Sashe 10
Sanadin Kenan Part 4 Complete Hausa Novel · about 11 min read
WAIWAYE
Laila ta cika iddarta, ba da jimawa ba zawarawa suka soma damun Dagaci da aike, ciki kuwa har da tsohon (fiance) dinta Mahdi maaikaci a gidan rediyon Jigawa. Dagaci ya zaunar da ita a wani marece ita da mahaifiyarta, ya ce.
Laila, yau wata uku kenan da gama iddarki, babu Maarouf babu aikensa, ga manema Allah ya ba ki tun gama iddarki, don haka na ba ki sati biyu ki fidda gwani a cikinsu, in kuma za ki bi shawarata to ki zabi Mahdi, da sabon gini gwanda yabe.
An sanshi, an san asalinsa, ke kika jawo ya janye auren ki a wancan lokacin, amma ya rage naki. Ni dai na ba ki sati biyu ki kawo min mijin aure cikin mutum hudun nan da suka addabe ni.
Kin san ni sarai bana son rainin hankali, ba don addini ne ya ba ki wannan yancin ba da sai dai ki ji na daura miki aure.
Laila na share hawaye ta tashi ta bar wajen, mahaifiyarta ta yi tsaki ta ce,
Halin mutum ya ja masa ya ishi mutane da koke-koke. Amma abin ki da mahaifiya, can cikin zuciyarta tausayin ta take ji, koda bata amfanuwa da komai a zaman Laila gidan Jikas,tana yi mata fatan komawa.
Mahdi tsohon saurayin Laila ne, har an sa musu ranar aure, ya aiko ya karbi kayanshi ya ce ya fasa, a sabili da har lokacin da aka yi musu baikon Laila ba ta daina sauraron sauran samarinta ba, shi kuma ga shi da kishi, ya yi ya yi ta bari ta ki, shi ya sa ya aiko ya ce ya fasa, ya karbi kayansa.
Iyayenta duka a lokacin babu wanda ya ga laifinsa don su ma shaida ne, sun kuma tsawatar mata a lokacin ta ki ji sabida giggiwarta. Don haka yanzu da ya dawo ya ce zai aure ta a bazawararta shi ko auren fari bai yi ba, duk suka hadu suka yi naam da shi. Amma har kwanakin da Baban ya diba mata suka cika Laila ta ki cewa uffan. Har kullum tunaninta na ba ta cewa, Maarouf zai dawo gare ta ko ba dade ko ba-jima.
To amma haka za ta yi ta zama tana jiran tsammanin warabbuka? (inji Mairon ABARI YA HUCE) Don haka ta yanke wa zuciyarta zuwa kai tsaye har inda Maarouf yake ta roke shi gafara, ta gaya masa ta yi nadama za ta rayu da shi da duk abin da ya yi mata umarni, yake kuma son ya rayu tare da shi. Don ta lura Hajiya Saude a wannan karon duk kawaicinta sai abin da Dan nata yake so za ta bi.
Ta yi shiri tsaf ta ce da mahaifiyarta za ta je Gwaram wajen wata tsohuwar aminiyarta, Innar ba ta hana ta ba, don ta san yadda suke da Hannatun. Amma data samu rayuwa yadda take so ai watsar da Hannatun tayi,Lailah kenan.
Tana zuwa tasha ta yi shatar karamar mota har Bauchi don bata son bata lokaci, tasan lokacin da yake dawowa daga ofis zata isa in a karamar motarta ne da yake akwai isassun kudi a tareda ita.
Sojojin da ke gadin gidan gwamnatin duk sun san fuskar Laila a matsayin matar mai girma gwamna, babu kuma wanda ya san ya sake ta a cikinsu sun dauka tafiya tayi kamar yadda ta saba duk da cewa wannan karon ta dade fiyeda tsammani, ko kuma sun samu sabani ne a dalilin sabon auren da yayi, don haka sun yi mamakin ganin a yadda ta zo yau da motar da ta kawo ta, sai suka ki yarda su barta ta shiga, suka ce ta jira sai sun yi bincike tukunna.
Waya suka yi ta bugawa har suka samu yin magana da Amina. Suka fada mata ko wace ce ta zo, kuma wai tana son a barta ta shigo. Amina ta yi musu iznin su barta ta shigo su kawo ta har downstairs.
A dakin Amina na da aka sauki Laila. Ta zuba uban tagumi, ta tsura wa hoton Maarouf da Amina da yarsu Ameena ido, suna manne da juna sun yi kyau, sun yi kyan har sun gaji. Katon hoto ne da ya kusan cinye bango guda, sun dauke shi ne a hotel dinsu na birnin Jeddah bayan Amina ta samu lafiyar kafafunta a karo na biyu.
Duniya juyi!.
Laila ta ce a zuciyarta, da ta tuna yadda ta ke zuba mulki a gidan nan rana daya duniya ta yi mata gwatson mage. Amina ta hambare gwamnatinta, ta maida ta kauye.
Tsanar Amina ta kara ninkuwa a zuciyar Laila, ji ta ke da da hali da ta danne ta da filo ta mutu ta huta. Amma ta yi amanna da cewa in har tana son ci gaba da zama da Maarouf dole ta koyi kissa wadda ada bata iya ba, take abubuwanta keke-da-keke, dole ta yakice wa kanta kishin Amina, ko ta ki ko ta so. Ta tusawa ranta kaunar wannan gawa ta ki ramin yar tasa.
Ta nisa, ta ja dogon numfashi, daidai lokacin da mai aiki ta shigo da trolleydin abincin rana, ta jere mata su a diningta gaishe ta ta fita. Babu wani girmamawa ko jin tsoro irin yadda suke mata a baya, kamar ma ba su ji dadin ganinta ba, sun tuno yadda ta ke cin zarafinsu ne ga shi yau ita da su an zama daya.
Sai da umarni za a ga uwargidan gwamna mai mutumta su da karrama su. Har gara ma su, sun fi ta tsafta da kyan gani a yadda ta koma din nan.
Maarouf ya fito daga wanka, bayan shigowarsa cin abincin rana.Amina na jiransa a gefen gado ta mike tana tsane masa jiki da karamin towel, ta fiddo masa kayan da zai sanya bayan ta feshe su da turarensa.
Dawowarsa kenan daga ofis ya shiga wankan ya fito. Sai da ta gama taimaka masa ya shirya ya janyo ta jikinsa yana fada mata, I have a green great giant surprise for you. Ki shirya wani kauye za mu je.
Ta kwantar da kai a kirjinsa tana shakar kamshinbath-gel din da yayi wanka dashi,sannan ta ce, Kana da baki your excellency, ka fara (attending) dinsu sannan mu tafi.
Ya dago fuskarta da tafukan hannayensa biyu ya soma (kissing) dinta lightly cikin wata irin siga har sai da dukkaninsu suka soma fitanutsuwarsu, sannan Amina ta yi karfin halin janyewa ta ce,
Da gaske kana da baki, I would like you to attend to them first, sai mu je duk inda za mu.
Harararta ya yi, sannan yayi tsaki yana saka rigarsa
Wadanne irin baki ne zan je inda suke alhalin ban san ko su waye ba?
Ka yi hakuri dai ka je, ka sani ba zan kawo wadanda za su cuce ka har sassan nan ba, haka (securities) din da ke cike da gidan nan, don Allah ka je.
Da mamakinta ya ce, Suna ina? Ai sai ki wuce mu je tare in dodanni ne su fara cinye ki, haka kawai za ki tura ni wajen wadanda ban sani ba, ban san me ya kawo su ba?.
Dariya Amina ta yi ta yi gaba ta zura takalminta marar tsayin dunduniya,
Na yarda, wuce mu je. Ni a gaba kai a baya.
Har ya zauna a kan kujerar hutawar da Amina ta fiya zama a kai lokacin aikinta a gidan bai gane Lailah ba, wadda kanta ke sunkuye. A sabili da abubuwa da yawa ya kasa gane ta. Na farko dai ta yi duhu tunda babu mayukan nan masu tsada na shafe-shafe. Na biyu ta yi lullubi wanda a da ba ta yi, sannan sitturun jikinta duk sun kode. Yana zama Amina ta kama hanyar fita, amma sai ta ji ya riko hannunta ta baya.
Juyowa ta yi ta dube shi da idanuwan nan nata masu kama da zaiba don sheki da kyalli, ta girgiza masa kai alamar ya barta ta tafi. Ita ma tata zuciyar fal da wani irin kishi da bata san tana da shi ba, jin ta tayi ta rikide kamar ba ita batamkar wata mai (multi-personality disorder)amma ta yi kokarin hadiye shi. Ta yi magana ba tareda ta yarda sun hada idanu ba.
Anty Laila ce ta zo ganinka.
Da haka ta kwace hannunta ta fice.
Laila ta sauko daga kan kujera ta rarrafo gabansa ta zube ta rushe da wani irin kuka.
Mikewa tsaye ya yi da hanzari.
Zan fita in zuwa ki ka yi ki tada min hankali. Me aka yi? Haka kawai ki zo min gida ki rusa kuka bayan ba wanda ya mutu cikin gidan?
Laila ta tabbatar in ya fita kyakkyawar damar da ta samu ta ganinsa ta kubuce mata, don ba ta isa ta ganshi a ofis ba ko wani waje, ta yi saurin kama kafarsa ta rike ta soma jero masa ban hakuri masu nuna tsantsar nadamarta.
Tana rokonsa ya yi mata alfarma cikin irin dimbin alfarmominsa ga alumma ya maida ita dakinta, ta yi alkawarin zai same ta mai biyayya a gare shi da zama lafiya da abokiyar zamanta, da kula da yar sa, da guje wa duk abin da ya furta ba ya so.
Sai da ta dasa aya ya janye kafarsa ya koma gefe ya zauna. Ya sarke hannayensa cikin na juna ya tallafi habar sa dasu. Ya dube ta sosai tana faman share ruwan idanunta. A nitse ya soma yi mata magana irin wadda bai taba gaya mata ba, ba ta kuma taba zaton yana kunshe da su a zuciyarsa ba.
Ta ya ya zan iya kuma ci gaba da zama da ke Laila? Ba kya girmama mahaifiya ta, ba ki damu da ita ba, ba kya kaunar abin da na haifa ko da da tausayi ne, ba kya tausaya min ba kya bani hakkin aure yadda ya kamata alhalin kinsan banida wata matar bayan ke kuma ni ba mazinaci bane, ba kya mutunta aurenki harkar neman kudi kawai ki ka sa a gaba.
Idan na ce ba na son abu ke kuma a lokacin za ki nuna min yanzu ki ka fara sonsa, kin maida ni bankin karbar kudi ba mijin aure ba. Tunda na aure ki ba ki taba girka min abin da zan ci da hannunki, ba ki taba kula da alamarina ba sai alamuran kawaye da buga-bugar karbar kudin siyasa ne kawai a gabanki. Na bi kowacce hanya don in zauna lafiya da ke na kasa billewa.
Na yi aure don in samu nutsuwa da karin zuria kin nuna ke mai iya aikata kisan gilla ce a kan hakan. Ta ina zaman aure zai ci gaba da irin wannan matar a ganinki Lailah?
Ki yi hakuri ki rungumi kaddarar da Allah ya rubuto mana, ta cewa za mu rayu tare na wucin gadi ne amma kowannenmu da tabbataccen abokin rayuwarsa wanda zai samu nutsuwa a tare da shi.
Na yi alkawarin zan yi muku komai na rayuwa ke da mijin da Allah ya ba ki, amma aure a tsakaninmu ya kare. Don ba zan so in tashi a ranar lahira da shanyayyen barin jiki ba na rashin yin adalci a tsakaninki da matata. Laila Im sorry, ki duba (account) dinki zuwa gobe za ki tadda sakona. Na barki lafiya.
Ya fice da hanzari ya bar Laila durkushe tana gursheken kuka. Baya so ya bar tausayin da ya tsirga a zuciyarsa ya yi tasiri. A ganin sa hakan da ya yi shi ne daidai, kuma shi ya fi dacewa da rayuwar kowannensu. Laila ba kaunarsa ta ke ba, kudinsa da kyale-kyalen rayuwar da ke tare da shi ta ke hange. Ya yarda da hakan, yana so ita ma ta yarda.
Ya yi alkawarin ba ta su (kudi da kyale-kyalen) amma ban da Maarouf da gangar jikinsa.
Haka Laila ta baro gidan gwamnati wutsiya a zage amma zuciyarta a dake. Ta tabbata ta bar gidan da mai shi har abada. Ta auna kalamansa a sikeli na hankali da tunani babu wanda ba ta amince gaskiya ya fada ba. Abu daya ne ba ta amince ba da Maarouf ya ce ba ta sonsa, kudinsa ta ke so. Ta amince farkon zuwansa rayuwarta da gaske kudin ta ke so, amma ban da yanzu. Ita kanta ba ta san hakan ba sai da ya bar rayuwarta kwata-kwata.
Ta amince ta hakura da Maarouf har abada, za ta je ta gina sabuwar rayuwa ta manta da shi da duk abin da ya shafe shi, tunda ba shi ne autan maza ba.
A washegarin ranar ta samu (alert) na zunzurutun kudi naira miliyan goma shha biyar cikin asusunta. Amma ga mamakinta ta kasa yin farin ciki da su. Yanzu ne ta gane cewa, SO YA FI KUDI, amma tata soyayyar ta zo (at a wrong time). Da a ce ta san (account number) dinsa mayar masa da su za ta yi.
A ranar ta tabbatar wa mahaifinta ta zabi Mahdi a matsayin mijin aure. Ta yi aniyar gyara zuciyarta ta koyi yin komai saboda Allah, ta daura aniyar yin amfani da damarta a lokacin da ta zo mata ba za ta kara wasa da ita ba, ta koyi girmama iyayen miji da yan uwanta da duk dan Adam din da rayuwa ta hada su tare. Za ta koyi daukar duniya da sauki ta rage (high taste) domin ba ya amfanar da kai komai. Ubangiji ya dankwafar da shaidan ne saboda girman kansa.
Ta yarda da duk laifuffukanta da Maarouf ya zano, wadanda ba za su bari ya iya ci gaba da rayuwar aure da ita ba. Tana rokon Allah ya sa yadda ta yi aniyar gyara halayen nan nata halayen su gyaru a rayuwar aurenta na gaba. Zuciyarta ta gyaru ta koma yin komai saboda Allah.
Laila ta cika iddarta, ba da jimawa ba zawarawa suka soma damun Dagaci da aike, ciki kuwa har da tsohon (fiance) dinta Mahdi maaikaci a gidan rediyon Jigawa. Dagaci ya zaunar da ita a wani marece ita da mahaifiyarta, ya ce.
Laila, yau wata uku kenan da gama iddarki, babu Maarouf babu aikensa, ga manema Allah ya ba ki tun gama iddarki, don haka na ba ki sati biyu ki fidda gwani a cikinsu, in kuma za ki bi shawarata to ki zabi Mahdi, da sabon gini gwanda yabe.
An sanshi, an san asalinsa, ke kika jawo ya janye auren ki a wancan lokacin, amma ya rage naki. Ni dai na ba ki sati biyu ki kawo min mijin aure cikin mutum hudun nan da suka addabe ni.
Kin san ni sarai bana son rainin hankali, ba don addini ne ya ba ki wannan yancin ba da sai dai ki ji na daura miki aure.
Laila na share hawaye ta tashi ta bar wajen, mahaifiyarta ta yi tsaki ta ce,
Halin mutum ya ja masa ya ishi mutane da koke-koke. Amma abin ki da mahaifiya, can cikin zuciyarta tausayin ta take ji, koda bata amfanuwa da komai a zaman Laila gidan Jikas,tana yi mata fatan komawa.
Mahdi tsohon saurayin Laila ne, har an sa musu ranar aure, ya aiko ya karbi kayanshi ya ce ya fasa, a sabili da har lokacin da aka yi musu baikon Laila ba ta daina sauraron sauran samarinta ba, shi kuma ga shi da kishi, ya yi ya yi ta bari ta ki, shi ya sa ya aiko ya ce ya fasa, ya karbi kayansa.
Iyayenta duka a lokacin babu wanda ya ga laifinsa don su ma shaida ne, sun kuma tsawatar mata a lokacin ta ki ji sabida giggiwarta. Don haka yanzu da ya dawo ya ce zai aure ta a bazawararta shi ko auren fari bai yi ba, duk suka hadu suka yi naam da shi. Amma har kwanakin da Baban ya diba mata suka cika Laila ta ki cewa uffan. Har kullum tunaninta na ba ta cewa, Maarouf zai dawo gare ta ko ba dade ko ba-jima.
To amma haka za ta yi ta zama tana jiran tsammanin warabbuka? (inji Mairon ABARI YA HUCE) Don haka ta yanke wa zuciyarta zuwa kai tsaye har inda Maarouf yake ta roke shi gafara, ta gaya masa ta yi nadama za ta rayu da shi da duk abin da ya yi mata umarni, yake kuma son ya rayu tare da shi. Don ta lura Hajiya Saude a wannan karon duk kawaicinta sai abin da Dan nata yake so za ta bi.
Ta yi shiri tsaf ta ce da mahaifiyarta za ta je Gwaram wajen wata tsohuwar aminiyarta, Innar ba ta hana ta ba, don ta san yadda suke da Hannatun. Amma data samu rayuwa yadda take so ai watsar da Hannatun tayi,Lailah kenan.
Tana zuwa tasha ta yi shatar karamar mota har Bauchi don bata son bata lokaci, tasan lokacin da yake dawowa daga ofis zata isa in a karamar motarta ne da yake akwai isassun kudi a tareda ita.
Sojojin da ke gadin gidan gwamnatin duk sun san fuskar Laila a matsayin matar mai girma gwamna, babu kuma wanda ya san ya sake ta a cikinsu sun dauka tafiya tayi kamar yadda ta saba duk da cewa wannan karon ta dade fiyeda tsammani, ko kuma sun samu sabani ne a dalilin sabon auren da yayi, don haka sun yi mamakin ganin a yadda ta zo yau da motar da ta kawo ta, sai suka ki yarda su barta ta shiga, suka ce ta jira sai sun yi bincike tukunna.
Waya suka yi ta bugawa har suka samu yin magana da Amina. Suka fada mata ko wace ce ta zo, kuma wai tana son a barta ta shigo. Amina ta yi musu iznin su barta ta shigo su kawo ta har downstairs.
A dakin Amina na da aka sauki Laila. Ta zuba uban tagumi, ta tsura wa hoton Maarouf da Amina da yarsu Ameena ido, suna manne da juna sun yi kyau, sun yi kyan har sun gaji. Katon hoto ne da ya kusan cinye bango guda, sun dauke shi ne a hotel dinsu na birnin Jeddah bayan Amina ta samu lafiyar kafafunta a karo na biyu.
Duniya juyi!.
Laila ta ce a zuciyarta, da ta tuna yadda ta ke zuba mulki a gidan nan rana daya duniya ta yi mata gwatson mage. Amina ta hambare gwamnatinta, ta maida ta kauye.
Tsanar Amina ta kara ninkuwa a zuciyar Laila, ji ta ke da da hali da ta danne ta da filo ta mutu ta huta. Amma ta yi amanna da cewa in har tana son ci gaba da zama da Maarouf dole ta koyi kissa wadda ada bata iya ba, take abubuwanta keke-da-keke, dole ta yakice wa kanta kishin Amina, ko ta ki ko ta so. Ta tusawa ranta kaunar wannan gawa ta ki ramin yar tasa.
Ta nisa, ta ja dogon numfashi, daidai lokacin da mai aiki ta shigo da trolleydin abincin rana, ta jere mata su a diningta gaishe ta ta fita. Babu wani girmamawa ko jin tsoro irin yadda suke mata a baya, kamar ma ba su ji dadin ganinta ba, sun tuno yadda ta ke cin zarafinsu ne ga shi yau ita da su an zama daya.
Sai da umarni za a ga uwargidan gwamna mai mutumta su da karrama su. Har gara ma su, sun fi ta tsafta da kyan gani a yadda ta koma din nan.
Maarouf ya fito daga wanka, bayan shigowarsa cin abincin rana.Amina na jiransa a gefen gado ta mike tana tsane masa jiki da karamin towel, ta fiddo masa kayan da zai sanya bayan ta feshe su da turarensa.
Dawowarsa kenan daga ofis ya shiga wankan ya fito. Sai da ta gama taimaka masa ya shirya ya janyo ta jikinsa yana fada mata, I have a green great giant surprise for you. Ki shirya wani kauye za mu je.
Ta kwantar da kai a kirjinsa tana shakar kamshinbath-gel din da yayi wanka dashi,sannan ta ce, Kana da baki your excellency, ka fara (attending) dinsu sannan mu tafi.
Ya dago fuskarta da tafukan hannayensa biyu ya soma (kissing) dinta lightly cikin wata irin siga har sai da dukkaninsu suka soma fitanutsuwarsu, sannan Amina ta yi karfin halin janyewa ta ce,
Da gaske kana da baki, I would like you to attend to them first, sai mu je duk inda za mu.
Harararta ya yi, sannan yayi tsaki yana saka rigarsa
Wadanne irin baki ne zan je inda suke alhalin ban san ko su waye ba?
Ka yi hakuri dai ka je, ka sani ba zan kawo wadanda za su cuce ka har sassan nan ba, haka (securities) din da ke cike da gidan nan, don Allah ka je.
Da mamakinta ya ce, Suna ina? Ai sai ki wuce mu je tare in dodanni ne su fara cinye ki, haka kawai za ki tura ni wajen wadanda ban sani ba, ban san me ya kawo su ba?.
Dariya Amina ta yi ta yi gaba ta zura takalminta marar tsayin dunduniya,
Na yarda, wuce mu je. Ni a gaba kai a baya.
Har ya zauna a kan kujerar hutawar da Amina ta fiya zama a kai lokacin aikinta a gidan bai gane Lailah ba, wadda kanta ke sunkuye. A sabili da abubuwa da yawa ya kasa gane ta. Na farko dai ta yi duhu tunda babu mayukan nan masu tsada na shafe-shafe. Na biyu ta yi lullubi wanda a da ba ta yi, sannan sitturun jikinta duk sun kode. Yana zama Amina ta kama hanyar fita, amma sai ta ji ya riko hannunta ta baya.
Juyowa ta yi ta dube shi da idanuwan nan nata masu kama da zaiba don sheki da kyalli, ta girgiza masa kai alamar ya barta ta tafi. Ita ma tata zuciyar fal da wani irin kishi da bata san tana da shi ba, jin ta tayi ta rikide kamar ba ita batamkar wata mai (multi-personality disorder)amma ta yi kokarin hadiye shi. Ta yi magana ba tareda ta yarda sun hada idanu ba.
Anty Laila ce ta zo ganinka.
Da haka ta kwace hannunta ta fice.
Laila ta sauko daga kan kujera ta rarrafo gabansa ta zube ta rushe da wani irin kuka.
Mikewa tsaye ya yi da hanzari.
Zan fita in zuwa ki ka yi ki tada min hankali. Me aka yi? Haka kawai ki zo min gida ki rusa kuka bayan ba wanda ya mutu cikin gidan?
Laila ta tabbatar in ya fita kyakkyawar damar da ta samu ta ganinsa ta kubuce mata, don ba ta isa ta ganshi a ofis ba ko wani waje, ta yi saurin kama kafarsa ta rike ta soma jero masa ban hakuri masu nuna tsantsar nadamarta.
Tana rokonsa ya yi mata alfarma cikin irin dimbin alfarmominsa ga alumma ya maida ita dakinta, ta yi alkawarin zai same ta mai biyayya a gare shi da zama lafiya da abokiyar zamanta, da kula da yar sa, da guje wa duk abin da ya furta ba ya so.
Sai da ta dasa aya ya janye kafarsa ya koma gefe ya zauna. Ya sarke hannayensa cikin na juna ya tallafi habar sa dasu. Ya dube ta sosai tana faman share ruwan idanunta. A nitse ya soma yi mata magana irin wadda bai taba gaya mata ba, ba ta kuma taba zaton yana kunshe da su a zuciyarsa ba.
Ta ya ya zan iya kuma ci gaba da zama da ke Laila? Ba kya girmama mahaifiya ta, ba ki damu da ita ba, ba kya kaunar abin da na haifa ko da da tausayi ne, ba kya tausaya min ba kya bani hakkin aure yadda ya kamata alhalin kinsan banida wata matar bayan ke kuma ni ba mazinaci bane, ba kya mutunta aurenki harkar neman kudi kawai ki ka sa a gaba.
Idan na ce ba na son abu ke kuma a lokacin za ki nuna min yanzu ki ka fara sonsa, kin maida ni bankin karbar kudi ba mijin aure ba. Tunda na aure ki ba ki taba girka min abin da zan ci da hannunki, ba ki taba kula da alamarina ba sai alamuran kawaye da buga-bugar karbar kudin siyasa ne kawai a gabanki. Na bi kowacce hanya don in zauna lafiya da ke na kasa billewa.
Na yi aure don in samu nutsuwa da karin zuria kin nuna ke mai iya aikata kisan gilla ce a kan hakan. Ta ina zaman aure zai ci gaba da irin wannan matar a ganinki Lailah?
Ki yi hakuri ki rungumi kaddarar da Allah ya rubuto mana, ta cewa za mu rayu tare na wucin gadi ne amma kowannenmu da tabbataccen abokin rayuwarsa wanda zai samu nutsuwa a tare da shi.
Na yi alkawarin zan yi muku komai na rayuwa ke da mijin da Allah ya ba ki, amma aure a tsakaninmu ya kare. Don ba zan so in tashi a ranar lahira da shanyayyen barin jiki ba na rashin yin adalci a tsakaninki da matata. Laila Im sorry, ki duba (account) dinki zuwa gobe za ki tadda sakona. Na barki lafiya.
Ya fice da hanzari ya bar Laila durkushe tana gursheken kuka. Baya so ya bar tausayin da ya tsirga a zuciyarsa ya yi tasiri. A ganin sa hakan da ya yi shi ne daidai, kuma shi ya fi dacewa da rayuwar kowannensu. Laila ba kaunarsa ta ke ba, kudinsa da kyale-kyalen rayuwar da ke tare da shi ta ke hange. Ya yarda da hakan, yana so ita ma ta yarda.
Ya yi alkawarin ba ta su (kudi da kyale-kyalen) amma ban da Maarouf da gangar jikinsa.
Haka Laila ta baro gidan gwamnati wutsiya a zage amma zuciyarta a dake. Ta tabbata ta bar gidan da mai shi har abada. Ta auna kalamansa a sikeli na hankali da tunani babu wanda ba ta amince gaskiya ya fada ba. Abu daya ne ba ta amince ba da Maarouf ya ce ba ta sonsa, kudinsa ta ke so. Ta amince farkon zuwansa rayuwarta da gaske kudin ta ke so, amma ban da yanzu. Ita kanta ba ta san hakan ba sai da ya bar rayuwarta kwata-kwata.
Ta amince ta hakura da Maarouf har abada, za ta je ta gina sabuwar rayuwa ta manta da shi da duk abin da ya shafe shi, tunda ba shi ne autan maza ba.
A washegarin ranar ta samu (alert) na zunzurutun kudi naira miliyan goma shha biyar cikin asusunta. Amma ga mamakinta ta kasa yin farin ciki da su. Yanzu ne ta gane cewa, SO YA FI KUDI, amma tata soyayyar ta zo (at a wrong time). Da a ce ta san (account number) dinsa mayar masa da su za ta yi.
A ranar ta tabbatar wa mahaifinta ta zabi Mahdi a matsayin mijin aure. Ta yi aniyar gyara zuciyarta ta koyi yin komai saboda Allah, ta daura aniyar yin amfani da damarta a lokacin da ta zo mata ba za ta kara wasa da ita ba, ta koyi girmama iyayen miji da yan uwanta da duk dan Adam din da rayuwa ta hada su tare. Za ta koyi daukar duniya da sauki ta rage (high taste) domin ba ya amfanar da kai komai. Ubangiji ya dankwafar da shaidan ne saboda girman kansa.
Ta yarda da duk laifuffukanta da Maarouf ya zano, wadanda ba za su bari ya iya ci gaba da rayuwar aure da ita ba. Tana rokon Allah ya sa yadda ta yi aniyar gyara halayen nan nata halayen su gyaru a rayuwar aurenta na gaba. Zuciyarta ta gyaru ta koma yin komai saboda Allah.