← Book details Sulthana Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 10 OF 28

Sashe 10

Sulthana Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Fitowa yayi daga cikin motan ya tsaya, shiru ne ya biyo baya nadan mintina Sannan ya dago ya K'alleta kanta a k'asa yace
"Sulthana"
Dagowa tai tadan K'alleshi sannan ta maida kai tace
"Na'am"
Ajiyan zuciya ya sauke yace
"Shekaranki nawa?"
Dan Jim tai kamar karta fadamai sai kuma ta dan dago batareda ta kalleshi bah tace
"Sha hudu"
Jinjina kai yayi yace
"Ajinki nawa a makaranta"
K'ara dago kai tai ta K'alleshi tareda girgixa kai
"Bana zuwa makaranta"
Kallanta yayi da Mamaki
"Meyasa?"
Kauda kai tai tareda turo Baki
"Baffa ya cireni"
Kallanta ya tsaya yi, Abinda ya fahimta da Yarinyan shine tana fuskantan kiyaiya a gidan zai iya cewa wajan kishiyar mahaifiyarta kuma abinda ya burgeshi da ita sam batasan wani bare yasan halinda take ciki.

Hakan ya burgeshi sosai, Muryanta yaji tana cewa zan shiga gida kada Baffa ya fito ya ganni. Bata jira mai zaice bah tabar wajan ta shiga cikin gida. Kurri yana kofar gidan, tausayin Sulthana ke ratsa shi. Runtse ido yayi ya bude a hankali yace
"Ina sanki Sulthana, zan iyayin komai a kanki. Insha Allahu zaki fita daga k'angin da kike ciki kwanan nan"

Ummy Abduol✍🏻
[28/08, 01:12] Friend Hussaini: 💐💐💐💐💐💐💐💐
💐💐💐💐
*SULTHANA*
💐💐💐💐
💐💐💐💐💐💐💐💐

By *Ummy Abduol*

*Page 86 to 90*

"Yarinyan nan tana cikin damuwa"
Kamar zai bita ya fasa ya shiga mota ya nufi Cikin garin kano. Zama tai Bakin Bishiyan Data saba Zama, Gyadan ta soma saidawa kamar yanda ta Saba. Atika dake kusa da ita tana saida Rogo ta yafici Ladi tana nuna mata wata hadaddiyar mota datazo wucewa
"Kai Ladi ji Wachan motan, Tafdi! Ni tunda nake ban taba ganin mota mai sama a bude bah"
Kyalkyacewa da dariya ladi tai tana tafawa
"Kai Wallah Motan nan Akwai Kyau, Allah ka bamu irin wanna motan"
Jin Yanda suke zuzuta motan yasa Sulthana ta dago ta K'alli motan, Lallai kuwa motan yanada Kyau, Murmushi ta soma tanabin Motar da K'allo. Duk mutanen dake K'asuwan kowa bin motar yake da K'allo cikeda Sha'awa, Wanda ta gani Cikin motan neh yasa Fara'ar dake Fuskanta yakau, Hijabin Fuskanta ta Turo Gaba ta Rufe Fuskanta dashi..

Zagaye yake yana yatsine Fuska, Waje ya samu yayi Parking Sannan ta fito. Mata sa binshi da K'allo suke harda Mazan, Dan D'an gayu neh na K'arshe. duk gungun Yara masu talla daya gani sai ya tambaya tareda Fadin sunanta anma duk suce basu santa bah, Ganin Yana Kokarin nufosu yasa Sulthana ta mik'e tana K'okarin daukan trayn Gyadan tah k'araf suka hada ido, Dauke kai tai Ta dauki Trayn Gyadan ta Fara tafiya. Binta Yayi tateda Kiran sunanta, Juyowa tai ta Murguda mai Baki
"Kah daina kiran sunana kuma ka daina bina"
Murmushi Yayi yanda ta murguda bakin Saita k'ara mai kyau
"Meyasa zakice na daina binki"
Batareda ta juyoba tace
"Nidai Dan Allah ka daina bina kada Yaya hafsatu ta ganmu taje ta fadama Baffa, Idan ta fadama Baffa dukana zeyi, Jiyama saida ya dakeni"

Tausayi ta bashi Ya sha gabanta yana K'allanta
"Kiyi Hakuri nasan mu muka ja miki dukah koh"
Batace mai komai bah tana k'okarin tafiya, hannu ya daga mata Yana cewa
"Tsaya mana, kudinki na jiya nakeso na Baki"
Kauda kai tai gefe
"Kah barshi, nidai dan Allah ka bani Hanya na Wuce"
Matsa mata Yayi ta soma Tafiya Yana K'allanta, meya tuna ya bita da Sauri tareda shan gabanta
"Tsaya tho kiji"
Tsayawa tai hannunta d'aya a kugu
"Inaso gobe mu hadu a Inda kike saida Gyada kamar wannan lokacin kinji"
Batacemai Komai bah ta cigaba da tafiya abinta. Binta yayi da K'allan tausayi, A Ranshi Yana raya
"She's Cute n Young, She need help. No matter how Zaki Kasance Cikin Farinciki nan daba"

Motarshi ya nufa dan komawa gida, Yara ya gani Yayyabe da Motan Sunata Shafawa, K'arasawa yayi dasauri ya koresu. Ganin Sunki Tafiya yasa ya Dauko bandir din yan Hamshin ya soma Raba Musu, ai a nan yaga wawaso harda manya. Tausayama Halinda yan K'auyen suke ciki yayi. Motan ya shiga ya tada Yabar kauyen Cikeda Tausayin Sulthana...

Gida Ya nufa Kai Tsaye, Horn yayi masu Gadi Suk'a budemai kofa, Saida yayi Parking Sannan ya Fito. Bodyguards din dadd ya gani a tsakar gidan, Murmushi Yayi
"Wel daddy is back"
Main palour ya nufa tareda Danna Bell, wata mai Aiki ce ta bude Tareda Zubewata gaidashi, Bai amsa bah ya Shiga falon Yana Fara'a Baiga kowa A falon bah. Wani Corridor ya nufa wanda zai sadashi dah Dinning area, a nan ya gansu zazzaune suna Lunch. Sallama yayi ya k'arasa ya rungume Daddy Yana dariya,
"I Missed uh Daddy"
Murmushi Daddy yayi Yana Shafa Kanshi cikeda Zolaya Yace
"Sai Kace nayi shekara kwana biyu fah nai"

Turo baki Mahnoor tai tareda Rungume Hannayenta
"Daddy kacema Bro Masroor ya daina Rungumeka shi babba neh"
Zama Masroor yayi akan Kujera suka fashe da Dariya duka, Hararanta yayi
"Lallai baki isah bah, Ai daddy nane"
Idonta ne ya ciko da K'walla ta kara hade rai tace
"Daddy na dai"
K'ara Fashewa da dariya sukai duka. Ganin Sunata mata dariya yasa ta fashe da kuka ta mik'e Tabar wajan tana kuka..

Hararan Masroor Daddy yayi
"Kaga kah koranmin Baby koh, Tho Maza ka tashi ka Lallasheta ta dawo taci abinci"
Turo baki Masroor Yayi yana Kai Loman Abinci
"Daddy kah kyaleta cikin wah Bah nata bah, Karta Cin"
Lekowa Mahnoor tai Tana Share kwalla
"Baza'a kyaleni din bah."
Guntse Dariya Mami da Daddy sukai dan Yanzu sunayi zasu takalo Rigima..

Rungume Mami tai ta Baya ta shagwabe Fuska
"Mami yanzu bro Masroor baya sona, Bro Yasir ne kawai ke Sona"
Cup din Juice Masroor ya dauka ya kora Sannan ya aje Yana cewa
"Kedai kika sani"
"Ahan ina Kaje dazo baka fadama Yasir bah, yazo nemanka neh kuma nasan din inda zaka tare kuke zuwa"
D'an jim yayi sannan yace
"Eh wannan fitan ni kadai neh, Banda Shi"
Murmushi Daddy yayi cikeda Nishadi
"Koh anje Wajan Sirikan nawa neh"
Suman Kanshi Ya Shafa Yana Y'ar Dariya.
"Aa Daddy"

Mami Itama Dariyan tai
"Ai dama bazaka fada bah, tho bari kaji gwara fa kama fada tun yanzu coz ana gama Hayaniyar siyasan nan Zamuje neman aure"
Turo Baki Masroor Yayi ya mik'e yabar Dinning din...

Ummy Abduol✍🏻
[28/08, 01:12] Friend Hussaini: 💐💐💐💐💐💐💐💐
💐💐💐💐
*SULTHANA*
💐💐💐💐
💐💐💐💐💐💐💐💐

By *Ummy Abduol*

*Page 96 to 100*

"Ina sanki Sulthana, zan iyayin komai a kanki. Insha Allahu zaki fita daga k'angin fa kike ciki kwanan nan"
Motanshi ya shiga yabar wajan cikeda tausayin halinda Sulthana take ciki.

Da zazzabi Sulthana ta tashi da asubah, dakyar ta iya mik'ewa ta fito tsakar gidan. Alwala tai ta koma zaure tai Sallah, Tana zaune Baffa ya fito ya tafi masallaci. Kasa shiga tai aikin data saba tayi a cikin gidan har wuraren k'arfe bakwai da rabi, Ameenatu ce ta fara fitowa daga daki ganin ko'ina batsa batsa yasa ta nufi zaure a fusace. Kwance ta sameta tanata rawar sanyi, tsaki Ameenatu tai tana magana cikin daga murya
"Wato dan kin raina mutane yau bazaki je kiyi aikinki bah. Uban wa kikeso ya miki shara da wanke wanke"
d'an dagowa Sulthana tai hawaye na gangarowa a idonta
"Dan Allah yaya Ameenatu kiyi hakuri banida lapia neh"
Duka takai mata dai dai nan Hafsatu ta k'araso wajan tana Murmushin Mugunta
"A'a yaya Ameenatu yau kuma Y'ar son ake duka"

Tsaki Ameenatu ta k'arayi tana nuna Sulthana da yatsa
"Wallahi idan baki tashi kinyi aikin daya kamata bah sai na miki dukan tsiya"
Kallanta hafsatu tai da mamaki, Yau kuma Ameenatu kecewa zata duki Sulthana, Lallai abin babba neh.
Kasa tashi Sulthana tai sai kuka datake Mara sauti, dakyar ta mik'e ta zauna tana k'allan Ameenatu data hada girar sama data k'asa
"Dan Allah yaya Ameenatu kiyi Hakuri"
Ai kamar zugata take nan da nan ta rufeta da duka, Hafsatu taga bati itama ta tayata. Bah abinda Sulthana take in banda ihu. Ihunta ya fito da Mama ta K'araso wajan dasauri..

Dakyar ta kwace Sulthana a hannunsu a fusace tace
"Wannan wanne irin iskanci meh Ameenatu, wai meke daunki me? Metai muku kuke dukanta haka kamar Allah ya aiko ku"
Ameenatu ta hade rai tana huci
"Dan wulakanci tun dazu yarinyan nan batai aikin gida bah, jibi gidan nan sannan ina mata magana tana cemin wani batada lapia"
K'allan Ameenatu Mama ta tsaya yi
"Lallai Ameenatu baiwarki ce ita da zakice dole sai tamiki aiki, ai rashin lapia ya wuce komai sai kuyi mata uzuri"
Hafsatu ta chuno baki
"Haba Mama ke kullum sai ki rinka hana ana hukunta yarinyan nan, Gaskiya..
Saukan Mari Hafsatu taji a fuskanta, a fusace Mama tace
"Wallahi ki kiyayeni Hafsatu, na lura abubuwanki nema suke su wuce wuri"
Nunasu da dan Yatsa tayi tana cewa
"Tho bari kuje, daga yau Sulthana bazata k'ara aikin gidan nan bah ku zakuyi. Meye ku anfanin ku"
Baffa ne ya bankado kyauren gidan ya shigo jin hayaniya, cirko cirko ya samesu a tsaye sai Sulthana dake Zaune a kasa tana kuka duk jini a hancinta da baki..

"Lapia??" Baffa ya tambayi Mama, Hafsatu ce ta koromai bayanin duk abinda ya faru. Nan ko Baffa yahau sababi ta inda yake shiga batanan yake fita bah, Ameenatu ta kalla yana cewa
"Ku cigaba da dukanta ai wannan ma iskanci neh"
Hafsatu ce ta cigaba da dukanta Mama na tsaye tana k'allan Baffa cikeda takaici, batace komai bah ta koma dakinta ranta bace. Itama Ameenatu daki ta koma a fusace, ligi ligi Hafsatu taima Sulthana Baffa na Tsaye. Saida ta duketa san rai Sannan ta kyalleta, Sannan Baffa yasata tai duk aikin Gidan yana Tsaye. Tanayi tana kuka dakyar tai aikin ta gama ta koma zaure ta zauna ta cigaba da kukanta..
Chapter 10 · 0% Book details