← Book details Sulthana Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 26 OF 28

Sashe 26

Sulthana Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

DA BAZARMU WRITERS ASSOCIATION

*Page 198*

Su Masroor kuwa suna chan gefe zaune sunyi jugum jugum kowa da abinda yake sakawa a ranshi sannan Abba ya gyara zama yaba Baffa labarin Soyaiyar dake tsakanin Sulthana da y'ayansu sanna ya d'aura da cewa

"Dole yanzu zamu kirata neh ta zaba wanda takeso a cikinsu"

Baffa ya b'ata rai

"Haba ranka ya dad'e ai duk wannan bai taso bah, kuma fah iyayenta neh ku da kanku kawai ku zaba mata wanda zata aura"

Daddy yayi murmushi yana k'allan Baffa

"Aa baza'ayi haka bah, idan mukai haka kamar mun tauyeta neh. Tho idan kuma muka zaba mata wanda ita bai kwanta mata bafa?"

Shiru Baffa yayi baice komai bah. Abba yad'au waya ya kira Umma yace su fito duka, duk suka fito daga dakin Mama itada Mami suka zauna k'an tabarman. Baffa Yacema Mama ta kira Sulthana tace tho

Dakin ta shiga ta kirata suka taho tare, koda sukazo sun samu Fareed da Masroor xaune a wajan. Kusada Mami ta zauna k'anta a kasa, Abba ya kalleta da fara'a

"Y'ata mun kiraki neh dan muji ra'ayinki. Munaso ki fada mana tsakanin Masroor da Fareed wa kikeso"

Gabanta neh ya fadi ta d'ago ta kalli Masroor taga kanshi a kasa ta maida dubanta ga Fareed shima kanshi a kasa. Kasa magana tayi gabanta na cigaba da bugawa. Mami ta tabota

"Sulthana kiyi Magana mana karkiji Tsoro ki Fada abinda ke ranki"

Shiru tayi nad'an mintina Sannan tad'an dago bakinta na rawa tace

"Ya Fa..."

Dasauri Fareed ya d'ago ya kalleta da Alamar Mamaki, Masroor ko runtse idonshi yayi zuciyarshi na bugawa da sauri. Umman Fareed tace

"Kiyi Magana mana Sulthana keh muke jira"

Ta maza tayi ta saukar dakanta kasa tace

"Yah Masroor"

Sauke kai Fareed yayi yana girgixa kai ahankali, dasauri ta tashi tabar wajan. Abba yace

"Tho Alhamdulillah tunda yarinya ta fadi wanda takeso yanzu sai ayi maganan sadaki koh"

Su Umma najin haka suka mik'e suka bar wajan, Su Fareed suma suka mik'e suka fita waje. Fareed ya share hawayen idonshi yace

"I'm very sorry friend"

Ya mik'ama Masroor hannu yace

"Congratulations am very happy for you, Allah ya sanya Alheri"

Jikin Masroor neh yayi sanyi shima ya mik'amai hannu

"Ni yakamata nabaka hakuri, bakai bah"

Fareed ya girgixa kai ya shiga mota ya zauna ya daura kanshi jikin stering motan ranshi jagule..

Sulthana na shiga d'akinsu ta fada kan gado ta fashe da kuka, Ameenatu ce ta dafata tana cewa

"Meke faruwa Sulthana?"

Mik'ewa zaune tayi hawaye chabe chabe a idonta, tace

"Bansan da wani ido ya Fareed zai kalleni bah. Gani nake kamar namai Butulci"

Hafsatu ta dafata tana Murmushi

"Mahnoor ta mana bayanin komai, kuma bakida laifi saboda bai sanar dake bah Sannan kuma na lura bah wai sanki yake bah tausayinki neh"

Sulthana ta k'ura mata ido da Mamaki, gyada mata kai Hafsatu tayi sannan ta juya ta Kalli Ameenatu wacce itama su take kallo ta juya ta maida dubanta ga Sulthana tace

"Ya Ameenatu ta dad'e tanasan Likitan nan, tun sanda ta soma ganinshi ta fara sanshi, kullum sai tayi min maganar shi."

Mik'ewa Ameenatu tayi rai b'ace

"Baki kyautamin bah Hafsatu Ashe bazaki iya rik'emin d'an sirrin nan dana baki bah"

Murmushi Sulthana tayi ta share hawayen Fuskanta ta mik'e ta fito tsakar gidan, ganin su Fareed basa wajan yasa tasa takalmanta ta fita kofar gida. Zaune ta sameshi cikin mota shida Masroor suna hira jefi jefi, nesa dasu ta tsaya Masroor na ganinta ya fito ya karaso inda take yana murmushi

"Har na cire rai Beauty, sai gashi nine gwaninki"

Hannu yasa ta rufe fuskanta tana dariya

"Dan Allah ya Masroor inaso nayi magana da Ya Fareed"

Murmushi ya mata

"Bbu komai ki sameshi a mota"

Dariyan jindadi tayi

"Thank uh Bro Masroor"

Da Sassarfa ta k'arasa bakin motan ta bud'e ta shiga tana Kallanshi

"Ya Fareed kayi hakuri dan Allah"

Sai a Sannan ya d'ago ya kalleta tareda k'irkiro Murmushi

"Bakimin komai bah Queen, Laifina neh da ban fadamiki tun tuni bah naiyi zurfin ciki, haka Allah yaso. Allah ya nufa ke bah Matata bace"

D'an dukar dakai tayi tana wasa da zoben dake hannunta tace

"Nagode ya Fareed, bazan t'aba mantawa dakaiba a rayuwata. Kayimin Abubuwa da dama wanda banida bakin godiya, ka taka muhimmiyar rawa a rayuwata thank uh v...."

Saurin katseta yayi ya d'aura yatsanshi a lebenshi

"Uh dn't have to thank me"

Jim tayi nad'an wani lokaci sannan tace

"Ya Fareed akwai wani abu danakeso kayimin dan Allah"

Batareda wani bata lokaci bah yace

"Menene shi Queen?"

Tacigaba da cewa

"Inaso dan Allah Ya Fareed ka auri ya Ameenatu"

Dasauri ya juyo yana kallanta da mamaki, gyada mai kai tayi tana y'ar murmushi. Kasumbar dake fuskanshi ya shafa

"Ita tace miki tana sona?"

Girgiza kai tayi alamar Aa. Ya numfasa yace

"But queen I have no feelings for ha, and zai iya yuwuwa bata sona. Kawai ki barshi nagode"

Ta turo baki ta soma gungunai

"Nidai Dan Allah Ya Fareed ka aureta, shes kind kuma batada matsala. Nasan zata soka and kuma kagani zaku saba"

Dariya yayi Mara sauti yana k'allanta kasa kasa, baisan ya musa mata kuma a ganinshi wannan karamci tamai and kuma bah lefi yarinyan tanada kyau Sam bata kamo k'afar Queen dinshi bah dukda ita b'akace.

Ya juyo da Fara'a kwamce kan Fuskanshi yace

"Shiknan Queen na Yarda"

Ihu ta saki tana dariya har saida Masroor ya K'ara sako wajan dasauri. Fitowa daga motan tayi ta shiga cikin gida da gudu. Dakyar suka shawo kan Ya Ameenatu ta fita wajan Fareed, a waya Sulthana ta fadama Masroor abinda ke faruwa, Yaji dadi sosai shima. Ameeantu da Fareed sun fahimci juna kuma har ya Amince zai aureta, su Daddy sunyi Mamaki sosai jin Maganan. Basu bar Kauyensu Sulthana bah saida aka tsaida Ranar Bikin Masroor da Sulthana sai Fareed da Ameenatu wata d'aya, Aka ba Baffa sadakinsu Dubu D'ari d'ari dan Baffa yace baison Asa Sadakin dayawa..

Mama ta rok'i Alfarman a bar mata Sulthana har zuwa ayi bikin. Baffa ya tambayi Sulthana ta amince batai Gardama bah, Masroor sam baiso haka bah bah yanda zaiyi hakanan ya hakura sukai musu Sallama suka tafi bayan Sun Cika Baffa da kudi. washe gari Mami ta turo Driver da Kayan Sawan Sulthana da Kayan Abinci dana sawa nasu Mama cike da Mota...

Kula Sosai Sulthana take samu a gidan Mahaifinta ta bangaren Mama da Baffa har takan rasa wayafi kula da ita. Kullum suna Makalle da Masroor a waya haka soyaiya Suke mai Tsafta da Shiga rai. Fareed na Xuwa wajan Ameenatu hakan yasa suka k'ara shakuwa da ita, ya sai mata waya itada Hafsatu. Shima Masroor na xuwa shida Yasir..

Mama ta zage tanata gyara Y'ayan nata daidai karfinta, Mami ma Tana aiko Mahnoor da Wasu kayan gyaran jikin anaba Mama dan tayi Musu. Yau Saura kwana biyar Biki, Yau Sulthana take expecting Mahnoor dan tace mata zatazo har a gama biki. Tana gidansu Sadiya K'awarta Wayan Sulthana yahau Ruri, ta d'auka da Fara'a tana cewa

"Kin iso neh"

Harta mik'e ta koma ta zauna tace

"Yah Hafsatu tana Nan kice ta kawoki"

Bata jira mai zatace bah ta kashe kiran. Sadiya dake gefenta tace

"Ta iso neh?"

Da Fara'a tace

"Eh wai da lefe suka zo"

Dariya Sadiya tayi ta mik'e dasauri

"Ah bari muje muga Lefe"

Tab'e baki Sulthana tayi sadiya tad'au mayafinta ta fita daga gidan dasauri. Tana fita Mahnoor ta shigo gidan itada ya Ameenatu, sulthana ta mik'e dasauri ta rungumeta tana Dariya

"Uh welcome"

Dagota Mahnoor tayi daga jikinta tana k'are mata kallo

"Friend kinga yanda kika koma? Kin K'ara kyau sosai"

Turo baki Sulthana tayi tana doka kafa a kasa. Nan suka zauna suka soma hiran yanda bikin zai kasance basu bar gidan bah sai Yanma lis lokacin sun tabbatar yan kawo lefe sun tafi..

Ummy Abduol✍🏻

💐💐💐💐💐💐💐💐
💐💐💐💐
*SULTHANA*
💐💐💐💐
💐💐💐💐💐💐💐💐

By *Ummy Abduol*

DA BAZARMU WRITERS ASSOCIATION

*Page 199*

Lefe na gani na Fada aka kawo kowaccen su akwati dozin biyu akai mata. Mutanen Kauyen sai shiga suke suna kallan kaya kowa na tofa Albarkacin bakinshi..

Ranar Alhamis Ameenatu da kawayenta Sukayi k'auye day, su kuma su Sulthana dukayi Fulani day itama itada nata k'awayen. Ranar Juma'a aka sasu Lalle da daddare. A Daren Masroor da Fareed sai d'an rakiyansu Yasir dukazo gidan, a tare amaren suka fito kowacce ta k'araso wajan angon nata. Masroor sai Kallan Sulthana yake da Murmushi

"Beauty kin k'ara kyau meye sirrin?"

Rufe fuskanta tayi da Hannayenda da sukasha had'adden kunshi. Ya rik'o hannunta yana kallo yace

"Waya miki wannan design din yayi kyau sosai"

D'an murmushi tayi ta turo baki

"Ya Masroor ka daina wannan maganan kanasa inajin kunya"

Dariya yayi yana shafa sumar kanshi

"Ki daina jin kunyana beauty, nidake yanzu mun zama d'aya karki manta gobe za'a daura mana aure ki zama tawa na xama taki"

Hannu tasa ta rufe fuskanta tana dariya K'asa kasa, daidai nan Yasir ya karaso wajan yace

"Ni kun barni chan gefe"

Ya kalli Sulthana

"Madam kinsan meye?"

Ta girgiza kai tana kallanshi, ya gyara tsayuwa ya sassauta Murya

"Nifah Sistern nan naki nakeso"

Tace "wah kenan?"

Yace "Hafasat"

Da zumud'i tace

"Dagaske?"

Kai ya gyada Mata, Masroor yayi saurin cewa

"Dallah kyalle wannan, mayaudari neh karki yarda
kadama ki fadamata"

Duka Yasir yakaimai

"Kai bansan fah iskanci i'm serious"

Sulthana tace

"Karka damu Ya Yasir zansan Yanda zanyi"

Godiya ya mata yabar wajan. Sun d'an taba hira sannan suka musu Sallama Suka tafi..

Washe Gari ya kasance ranar Sati, a ranar duban mutane suka shaida d'aurin auren Fareed da Ameenatu, sai Masroor da Sulthana. D'aurin auren daya samu hallartar Manyan Mutane tun daga kan shi kanshi shugaban k'asa, Gwamnoni, sarakuna da saurayan Manyan mutane masu fada aji a nigeria..

Har hawaye saida Baffa yayi dan bai taba tunanin zaiga irin wadannan Mutanen bah a rayuwarshi. Masroor baki yak'i rufuwa, Ana gama d'aurin aure yad'au wayanshi ya soma nemqn layin beauty. Ya dad'e yana ringing kamin a kawo mata ta d'auka tana y'ar Murnushi, cikeda Farinciki yace

"Beauty am now urs uh are mine. An d'aura"
Chapter 26 · 0% Book details