← Book details Shu'umar Masarauta Part 2 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 21 OF 27

Sashe 21

Shu'umar Masarauta Part 2 Complete Hausa Novel · about 6 min read

  Da sauri na faɗa bukkarmu na ɗabo gurun damatsan hannuwana da wuya, na kunce fatar mesar da ke ɗaure a ƙuguna na ɗaura ta damisa sannan na ɗauko kwari da baka haɗe da zabgegiyar adda na fito wurin da su Goga suke tsaitsaye. Suna ganina suka yi yunƙurin saka kai a hanzarce na dakatar da cewar, "Wannan fitar ba taku ba ce saboda Barde gidanmu ya taɓo ba ku ba, na yi rantsuwa da abar bauta ba zan dawo gida ba sai na sauke kan Barde daga gangar jikinsa, weeeehuuuuhuuuuu sai ni sarauniyar baka jikar marigayi Baushe amanar kura kawanciyarka ka huta muna tafe idan dabbobi sun ƙare. Sai ni yaƙi ban san wasa ba Abar bauta ta buɗa mana matuƙar na saka kai ko yau ko yanzu ban san namiji ba sai na ga tabo a jikinsa, wahala a hanyar tugu wuya a hanyar badake wuya ko da magani babu daɗi ko ana ha maza ha mata sai na dawo da kan Barde a hannuna." Ina gama zabga kirari cikin haɗin baki tawagar da ke wurin suka furta, "Dawa dai Sarauniyar kwari da baka, Abar bauta ta buɗa miki a dajin Gurɓu." Har na saka kai zan fita na dawo wurin Mahaifiyata na russuna saitin kunnenta ina faɗin, "Ki roƙar mini abar bauta da ta rinjayi ɗayan ruhin kar ya ziyarce ni ina tsoron kada Barde ya yi nasara akaina." Cike da ƙwarin gwiwa ta furta min, "Sa'a dai Sarauniya abar bauta ta buɗa miki ɓoyayyan ruhi ba zai ƙara ziyartar ki ba." Ina gama sauraronta na fice daga cikin gidan cike da ƙwarin gwiwa na nufi wurin da na tabbatar Barde na zama da ƴan koronsa.

Daular Sarki Damina.

   Daga kogon boka mai zamani ya so kai ziyara bukkar babban dodo amma sai ya ga mafi dacewa ya fara zuwa wurin al'ummarsa ya umarci rundunar mayaƙansa da su fita yi masa farautar duk wata halitar bil'adam, musamman daga tsagin maharba da mafarauta kamar yadda suka saba yi a baya. A tsaitsaye suke dubbanin mutanen daular don a zatonsu maganin warakar annobar da ke damunsu aka kawo musu, Waziri ne ya yi gyaran murya sannan ya furta, "Ya ku waɗannan jama'a ya kamata kowa ya nutsu don jin saƙon da Sarauniya sha-kundum ta aiko." Tamkar ɗaukewar ruwan sama haka wurin ya yi tsit, Sarki Damina ya yi gyaran murya sannan ya dube su ɗaya bayan ɗaya  ya sanar da su duk yadda suka yi da boka Mai zamani sannan ya ɗora da cewa, "Ina umartar manyan mayaƙan dakarun daular nan da su hanzarta fita cikin gaggauwa don yi mana farautar bayi kamar yadda suka saba a baya, kuma su yi sani cewa ya zama wajibi su farmako mana La'anannun hallitar can ta maharba da mafarauta a ko ina suke a faɗin duniya. Wannan umarni ne daga Sarauniya sha-kundum idan ba haka ba bala'in da muka shiga da wanda muke ciki a yanzu shafar mai ne akan abin da zai faru da mu a gaba." Yana rufe baki zaratan dakarun mayaƙan suka fara fita a guje zuwa mahallansu kowanne na fito wa da manyan makamai, runduna guda suka yi tsaya a gaban sarki Damina. Sai da ya ƙare musu kallo sannan ya kasa su gida huɗu, manyan zaratan mayaƙan ya ce su bi gabas hanyar da za ta sada su da ƙasar Dabur. Runduna ta biyu ya ce su bi Yamma hanyar da za ta sada su da ƙasar Baƙasud, runduna ta uku ya ce su bi kudu hanyar da za ta sada su da ƙasar Mubali sai tawaga ta huɗu da ya umarce su da Arewa wacce za su isa da Ƙasar Surima. Lokaci ɗaya suka bazama a yunwace da farauto kowanne irin bil'adam kamar yadda Sarkin da yake mulkarsu ya ba su umarni.

*KU MATSO KU TAHO*💃🏼

Wannan labarin salonsa na daban ne💃🏼 cike yake da sarƙaƙiya da tsananjn ban tausayi😰  ku dai kar ku bari a yi babu ku.🏂

Littafin kuɗi ne idan kina buƙata 400 ne ta Account 3090957579 Aisha Adam, First bank. Za ki turo evidence ta wannan lambar 0706 206 2624 Idan kati ne MTN. Idan kika bari na kammala cmplt 700 ne.

Idan kin san kin sayi ɗaya daga cikin litattafan nan *AN YA BAIWA? KO DUBU JIKAR MAI CARBI KO ZAUJATU JINNUL-ASHIQ* za ki biya 300 wannan ragin na waɗanda suka sayi wannan littafan nan ne kaɗai.💃🏼

Na ɗaga hannuwa riƙe da takobi da kwari da baka na salaƙe na sunkuyar da kai ina miƙa gaisuwa da kirari cau cau cau cau, sai ni Ameera 'yar Alhaji Adamu Amiriyan Mamanta, uwar Aslam da Ayman Amanar Oganta turmi sha daka 🥰
Wiiiiiiihuuuuuuhuuuu mace mai kamar maza ko cikin maza sai an duba domin wuya ake yi wa lissafi daɗi sai an jinkirta. Allah dai ya biya wuya a ƙofar Na'isa, wuya a ƙofar Kabuga wuya a ƙofar Nasarawa wuya a doka wuya, wuya a ƙofar kansakali mun buga a dajin Jemagu mun buga a dajin Falgore ko dajin Sambisa albarka. Sai ni ƴar Kanawan dabo amanar mutanen Rigana, idan ka ga matsoraci ko rago a Rugana baƙo ne domin jarumi ba'a nuna masa hanya, sa'a dai 'yar gaban goshin *FIRST CLASS WRITER'S* Amanar Marubuta La'ilaha'illahu. Sai ni ta hannun Matar Habibu ni ce dai ƙawar Mum Amnash amanar Masoyanta, cau cau cau cau makaranta ku matso ku ji wannan kafcan don idan kika bari aka yi babu ke an barki a baya. Domin duk wacce ta bari aka yi wannan tafiyar babu ita ta fita daga cikin jaruman mata masu aji.🌚

*Ummou Aslam Bint Adam*🌚
[8/20, 7:26 PM] Ameera Adam🌚: *BAƘAR DAULA*

      ©AMEERA ADAM

FIRST CLASS WRITER'S ASSO...
 
Tsokaci: Ƙirƙirarran labari ne bai faru a gaske ba, ban rubuta don cin zarafin kowacce ƙabila ko yanki ba. Daga sunayen garuruwa zuwa na abin bauta duk ƙirƙirarru ne, kuma ban lamunce a sauya min littafi ta kowacce siga ba tare da izinina ba.⚠️

                  2

Fita ta ke da wuya na ci karo da Mahaifina da ya sawo kai ciki kafaɗarsa maƙale da barewa da ingarman zaki, ganin yanayina ya tabbatarsa masa akwai wani abu da yake faruwa don ya san fitarsa ban yi da shi zan shiga dawa ba. Cike da ladabi na miƙa masa gaisuwa irin tamu ta maharba ina faɗin, "Dawa dai Sarkin sarakuna uban dawa ga tsini ga mashi, ina gwanin wani ga nawa gamji kake ka fi ƙarfin saran maƙiya ɗan butar uban nan. A lafiya garnaƙaƙi uƙubar Gabatarawa, Abar bauta ta buɗa maka ka ci gaba da maganin munafukan mafarauta, sha zamanka ka ci gaba da kai dabbobi ƙasa wallahi ko yau ko gobe ko baka nan muna yi maka yaƙi." Cikin jin daɗi Mahaifina ya jingina gorar hannunsa da tawa sannan ya furta, "Dawa dai Sarauniya Abar bauta ta buɗa miki ko dare ko rana a dokar daji. Cau cau cau amanar Baushe wata wuyar sai a tsakiyar tsaunin Mani." Ɗora kokarata na yi a wuya na saɓi hanya tare da furta, "Sa'a dai ruwan saman mai dukan basarake da faƙiri, shawarar Duba amanar Duna." Kai tsaye mazaunin Barde na tunkara da ke cikin ƙasurgumin dajin Gurɓu, duhun almuru har ya fara karaɗe gari don haka na ƙara ƙaimi domin na cin musu don ba na son Barde ya sake shaƙar doguwar iskar numfashi. 

Ganin dajin na sake yi min nisa kuma ina gudun rasa Barde a yammacin, ya sa na lalubi ramin bushiya cikin nasara na fisgota da ƙarfi tsiya, ƴar ƙaramar aska na ciro ya tsaga bayanta sannan lalubi ganyan tunfafiya na murje a bayanta, na damƙi ƙayoyi na soka a tsakiyar kanta. Sai da na kalli kusurwa huɗu da ita a hannuna sannan na saita hanyar da za ta sada ta da mazaunin su Barde na dire ta a ƙasa tare da furta, "Bisa ga Barde amanar Lado, ko tsuntsu kika gani kar ki bar shi ya kubce."
Chapter 21 · 0% Book details