← Book details Sulthana Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 3 OF 28

Sashe 3

Sulthana Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Bell din makaranta Aka kada ta K'alleshi tana Yar Murnushi
"Habiby Mu hadu Anjima da Magriba a dandali"
Bata jira mai zaice bah ta shiga makaranta dasauri. Murmushin cin nasara yayi a ranshi Fadi yak'e
"Keh kina tunanin ni Ahmad Aurenki zanyi, Baridai na Samu abinda nake nema bak'i kara ganina a garin nan"..

Yauma kamar jiya Baffa dakansh ya diban mata Gyadan ta Dafa ta Fito Talla, Mutane sai kallanta suke da Mamaki dan basu taba ganin yayan Mallan jamilu da Talla bah, Bakin Kasuwa taje Yauma Anma Tai Rashin Sa'a Baifi Gwangwani hudu aka siya bah Har Gaf da Magriba, Ganin Dare na Neman Yi yasa ta dawo Gida cikeda Fargaban Abinda Baffa Zaiyi mata, Bata sameshi a gida bah Yana Wajan Almajiransa, a Kofar dakinshi ta aje Gyadar ta Shiga aikinta na Yanma..

Sai Bayan Isha'i ya Shigo Gidan dasauri, Gyadan da ta ajemai a kofar dak'i ya K'alla yayi kwafa ya Shiga Cikin Daki, Baifi Minti Goma Bah Ya Fito Dasauri Ya Shiga Dakin Mama
"Saratu! Saratu!!"
Mama data Sallame Sallah ta K'alleshi da Mamaki
"Lapia Mallan Kake Kwalamin Kira haka??"
Kin Shiga dakina neh kin dauki Kudi"
Kallanshi tai da Alamar Mamaki, "Ban ganeh Kudi bah, na Taba daukan kudinka ban fadama bah"
Bai kara cewa komai bah Ya fita daga Dak'in, Sulthana ya soma Kwalama Kira, Ta Shigo Tsakar Gidan Dasauri tareda Rusunawa
"Na'am Baffa"
Ido Ya zazzaro yana Kallanta
"Kudina Zaki bani da Kika dauka"
Mama ta Kalla dasauri sannan ta maida dubanta ga Baffan dake Tsafe ya Kafeta da Ido
"Wallahi Baffa ban dau Maka Kudi bah"
Ameenatu Dake Dak'i ita da K'awarta habiba ta fito dasauri
"Baffa Lapia"
Kudi na Ajiye a daki ko kin Gani?"
Girgiza kai tai dasauri
"Aa banga kudi bah"
Ina Hafsatu? Cewar Mama
Dan Jim Ameenatu tai Sannan Tace
"Tunda Akai Magriba ta fita Bata Dawo bah"

Dak'i Baffa Ya shiga Chan sai Gashi da Dorina katuwa mai Baki dayawa, Mama ta Kalleshi
"Meh Zakayi Mallan"
Keh! Nan da nan Jikin Sulthana yadau Rawa
"Wallahi Baffa Bandau maka kudi bah, Dan Allah kai Hakuri Karka dakeni"
Daka Mata Tsawa Yayi
"Ki Fito Min da Kudina, Oho! Wato dan nace bazan saki a makaranta bah shine kika satan min kudi dan ki koma makaranta koh"
Kuka sosai Sulthana take
"Wallahi Baffa ban dau maka kudi bah, Dan Allah Karka Dakeni."
Hakuri Ameenatu ta soma bah Baffa anma ko Kallanta Beyi bah, Bulalan dake Hannunshi ya soma dukanta Dashi ta koina, ihu Sulthana take Tana Rokonshi Anma ina. Rike bulalan Mama tai a Fusace
"Haba Mallan, Wannan Wane irin rashin imani neh, wanne tabbaci kake dashi na cewa ita tadau maka kudi"
Huci sosai Baffa Yake
"Sakar min Bulalan nan Saratu, Yayana basa Sata, Saida Wannan Yar Iskan Yarinyan ki sakar min Bulala nace"
Bazan Saki bah, mallan Kaji Tsoron Allah"
Wani Tsawa ya saki tareda Fizge bulalan Daga Hannun Mama, Rusunawa Ameenatu tai tana Kuka tareda Rokon Baffa, Anma Ko Kallanta Beyi bah, Saida Ya duketa San Ranshi Sannan Ya Kyaleta. Kuka Sosai Sulthana take, Duk Jikinta ya Farfashe. Dakyar ta Mike Tsaye, ya Kalleta a Harzuk'e Ficemin Daga Gida Karna K'ara Ganinki a Gidan nan..

Kuka Sosai ta k'ara Fashewa dashi tana bashi Hakuri, Binta yayi da Bulalan ta Falla a guje tabar Gidan ya koma Ciki ya rufe Kofa, Yana Shiga Yaga Mama ta fito Sanye da Hijabi, Ya kalleta da Mamaki, Ina Zaki?
"Gaskiya Mallan bazan cigaba da zama a gidan nan kana Azabtar da Yarinyan nan bah Na gaji Gaskiya"
Kafada Ya daga Tareda Cewa
"Idan Har kika fita kofar gidan nan tho ki sani a bakin Aurenki"
Ameenatu da har lokacin tak'e Tsugunne a Kasa tana Kuka ta dago ta Kalleshi da Mamaki...

*Ummy Abduol*✍🏻
[28/08, 01:12] Friend Hussaini: 💐💐💐💐💐💐💐💐
💐💐💐💐
*SULTHANA*
💐💐💐💐
💐💐💐💐💐💐💐💐

By *Ummy Abduol*

*Page 26 to 30*

Ameenatu da har lokacin tak'e tsugunne a kasa tana kuka ta dago ta kalleshi da mamaki
"Mallan Yanzu dah bakinka kake Fadin irin wannan maganan" cewar Mama Tsaki yayi batare da yace komai bah yayi shigewarshi dak'i
Dosar kofan fita Mama tai Ameenatu ta mik'e dasauri ta kamota tana cigaba da kuka
"Mama dan Allah karki tafi, kiyi Hakuri"
Hawaye ne ya gangaro a idon mama

"Na gaji da zama ana Azabtar da Yarinya ina kallo banida halin magana, Duk inda naji sai aita nunani ana gulmana mutane sai suyita tunanin ni nake wahalar da Sulthana"
Hawayen idonta Ameenatu ta Share
"Mama karki manta idan har kika fita kin saku, Dan Allah Mama karki fita kiyi Hakuri, Idan Kika fita Zamu Shiga wani hali"
Murmushin takaici Mama tai
"Ameenatu duba ki gani yanda ya Kori yarinyan nan da Daren nan, Ina Yake tunanin Zata? Yanda Kauyen nan Yakeda Hatsari kuma gata K'arama"
Shiru Ameenatu Tai nadan wani lokaci.

Sallaman Hafsatu sukaji ta shigo Gidan Rik'e da Bak'ar leda ganinsu Mama a tsaitsaye Yasa Ta K'araso kusa dasu
"Mama lapia meya Faru?"
Ameenatu ce ta shiga zaiyana mata duk abinda ya faru, Dan Murmushi tai tareda Girgiza Kai Sannan ta Kalli Mama
"Tho Mama mu ina ruwanmu, tunda ya koreta ai shiknan mun munma huta wallahi"
Tsaki Ameenatu taja
"Hafsatu kinada Matsala, Bansan Keh inda kikasa gaba a rayuwarki bah"
Turo baki tai ta kauda kai..

Mama ta dafa Kafadar Ameenatu
"Ameenatu kuje ku nemo Sulthana dan Allah, Kunga Dare neh Akwai hatsari"
Kara turo baki hafsatu tai tana Gungunai
"Ni Mama na Gaji Wallahi"
Tsawa mama ta daka Mata, Hijab Ameenatu ta koma ta dauko suka fito itada Kawarta Habiba suka Fita Hafsatu na Binsu a Baya, Sallama Habiba tama Ameenatu ta wuce gida, Ameenatu ta juya ta Kalli Hafsatu dake tafiya kamar wacce kwai ya fashema a ciki
"Haba Hafsatu ki dago kafa Mana Wai meye Haka"

Dogon Tsaki Hafsatu taja nifa Gaskiya Ya Ameenatu kun Takura min, Allah badan Mama ta matsaba bah Abinda zai kara fito dani da Dadaren nan. Girgiza kai Kawai Ameenatu tai ta cigaba da Tafiya tana haske hasken Hanya da Torch light..

Sulthana kuwa tana Fitowa Gudu kawai take batareda tasan inda ta nufa bah, Saida tai mai isarsa Sannan ta Samu guri ta zauna Tana kuka sosai mai Sauti, Kuka take kamar ranta zai Fita
"Umma meyasa kika tafi kika barni? Meyasa baki bari mun tafi tare bah. Ina sanki Umma, ina Kewanki"
Kuka ta cigaba dayi gwanin ban tausayi, duk ilahirin Jikinta zugi yake mata bin jikinta tai da K'allo taga duk Baffa ya fafasa mata jiki. Nan da nan jikinta yayi zafi, Idanunta suka fara Lumshewa. Kangon Ginin Kasan dak'e Gefenta Ta mik'e dakyar tana Ganin Jiri ta k'arasa ta Shiga Cikin Kangon ta zauna, Jin Jirin tai na K'aruwa ta lumshe ido da k'arfi ta Bude tareda Girgiza kai. A hankali ta Sulale a Wajan..

Bah Indah su Ameenatu basu jeh bah, Tun daga Gidan Kawayen Sulthana Har Wuraren dah suk'e zaton Zata Iya boyema, Anma bata bah Alamarta. Hankalin Ameenatu Yakai Kololuwa Wajan Tashi, Ganin Dare Yayi sosai Yasa Suka Koma Gida. A tsakar gida Suka samu Mama sai kaiwa da komowa take, Tana ganinsu ta K'araso dasauri
"Yaya kun Ganta?"
Kasa magana Ameenatu tai, Hafsatu ce ta Yatsine Fuska
"Duk inda Muke tunanin Za'a sameta munje bamu ganta bah"
Bata jirah mai Mama zatace bah ta Wuce dakinsu..

Kuka Ameenatu tahau yi a hankali Kanta a K'asa, Mama ta dafata itama hankali tashe,
"Kiyi Hakuri Ameenatu, Insha Allahu Za'a ganta jeki kwanta kinji"
Kai kawai tai k'arfin Halin Dagawa ta Nufi dakinsu jiki a Sanyaye...

Hasken daya Haska mata Fuska neh Yasa ta Bude ido dak'ar, Ganin Gari ya Waye Tangaran da Alamar Rana mah ta Farayi Yasa ta Mik'e Zaune Dakyar tana Yatsine Fuska. Wanne Irin Mugun Ciwo Kanta keh mata da duk ilahirin Jikinta, dakyar ta mik'e tsaye Ganin Har yanzu tana Jin Jiri Yasa ta koma ta Zauna Tana Hawaye a Hankali. Abubuwan da Suka Faru jiya suka Dawo mata, Kuka ta Fara Sosai Tareda Daura Hannayenta Biyu akai
"Umma Ki Dawo dan Allah, Ina Sanki meyasa zaki tafi ki Barni, Wallahi Baffa naso ya Kasheni. Dan Allah Umma ki dawo mu zauna tare, Kin Barni Cikin..."
Kukan neh Yaci Karfinta, Sulalewa tai ta kwanta Tana Shafa Ciyayin Dake Kasan wajan tana Cigaba da Kuka..

Ta dade a haka Sannan Ta daure ta Mik'e ta Fito daga kangon Tana tafiya Saboda Yanda Takejin Jikinta yana mata Ciwo. Duk inda Ta Wuce K'allanta ake, Sai Yanzu ta Tuna Koh Dan kwalli babu a kanta. Runtse ido tai wasu Sabbin Hawaye suka gangaro Mata, Direct Gidansu Sadiya Ta Wuce dan Duk Kauyen nan ita kadaice Tasan Zata iya Taimaka mata da Wani abun...

*Ummy Abduol*✍🏻
[28/08, 01:12] Friend Hussaini: 💐💐💐💐💐💐💐💐
💐💐💐💐
*SULTHANA*
💐💐💐💐
💐💐💐💐💐💐💐💐

By *Ummy Abduol*

*Page 31 to 35*

_kuyi min afuwa jina shiru da kukai, Hakan ya faru neh bisa Rashin Lapia danai. Anma Alhamdulillah naji sauqi, Nagode Sosai da Kulawarku a Kaina_

Dis page x 4 uh besty *Ayoosh Gidado Yar'adua "My Gidos"*

Direct Gidansu Sadiya ta wuce dan duk kauyen nan ita kadai tasan zata iya taimaka mata da wani abun. Dakyar ta karasa gidan ta Shiga da Sallama, A Tsakar gida ta Samu Sadiya tanayi ma Mamanta Sallama Zata tafi makaranta.
Juyowa tai ta K'alleta da Mamaki
"Sulthana! Daga ina kike? Jiya su Yaya Ameenatu nata nemanki"
Waje ta samu ta zauna a tsakar gidan tareda tafe kai, Dasauri Sadiya ta karaso inda take
"Mama! Mama!! Fito kiga Sulthana"
Mama da Baba suka fito a Tare dasauri,
"Lapia Sulthana meke Faruwa" cewar Mama
Kuka ta Fashe dashi Kanta a Kasa, Baban Sadiya neh ya K'alleta Cikeda tausaya wah
"Sulthana, Yi Magana Mana"
Kasa magana tai sai kukan data K'ara Fashewa dashi, Mama ta K'alli Baba tana nunamai Sulthana Hankali Tashe
"Mallan Kalli jikin Yarinyan nan, Duk yanda akai Duka Akai mata"
Sai a Sannan Baba ya lura da Raunukan dake Jikinta.
Chapter 3 · 0% Book details