BABI NA GOMA SHA
Uwa Uwa Ce Part 2 Complete Hausa Novel · about 13 min read
AYA.
"Ranka ya dade kana da bako."
DPO Yahaya ya dago kai cikin bacin rai ya kalli Sergent din da ya yi maganar a tsorace.
"Me na ce muku dazu?"
"Duk wanda yazo ace ka dan fita" ya ce sannan ya gyara tsayuwa rabin jikinsa a bayan kofa "Yallabai mun nemi ya sanar damu matsalar da ta kawo shi ya kafe lallai kai yake son gani."
Girgiza kai ya yi ya fasa yin fadan da da ya yi niyya. Yau din kamar hadin baki tun sassafe ake abu daya. Daga wannan case din sai wancan. Wani abin ma sai kayi tunanin al'ummar tamu ta rasa alkibla. Cuta, ha'inci, mugunta, magudi da uwa uba zina. Kansa ya dauki caji yana ta ciwo. Shi yasa ya bayar da umarnin ace baya nan domin ya huta. Tunda an riga an fada masa bashi da zabin da ya wuce sauraron mutumin.
Sallamar kadai yaji ya gane surukinsa, babban wa ga matarsa. Ba shiri ya mike domin nuna girmamawa a gareshi. Mutumin akwai mutumci da halin girma.
Ilai kuwa da shigowarsa kalmar hakuri ya fara amfani da ita "ayi min hakuri Yahaya. Na san aikinku babu hutu."
"Haba Yaya Salihi ai sai kasa naji babu dadi" ya amsa masa a yayinda suke musabaha.
Bayan 'yan gaishe gaishe Salihi ya zayyane masa duk abin da ya sani game da Habibu na ma'aikatar lafiya. DPO Yahaya ya dinga gyada kai har ya gama.
"Akwai wani mugun dan ta kife mai cin kudaden mutane a cikin ministry of health. Ka san ai jurisdiction dinmu ne .."
"Dalilin kenan da na kawo maka case din."
DPO Yahaya ya ce ya kwantar da hankalinsa zai bi kanun komai
"Sunan ne naji ya zo daya ina tsammanin wanda nake zargi ne. Sau biyu yana zuwa nan amma sai kaji daga sama an ce a sake shi."
Salihi ya dan cije lebe "kana nufin idan shi ne sakinsa zaka yi?"
Da sauri DPO Yahaya ya gyara zancensa domin kuwa ya jima yana son Habibu ya shiga gonar da ta kusance shi. Irin gonar da idan Habibu ya sallami na sama dashi da kudi shi kuma zai nuna bacin ransa akan rashin goyon baya daga abokan aikinsa.
"Duk yadda akayi dubunsa ce zata cika. Yaya Salihi ka dawo gobe kawai in sha Allahu iwar haka yana cell."
Shawara suka zauna yi akan yadda zasu bullo masa a saka shi fiddo kudaden Uwani. DPO Yahaya ya dan muskutu gaban kujerarsa cikin muryar da babu cin fuska a tattare da ita ya ce,
"Amma don Allah garin yaya Maman Mubashir tayi wannan sakacin? A gaskiya ko babu addini a al'adance ma banga dalilin da zaisa mace ta riki wani namiji amini idan ba shakikinta ko miji ba. Duk da na san cewa muma mazan bamu cika kyautawa ba. Idan harkar kudi ta hadamu da mace sai muyi taking advantage din kyautatawarta mu danne mata kudi. To amma duk da haka wannan ba hujja bace da za ta dinga budewa wani shirgegen kato sirrin da mijinta bai sani ba."
Salihi sai ya yi murmushi. Kafin ya tashi ya ce masa zai dauki kwakkwaran mataki akanta. Sai dai yafi kowa sanin Uwaninsa. Duka abubuwan da tayi babu guda da zai yi mata uzuri akan shi. Bata kyauta ba iya rashin kyautawa. Duk da haka gidan da ta taso ya taka muhimmiyar rawa wurin shaping din rayuwarta. Bakin halinta na rowa ba komai bane illa nason da halin mahaifinta ya yi a jikinta da kuma tsoron kada a maimaita wata Innayo din da ita.
Domin ya sami cikakkiyar yarda tsakaninsa da ita da sauyin hali sai ya nuna mata cewa ba kowane namiji bane Alh. Rabi'u. Dukiyar matarsa ba tasa bace kuma nauyin dawainiyarta da ta yaransu a wuyansa yake shi namiji. A karshe yana son ta bambance tsakanin kyautatawar da mata kan iya yiwa mazajensu domin lada da rainin wayon maza marasa tsoron Allah. Irin mazan dake sarayar da ayyukan da suka wajaba a garesu su barwa mace daga taimako. Sune suke tsorata mata da yawa su kasa taimakon mazajensu koda suna da halin yin hakan.
Kwalla fal idanun Innayo a lokacin da Honourable Habu yayi mata kyakkyawan albishir.
"Hasiyan ce dai da ciki ko?"
Kunyar da ya manta da ita a lokacin da ya iso gidan har ya fada mata da bakinsa ce ta kama shi. Ya dan dukar da kai yana murmushi. Ita ma murmushin ta mayar masa wanda ya koma dariyar farinciki.
"Fadi komai kan ka tsaye ai auta ce babu mai cewa mun yi rashin kunya."
Honourable dai sai dariya mai hade da kunya. Asibitin da Hasiyan take kwance ta tambaye shi sai ga Asabe a kansu kamar daga sama ta fado. Daga dakinta taji kamar suna ambaton Mariya domin 'ya' kawai taji da kuma asibiti. Bayan abin da ta gani dazu a firgice ta fito.
"Me ya sami Mariyan? Ina Munzalin?" Ta ce yayinda take waigawa hagu da dama tana dube dube.
Innayo tayi mamakin abin da ya tayar mata da hankali haka. Ba abin ta tambaya ba ta san tsaf za ta gwasaleta.
"Hasiya ce a asibiti."
"Au tooo...to Allah Ya sauwake" ta ce a sanyaye tana juyawa dakinta.
Innayo bata ma bi ta kanta ba ta shirya ita da su Salima zasu tafi asibitin. Dakinta ta koma inda ta baro Uwani tana ta kai gwauro da mari ita kadai.
"Na san cewa a karkashin wani kike nima ba zan so ki dinga yawo da aurenki ba. Amma ai ko sakon gaisuwa ga kanwarki kya bayar. Zumuncin da kike wulakantawa Uwani shi ne gatanki. Ba don kinsa kafa kin tattaka shi ba da bamu ga rana irin ta yau ba akan aurenki."
Kunyar rashin tunaninta taji da kanta.
"Kiyi hakuri Innayo. Ku gaisheta kafin na zo."
Murmushin takaici Innayo din tayi ta fita tana cewa "da girmanki baki san gatse ba. A yadda Hasiya ta dade tana neman haihuwa na zata kiran mijinki zaki yi ki nemi izinin zuwa dubota. Komai girman farincikin da zai gilma a gidan nan indai ba ke ya raba ba wato ba za kiyi murna ba..."
Har tayi waje Uwani tana jiyota. Abin ma sai ya sata murmushin da bata yi niyya ba. Autar Innayo da ciki kuma bata je dubiya ba. Ta san ba makawa yau sai ta kwana tana jin mitar mahaifiyarta. Sai dai kuma abin da yake damunta yafi karfin samun cikin Hasiya a yanzu dai. Hakuri ta sake bayarwa da sakon gaisuwar ta koma ciki. Suna fita ta fito ita ma ta shiga dakin Asabe. Daga bakin kofa ta tsaya cikin shiri don har mayafi ta yafa. Abin da ya kaita ta fada ba tare da kwana kwana ba.
"Gidan Munzali za ki kwatanta min ko ki rakani."
Da tsananin mamaki Asabe tayi mata duba irin na wanda ake tsammanin ya yi makuwa "gidan Munzali kuma?"
Uwani sai ta dauko waya ta mika hannu gareta don bata ga dalilin mamakin da Asabe ta nuna ba. Ta rasa gane me yasa kowa yake ganin kamar bata son zumunci. Waye cikinsu yake zumuncin da ita?
"Bani nambarsa idan kwatancen ba zai samo ba"
Asabe sai ta sabi mayafi. Yau din gani take kamar duniya tana hajijiya da ita. Ba kuma don abin da ta gani a tattare da Qibdiyya ba kadai. Harda maganganun Munzali. Tunaninta ya kasa hasko mata inda zantukansa suka dosa.
Da yake mai hali ba ya fasawa suna samun adaidaita sahu Asabe sai cewa tayi "amma dai ke za ki biya min ko? Tunda dai ke zan raka."
Uwani ta hade girar sama "Munzalin ba danki bane? To nima ba kudi gareni ba. In ba za ki biya ba ki kwatanta min."
Asabe tayi azamar gyara zama tana kallon idanun Uwani "Idan baki nuna min halinki ba ai bana ce ke din tsatson Alh. Rabi'u bace."
Direban da yaji irin maganganunsu sai ya tsaya cak a tsakar titi.
"Hajiyoyi ku sauka don Allah kafin mu isa mu soma rigima daku akan kudi."
"Muje zan biya" cewar Uwani tana hararar Asabe da gefen ido.
"Wai ma me zaki je yi a gidan Munzali?"
"Abin da yasa kika biyoni maimakon yi min kwatance ne zai kaini."
Asabe ta hangame baki "kema ya fada miki?"
"Labe nayi muku duk da dai hargaginki ne ya sani zuwa ba wai nayi niyya bane." Uwani ta bata amsa kai tsaye.
"Nice nake hargagin? Lallai Uwani baki da mutumci. Koda yake ki ka yiwa gyatumarki ma wace ni?" Cewar Asabe tana kara kulewa.
Uwani bata kulata ba. Hankalinta ya yi gaba cikin tunanin nawa zata caji Munzali idan ta duba 'yarsa. Ko babu komai yadda ake labarin arzikinsa da son da yakewa 'yar dole ya mata hasafi. Kila ma ya hada da toshiyar baki.
Banda 'ya'yan cikinta da jikoki babu wanda ya yi saura a bangaren Baaba Mari. Jama'ar gidan manya suna asibitin da Mal. Inuwa ya jagoranci kai Mal. Sa'adu. Sauran kuwa musamman mata suna bangarensu a tsorace. Labari yazo musu cewa Baaba Mari da kanta ta aika kiran Mal Sa'adu. Gashi daga shigarsa bai fito da kafarsa ba sai gadon asibiti.
A asibitin kuwa tunda Mal. Sa'adu ya dan farfado ya soma cewa a kai shi gida yana son ganin Baaba Mari.
Wannan abu ya harzuka Deluwa musamman taga ko sannun da take ta ce masa bai amsa ba.
"Jama'a ku kawo min dauki. Mari ta fito da maitarta fili ta lashe kurwar Malam."
'Yan koranta da na Mal. Sa'adu suka dinga jinjina kai alamun amincewa. Shi kuwa wanda ake yi dominsa ransa sai ya baci. Abu ne da bai taba zato zai ji a ransa ba sai gashi a yau duk kalmar batanci da za a fada akan matar kaninsa sai yaji tamkar an loda masa kaya ne a kansa. Tuntuni ya fahimci illolin da take son nuna masa game da bara. Sai ya zabi ya take gaskiya saboda bata kai matsayin da zai dauki shawararta ba. Kuma sauran yaransu masu zuwa ai kowa ya dawo lafiya. Gabansa ya fadi da wani tunanin ya mamaye kwanyarsa. Shi ganau ne ba jiyau ba akan canjin da aka samu cikin 'ya'yansu da na makota.
Akwai uban da yake zuwa wurinsa yana yiwa dansa rubutu domin neman a raba shi da dauke dauke. Ya gallabi gidansu da makota babu damar mutum ya yi ajiya.
Wani kuma dan ya addabesu da haurawa matan aure cikin dare yana musu fyade.
Ga kwararren malamin tsibbu wanda matan aure suke tarawa arzikinsu akan mallakar miji da korar kishiya.
Suna da dan kwaya wanda har a kwata ana tsinto shi.
Akwai wanda ya koyo mugunta da tsantsar cin zali. Sau biyu yana zubarwa matarsa ciki da duka sannan ya karya mata cinya.
Wani ma dan damfara ya zama. Yana can Dubai ana damawa dashi
Wasu sun bata har yau babu su babu labarinsu.
A karshe akwai wadanda suka rasu sai dai a kawo gawa. Wani ma sai dai labari ya riski iyayensa bayan an binne shi.
Wadannan halaye hatta a makaratun boko na kwana ba baki bane saboda wahalar dake cikin tarbiyya. A can safe, rana, yamma da dare duka akwai ido akan yaran. Amma basu tsira ba. Idanun masu kular sun yiwa daliban kadan. Dalibai sama da arba'in a karkashin kulawar mutum daya na wani lokaci. Dole a sami masu kangarewa ba tare da sani ba. To ina ga makarantar allo wadda idon bai wuce na malami ba? Yaran kuma suna fita a duk lokutan cin abinci neman na kansu?
Duk da haka akwai wadanda suka yi dacen samun alkhairi daga zuwa karatu. 'DACE suka yi' Mal. Sa'adu ya tunatar da kansa. Irin dacen da wadanda suka fadawa halaka basu yi ba. Karatu ba zai taba tafiya babu tarbiyya ba. Tarbiyya kuwa tana samun kwakkwaran tubali ne a inda ake bayar da kulawa. Ita kuwa kulawa sai an jure an daure domin bayar da tarbiyar akwai wuya. Zamanin baya ido kadai d'a zai hada da mahaifiyarsa ya fahimci sakon dake cikinsa kuma ya yi aiki dashi. Yanzu kuwa sai ka zare idon shi ma ya bude maka nasa kirikiri yana dariya. Ka dake shi cikin sakan talatin ya manta ya sake maimaita laifin. Akwai wuya...ke uwa kina yi ma ya aka kare balle an kai dan nesa babu mai kwabarsa.
Mari ta ce ba za ta yafe masa ba.
Abbati ya zama dan luwadi...Wa Iyazu Billah.
Da me zai ji? Tsatson gidansu da yake alfahari da kyawunsa shi ne aka sami reshe guda ya lalace. Bayan sadaukar da rayuwarsa wurin ganin gidansu ya cigaba da amsa sunan gidan Malamai yanzu wannan masifa ta bullo. Zuciyarsa bata son karba amma kwakwalwarsa ta san gaskiya. Idan ma yaki neman gyara shi ne babban mai kwana ciki. Ba don ya so ba ya yiwa Deluwa magana akan kalamanta.
"Ba zan lamunci wannan shirmen ba Deluwa. Idan ba za ki iya kama bakinki daga barin aibata Mari ba ki wuce gida.
Kirji ta dafe ba shiri kamar tana gudun faduwarsa. Ta dube shi idanu a waje.
"Malam Mari ka ke karewa? Mari dai wadda muke raba dare muna kwashewa albarka ni da kai? Kaiiii..." Ta fada da karfi tana girgiza kai "Yasin da wata a kasa. Mari ta karawa bokanta kudi aiki ya ci."
Mal. Sa'adu da ya san shiru sosai yake bukata domin samun nutsuwar tunani da neman mafita tamke fuska ya yi. Bai bata damar roko ba ya ce lallai ta koma gida baya son zamanta a asibitin. Bata yi masa musu ba ta tafi gidan. Amma tana zuwa dakin Baaba Mari ta nufa tana danna ashariya.
Yamma tayi, gari ya soma duhun da dakuna suke bukatar haske. Lokacin da Asabe da Uwani suka yi sallama a falon gidan Munzali basa ganin kofofi da matattalar dake wurin. Ko ina dund'um an saki labulaye. Kwada sallama suka dinga yi da karfi tunda Maigadi ya tabbatar musu cewa ya shigo sannan ga motar da ya fita da ita a wurin parking. Uwani ta so shagala da kallon tsala tsalan motocin dake zube a wurin. Ga gidajen daga waje ma sun hadu. Tsarin fuskantar juna da suke yi dana Abbati ya sake burgeta.
Shigowar Kande ce ta kawo karshen sallamar tasu. Da yake ta san Asabe sai ta gaishesu da girmamawa.
"Alhamdulillahi kun zo Hajiya. Yanzu nake fakon idan aka yi Magriba Alh. Munzali bai fito ba zan taho gidan naki."
"Me ya faru kuma?" Cewar Asabe da saurinta.
Kande ta labarta musu yanayin da Munzali ya shigo gidan yana harhada hanya. Da ganinsa baya cikin nutsuwa ko kadan. Qibdiyya tana kafadarsa tayi bacci. Da ta nemi karbarta har wata tsawa ya daka mata. Dole taja baya ta zuba masa ido. Hawaye ne tabbas taga saukowarsu daga idanunsa. Sai dai kafin ta gama janyo tunanin da ya dace tayi, ya haye sama sai karar buga kofa taji.
"Ki hau ki kira min shi da Qibdiyyan" inji Uwani ga Asabe tana ajiye dan akwatin tafi da gidanka na kayan asibiti.
Hantar cikinta sai da ta dan kada don bata manta maganganunsa na dazu ba.
"Ban gane in hau ba? Don rashin tausayi tsofai-tsofai dani zaki sani hawan bene."
Uwani ta tabe baki. Abin kirki tazo yi amma halinta kam ya zanu akan dutse.
"Gidan danki ne fa kuma ni ban taba zuwa ba. Ke ya dace ki hau."
"Sai an magana ku dinga cewa ubanku daya. Da su Maimuna ne ai ba za ki ce yau kika fara..."
Sauran maganar makalewa tayi don tuni Uwani ta kusa kure benen.
Kankanin lokaci ya sadata da wani katafaren falo wanda yake cike da ababen more rayuwa. Kofofin dake cikinsa ta dinga kallo tana neman kofar dakinsa. Cikin sa a sai ta hango takalmin Qibdiyya a bakin kofar daya daga ciki. Duk yadda aka yi nan suke. Bata ji ko dar ba don dakakkiyar zuciya gareta ta karasa kofar dakin tana kwankwasawa gami da yin sallama.
Munzali yana zaune a gaban gadonsa inda ya shimfide Qibdiyya ya hada kai da gwiwa yaji sallamarta. Yayi matukar mamaki duk da ya san taji komai bayan haduwarsu ta dazu. Bai motsa daga inda yake ba kawai ya dago kai.
"Shigo."
"Ranka ya dade kana da bako."
DPO Yahaya ya dago kai cikin bacin rai ya kalli Sergent din da ya yi maganar a tsorace.
"Me na ce muku dazu?"
"Duk wanda yazo ace ka dan fita" ya ce sannan ya gyara tsayuwa rabin jikinsa a bayan kofa "Yallabai mun nemi ya sanar damu matsalar da ta kawo shi ya kafe lallai kai yake son gani."
Girgiza kai ya yi ya fasa yin fadan da da ya yi niyya. Yau din kamar hadin baki tun sassafe ake abu daya. Daga wannan case din sai wancan. Wani abin ma sai kayi tunanin al'ummar tamu ta rasa alkibla. Cuta, ha'inci, mugunta, magudi da uwa uba zina. Kansa ya dauki caji yana ta ciwo. Shi yasa ya bayar da umarnin ace baya nan domin ya huta. Tunda an riga an fada masa bashi da zabin da ya wuce sauraron mutumin.
Sallamar kadai yaji ya gane surukinsa, babban wa ga matarsa. Ba shiri ya mike domin nuna girmamawa a gareshi. Mutumin akwai mutumci da halin girma.
Ilai kuwa da shigowarsa kalmar hakuri ya fara amfani da ita "ayi min hakuri Yahaya. Na san aikinku babu hutu."
"Haba Yaya Salihi ai sai kasa naji babu dadi" ya amsa masa a yayinda suke musabaha.
Bayan 'yan gaishe gaishe Salihi ya zayyane masa duk abin da ya sani game da Habibu na ma'aikatar lafiya. DPO Yahaya ya dinga gyada kai har ya gama.
"Akwai wani mugun dan ta kife mai cin kudaden mutane a cikin ministry of health. Ka san ai jurisdiction dinmu ne .."
"Dalilin kenan da na kawo maka case din."
DPO Yahaya ya ce ya kwantar da hankalinsa zai bi kanun komai
"Sunan ne naji ya zo daya ina tsammanin wanda nake zargi ne. Sau biyu yana zuwa nan amma sai kaji daga sama an ce a sake shi."
Salihi ya dan cije lebe "kana nufin idan shi ne sakinsa zaka yi?"
Da sauri DPO Yahaya ya gyara zancensa domin kuwa ya jima yana son Habibu ya shiga gonar da ta kusance shi. Irin gonar da idan Habibu ya sallami na sama dashi da kudi shi kuma zai nuna bacin ransa akan rashin goyon baya daga abokan aikinsa.
"Duk yadda akayi dubunsa ce zata cika. Yaya Salihi ka dawo gobe kawai in sha Allahu iwar haka yana cell."
Shawara suka zauna yi akan yadda zasu bullo masa a saka shi fiddo kudaden Uwani. DPO Yahaya ya dan muskutu gaban kujerarsa cikin muryar da babu cin fuska a tattare da ita ya ce,
"Amma don Allah garin yaya Maman Mubashir tayi wannan sakacin? A gaskiya ko babu addini a al'adance ma banga dalilin da zaisa mace ta riki wani namiji amini idan ba shakikinta ko miji ba. Duk da na san cewa muma mazan bamu cika kyautawa ba. Idan harkar kudi ta hadamu da mace sai muyi taking advantage din kyautatawarta mu danne mata kudi. To amma duk da haka wannan ba hujja bace da za ta dinga budewa wani shirgegen kato sirrin da mijinta bai sani ba."
Salihi sai ya yi murmushi. Kafin ya tashi ya ce masa zai dauki kwakkwaran mataki akanta. Sai dai yafi kowa sanin Uwaninsa. Duka abubuwan da tayi babu guda da zai yi mata uzuri akan shi. Bata kyauta ba iya rashin kyautawa. Duk da haka gidan da ta taso ya taka muhimmiyar rawa wurin shaping din rayuwarta. Bakin halinta na rowa ba komai bane illa nason da halin mahaifinta ya yi a jikinta da kuma tsoron kada a maimaita wata Innayo din da ita.
Domin ya sami cikakkiyar yarda tsakaninsa da ita da sauyin hali sai ya nuna mata cewa ba kowane namiji bane Alh. Rabi'u. Dukiyar matarsa ba tasa bace kuma nauyin dawainiyarta da ta yaransu a wuyansa yake shi namiji. A karshe yana son ta bambance tsakanin kyautatawar da mata kan iya yiwa mazajensu domin lada da rainin wayon maza marasa tsoron Allah. Irin mazan dake sarayar da ayyukan da suka wajaba a garesu su barwa mace daga taimako. Sune suke tsorata mata da yawa su kasa taimakon mazajensu koda suna da halin yin hakan.
Kwalla fal idanun Innayo a lokacin da Honourable Habu yayi mata kyakkyawan albishir.
"Hasiyan ce dai da ciki ko?"
Kunyar da ya manta da ita a lokacin da ya iso gidan har ya fada mata da bakinsa ce ta kama shi. Ya dan dukar da kai yana murmushi. Ita ma murmushin ta mayar masa wanda ya koma dariyar farinciki.
"Fadi komai kan ka tsaye ai auta ce babu mai cewa mun yi rashin kunya."
Honourable dai sai dariya mai hade da kunya. Asibitin da Hasiyan take kwance ta tambaye shi sai ga Asabe a kansu kamar daga sama ta fado. Daga dakinta taji kamar suna ambaton Mariya domin 'ya' kawai taji da kuma asibiti. Bayan abin da ta gani dazu a firgice ta fito.
"Me ya sami Mariyan? Ina Munzalin?" Ta ce yayinda take waigawa hagu da dama tana dube dube.
Innayo tayi mamakin abin da ya tayar mata da hankali haka. Ba abin ta tambaya ba ta san tsaf za ta gwasaleta.
"Hasiya ce a asibiti."
"Au tooo...to Allah Ya sauwake" ta ce a sanyaye tana juyawa dakinta.
Innayo bata ma bi ta kanta ba ta shirya ita da su Salima zasu tafi asibitin. Dakinta ta koma inda ta baro Uwani tana ta kai gwauro da mari ita kadai.
"Na san cewa a karkashin wani kike nima ba zan so ki dinga yawo da aurenki ba. Amma ai ko sakon gaisuwa ga kanwarki kya bayar. Zumuncin da kike wulakantawa Uwani shi ne gatanki. Ba don kinsa kafa kin tattaka shi ba da bamu ga rana irin ta yau ba akan aurenki."
Kunyar rashin tunaninta taji da kanta.
"Kiyi hakuri Innayo. Ku gaisheta kafin na zo."
Murmushin takaici Innayo din tayi ta fita tana cewa "da girmanki baki san gatse ba. A yadda Hasiya ta dade tana neman haihuwa na zata kiran mijinki zaki yi ki nemi izinin zuwa dubota. Komai girman farincikin da zai gilma a gidan nan indai ba ke ya raba ba wato ba za kiyi murna ba..."
Har tayi waje Uwani tana jiyota. Abin ma sai ya sata murmushin da bata yi niyya ba. Autar Innayo da ciki kuma bata je dubiya ba. Ta san ba makawa yau sai ta kwana tana jin mitar mahaifiyarta. Sai dai kuma abin da yake damunta yafi karfin samun cikin Hasiya a yanzu dai. Hakuri ta sake bayarwa da sakon gaisuwar ta koma ciki. Suna fita ta fito ita ma ta shiga dakin Asabe. Daga bakin kofa ta tsaya cikin shiri don har mayafi ta yafa. Abin da ya kaita ta fada ba tare da kwana kwana ba.
"Gidan Munzali za ki kwatanta min ko ki rakani."
Da tsananin mamaki Asabe tayi mata duba irin na wanda ake tsammanin ya yi makuwa "gidan Munzali kuma?"
Uwani sai ta dauko waya ta mika hannu gareta don bata ga dalilin mamakin da Asabe ta nuna ba. Ta rasa gane me yasa kowa yake ganin kamar bata son zumunci. Waye cikinsu yake zumuncin da ita?
"Bani nambarsa idan kwatancen ba zai samo ba"
Asabe sai ta sabi mayafi. Yau din gani take kamar duniya tana hajijiya da ita. Ba kuma don abin da ta gani a tattare da Qibdiyya ba kadai. Harda maganganun Munzali. Tunaninta ya kasa hasko mata inda zantukansa suka dosa.
Da yake mai hali ba ya fasawa suna samun adaidaita sahu Asabe sai cewa tayi "amma dai ke za ki biya min ko? Tunda dai ke zan raka."
Uwani ta hade girar sama "Munzalin ba danki bane? To nima ba kudi gareni ba. In ba za ki biya ba ki kwatanta min."
Asabe tayi azamar gyara zama tana kallon idanun Uwani "Idan baki nuna min halinki ba ai bana ce ke din tsatson Alh. Rabi'u bace."
Direban da yaji irin maganganunsu sai ya tsaya cak a tsakar titi.
"Hajiyoyi ku sauka don Allah kafin mu isa mu soma rigima daku akan kudi."
"Muje zan biya" cewar Uwani tana hararar Asabe da gefen ido.
"Wai ma me zaki je yi a gidan Munzali?"
"Abin da yasa kika biyoni maimakon yi min kwatance ne zai kaini."
Asabe ta hangame baki "kema ya fada miki?"
"Labe nayi muku duk da dai hargaginki ne ya sani zuwa ba wai nayi niyya bane." Uwani ta bata amsa kai tsaye.
"Nice nake hargagin? Lallai Uwani baki da mutumci. Koda yake ki ka yiwa gyatumarki ma wace ni?" Cewar Asabe tana kara kulewa.
Uwani bata kulata ba. Hankalinta ya yi gaba cikin tunanin nawa zata caji Munzali idan ta duba 'yarsa. Ko babu komai yadda ake labarin arzikinsa da son da yakewa 'yar dole ya mata hasafi. Kila ma ya hada da toshiyar baki.
Banda 'ya'yan cikinta da jikoki babu wanda ya yi saura a bangaren Baaba Mari. Jama'ar gidan manya suna asibitin da Mal. Inuwa ya jagoranci kai Mal. Sa'adu. Sauran kuwa musamman mata suna bangarensu a tsorace. Labari yazo musu cewa Baaba Mari da kanta ta aika kiran Mal Sa'adu. Gashi daga shigarsa bai fito da kafarsa ba sai gadon asibiti.
A asibitin kuwa tunda Mal. Sa'adu ya dan farfado ya soma cewa a kai shi gida yana son ganin Baaba Mari.
Wannan abu ya harzuka Deluwa musamman taga ko sannun da take ta ce masa bai amsa ba.
"Jama'a ku kawo min dauki. Mari ta fito da maitarta fili ta lashe kurwar Malam."
'Yan koranta da na Mal. Sa'adu suka dinga jinjina kai alamun amincewa. Shi kuwa wanda ake yi dominsa ransa sai ya baci. Abu ne da bai taba zato zai ji a ransa ba sai gashi a yau duk kalmar batanci da za a fada akan matar kaninsa sai yaji tamkar an loda masa kaya ne a kansa. Tuntuni ya fahimci illolin da take son nuna masa game da bara. Sai ya zabi ya take gaskiya saboda bata kai matsayin da zai dauki shawararta ba. Kuma sauran yaransu masu zuwa ai kowa ya dawo lafiya. Gabansa ya fadi da wani tunanin ya mamaye kwanyarsa. Shi ganau ne ba jiyau ba akan canjin da aka samu cikin 'ya'yansu da na makota.
Akwai uban da yake zuwa wurinsa yana yiwa dansa rubutu domin neman a raba shi da dauke dauke. Ya gallabi gidansu da makota babu damar mutum ya yi ajiya.
Wani kuma dan ya addabesu da haurawa matan aure cikin dare yana musu fyade.
Ga kwararren malamin tsibbu wanda matan aure suke tarawa arzikinsu akan mallakar miji da korar kishiya.
Suna da dan kwaya wanda har a kwata ana tsinto shi.
Akwai wanda ya koyo mugunta da tsantsar cin zali. Sau biyu yana zubarwa matarsa ciki da duka sannan ya karya mata cinya.
Wani ma dan damfara ya zama. Yana can Dubai ana damawa dashi
Wasu sun bata har yau babu su babu labarinsu.
A karshe akwai wadanda suka rasu sai dai a kawo gawa. Wani ma sai dai labari ya riski iyayensa bayan an binne shi.
Wadannan halaye hatta a makaratun boko na kwana ba baki bane saboda wahalar dake cikin tarbiyya. A can safe, rana, yamma da dare duka akwai ido akan yaran. Amma basu tsira ba. Idanun masu kular sun yiwa daliban kadan. Dalibai sama da arba'in a karkashin kulawar mutum daya na wani lokaci. Dole a sami masu kangarewa ba tare da sani ba. To ina ga makarantar allo wadda idon bai wuce na malami ba? Yaran kuma suna fita a duk lokutan cin abinci neman na kansu?
Duk da haka akwai wadanda suka yi dacen samun alkhairi daga zuwa karatu. 'DACE suka yi' Mal. Sa'adu ya tunatar da kansa. Irin dacen da wadanda suka fadawa halaka basu yi ba. Karatu ba zai taba tafiya babu tarbiyya ba. Tarbiyya kuwa tana samun kwakkwaran tubali ne a inda ake bayar da kulawa. Ita kuwa kulawa sai an jure an daure domin bayar da tarbiyar akwai wuya. Zamanin baya ido kadai d'a zai hada da mahaifiyarsa ya fahimci sakon dake cikinsa kuma ya yi aiki dashi. Yanzu kuwa sai ka zare idon shi ma ya bude maka nasa kirikiri yana dariya. Ka dake shi cikin sakan talatin ya manta ya sake maimaita laifin. Akwai wuya...ke uwa kina yi ma ya aka kare balle an kai dan nesa babu mai kwabarsa.
Mari ta ce ba za ta yafe masa ba.
Abbati ya zama dan luwadi...Wa Iyazu Billah.
Da me zai ji? Tsatson gidansu da yake alfahari da kyawunsa shi ne aka sami reshe guda ya lalace. Bayan sadaukar da rayuwarsa wurin ganin gidansu ya cigaba da amsa sunan gidan Malamai yanzu wannan masifa ta bullo. Zuciyarsa bata son karba amma kwakwalwarsa ta san gaskiya. Idan ma yaki neman gyara shi ne babban mai kwana ciki. Ba don ya so ba ya yiwa Deluwa magana akan kalamanta.
"Ba zan lamunci wannan shirmen ba Deluwa. Idan ba za ki iya kama bakinki daga barin aibata Mari ba ki wuce gida.
Kirji ta dafe ba shiri kamar tana gudun faduwarsa. Ta dube shi idanu a waje.
"Malam Mari ka ke karewa? Mari dai wadda muke raba dare muna kwashewa albarka ni da kai? Kaiiii..." Ta fada da karfi tana girgiza kai "Yasin da wata a kasa. Mari ta karawa bokanta kudi aiki ya ci."
Mal. Sa'adu da ya san shiru sosai yake bukata domin samun nutsuwar tunani da neman mafita tamke fuska ya yi. Bai bata damar roko ba ya ce lallai ta koma gida baya son zamanta a asibitin. Bata yi masa musu ba ta tafi gidan. Amma tana zuwa dakin Baaba Mari ta nufa tana danna ashariya.
Yamma tayi, gari ya soma duhun da dakuna suke bukatar haske. Lokacin da Asabe da Uwani suka yi sallama a falon gidan Munzali basa ganin kofofi da matattalar dake wurin. Ko ina dund'um an saki labulaye. Kwada sallama suka dinga yi da karfi tunda Maigadi ya tabbatar musu cewa ya shigo sannan ga motar da ya fita da ita a wurin parking. Uwani ta so shagala da kallon tsala tsalan motocin dake zube a wurin. Ga gidajen daga waje ma sun hadu. Tsarin fuskantar juna da suke yi dana Abbati ya sake burgeta.
Shigowar Kande ce ta kawo karshen sallamar tasu. Da yake ta san Asabe sai ta gaishesu da girmamawa.
"Alhamdulillahi kun zo Hajiya. Yanzu nake fakon idan aka yi Magriba Alh. Munzali bai fito ba zan taho gidan naki."
"Me ya faru kuma?" Cewar Asabe da saurinta.
Kande ta labarta musu yanayin da Munzali ya shigo gidan yana harhada hanya. Da ganinsa baya cikin nutsuwa ko kadan. Qibdiyya tana kafadarsa tayi bacci. Da ta nemi karbarta har wata tsawa ya daka mata. Dole taja baya ta zuba masa ido. Hawaye ne tabbas taga saukowarsu daga idanunsa. Sai dai kafin ta gama janyo tunanin da ya dace tayi, ya haye sama sai karar buga kofa taji.
"Ki hau ki kira min shi da Qibdiyyan" inji Uwani ga Asabe tana ajiye dan akwatin tafi da gidanka na kayan asibiti.
Hantar cikinta sai da ta dan kada don bata manta maganganunsa na dazu ba.
"Ban gane in hau ba? Don rashin tausayi tsofai-tsofai dani zaki sani hawan bene."
Uwani ta tabe baki. Abin kirki tazo yi amma halinta kam ya zanu akan dutse.
"Gidan danki ne fa kuma ni ban taba zuwa ba. Ke ya dace ki hau."
"Sai an magana ku dinga cewa ubanku daya. Da su Maimuna ne ai ba za ki ce yau kika fara..."
Sauran maganar makalewa tayi don tuni Uwani ta kusa kure benen.
Kankanin lokaci ya sadata da wani katafaren falo wanda yake cike da ababen more rayuwa. Kofofin dake cikinsa ta dinga kallo tana neman kofar dakinsa. Cikin sa a sai ta hango takalmin Qibdiyya a bakin kofar daya daga ciki. Duk yadda aka yi nan suke. Bata ji ko dar ba don dakakkiyar zuciya gareta ta karasa kofar dakin tana kwankwasawa gami da yin sallama.
Munzali yana zaune a gaban gadonsa inda ya shimfide Qibdiyya ya hada kai da gwiwa yaji sallamarta. Yayi matukar mamaki duk da ya san taji komai bayan haduwarsu ta dazu. Bai motsa daga inda yake ba kawai ya dago kai.
"Shigo."