Sashe 8
Sanadin Kenan Part 4 Complete Hausa Novel · about 3 min read
To a binciken su shi da Amina da sauran likitocin bangaren su na ATBU Teaching Hospital sun gano matsala babba a tare da Ameena. Sun gano cewa kashin kafarta na hagu bai gama yin kwari ba, yana bukatar wani irin gashin wanda ba su da injin yinsa sai a waje.
Dr. Usman ya ce ya san wani asibitin da suke irin wannan aikin a Vienna (Austria) wadanda sukawarkar da EFCC Lamido Nasir (Babban Goro) da kuma wani a Jeddah (Saudi-Arabia).
Maarouf ya zabi na Jeddah, ko ba komai bai karya (patriotism) dinsa na yin alaka da kasashen Turai ba. Ya soma yi musu shirin tafiya Jidda shi da Amina da Ameena.
Ranar wata asabar jirgin KLM ya daga dasu zuwa Saudi-Arabia. Madinatul-Munawwara suka wuce kai tsaye don fara yin umrah musamman akan Allah ya basu saar abin da suka zo nema, daga Madina suka wuto Makkah suka yi cikakkiyar umrah, duk adduoinsu a kan lafiyar Ameena ne na neman nasara a kan aikin da za a yi mata.
Sannan suka isa asibitin da suka zo a Jeddah (Solayman Faqeeh) aka fara yi wa Ameena(Radiotherapy)na musamman. Amina ta ja gefe tana kuka fuskarta cikin mayafinta kawai saboda tausayin Ameena. Yarinya karama tana shan azabar da bata misaltuwa a yan kananan shekarunta da basu kai goma ba.
A duk lokacin da ta ga ana yi wa Little therapy din nan ba ta iya daurewa sai ta yi hawaye kamar ba likita ba. A karan-kanta yanzu in zaa bata trillion ba abinda zata iya kara iya yiwa Ameena. Ba don komai ba sai don tausayi da sarewa. Daga ita har ubanta tausayinsu take ji har batasan wa tafi tausayi ba tsakanin yar da ubanta. Amina keda ciwon a jikinta amma zata iya rantsuwa Maarouf zai fi so a dawo da ciwon jikinsa in har zata samu lafiya. Tana ganin yadda baya iya barci tun saukar su a Saudi.
A makkah da madinah a masallaci yake kwana. Anan jeddah kuwa bisa dardumarsa. Da gaske Allah ba ya hada maka komai a rayuwa, in ya baka wannan sai ya jarrabeka da wancan, shi kuma Maarouf Ji-kas ga ta inda allah yake jarrabarsa (ciwon Da).
Ganin halin da take kasancewa in sunzo asibitin tare sai Maarouf ya daina zuwa asibitin da ita, ya gwammace ya zo shi da wadanda suka rako su (securities) dinsa. A hotel din da suka sauka (Aljamjoum) yake baro ta ya zo asibitin da masu tsaron lafiyarsa.
Ba su fara samun nutsuwa ba sai da manyan likitocin na asibitin (Doctoor Solayman Faqeeh) suka tabbatar musu kafafun Ameena sun samu waraka cikin yardar Ubangiji, amma zai iya yiwuwa wani lokacin ta yi fama da dan ciwon kafa kadan-kadan, da zarar ta yi complain din hakan sun rubuta magungunan da za’a bata ta dinga sha a take ciwon zai daina.
Sai a lokacin ne Maarouf da Amina suka samu lokacin junansu, aka biya bashin soyayyar da aka ci kwana da kwanaki wanda tashin hankalin ciwon Amina ya mantar dasu.
Sun yi honey-moonmai tsayawa a zucci fiye da na farkon aurensu a Transcorp. Wata guda da rabi suka kwashe a Saudi-Arabia sannan suka tattaro suka dawo gida Nigeria.
Daga airport kai tsaye direban da ya kwaso su Ji-kas ya wuce da su. Maarouf bai kwana ba ya koma Bauchi su kuwa suna tare da Hajiya har tsayin kwana uku. A nan ne Amina ke yi mata bayanin matsalar da ta fidda su Jeddah. Hajiya Saude ta ce, Kai! Wato dan Adam har ya mutu ba zai huta da kaddarorinsa ba, Allah ka kara mana lafiya bakidaya, Allah ya kara miki lafiya mai dorewa Amina.
Da suka koma Bauchi da wata daya aka mayar da Ameena makaranta bayan ta kara samun kyakkyawar kulawa a hannun Antynta.
Dr. Usman ya ce ya san wani asibitin da suke irin wannan aikin a Vienna (Austria) wadanda sukawarkar da EFCC Lamido Nasir (Babban Goro) da kuma wani a Jeddah (Saudi-Arabia).
Maarouf ya zabi na Jeddah, ko ba komai bai karya (patriotism) dinsa na yin alaka da kasashen Turai ba. Ya soma yi musu shirin tafiya Jidda shi da Amina da Ameena.
Ranar wata asabar jirgin KLM ya daga dasu zuwa Saudi-Arabia. Madinatul-Munawwara suka wuce kai tsaye don fara yin umrah musamman akan Allah ya basu saar abin da suka zo nema, daga Madina suka wuto Makkah suka yi cikakkiyar umrah, duk adduoinsu a kan lafiyar Ameena ne na neman nasara a kan aikin da za a yi mata.
Sannan suka isa asibitin da suka zo a Jeddah (Solayman Faqeeh) aka fara yi wa Ameena(Radiotherapy)na musamman. Amina ta ja gefe tana kuka fuskarta cikin mayafinta kawai saboda tausayin Ameena. Yarinya karama tana shan azabar da bata misaltuwa a yan kananan shekarunta da basu kai goma ba.
A duk lokacin da ta ga ana yi wa Little therapy din nan ba ta iya daurewa sai ta yi hawaye kamar ba likita ba. A karan-kanta yanzu in zaa bata trillion ba abinda zata iya kara iya yiwa Ameena. Ba don komai ba sai don tausayi da sarewa. Daga ita har ubanta tausayinsu take ji har batasan wa tafi tausayi ba tsakanin yar da ubanta. Amina keda ciwon a jikinta amma zata iya rantsuwa Maarouf zai fi so a dawo da ciwon jikinsa in har zata samu lafiya. Tana ganin yadda baya iya barci tun saukar su a Saudi.
A makkah da madinah a masallaci yake kwana. Anan jeddah kuwa bisa dardumarsa. Da gaske Allah ba ya hada maka komai a rayuwa, in ya baka wannan sai ya jarrabeka da wancan, shi kuma Maarouf Ji-kas ga ta inda allah yake jarrabarsa (ciwon Da).
Ganin halin da take kasancewa in sunzo asibitin tare sai Maarouf ya daina zuwa asibitin da ita, ya gwammace ya zo shi da wadanda suka rako su (securities) dinsa. A hotel din da suka sauka (Aljamjoum) yake baro ta ya zo asibitin da masu tsaron lafiyarsa.
Ba su fara samun nutsuwa ba sai da manyan likitocin na asibitin (Doctoor Solayman Faqeeh) suka tabbatar musu kafafun Ameena sun samu waraka cikin yardar Ubangiji, amma zai iya yiwuwa wani lokacin ta yi fama da dan ciwon kafa kadan-kadan, da zarar ta yi complain din hakan sun rubuta magungunan da za’a bata ta dinga sha a take ciwon zai daina.
Sai a lokacin ne Maarouf da Amina suka samu lokacin junansu, aka biya bashin soyayyar da aka ci kwana da kwanaki wanda tashin hankalin ciwon Amina ya mantar dasu.
Sun yi honey-moonmai tsayawa a zucci fiye da na farkon aurensu a Transcorp. Wata guda da rabi suka kwashe a Saudi-Arabia sannan suka tattaro suka dawo gida Nigeria.
Daga airport kai tsaye direban da ya kwaso su Ji-kas ya wuce da su. Maarouf bai kwana ba ya koma Bauchi su kuwa suna tare da Hajiya har tsayin kwana uku. A nan ne Amina ke yi mata bayanin matsalar da ta fidda su Jeddah. Hajiya Saude ta ce, Kai! Wato dan Adam har ya mutu ba zai huta da kaddarorinsa ba, Allah ka kara mana lafiya bakidaya, Allah ya kara miki lafiya mai dorewa Amina.
Da suka koma Bauchi da wata daya aka mayar da Ameena makaranta bayan ta kara samun kyakkyawar kulawa a hannun Antynta.