← Book details Sulthana Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 20 OF 28

Sashe 20

Sulthana Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Sa'ood ya soma magana yana k'allan Fareed

"Zamanka da mace ku biyu bah abu baneh mai kyau, shedan ake gudu."

Ajiyan zuciya Fareed yayi

"Gaskiya neh Sa'ood, saidai kasan Matsalan Ummah bazata taba yarda Sulthana ta zauna da ita ba kuma ma kagani yanzu bah zama take bah"

Shiru Sa'ood yayi yana tunani chan yace

"Dole mu nemi mafita dan wannan bah abu mai yuwuwa baneh"

Fareed ya d'ago yana cewa

"Ga shawara"

Sa'ood ya ce

"Ina jinka"

"Mezai hana nasata a boarding school har zuwa sanda zan sanar da Abba da ummah"

Murmushi Sa'ood yayi

"Yes haka ya kamata"

Sun aje akan ranar monday da Sassafe zasu kaita zaria academy dan mata registration..

Abubuwan sunma Yasir yawa gashi kullum sai Masroor ya kirashi akan Zuwa kauyensu Sulthana. Yau yana barin School kauyen ya nufa kai tsaye. Batareda wani d'ar bah yasamu Almajiri yace yamai Sallama da Sulthana. Almajirin yace

"Ai Sulthana ta b'ace ba'a ganta bah yanzu sati uku knan"

Hankali tashe Yasir yace

"Garin yaya?"

Almajirin ya tab'e baki yace

"Nima ban sani bah, andai ce Mallan ne ya koreta."

Ran Yasir ba karamin Baci yayi bah yace

"Mallan din na nan"

Yaran yace

"Ai mallan bashida lapia tun ranar data bace ya fadi a bakin Masallaci har yanzu bai warke bah"

Hannu yasa a Aljihu ya ciro d'ari biyu ya mik'ama yaran yana murmushi

"Gashi abokina nagode"

Amsa yaran yayi tareda godiya shi kuma ya shiga motanshi yabar kauyen Hankali tashe. Yanzu taya zai gayama Masroor wannan mummunan labarin.

Yini yasir yayi cikeda fargaban yanda zai fadama abokin nashi wannan labarin. Yakoyi sa'a bai kirashi bah sai washe gari, da kyar ya dauka suka gaida Masroor yayi saurin cewa

"Yasir kakoje?"

Shiru Yasir yayi har saida Masroor yace

"Kana jina kuwa?"

Ajiyan zuciya Yasir ya saki yace

"Ina jinka friend, naje anma ban samu ganinta bah"

Nan da nan Masroor ya rud'e ya shiga jeromai tambayoyi

"Meyasa baka ganta bah?? Bata nan neh? Ko taje talla?? Pls Yasir yimin magana uh sound strange"

Ta maza yasir yayi ya zaiyanema Masroor duk yanda sukai da Almajirin daya samu a kofar gidansu Sulthana. Wayan dake Hannun Masroor ne ya fadi hawaye suka cika idonshi, kuka ya saki mai sauti tana kiran sunanta da k'arfi. Neighbours dinshi suka fifito suka tsaya a bakin kofan hankalinsu tashe jin yanda yake kuka da k'arfi yana fashe fashe..

Saida yayi mai isarsa sannan ya mik'e idanunshi sunyi luhu luhu ya shiga toilet yayi alwala ya soma kai kukanshi ga ubangiji _oh Masroor I pity uh_

Washe gari da safe Fareed da Sulthana suna kan dinning suna breakfast kamar yanda suka saba y'an kwanakin. Maganan sata a makaranta ya mata. Tayi farinciki sosai daga baya kuma ta hade rai

"Yanaga kuma kin chanza meya faru?

Rau rau tayi da ido

"Yaya Fareed yanzu shiknan bazan k'ara ganin Mama da yaya Hafsatu da yaya Ameenatu bah"

Goshinshi ya dafa

"Oh God! Sulthana ki cire wadan nan mutanen a ranki su basa sanki kece kawai kika damu dasu"

Hawayen dake makalle a idonta suka zubo tana girgiza

"Ina Sansu Yaya Fareed suma suna sona"

D'an jim yayi ya mik'e yana cewa

"Shiknan yanzu dai bansan kukan, ki shirya gobe da Sassafe zamu tafi. Idan akai hutu saiki je"

Ihu ta saki tana Y'ar Murmushi

"Nagode Ya fareed"

Kai kawai ya gyada ya bar wajan a zuciyarshi yana raya. Lallai rashin kula da gata yasa Sulthana shiru shiru dan yanzu data d'an wartsake ya hango k'iriniya da shagwaba a idanunta..

Washe gari da wuri da wuri suka tashi, da kanshi ya shirya mata kayanta a trolley da duk abinda take buk'ata. Saida ya tsaya a wani babban supermarket yayi mata sayaiyya sosai sannan suka biya ta gidansu Sa'ood ya daukeshi suka nufi zaria..

Bayan gwajinda akai mata Mallaman sukace za'asata a js1 rok'onsu Sa'ood yayi asata a js3 saboda ta girma she is 15. Hakan ko akai saida akai mata komai aka kaita hostel dinsu sannan su Fareed suka dawo gida...

Haka rayuwa ta cigaba da tafiya. Ta bangaren Masroor kuwa
Kullum da tunanin Sulthana yake kwana dashi yake tashi, yanzu Masroor ya koma shiru shiru bashida hayaniya. Hoton Sulthana shi yazan mai tv, lokaci lokaci yakan sa Yasir yajemai Kauyensu Sulthana ko da wani labari gameda ita anma bbu. Yasir na matuk'ar tausayama abokin nashi hakama Mami dan Yasir ya sanar da ita duk abinda ke faruwa...

Sulthana taji dad'in makarantan sosai dan a ranar datazo tai k'awa mai suna Aisha ibrahim itama y'ar jahar kano ce. Yarinyar wani senator ne a gwamnatin dakaci yanzu. Y'ar gayuce sosai ga Rashin ji da Tsiwa, tasu tazo d'aya sosai da Sulthana, wajanta take koyan Abubuwa kamar karatu da sauransu..

*Bayan shekara d'aya*

Sulthana na hango tsaye a wajan makaranta sanye da k'ayan hostel hannunta Rik'e da trolleynta, ta k'ara tsawo da cika, fatanta ya murje tayi kyau sosai. gefenta k'awarta Ayoush itama tsaye da Alama hutu akai saboda yanda dalibai keta fitowa da jakunkunan su. Hira suk'e suna dariya chan saiga wata had'adiyar mota k'irar doddge tai parking. Fareed ne ya fito daga motan sabye da Farar yadi sai baza k'amshi yake. K'arasowa inda suke tsaye yayi yana y'ar murmushi,

"Am sorry Queen I know i'm late"

Zaumbure baki tai ta kauda kai gefe, dariya Ayoush take k'asa kasa ta gaidashi da kanta ta saka jakan Sulthana a motar sannan ta karasa inda take tsaye

"Queen kiyi haquri mana kuje kinji"

Murmushi Sulthana taima Ayoush suka rungume juna sannan Sulthana ta shiga yaja sai kano ta dabo..

Fushi Queen dinshi keyi dashi, bah yanda beyi bah daran ranar ta rakashi yanada Dinner anma taki wai ita barci take ji. Hakanan ya hak'ura ya kira Sa'ood sukaje tare..

Masroor ne xaune cikin jirgi yau cike yake da farinciki zai dawo nigeria wajan iyayenshi. K'arfe hudu na shidda na yanma jirginsu ya dauka a kano, koda ya dauko Yasir ya gani tsaye shida Mami da Umma'n Fareed sai wasu mata dake bayanshi dukansu fuskokinsu d'auke da murmushi..

Dasauri ya k'arasa ya rungume Mami cikeda farinciki sannan ya rungume Yasir sunama Juna Dariya. D'an rusunawa k'adan yayi ya gaida Umman Fareed ta amsa fuska a sake, Mahnoor ta fito daga mota da gudu itama ta rungumeshi

"I missed uh bro"

Kanta ya shafa yana murmushi

"I missed uh too lil sis"

Yasir ya k'araso wajansu yace

"Dare yayi muje gida kwayi maganan"

Hannun Mahnoor Masroor ya kama suka shiga mottoci suka dun guma zuwa government house. A chan ma taron jama'a ya gani dan murnar dawowanshi da kuma murnar kammala karatunshi. Cikin taron harda Fareed da abokinshi Sa'ood suma sun samu halarta, anyi ciye ciye da adduo'i sannan kowa ya tafi gida..

Washe Gari dasafe Mahnoor zaune itada Masroor suna breakfast, Mahnoor tace

"Bro yaushe zamuje wajan Sulthana tunda ka dawo"

D'agowa yayi dasauri ya kalleta tareda sakin Fork din dake hannunshi..

Ummy Abduol✍🏻

💐💐💐💐💐💐💐💐
💐💐💐💐
*SULTHANA*
💐💐💐💐
💐💐💐💐💐💐💐💐

By *Ummy Abduol*

*DA BAZARMU WRITERS ASSOCIATION*

_Mak'i Gani Ya Kauda Idonsa_

*Page 171 to 175*
Dedicated dis page to Aunty Nurse (Ayoush) Allah dawo min dake nigeria Lapia.

D'agowa yayi dasauri ya kalleta tareda sakin fork din dake hannunshi. Ta fama mai tsohon kumin daya dad'e a zuciyarshi baice mata komai bah ya mik'e yabar wajan. Mahnoor ta bishi da kallo cikeda Mamaki..

A kauye Mallan ciwonshi sai gaba yake kullum cikin magani anma babu abinda ya chanza. Rayuwa knan! Duk yan kudadenshi sun tafi wajan magani, Almajiranshi duk sun gudu sun tafi gida. Yanzu Mallan da iyalinsu sun zama abin tausayi Abinci ma dak'yar suke samu watarana ma haka suke kwanciya basuci komai bah. _niko Ummy Abduol nace dama rayuwa haka take, yau gareka gobe ga wani. Abinda ka shuka shi zaka girba in Alkhairi ka shuka shi zaka gani, in kuma sharri neh shidin dai zaka gani_

_Allah kasa mufi k'arfin zuciyarmu. Ka bamu ikon aikata Alkhairi ka nisantar da zuciyarmu da Aikata sharri Ameen_

Sulthana zaune a palour yana k'allo taji bud'e gate din gidan, mik'ewa tai dasauri ta fito haraban gidan dan dama shi take jira. Yana parking ta bud'e mai murfin motan tanamai Murmushi

"Ya Fareed tun dazu nake jiranka, ko ka fasa kaini yawon"

Goshinshi ya fada tareda furzar da aska

"Oh God! Queen bakya mantuwa neh?"

D'an zaro ido tayo cikeda shagwaba tace

"Yauwa nama tuna kace zaka saimin phone"

Muryan shagwaba yayi shima yace

"Tho Queen sai ki bari idan na huta"

Dariya ta kyalkyale dashi ya mik'a mata breifcase dinshi ta amsa tana tafe yaba binta a baya. Abinci mai rai da lapia ta dafamai ta jera a dinning, kallan warmers din yayi da Mamaki

"Waya kawo wadan nan abincin"

Bubuga k'afa tayi a kasa tana turo baki

"Nifah na dafa fah"

Iyeh yace cikeda mamaki

"Waya koya miki girki?"

Hannunshi ta kama ta zaunar dashi kan kujeran dinning din tana murmushi

"A school mana, ai munayin Home economics"

Gyada kai kawai yayi dai dai lokacinda ya saka loma d'aya. Ya lumshe ido ya bud'e

"Umm! Wannan ai saiya ciremin kunni"

Dariya tayi ta zauna itama ta zuba nata, saida yaci yayi nak Sannan ya mik'e yana cewa

"Bari nayi wanka na shirya sai muje"

Tsalle tayi tana dariya

"Thank uh ya Fareed dts why I love uh"

Da mamaki ya k'alleta tai saurin juyawa ta shiga dakinta tana cigaba da dariya.

Masroor neh yayi paking a kofar gidansu Yasir. Waya ya dauka ya kiranshi ya sanar dashi isowar shi, ba'adau lokaci bah ya fito yana murmushi

"Har ka gama hutawan?"

Kai kawai Masroor ya gyada ya shiga mota ya zauna, yasir na ganin haka shima ya shiga ya zauna yana k'allanshi

"Yadai friend meke faruwa?"

Batareda ya kalli yasir bah yace

"Inaso neh muje gidansu Beauty"

Yasir ya yatsine fuska

"Muje muyi meh kuma Masroor? Duk sanda naje bana samunta bata dawo bah. Pls Friend ka cire yarinyan nan a zuciyarka myb ma bata raye"

Dago jajayen idanunshi yayi ya zubama Yasir,

"Wannan wanne irin magana neh Yasir? Na cire beauty a raina fah kace??"

Runtse ido yayi ya bude

"Bazan iya bah yasir, bazan iya bah. Indai zaka rakani to idan kuma bazaka rakani bah"

Ya nunamai kofa

"Zaka iya tafiya zanje ni kadai"

Murmushin takaici Yasir yayi

"Muje"
Chapter 20 · 0% Book details