa tsofaffin gwangwanye albishir sun kusa samun karuwa.)
Kuka Lilu yake tamkar yaron goye. Karshen sakon ma da kyar ya iya karantawa saboda cikar hawaye. Nambar ya kwashe ya zuba a wayarsa. Tunda ya kai nambobi shidan farko sunaye masu shigen nambar suka dinga raguwa. Yana saka ta bakwai sai ya rage suna daya.
YA YUMNA kamar yadda suke kiranta shi dasu Sauda a matsayinta na aminyar yayarsu.
Kin tsayawa ya yi sai da ya rubuce ta duka ya tabbatar da sunan da ya gani. Yana jin lokacin da zazzabi ya rufe shi hade da wani irin sanyin jiki. Bashi da hujjar karyatawa saboda harafin da ya gani a wayar Alh. Tahir ya kara bashi tabbaci.
"La haula wala quwwata illa billa. Abba? Ya Yumna?"
A gigice ya mike da ya tuna ma'anar sakon karshe. Indai Yumna ciki ne da ita kenan komai ma ya faru tsakaninsu. Zuciyarsa a take ta tashi saboda kyamar hakan da yaji. Ya fada bandaki ya amayar da duk abin da ke cikinsa. Baki kawai ya kuskure bayan ya gama ya fita daga dakin.
Duk gidan Alh. Tahir babu wanda Jiddo ta tsana a tsukin kwanakin nan kamar Suhaib. Da can da baya shiga shirginta mantawa ma take dashi. Iyakarsu da juna idan zasu wuce kuma suna kusa taji sautin tsakinsa. Tsakin da tun aurenta da ubansa take ji kuma bai taba damunta ba. Ba kuma wani abu ne ya janyo yake yi mata shi ba sai kamasu da aka yi a daki wanda shi ma yaje wurin.
Abubuwan da suka biyo baya da auren nasu sun taimaka kwarai wurin dasa masa tsanarta. Sai gashi bayan shekaru sun shude ta sake bude kofar sabunta zarginta a zuciyarsa. Alal hakika bai yi wani mamaki ba lokacin da yaga tana shirin barin wurin dinner da makaniken nan. Sanannen abu ne cewa indai bawa ya kulla aminci da zina to ba makawa sai ta kawo masa ziyara watarana. Mahaifinsu yace yaji ya gani wurin sabon Allah. Dolensa kuwa ya girbi shukar da yayi ko ba dade ko ba jima. Shi dai adduarsa kullum bata wuce Allah Ya tsare masa mahaifiyarsa da kannensa.
Sallama hade da kwankwasa kofa ya yi da ya isa bangarenta. Mai'aikinta ce ta amsa ta bude masa. A hakimce kan two-seater yaganta tana waya. Ganinsa a tsakar falonta ya mugun firgitata. Lafiya ko rashinta basu taba kawo shi inda take ba. Yau da yazo ta san lallai akwai matsala. Wayar faduwa tayi daga hannunta ta kuma gyara zama ba shiri.
"Nambar makaniken nan zaki bani." Cewar Suhaib, fuska babu annuri.
Jiddo sai ta daburce duk saboda gudun tonon asiri. A haka ta cije ta harare shi.
"Rashin kunyarka ta isheni Suhaib. Idan ban ci darajar shekaruna ba ai ya kamata in ci na matsayina a gidan nan."
Surutunta bashi da gurbi a kwakwalwarsa balle yaci darajar neman ta maimaita domin ya fahimta.
"Zan samu ko in tafi?"
Rainin wayonsa ya sake bata haushi. Wato ma bai ji abin da tace ba bare ta san ran zai yi aiki dashi. Yatsina fuska tayi ita a dole bata san me yake nufi ba ta ce,
"Wane makaniken?"
Wannan karon Suhaib ne ya hango rainin wayonta. Sai da ya dage girarsa daya sama ya murmusa. Harsashi zai hada mata a wurin Alh. Tahir don ranar tada bom din bata zo ba. Wannan ba aikinsa bane. Lokaci da talalar Ubangiji ga bawan da ya dage akan aikin sabo zai cimmata wataran.
Wata irin murya ya yi amfani da ita sai a rantse sangartaccen da ne a gaban mahaifiyarsa yana zuba shagwaba.
"Don Allah ki bani Anti Jiddo."
Ita kanta da taji muryar sai da ta kara tsorata fiye da farkon zuwansa. Ta san dole akwai abin da yake nufi da haka. Ba dai ta zata maigidan ne da kansa ya shigo falon ba tare da ta kula ba sai yanzu.
Ran Alh. Tahir fari kal kamar takarda yau ga Suhaib a bangaren Jiddo. Yadda yake magana ya nuna masa sun jima da daidaitawa. Ya dinga zuba murmushi kamar sakarai har yana mantawa da halin da yake ciki.
"Wato kin saka danki a daki yana ta shagwaba aka rasa wanda zai amsa min sallama ko? Wai ma mene ne yake faruwa zan yi alkalanci."
Suhaib ya yi saurin bashi amsa kafin ta sami damar juya zancen.
"Nambar makanikenta na Kano nake so Abba shi ne taki bani wai sai na yarda gobe zan rakata shopping"
Wohohooo. Alh. Tahir da shi ma ba wani samun hira daga Suhaib din yake ba duk irin son da yake masa sai yaji kansa ya yi gingirin. Murmushi yaki yankewa a fuskarsa.
"To ai sai ka amince dan Jiddo"
'I reject it! Tuff, tuff' cewar Suhaib a zuci yana jin tsigar jikinsa na tashi saboda an kira shi dan Jiddo.
"Na amince. Don Allah ki bani"
Tsabar mamaki sai ta kasa cewa komai banda kai da take gyadawa kamar kadangaruwa taga manja. Sunan Danliti ta lalubo tunda Alh. Tahir ya musu karan tsaye yaki tafiya. Dama al'adarsa ce shiga bangaren kowa idan zai fita ko ya dawo.
Bayan Suhaib ya kwafe nambar ne Alh. Tahir yake tambayarsa me zai hada shi da makanike a Kano.
"Wani case ne babba ya taso tsakaninmu dashi."
Alh. Tahir ya dan bata fuska
"Ban gane ba? Wani abu ya yi maka?"
Suhaib ya yi hanyar kofa yana cewa "a'a, motar Anti Jiddo yaso lalatawa ba don Allah Ya kaini wurin da suke ba da wuri."
Sautin cikin Jiddo har kunnuwansu saboda tsoro. Suhaib kuwa ya fice yana jin Alh. Tahir na tambayarta me ya sami motar har aka nemo makanike shi bai sani ba. Rantse rantsenta kadai ya jiyo ya kara gaba don bashi da lokacin jin karairayin da zata yi.
Lilu kuma da ya fito bai zame ko ina ba sai bangarenta Mami Khadija. Ya yi zaton samunta ta kwanta ko shirin kwanciyar kamar kowa sai yaga sabanin haka. Laptop ce a gabanta ga tulin takardu ta soma barbazawa tana aiki. Gaban table din da aka yi mata musamman saboda aikinta yaje ya mika mata wayar.
"Ga wayar mijinki idan ya dawo ki bashi."
Tun shigowarsa take kallonsa amma furucinsa yasa ta koma yi masa firgitaccen kallo.
"Mijina? Mijina fa ka ce Lilu. Ko dai nice ban ji ba da kyau?" Ta furta a sanyaye.
Lilu ya cije lebe cikin bacin ran tuna abubuwan da ya gani.
"Mijinki maigidan nan nake nufi."
Laptop din ta tura gefe ta tashi tsaye tana dubansa.
"Ko agolanci nazo da kai gidan nan bana tunanin za ka iya budar baki ka kira wanda nake aure Mijina."
Duk shashancin Lilu bai taba zina ba. Mami Khadija ta dasa musu tsananin kyamar wannan laifin tun basu san kawunansu ba. Yafi kowa fitina a gidan amma akwai iyakokin da ko a mafarki bai hango kansa da ketaresu ba.
Kalaman Mamin murmushi suka saka shi.
"Mamina kinfi karfin haka a wajena. Wallahi indai mai mutumci wanda ya san darajar kansa data iyalinsa kika aura ni mai tayaki yi masa biyayya ne."
Da ya gama maganar ya dora wayar a kusa da tata ya fice da sauri. Zama a gabanta karyar masa da zuciya zai sake yi ya kaishi ga kuka. Tausayinta yake ji sai dai kuma jikinsa ya bashi ta jima da sani. A hanyar zuwa dakin ya dinga tuno irin nasihunta da fada da suna yara har kawo ga yanzu. Kusan komai yafi ta'allaka akan zina.
'Ba halinsa bane!' shi ne abin da Mami Khadija ta fara fadawa kanta a lokacin da taji kamar ta kwashe shi da mari. Kwalla ce ta taho mata saboda jikinta yana bata da wuya idan ba sirrin boye ne ya fito fili a wurinsa ba. Yadda Farha ta sani bayan Suhaib gashi yau shi ma ya sani. A ranta ta dinga tsarkake Mulkin Ubangijin da ya haramta zina. Hakika wannan kaba'ira tana zubar da mutumcin mai mutumci. Yau Lilu da bakinsa yake kiran mahaifinsa da wani suna ba Abba ba.
Kallon wayar tayi sau daya ta kawar da kanta. Alh. Tahir na shigowa bangarenta daga wurin Jiddo ta damka masa wayar daga bakin kofar da ta tare don kada ya shigo ciki.
"Lilu ne ya kawo"
Gumi a take ya tsatstsafo akan goshinsa.
"Ya ce wani abu ne?"
Mami Khadija ta kalle shi ido cikin ido ta ce "ya ce ga wayar mijina na bashi idan ya dawo"
Alh. Tahir ya karkata gefen fuskarshi gareta yana son tabbatar da abin da ta ce.
"Mijinki? Dani yake?"
Cikin ko in kula ta ce "a iya sani na ba."
Daga haka ta rufe kofarta ta barshi a wurin yana jinjina girman abin da yake samunsa a tsukin nan.