Sashe 17
Sulthana Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Murmushi yayi yabi bayanta, kusa ita ya zauna yana k'allanta. Kauda kai tayi ya juyo da fuskanta. Hawaye ya gani na gangarowa daga idonta
"Omg! Haba Beauty meya faru? Meyasa kike kuka"
Ai kaman jira take ta fashe da kuka harda shesheka, kanshi ya dafa
"Pls stop crying banasan kukanki beauty"
Hankie ya dauko ya soma goge mata hawayen dake fuskanta yana murmushi
"Me aka miki kike kuka?"
Zumburo baki tai
"Bakai baneh ka daina zuwa bah kullum sai nazo nan ina jiranka"
Kallanta yayi da Mamaki
"Kinyi kewana neh?"
Hannu tasa ta rufe fuskanta tana murmushi, shima murmushin yake cikeda Farinciki
"Oh come on! Fadamin kinyi kewana?"
Kai ta gyada mai, murmushi yayi mai sauti
"Nima nayi kewanki beauty, idan natambayeki wani abu zaki fadamin?"
Eh tace tana kallanshi, saida yayi jim sannan yace
"Kina sona?"
Dasauri ta mik'e tabar wajan tana dariya. Shima dariyan yayi kasa kasa, dakyar ya lallabata ta dawo ta zauna yace
"I so much love uh my beauty ina sanki sosai"
Hannayenta biyu tasa ta rufe fuskanta tana murmushi...
Shakuwa mai k'arfi ya k'ara shiga tsakaninsu, har Mami da daddy sun saba da hiran Sulthana da Masroor ke musu kullum. Lokaci nata tafiya, har yanzu bah abinda ya chanza dangane da k'iyayar da Baffa kema Sulthana...
*Bayan wata d'aya*
Alhamdulillah anyi Election Allah yaba Daddy sa'a yanxu shine gwamnan Jahar Kano, Alhaji shuaibu mahaifin Fareed shine mataimakinshi. Bayan komawansu government house Masroor ya matsama Mami akan zuwa gidansu Sulthana saboda nan da sati d'aya zai koma school, Mami na samun Daddy da maganan yace
"Nima abin na raina mantawa nai ban fada miki bah, gobe in Allah ya kaimu za'aje nema mai aurenta"
*tho fah* anya kuwa?
Ummy Abduol✍🏻
[28/08, 01:12] Friend Hussaini: 💐💐💐💐💐💐💐💐
💐💐💐💐
*SULTHANA*
💐💐💐💐
💐💐💐💐💐💐💐💐
By *Ummy Abduol*
*DA BAZARMU WRITERS ASSOCIATION*
*Page 146 to 150*
*Masroor Fans* Wannan shafin naku neh... fatan Alheri gareki *Hajiya Fateema* kinfi kowa san littafin ina godiya da soyaiyarki gareni.
"Nima abin na raina mantawa nai ban fada miki bah, gode in Allah ya kaimu za'aje nema mai aurenta"
Dad'i sosai Mami taji ai dasauri ta fita ta k'ira Masroor a waya Tareda fadamai Albishir. Murna wajan Masroor ba'a magana suna gama wayan ya kira yasir ya sanar dashi lokacin shi yana hanyar zuwa wajan Fareed dan kwanakin nan da akai election tare suketa shige da fice hakan yasa suka k'ara sabawa sosai..
Yana isa Asibitin yamai waya ya sanar dashi isowarsa. Fitowa Fareed yayi yana murmushi
"Old friend na d'auka fah wasa kakemin"
D'an dariya Masroor yayi yana shafa suman kanshi
"Ai nafika zumunci"
Hannu Fareed ya mik'a mai suka tafa suna dariya
"Kaji talle kema audi gori, duk bah wannan bah friend. Naga sai annashuwa kakene fadamin meya faru?"
K'ayattacen murmushi Masroor yayi
"Gobe in Allah ya kaimu za'aje nema min aure"
"Woaw" Fareed yace cikeda farinciki
"Who is dis lucky beb"
Masroor ya girgiza kai
"Sunanta su...koda yake zaka ganta wata rana da kanta zata fadama sunanta"
Hannu Fareed ya mik'a mai
"I'm very happy 4 uh Friend, Allah ya kaimu musha biki"
"Ameen, tho kaifa yaushe ne nakan?" cewar Masroor
Ajiyan zuciya Fareed ya sauke
"Nikam bah yanzu bah"
Da mamaki Masroor ya kalleshi
"Why?"
Juyowa Fareed yayi yana fuskantan Masroor
"Wata yarinya na gani shes young n beautiful. Saidai yarinyan na cikin Matsala infact namadai je naga mahaifinta yak'i amincewa"
Gaban Masroor neh ya ya fadi. Zuciyarshi ta shiga zargin kodai shine wanda sulthana take fada mishi likitan dayaje nemanta. Dagowa yayi da Alamar damuwa
"Y'ar wacece aina take?"
Murmushin takaici Fareed yayi yana girgiza kai
"Bah y'ar kowa bace, a kauye ma suke."
Kan Masroor neh ya soma sara mai, juyawa kawai yayi fareed ya matso yace
"A'a Old friend bamu gama hiran bafa ina kuma zaka?"
Da hannu ya nunama Fareed kanshi dak'yar ya iya cewa
"Gida zani kaina ke ciwo"
Bai jira mai fareed din zaice bah ya figi mota yabar Asibitin da sauri ya nufi gida...
Hankali tashe ya k'arasa gida, side dinshi ya wuce kai tsaye bai kuma fitowa bah har washe gari...
Safiyar Ranar lahadi da wuri Abokanan daddy su biyu suka shirya Yasir ya musu jagora zuwa k'auyensu Sulthana. Kasancewar bai taba zuwa bah da kwatance Suka gane gidan, a kofar gidansu sukai Parking motarsu. Mallan na ganin Katuwar mota ya mik'e dasauri ya fito daga runfar Almajiransu..
Yasir ne ya fito ya k'arasa suka gaisa da Mallan sannan ya fada mai tareda baki suke. Nan da nan Mallan yahau washe baki ganin mutanen da suka fito daga motan daga gani bah k'ananan mutane baneh..
Tabarma ya dauko ya shimfida suka zazzauna, Mallan ya soma gaidasu suka amsa, d'aya daga cikinsu ne ya fara magana
"Sunana Alhaji ilyasu sai kuma abokina Alhaji Tanimu, daga Cikin Gari muke. Alhaji Aminu Datty gwamna maici yanzu shine ya turo mu dan mu naima ma d'anshi auren Y'arka"
Nan da nan Mallan ya rud'e,
"Anya bayin Allah ni kuwa Mallan Jamilu?"
Alhaji Tanimu yayi Murmushi ganin Yanda ya rud'e
"Kwarai kai"
Gyara zama yayi jikinshi na rawa
"Wacce daga ciki Ameenatu koh Hafsatu?"
Yasir dake gefe yace
"Sulthana"
Had'e rai Mallan yayi baice komai bah, ganin yanda ya sauya fuska yasa Alhaji ilyasu cewa
"Koh Akwai damuwa neh"
Dagowa yayi ya kallesu d'aya bayan d'aya sannan ya bud'e baki ya fara magana
"A gaskiya bazan cuceku bah, saboda d'an babban gida kaman wannan bai kamata na rufeshi bah"
Shiru yayi na wasu lokuta, Alhaji tanimu yace
"Mallan muna jinka"
Abinda Mallan ya fadane yasa ni Ummy Abduol na mik'e dasauri har saida Wayata ta fadi garin fargana
" *A Gaskiya banine uban Sulthana bah, Sulthana shegiya ce batada Ubah*"
Tabdi Jam!...
Kuyi Managing wannan
Ummy Abduol✍🏻
[28/08, 01:12] Friend Hussaini: 💐💐💐💐💐💐💐💐
💐💐💐💐
*SULTHANA*
💐💐💐💐
💐💐💐💐💐💐💐💐
By *Ummy Abduol*
*DA BAZARMU WRITERS ASSOCIATION*
*Page 151 to 155*
"A gaskiya banine uban Sulthana bah, Sulthana shegiya ce batada ubah"
Mikewa Yasir yayi dasauri yana nuna Mallan da Yatsa
"Mallan k'iyayar da kakema y'arka har takai haka? Kace bakai ka haifeta bah"
Alhaji tanimu ya had'e rai yana k'allan Yasir
"Wanne irin rashin hankali neh wannan? Wayasa bakinka a maganan nan"
Zama Yasir yayi yana huci ranshi bace. Alhaji tanimu ya maida dubansa ga Mallan fuskanshi bah walwala
"Tho Mallan tunda kace bakai baneh ka haifeta, tho ina mahaifinta yake"
Mallan ya yatsine fuska
"Bansan inda Mahaifinta yake bah, kawai dai ni rik'onta nake"
Mikewa Alhaji ilyasu yayi, Alhaji tanimu ma ya mik'e yana cewa
"Mun gode Mallan mu zamu tafi"
Baice musu komai bah suka kakkabe babban rigansu suka shigaa mota Yasir yajasu suka bar kauyen kowa ransh b'ace..
Yanmacin ranar Sulthana tadau gyadanta kamar yanda ta saba, Bakin tasha ta nufa ko kamin ta k'arasa ta hango motar Masroor pake a inda suka saba zama, da sauri ta k'arasa tana murmushi. Ta mirrown motan ya hangota zuwa ya fito dasauri ya nufeta yana huci
"Dama labarinda kika fadamin duk k'arya neh Sulthana? Ke ashe shegiya ce bakida uba"
Trayn kanta neh ya fadi ta k'walallo ido tana kallanshi da Mamaki, cigaba yayi da Magana cikin kakkausan Murya
"Kin cuceni Sulthana, dama duk abinda kika fadamin k'arya neh? Duk sanda nake miki? Duk lokacinda na bata akanki"
Tsugunawa Sulthana tai ta fasa ihu tareda daura hannu aka
"Yaya Masroor waya fadama wannan maganan? Wallahi k'arya neh Baffa shine Babana"
Ranshi b'ace ya juya Mata baya
"Shi Baffan zai miki Karya neh? Haba Sulthana Kinsa Mahaifina dani munji kunya, why Sulthana why?? Nasan baki sani bah Mahaifina neh Gwamna mai ci yanzu Alhaji Aminu"
Dagowa tayi da Mamaki tana K'allanshi
"Danasan Abinda zai faru knan daban bari Aminan mahaifina sunzo bah. Yanzu da wani ido zan kalli Daddy nah?"
Kuka sosai Sulthana take Hankalinta tashe
"Dan Allaha yaya Masroor karka gujeni, kai kad'ai ke sona kake tausaya min. Idan ka tafi ya zanyi"
Tsugunawa Yayi kusada ita zuciya na cinshi
"Sulthana Bazan iya bah"
Bai jira mai zatace bah ya shiga mota ya bar wajan a guje. Kuka ta k'ara fashewa dashi kamar ranta xai fita, hakanan ta d'au trayn gyadan ta nufo gida tana cigaba da kuka.
Zaure ta zauna ta cigaba da kukanta, saida tai mai tsarta Sannan ta mik'e rai bace ta shiga cikin gidan. Zaune ta samu duka y'an gidan a k'atuwar tabarma da Alama iska suk'e sha. Karasawa tai ta aje trayn a gaban Baffa ta tsugunna akan tabarman k'anta a kasa ta fara magana
"Baffa mai nai maka ka tsaneni baka sona? Idan na maka laifi neh kai hakuri. Meyasa kace bakai ka haifeni bah"
Da mamaki Mama ta k'alli Mallan Gabanta na faduwa
"Mallan Abinda Sulthana ta fada Gaskiya neh"
Tsaki yayi tareda kauda kai
"Hakaneh mana, bazai yuwu bah ace d'an gwamna guda yazo neman aurenta batareda na fadamai abinda ke faruwa bah. Tho yau ku shaida zan amayar da Abinda yake cikina"
Hafsatu ta mik'e dasauri tareda dafe k'irji
"Dan gwamna"
Daga kai Mallan yayi yana k'allan Hafsatu
"Kwarai kuwa"
Hankalin Ameenatu neh ya tashi tace
"Baffa muna jinka me kace zaka fada"
Sulthana ya nuna da Hannu yana cewa
"Sulthana bah y'ata bace, Shegiya ce batada uba. Cikin Shege uwarta tai ta haifeta"
Ihu Sulthana ta saki ta mik'e Dasauri ta daura hannu a kai ta fashe da kuka, rasa inda zatasa kanta tai ta dawo gaban Mallan ta tsugunna tana kuka sosai
"Baffa kai hakuri karka ce haka, ni yarinyanka ce haka Umma tace"
Tsaki yayi
"Karya umman naki takeyi, niba ubanki baneh"
Mutuwar Zaune Mama tai itada Ameenatu, Hafsatu ko cewa take
"Ashe gado tai, shiyasa itama take bin maza. Lallai gwara Baffa daka fadamana"
Kamar mahaukaciya Sulthana ta zama a cikin gidan, ihu kawai take tana kuka kwi kwi. Mama tai k'arfin Halin cewa
"Tunda nake ko a tarihan da mahaifana suka bani ban tabajin inda Uba yakema Y'arshi hakaba sai kai. Kaicona da aurenka Mallan"
Mik'ewa Mallan yayi yana huci
"Ni kike jifa da irin Wadannan Kalaman?"
Kauda kai Mama tai Ranta bace. Baffa ya dakama Sulthana Tsawa yanacewa
"Tunda abin naki ya zama haka maza ki tattara inaki inaki ki tafi ki nemi ubanki. Kada ki kuskura na fito daki na ganki a cikin gidan nan"
"Omg! Haba Beauty meya faru? Meyasa kike kuka"
Ai kaman jira take ta fashe da kuka harda shesheka, kanshi ya dafa
"Pls stop crying banasan kukanki beauty"
Hankie ya dauko ya soma goge mata hawayen dake fuskanta yana murmushi
"Me aka miki kike kuka?"
Zumburo baki tai
"Bakai baneh ka daina zuwa bah kullum sai nazo nan ina jiranka"
Kallanta yayi da Mamaki
"Kinyi kewana neh?"
Hannu tasa ta rufe fuskanta tana murmushi, shima murmushin yake cikeda Farinciki
"Oh come on! Fadamin kinyi kewana?"
Kai ta gyada mai, murmushi yayi mai sauti
"Nima nayi kewanki beauty, idan natambayeki wani abu zaki fadamin?"
Eh tace tana kallanshi, saida yayi jim sannan yace
"Kina sona?"
Dasauri ta mik'e tabar wajan tana dariya. Shima dariyan yayi kasa kasa, dakyar ya lallabata ta dawo ta zauna yace
"I so much love uh my beauty ina sanki sosai"
Hannayenta biyu tasa ta rufe fuskanta tana murmushi...
Shakuwa mai k'arfi ya k'ara shiga tsakaninsu, har Mami da daddy sun saba da hiran Sulthana da Masroor ke musu kullum. Lokaci nata tafiya, har yanzu bah abinda ya chanza dangane da k'iyayar da Baffa kema Sulthana...
*Bayan wata d'aya*
Alhamdulillah anyi Election Allah yaba Daddy sa'a yanxu shine gwamnan Jahar Kano, Alhaji shuaibu mahaifin Fareed shine mataimakinshi. Bayan komawansu government house Masroor ya matsama Mami akan zuwa gidansu Sulthana saboda nan da sati d'aya zai koma school, Mami na samun Daddy da maganan yace
"Nima abin na raina mantawa nai ban fada miki bah, gobe in Allah ya kaimu za'aje nema mai aurenta"
*tho fah* anya kuwa?
Ummy Abduol✍🏻
[28/08, 01:12] Friend Hussaini: 💐💐💐💐💐💐💐💐
💐💐💐💐
*SULTHANA*
💐💐💐💐
💐💐💐💐💐💐💐💐
By *Ummy Abduol*
*DA BAZARMU WRITERS ASSOCIATION*
*Page 146 to 150*
*Masroor Fans* Wannan shafin naku neh... fatan Alheri gareki *Hajiya Fateema* kinfi kowa san littafin ina godiya da soyaiyarki gareni.
"Nima abin na raina mantawa nai ban fada miki bah, gode in Allah ya kaimu za'aje nema mai aurenta"
Dad'i sosai Mami taji ai dasauri ta fita ta k'ira Masroor a waya Tareda fadamai Albishir. Murna wajan Masroor ba'a magana suna gama wayan ya kira yasir ya sanar dashi lokacin shi yana hanyar zuwa wajan Fareed dan kwanakin nan da akai election tare suketa shige da fice hakan yasa suka k'ara sabawa sosai..
Yana isa Asibitin yamai waya ya sanar dashi isowarsa. Fitowa Fareed yayi yana murmushi
"Old friend na d'auka fah wasa kakemin"
D'an dariya Masroor yayi yana shafa suman kanshi
"Ai nafika zumunci"
Hannu Fareed ya mik'a mai suka tafa suna dariya
"Kaji talle kema audi gori, duk bah wannan bah friend. Naga sai annashuwa kakene fadamin meya faru?"
K'ayattacen murmushi Masroor yayi
"Gobe in Allah ya kaimu za'aje nema min aure"
"Woaw" Fareed yace cikeda farinciki
"Who is dis lucky beb"
Masroor ya girgiza kai
"Sunanta su...koda yake zaka ganta wata rana da kanta zata fadama sunanta"
Hannu Fareed ya mik'a mai
"I'm very happy 4 uh Friend, Allah ya kaimu musha biki"
"Ameen, tho kaifa yaushe ne nakan?" cewar Masroor
Ajiyan zuciya Fareed ya sauke
"Nikam bah yanzu bah"
Da mamaki Masroor ya kalleshi
"Why?"
Juyowa Fareed yayi yana fuskantan Masroor
"Wata yarinya na gani shes young n beautiful. Saidai yarinyan na cikin Matsala infact namadai je naga mahaifinta yak'i amincewa"
Gaban Masroor neh ya ya fadi. Zuciyarshi ta shiga zargin kodai shine wanda sulthana take fada mishi likitan dayaje nemanta. Dagowa yayi da Alamar damuwa
"Y'ar wacece aina take?"
Murmushin takaici Fareed yayi yana girgiza kai
"Bah y'ar kowa bace, a kauye ma suke."
Kan Masroor neh ya soma sara mai, juyawa kawai yayi fareed ya matso yace
"A'a Old friend bamu gama hiran bafa ina kuma zaka?"
Da hannu ya nunama Fareed kanshi dak'yar ya iya cewa
"Gida zani kaina ke ciwo"
Bai jira mai fareed din zaice bah ya figi mota yabar Asibitin da sauri ya nufi gida...
Hankali tashe ya k'arasa gida, side dinshi ya wuce kai tsaye bai kuma fitowa bah har washe gari...
Safiyar Ranar lahadi da wuri Abokanan daddy su biyu suka shirya Yasir ya musu jagora zuwa k'auyensu Sulthana. Kasancewar bai taba zuwa bah da kwatance Suka gane gidan, a kofar gidansu sukai Parking motarsu. Mallan na ganin Katuwar mota ya mik'e dasauri ya fito daga runfar Almajiransu..
Yasir ne ya fito ya k'arasa suka gaisa da Mallan sannan ya fada mai tareda baki suke. Nan da nan Mallan yahau washe baki ganin mutanen da suka fito daga motan daga gani bah k'ananan mutane baneh..
Tabarma ya dauko ya shimfida suka zazzauna, Mallan ya soma gaidasu suka amsa, d'aya daga cikinsu ne ya fara magana
"Sunana Alhaji ilyasu sai kuma abokina Alhaji Tanimu, daga Cikin Gari muke. Alhaji Aminu Datty gwamna maici yanzu shine ya turo mu dan mu naima ma d'anshi auren Y'arka"
Nan da nan Mallan ya rud'e,
"Anya bayin Allah ni kuwa Mallan Jamilu?"
Alhaji Tanimu yayi Murmushi ganin Yanda ya rud'e
"Kwarai kai"
Gyara zama yayi jikinshi na rawa
"Wacce daga ciki Ameenatu koh Hafsatu?"
Yasir dake gefe yace
"Sulthana"
Had'e rai Mallan yayi baice komai bah, ganin yanda ya sauya fuska yasa Alhaji ilyasu cewa
"Koh Akwai damuwa neh"
Dagowa yayi ya kallesu d'aya bayan d'aya sannan ya bud'e baki ya fara magana
"A gaskiya bazan cuceku bah, saboda d'an babban gida kaman wannan bai kamata na rufeshi bah"
Shiru yayi na wasu lokuta, Alhaji tanimu yace
"Mallan muna jinka"
Abinda Mallan ya fadane yasa ni Ummy Abduol na mik'e dasauri har saida Wayata ta fadi garin fargana
" *A Gaskiya banine uban Sulthana bah, Sulthana shegiya ce batada Ubah*"
Tabdi Jam!...
Kuyi Managing wannan
Ummy Abduol✍🏻
[28/08, 01:12] Friend Hussaini: 💐💐💐💐💐💐💐💐
💐💐💐💐
*SULTHANA*
💐💐💐💐
💐💐💐💐💐💐💐💐
By *Ummy Abduol*
*DA BAZARMU WRITERS ASSOCIATION*
*Page 151 to 155*
"A gaskiya banine uban Sulthana bah, Sulthana shegiya ce batada ubah"
Mikewa Yasir yayi dasauri yana nuna Mallan da Yatsa
"Mallan k'iyayar da kakema y'arka har takai haka? Kace bakai ka haifeta bah"
Alhaji tanimu ya had'e rai yana k'allan Yasir
"Wanne irin rashin hankali neh wannan? Wayasa bakinka a maganan nan"
Zama Yasir yayi yana huci ranshi bace. Alhaji tanimu ya maida dubansa ga Mallan fuskanshi bah walwala
"Tho Mallan tunda kace bakai baneh ka haifeta, tho ina mahaifinta yake"
Mallan ya yatsine fuska
"Bansan inda Mahaifinta yake bah, kawai dai ni rik'onta nake"
Mikewa Alhaji ilyasu yayi, Alhaji tanimu ma ya mik'e yana cewa
"Mun gode Mallan mu zamu tafi"
Baice musu komai bah suka kakkabe babban rigansu suka shigaa mota Yasir yajasu suka bar kauyen kowa ransh b'ace..
Yanmacin ranar Sulthana tadau gyadanta kamar yanda ta saba, Bakin tasha ta nufa ko kamin ta k'arasa ta hango motar Masroor pake a inda suka saba zama, da sauri ta k'arasa tana murmushi. Ta mirrown motan ya hangota zuwa ya fito dasauri ya nufeta yana huci
"Dama labarinda kika fadamin duk k'arya neh Sulthana? Ke ashe shegiya ce bakida uba"
Trayn kanta neh ya fadi ta k'walallo ido tana kallanshi da Mamaki, cigaba yayi da Magana cikin kakkausan Murya
"Kin cuceni Sulthana, dama duk abinda kika fadamin k'arya neh? Duk sanda nake miki? Duk lokacinda na bata akanki"
Tsugunawa Sulthana tai ta fasa ihu tareda daura hannu aka
"Yaya Masroor waya fadama wannan maganan? Wallahi k'arya neh Baffa shine Babana"
Ranshi b'ace ya juya Mata baya
"Shi Baffan zai miki Karya neh? Haba Sulthana Kinsa Mahaifina dani munji kunya, why Sulthana why?? Nasan baki sani bah Mahaifina neh Gwamna mai ci yanzu Alhaji Aminu"
Dagowa tayi da Mamaki tana K'allanshi
"Danasan Abinda zai faru knan daban bari Aminan mahaifina sunzo bah. Yanzu da wani ido zan kalli Daddy nah?"
Kuka sosai Sulthana take Hankalinta tashe
"Dan Allaha yaya Masroor karka gujeni, kai kad'ai ke sona kake tausaya min. Idan ka tafi ya zanyi"
Tsugunawa Yayi kusada ita zuciya na cinshi
"Sulthana Bazan iya bah"
Bai jira mai zatace bah ya shiga mota ya bar wajan a guje. Kuka ta k'ara fashewa dashi kamar ranta xai fita, hakanan ta d'au trayn gyadan ta nufo gida tana cigaba da kuka.
Zaure ta zauna ta cigaba da kukanta, saida tai mai tsarta Sannan ta mik'e rai bace ta shiga cikin gidan. Zaune ta samu duka y'an gidan a k'atuwar tabarma da Alama iska suk'e sha. Karasawa tai ta aje trayn a gaban Baffa ta tsugunna akan tabarman k'anta a kasa ta fara magana
"Baffa mai nai maka ka tsaneni baka sona? Idan na maka laifi neh kai hakuri. Meyasa kace bakai ka haifeni bah"
Da mamaki Mama ta k'alli Mallan Gabanta na faduwa
"Mallan Abinda Sulthana ta fada Gaskiya neh"
Tsaki yayi tareda kauda kai
"Hakaneh mana, bazai yuwu bah ace d'an gwamna guda yazo neman aurenta batareda na fadamai abinda ke faruwa bah. Tho yau ku shaida zan amayar da Abinda yake cikina"
Hafsatu ta mik'e dasauri tareda dafe k'irji
"Dan gwamna"
Daga kai Mallan yayi yana k'allan Hafsatu
"Kwarai kuwa"
Hankalin Ameenatu neh ya tashi tace
"Baffa muna jinka me kace zaka fada"
Sulthana ya nuna da Hannu yana cewa
"Sulthana bah y'ata bace, Shegiya ce batada uba. Cikin Shege uwarta tai ta haifeta"
Ihu Sulthana ta saki ta mik'e Dasauri ta daura hannu a kai ta fashe da kuka, rasa inda zatasa kanta tai ta dawo gaban Mallan ta tsugunna tana kuka sosai
"Baffa kai hakuri karka ce haka, ni yarinyanka ce haka Umma tace"
Tsaki yayi
"Karya umman naki takeyi, niba ubanki baneh"
Mutuwar Zaune Mama tai itada Ameenatu, Hafsatu ko cewa take
"Ashe gado tai, shiyasa itama take bin maza. Lallai gwara Baffa daka fadamana"
Kamar mahaukaciya Sulthana ta zama a cikin gidan, ihu kawai take tana kuka kwi kwi. Mama tai k'arfin Halin cewa
"Tunda nake ko a tarihan da mahaifana suka bani ban tabajin inda Uba yakema Y'arshi hakaba sai kai. Kaicona da aurenka Mallan"
Mik'ewa Mallan yayi yana huci
"Ni kike jifa da irin Wadannan Kalaman?"
Kauda kai Mama tai Ranta bace. Baffa ya dakama Sulthana Tsawa yanacewa
"Tunda abin naki ya zama haka maza ki tattara inaki inaki ki tafi ki nemi ubanki. Kada ki kuskura na fito daki na ganki a cikin gidan nan"