Sashe 7
Sanadin Kenan Part 4 Complete Hausa Novel · about 7 min read
*****
A wannan satin Ameena karama ta zo hutun (third-term) daga makarantar da Babanta ya kai ta a Lagos. Ta tadda Antinta a upstairs’ tare da Babanta a gida daya kuma daki daya. Ta kuwa hau murna ba yar kadan ba. Kullum tana manne da Antin nata ko tsakiyar iyayen nata biyu tana sakin hira. Farin ciki ya cika ta ta rasa inda za ta sanya kanta don farin ciki.
Amina ta roki Maarouf da ya shirya musu zuwa Ji-Kas ita da Little za su je su yi wa Hajiya kwana uku.
Ya ce, Ni kuma fa? Haka za ku bar ni ni daya kamar maye Amina da Amina?
Kwana uku kamar kiftawar ido ne Your Excellency, na kwana biyu ban ga Hajiya ba, Ameena ma tana ta zancenta. Nayi-nayi ka dawo da Anty Laila ai ka ki saboda irin haka, mai mata daya fa aka ce aminin gwauro ne.
Nan da nan ya yi fuska, Kin jawo wa kanki fasa zuwa Ji-kas din, na kuma gane ba kya kishina ko kadan Amina. Ai sai ki dawo da Lailar tunda igiyar aurenta ai tana hannunki.
Na tuba, na bi Allah na bi ka, ba nufina kenan ba. Kawai na ga ya kamata zuwa yanzu a ce ka huce daga fushin da ka ke yi da ita, amma tunda hakan shi ne decision dinka ba ni da say Baban Ameena.
Da kyar ta shawo kansa ya sauko daga fushin nasa. Wannan ta sha faruwa ba sau daya ba, ba sau biyu ba tun barin Laila gidan da dawowar Amina daga jinya a asibitin da Laila ta yi mata sanadin minor-surgery a cikin kai.
Idan Maarouf ya ce ba ta kishinsa a kan Laila hankalinta yana tashi. Domin da bacin rai yake fada, ko uwar da ta haife shi tunda ya nuna mata ba ya son zancen komen Laila ta daina yi masa sai ita?
A nata bangaren Amina ba rashin kishi ba ne, ba dai ta son zama kwarkwata fidda mai giji, ba ta so a ce a kanta wani ya shiga wani hali ko kankani, zuciyarta mai kyau ce maabociyar imani, idan akwai abin da ta ke kishi a duniya, to Maarouf Ji-Kas ne!Kishi kuwa wanda ko a tarihi babu irinsa. Amma na musulunci.
Ta kudire a zuciyarta ba za ta kyale shi ba, in dai ta samu faraga ta ganinshi cikin nishadi za ta ambato neman alfarmarta na a mayar da Laila ba don halinta ba. Tunda Annabi mai tsira da aminci ya ce, Imanin dayanku ba ya cika har sai ya so wa dan uwansa abin da yake so wa kansa.
Tana so wa kanta Maarouf tana so wa kanta rayuwa da shi. Ta tsaya ma tana cewa tana sonshi bata baki ne, don haka tana kishin abinta. Sai dai ba za ta bari kishin ya dakusar da kaifin imaninta ba.
****
Sun isa Ji-kas lafiya ana kiraye-kirayen sallar magriba. Hajiya tana alwala sai ji ta yi Little ta dafe ta ta baya. Ta ce, Ho! yar nema, ni kada ki karasa ni.
Little Ameena na dariya ta ce da karfi, Hajiyan Ji-kas!.
Ta ce, Ni Saudatu sunana, ubanki ne Ji-Kas!
Amina da kishiyar Hajiyan suka yi dariya, Hajiya da jikanyarta kullum suka hadu sai sun ba da dariya.
Amina ta nemi buta ita ma ta yi alwala suka bi jamin sallar magariba daga masallaci. Hajiya ta rasa ina ta-ka-sa-ka, ina ta-ka-a-je da surukarta, inda duk ta mika hannu kwano ta ke janyowa cike da abincin da makota ke kawo mata da wanda mai aikinta ta dafa mata, fadi ta ke,
Zabi wanda za ki ci Dr. Amina, kin san nan kauye ne ba ma cin cima kala daya. Zabi duk wanda ki ke so.
Amina ta yi murmushi ta zabi burabuskon gero da miyar taushe wanda aka dafa wa Hajiya. Hira suke sosai kamar uwa da yarta yawanci duk a kan abin da ya shafi Maarouf ne da siyasarshi.
Ana haka Amina ta sako zancen Laila, Hajiya ba za ki roki Baban Ameena ya maida Anty Laila ba? Saura kadan fa ta kare iddarta. Bana so su rabu kwata-kwata a dalilina.
Hajiya ta girgiza kai,
Ko kusa, kada ki kara sanya wa ranki da ke cikin dalilan rabuwarsu. An samu sabanin halayya tsakanin Maarouf da Laila, mun ganganda (rushing) wajen tabbatar da aure a tsakaninsu ba tare da binciken halayya ba, inda za ki san ba ke ce sanadi ba hatta iyayenta da yan uwanta ba sa jin dadinta, sanda tana gidan yaron nan. Sawun barawo naki alamarin ya taka don haka ki daina damun kanki.
Zan tsaya kan ya maida ta din amma ba yanzu ba, sai ta kara tarbiyyantuwa. Don labari yana zuwar min kala-kala tana can nadamar rayuwa ta ishe ta duk surfen gidansu da sanwar gidansu ita ta ke yinta, kin ga ko ai Laila in mai hankali ce dole ta shiga karatun ta-nutsu.
Amina ta langabar da kai, Ni tsorona Hajiya kada iddar ta kare wani ya fito ya aure ta.
Hajiya ta ce, To ba shi kenan ba?Allah ya hada kowa da rabonsa. Ni yanzu na daina gaggawa a kan aure Aminatu.
Dole Amina ta yi shiru don ta fahimci daga Hajiyar har danta sun hau doki guda, ba za ta iya sauko da su ba, sai ranar da Allah ya nufa.
Da za su kwanta ta canza zuwa kayan barci masu kauri ta daura zanin atamfa a kai, ta kakkabe wa Hajiya gado, kayan da ta tara tsibi guda ba ninki bayan ba masu dauda ba ne, ta ninke mata su ta shirya mata a sif, lungu da saqo na dakin Amina ta bi ta kakkale shi tana mamakin wace irin mai aiki ce Tambai da a kicin da dahuwar abinci kawai ta ke aiki?
To daga ita har Hajiyar sun kwana biyu ba za su iya wannan (neatness) din ba. Ta sawa ranta alkawarin zuwa Ji-Kas akai-akai da kula da Hajiya kamar yadda za ta kula da Goggo, ta wanke mata bayi kal sai sheki da tashin kamshi yake kamar ba bayan gida ba.
Ta kuma koya wa Tambai yadda ake wankin bayi na zamani ta gane sosai. Hajiyar sai albarka ta ke sanya mata har suka kwanta barci.
Washegari ita ta yi wa Hajiya girkin rana da na dare. Har zuwa ranar da za su taho ita ke yi wa Hajiya girki da shara da gyaran bangarenta.
Babu abinda Maarouf bai sanya mata ba na saukaka rayuwa, amma ba sa samun kulawa yadda ya kamata sakamakon Tambai din ta kwana biyu, kuma girman kauye ce.
A kwana ukku da Amina ta yi Hajiya Saude gani ta yi sassanta ya dawo sabo kal. Ta yi kewar su ba kadan ba bayan komawarsu Bauchi. Kowa na gidan ya yi kewar Amina don mutum ce mai saukin kai da dadin muamala duk yayan Baba Liman sun saba da ita.
****
WATA SABUWA
Bayan Little ta koma makaranta da sati biyu aka bugowa Babanta waya daga ofishin shugabar makarantarsu cewa ba ta da lafiya. A take ya tsallake abin da ke gabansa ya shirya musu tafiya Lagos shi da Amina. A Clinic din makarantar suka riske ta a kwance ana kula da ita. Ya karasa jikin gadon jikin sa na kyarma ya dafa kanta ya tambaye ta me ke damunta?
Cikin sassanyar muryarta take masa bayani.
Daddy watarana in na zauna ba na iya tashi tsaye sai an daga ni.
Hankalin Amina da na Maarouf ya yi mummunan tashi.
Ameena little ta cigaba da cewa,
Cikin kashin kafata in na tsugunna sai in ji kamar zai tsage, sannan kafafuna suna karkarwa in na dade a tsaye.
A take Amina ta janyo ta ta soma dudduba ta, to babu kayan aiki a tare da ita, don haka ta nemi izinin Maarouf na son yin magana da Dr. Turaki.
Shi ya kira shi da kansa ya hada su. Amina ta gaya masa matsalar da ta biyo bayan warkewar Ameena. Suka yi magana irin tasu ta likitoci. Ta mika wa Maarouf wayar ya ce da shi su zo da ita asibiti a duba ta sosai. Makaranta ta ba da izni suka taho da Ameena Bauchi.
A wannan satin Ameena karama ta zo hutun (third-term) daga makarantar da Babanta ya kai ta a Lagos. Ta tadda Antinta a upstairs’ tare da Babanta a gida daya kuma daki daya. Ta kuwa hau murna ba yar kadan ba. Kullum tana manne da Antin nata ko tsakiyar iyayen nata biyu tana sakin hira. Farin ciki ya cika ta ta rasa inda za ta sanya kanta don farin ciki.
Amina ta roki Maarouf da ya shirya musu zuwa Ji-Kas ita da Little za su je su yi wa Hajiya kwana uku.
Ya ce, Ni kuma fa? Haka za ku bar ni ni daya kamar maye Amina da Amina?
Kwana uku kamar kiftawar ido ne Your Excellency, na kwana biyu ban ga Hajiya ba, Ameena ma tana ta zancenta. Nayi-nayi ka dawo da Anty Laila ai ka ki saboda irin haka, mai mata daya fa aka ce aminin gwauro ne.
Nan da nan ya yi fuska, Kin jawo wa kanki fasa zuwa Ji-kas din, na kuma gane ba kya kishina ko kadan Amina. Ai sai ki dawo da Lailar tunda igiyar aurenta ai tana hannunki.
Na tuba, na bi Allah na bi ka, ba nufina kenan ba. Kawai na ga ya kamata zuwa yanzu a ce ka huce daga fushin da ka ke yi da ita, amma tunda hakan shi ne decision dinka ba ni da say Baban Ameena.
Da kyar ta shawo kansa ya sauko daga fushin nasa. Wannan ta sha faruwa ba sau daya ba, ba sau biyu ba tun barin Laila gidan da dawowar Amina daga jinya a asibitin da Laila ta yi mata sanadin minor-surgery a cikin kai.
Idan Maarouf ya ce ba ta kishinsa a kan Laila hankalinta yana tashi. Domin da bacin rai yake fada, ko uwar da ta haife shi tunda ya nuna mata ba ya son zancen komen Laila ta daina yi masa sai ita?
A nata bangaren Amina ba rashin kishi ba ne, ba dai ta son zama kwarkwata fidda mai giji, ba ta so a ce a kanta wani ya shiga wani hali ko kankani, zuciyarta mai kyau ce maabociyar imani, idan akwai abin da ta ke kishi a duniya, to Maarouf Ji-Kas ne!Kishi kuwa wanda ko a tarihi babu irinsa. Amma na musulunci.
Ta kudire a zuciyarta ba za ta kyale shi ba, in dai ta samu faraga ta ganinshi cikin nishadi za ta ambato neman alfarmarta na a mayar da Laila ba don halinta ba. Tunda Annabi mai tsira da aminci ya ce, Imanin dayanku ba ya cika har sai ya so wa dan uwansa abin da yake so wa kansa.
Tana so wa kanta Maarouf tana so wa kanta rayuwa da shi. Ta tsaya ma tana cewa tana sonshi bata baki ne, don haka tana kishin abinta. Sai dai ba za ta bari kishin ya dakusar da kaifin imaninta ba.
****
Sun isa Ji-kas lafiya ana kiraye-kirayen sallar magriba. Hajiya tana alwala sai ji ta yi Little ta dafe ta ta baya. Ta ce, Ho! yar nema, ni kada ki karasa ni.
Little Ameena na dariya ta ce da karfi, Hajiyan Ji-kas!.
Ta ce, Ni Saudatu sunana, ubanki ne Ji-Kas!
Amina da kishiyar Hajiyan suka yi dariya, Hajiya da jikanyarta kullum suka hadu sai sun ba da dariya.
Amina ta nemi buta ita ma ta yi alwala suka bi jamin sallar magariba daga masallaci. Hajiya ta rasa ina ta-ka-sa-ka, ina ta-ka-a-je da surukarta, inda duk ta mika hannu kwano ta ke janyowa cike da abincin da makota ke kawo mata da wanda mai aikinta ta dafa mata, fadi ta ke,
Zabi wanda za ki ci Dr. Amina, kin san nan kauye ne ba ma cin cima kala daya. Zabi duk wanda ki ke so.
Amina ta yi murmushi ta zabi burabuskon gero da miyar taushe wanda aka dafa wa Hajiya. Hira suke sosai kamar uwa da yarta yawanci duk a kan abin da ya shafi Maarouf ne da siyasarshi.
Ana haka Amina ta sako zancen Laila, Hajiya ba za ki roki Baban Ameena ya maida Anty Laila ba? Saura kadan fa ta kare iddarta. Bana so su rabu kwata-kwata a dalilina.
Hajiya ta girgiza kai,
Ko kusa, kada ki kara sanya wa ranki da ke cikin dalilan rabuwarsu. An samu sabanin halayya tsakanin Maarouf da Laila, mun ganganda (rushing) wajen tabbatar da aure a tsakaninsu ba tare da binciken halayya ba, inda za ki san ba ke ce sanadi ba hatta iyayenta da yan uwanta ba sa jin dadinta, sanda tana gidan yaron nan. Sawun barawo naki alamarin ya taka don haka ki daina damun kanki.
Zan tsaya kan ya maida ta din amma ba yanzu ba, sai ta kara tarbiyyantuwa. Don labari yana zuwar min kala-kala tana can nadamar rayuwa ta ishe ta duk surfen gidansu da sanwar gidansu ita ta ke yinta, kin ga ko ai Laila in mai hankali ce dole ta shiga karatun ta-nutsu.
Amina ta langabar da kai, Ni tsorona Hajiya kada iddar ta kare wani ya fito ya aure ta.
Hajiya ta ce, To ba shi kenan ba?Allah ya hada kowa da rabonsa. Ni yanzu na daina gaggawa a kan aure Aminatu.
Dole Amina ta yi shiru don ta fahimci daga Hajiyar har danta sun hau doki guda, ba za ta iya sauko da su ba, sai ranar da Allah ya nufa.
Da za su kwanta ta canza zuwa kayan barci masu kauri ta daura zanin atamfa a kai, ta kakkabe wa Hajiya gado, kayan da ta tara tsibi guda ba ninki bayan ba masu dauda ba ne, ta ninke mata su ta shirya mata a sif, lungu da saqo na dakin Amina ta bi ta kakkale shi tana mamakin wace irin mai aiki ce Tambai da a kicin da dahuwar abinci kawai ta ke aiki?
To daga ita har Hajiyar sun kwana biyu ba za su iya wannan (neatness) din ba. Ta sawa ranta alkawarin zuwa Ji-Kas akai-akai da kula da Hajiya kamar yadda za ta kula da Goggo, ta wanke mata bayi kal sai sheki da tashin kamshi yake kamar ba bayan gida ba.
Ta kuma koya wa Tambai yadda ake wankin bayi na zamani ta gane sosai. Hajiyar sai albarka ta ke sanya mata har suka kwanta barci.
Washegari ita ta yi wa Hajiya girkin rana da na dare. Har zuwa ranar da za su taho ita ke yi wa Hajiya girki da shara da gyaran bangarenta.
Babu abinda Maarouf bai sanya mata ba na saukaka rayuwa, amma ba sa samun kulawa yadda ya kamata sakamakon Tambai din ta kwana biyu, kuma girman kauye ce.
A kwana ukku da Amina ta yi Hajiya Saude gani ta yi sassanta ya dawo sabo kal. Ta yi kewar su ba kadan ba bayan komawarsu Bauchi. Kowa na gidan ya yi kewar Amina don mutum ce mai saukin kai da dadin muamala duk yayan Baba Liman sun saba da ita.
****
WATA SABUWA
Bayan Little ta koma makaranta da sati biyu aka bugowa Babanta waya daga ofishin shugabar makarantarsu cewa ba ta da lafiya. A take ya tsallake abin da ke gabansa ya shirya musu tafiya Lagos shi da Amina. A Clinic din makarantar suka riske ta a kwance ana kula da ita. Ya karasa jikin gadon jikin sa na kyarma ya dafa kanta ya tambaye ta me ke damunta?
Cikin sassanyar muryarta take masa bayani.
Daddy watarana in na zauna ba na iya tashi tsaye sai an daga ni.
Hankalin Amina da na Maarouf ya yi mummunan tashi.
Ameena little ta cigaba da cewa,
Cikin kashin kafata in na tsugunna sai in ji kamar zai tsage, sannan kafafuna suna karkarwa in na dade a tsaye.
A take Amina ta janyo ta ta soma dudduba ta, to babu kayan aiki a tare da ita, don haka ta nemi izinin Maarouf na son yin magana da Dr. Turaki.
Shi ya kira shi da kansa ya hada su. Amina ta gaya masa matsalar da ta biyo bayan warkewar Ameena. Suka yi magana irin tasu ta likitoci. Ta mika wa Maarouf wayar ya ce da shi su zo da ita asibiti a duba ta sosai. Makaranta ta ba da izni suka taho da Ameena Bauchi.