Sashe 23
Me Zanyi Da Ita Part Complete 2 Complete Hausa Novel · about 7 min read
Cak tayi da tea cup a hannunta tana ‘kare masa kallo cikin shigar doguwar rigar ta ta shadda as usual yanzu ma kanta ba d’ankwali. Sarai yaji idonta a kansa yayi mata banza yana dur’kushe a gefe yana gaida su dada da Hajiya mama da momma. Dada ta dubi shatu tsaki tayi “kiji min ‘yar banzar yarinya ba zaki gaida mijinnaki ba.” Da sauri yace “ta bar gaisuwarta jeki bedrroom d’ina da toilet ki gyara min” ya fad’a yana tsareta da ido tsaki momma tayi “akan me duk ina house helpers d’in gidan da sai ita zata gyara maka don wani sabon iyayi gidan ma da yau zaka barshi.” Dada ta zabura tace “Auzubillahi kuji min mata tana neman jawo mana masifa da ranar nan ruguzu ta fad’o mana aikin mijinnata ne ba za tayi ba to kuma idan bu’katar ta yake fa ba iya sharar za tayi ba tashi ki fice kafin na kai miki mangara a’a wallahi ba ruwana idan rashin kunya zaki saka ta dinga yi masa ba kuwa zanje zaman d’akin nan ba ki hana a raya sunnahr muhammaduna rasulillahi d’an Abdullahi. Kai tashi ka bi matarka kaji.” Mommah gaba d’aya ran ta ya ‘baci har ya mi’ke a zafafe tabi bayansa suna zuwa corridor tace “kai ji mana kuma wallahi ko hannu ka ri’ke mata ban
Yafe ba.” Tana fad’a ta juya Imran shi dariya ma ta bashi ya juya kawai a zuciyarsa yace “kin san kina tsoron hakan kika yi mata aure kash ina ma bana gudun ayi min dariya da ayau zan mayar miki da shalelen taki cikakkiyar mace.”
*🤍ME ZAN YI DA ITA?*🤍
NAZEEFAH SABO NASHE
FREE📚
08033748387
-23
ELEGANT ONLINE WRITERS........
Suna shiga bed room d’in ya ja ‘kofa ya rufe, fuska a d’aure yake kallonta,ya tsareta da ido sosai kafin yace,”sakonki na jiya ya isar min, wai ke ki nuna min kin cika mace ko?har kin fara period, amma ban san ke wawuya bace sai yanzu,wa yace miki mace tana bari ma a gane tana period? Baki san abin kunya bane hakan?” Turo baki tayi kawai tana kallonsa,sai kuma a lokacin wata shahararriyar kunyarsa ta kamata,ta ji sam bata kyauta ba yanzu shikkenan ya gane mata sirrin ta? Sirrin da mommah tayi ta jan kunnenta akan kada ta bari a gani, da sauri ta runtse idonta.
Tsaki ya ja “Dama kafin na dawo ki tabbata kin fitar da ‘kazantarki daga toilet d’in ki kuma wanke min bin d’ina,and then lastly ki tabbatar kin wanke anything dake toilet d’in ya dawo kamar sabo, wawuyan yarinya kawai.” Ya fad’a yana kai mata ran’kwashi, daga haka ya fice ya kuma kulleta da key ta baya.
Sai sannan shatu ta bud’e idonta, tana sakin ajiyar zuciya, a hankali tace “Wai ni Shatu mai na aikata mutuminnan yanzu zai sake min kallon ‘kazama.” Tsaki ta ja ta shige toilet d’in, very neat ta samu toilet d’in,amma haka nan ta ‘kara wankeshi.
Momma jin shirun yayi yawa, da sauri ta danna kiransa a waya don hankalinta sam ya gaza kwanciya. Tsawon lokaci wayar tana ringing shi kuwa yana kallo yana driving ya’ki receiving call d’in sai murmushi yake, ya san mai take yiwa bata san ko bindiga aka saka masa ba zai iya aikata abinda take tunani ba.
Ji yayi text message ya shigo, ya bud’e yana murmushi had’e da ware ido kamar yarda hakan ya zame masa jiki. “Wallahi ka aikatawa yarinyar nan wani abin sai ka sani.” Dariya yayi sosai har da dukan sitiyari. A zuciyarsa yace “Ai kuwa yanzu wasan zai fara Mommah.”
********************************
Cikin kuka da tashin hankali take kallon mahaifiyrta, “Yanzu Anty duk burin da naci ya tafi a banza kenan? Yarinyar nan tarewa za tayi? Kuma ana nufin itama Imran mallakinta ne kamar yarda yake mallakina? Tana da right da komai a kansa, zata had’a jiki dashi? Komai da zaiyi min zai mata?” Cikin tashin hankali ta sake rintse ido. “Na shiga uku Anty pls kiyi wani abu mana, wallahi ji nake kamar zuciyata zata buga.” Tsaki Zainab tayi kafin tace “Ke bana son shashancin banza ki tsaya ki saurari abinda zan ce miki,ko jiya munyi waya da shuwa ta tabbatar min da ta koma gurin mutuminnan abinda ya sake ce mata kenan dole ki san yarda kika yi kika bashi maganinnan yaci a nama, a kuma ranar da yaci ake so lallai ya had’a shimfid’a da ita, yace min wallahi da zarar anyi haka kashegari zai sake ta kuma ba zai sake waiwayarta ba.” Kukan ta sake saki “Ni fa anty a sake wata shawarar wallahi ba zan amince ya shafi jikinta ba,balle har su had’a shimfid’a Imran nawa ne ni kad’ai.” Tsaki Anty tayi ta mi’ke a zuciye tace “Sai ki shirya zama da ita din-din-din a matsayin kishiya,ni dai abinda naga zan iya yi kenan shashasha ko meye abin damuwa?abin rana d’aya lokaci d’aya, kuma wallahi kika sa nayi asarar kud’ina ranki ne idan yayi dubu zai ‘baci,kin san nawa na kashe? Ban da tafiya cikin jeji da shuwa ta kwana tana yi a garinsu, to kije kiyi yarda kike so, ki bari suyi surkullensu na fulani su su mallakeshi,kin san dai yarinyar nan ta fiki komai da komai.” Runtse idonta shaheeda tayi murya na rawa tace “zan gwada Anty Allah ya bani iko.” Antyn ta dafa ta yauwa “ko ke fa idan kika yi hakan shine zaki samu kansa,ki ci karanki babu babbaka.” Shaheedah ta saki ajiyar zuciya tana dafa hannun mamanta tace “Amma Anty ta yaya zai amince ya kusanceta bayan kin san ba son auren yake ba.” Anty tayi murmushi “Yaro-Yaro ne ai ba yanzu zakiyi ba sai lokacin da muka so ta bar gidan,a lokacin dama kin tsara tafiya Abuja sai ki bashi a nama yaci,to kafin ki tafi ki tabbatar kin bashi desire tablet a cikin tea da safe mai ‘karfin gaske,idan ya bu’kace ki kice period kike ko kuma kafin maganin ya fara aiki kiyi sauri ki tafi shikkenan fa fa’kat, burinmu na farko zai cika.” Dariya shaheedah tayi ta rungume Antyn ta cikin tsananin farin ciki,hankalinta kam yanzu hundred percent ya kwanta.
Da yamma kafin a kai amarya Momma ta kira Imran, ba ‘bata lokaci yazo, tana kallonsa su biyu a
Parlourn tace “Nasiha zan maka Imran a matsayina na mahaifiyarka duk runtsi duk wuya ka kula da iyalinka,amana ce ubangiji ya dan’ka maka a hannunka, kayi adalci a tsakaninsu Imran kada kaga ita wannan yarinya ce ka cuceta ko ka zalunceta,zata tare nan da kwana shidda....” da sauri Imran ya zaro ido yace “kwana shidda Mommah ai naga tayi ‘karama.” Mommah tsaki tayi”Ni kaina ba’a son raina hakan zata faru ba ba yarda zanyi ne, sai dai ina son in ja kunnenka hakan ba yana nufin na baka lasisin kula ta bane, wallahi ban amince ba kada wata mu’amala ta had’aku,
Ka bar ta tayi karatunta please Imran.”
Ransa a ‘bace ya saki ajiyar zuciya yana tunanin mai zai kaishi kusantarta ko shi ya kawo maita duniya, gaskiya bai ji dad’in lamarin tariyar nan ba, har hakan ya gaza ‘boyuwa a
Fuskarsa,sai dai bai ce komai ba ya mi’ke ya tafi bayan ya zaro key d’in part d’in shatu na gidansa ya mi’kawa mommah kamar yarda ta bu’kata.
Tunda ya koma bedroom d’insa ya zubawa kayan da abokansa suka had’a masa na komawa gidansa kallo,idan ka ganshi zaka yi zaton kayan yake kallo,Sai dai tuni zuciyarsa ta tafi tunanin neman mafitar yarda zaiyi da auren Shatu, tunani iri-iri ya shigeshi wata zuciyar tace kawai ya saketa ya gudu da matarsa su bar ‘kasar, a duk shawarwarin wannan ce tafi tsaya masa.
Tsaf Amarya Shaheedah ta fito a cikin shigar laffaya sai zabga ‘kamshi take kai kace anyi ‘barin turare a jikinta,sanye take cikin pink d’in laffaya, ta dai rufe kanta amma idonta ko alamar kuka babu,
Burinta a yau ya cika na auran Imran, kamar yarda ta dad’e tana mafarki,yau dai ga ta a matsayin matarsa,don haka take jin kamar taje ta kai kanta ganin su masu kaiwar basa sauri sun tsaya sai zagaye suke da ita wajen ‘yan uwa.
Gida yayi kyau ya sha kayan alfarma na gani a fad’a,sai zabga ‘kamshi yake. Amarya tun daga haraba take sakin murmushi cikin laffaya.
Kowa ya yaba sannan masu kawota suka tattara suka tafi, ‘yan mata zuciyarsu cike da burin samun irin gidan ko makwafinsa.
Ango dai tunda abokansa suka fara siyan baki yake sakin tsaki,burinsa suyi su tattara su tafi,tunda ya dad’e yana jiran wannan ranar a matsayinsa na kamilin saurayi.
Abubuwan da suka faru a daren abubuwane da baza su manta su ba a kaf tarihin rayuwarsu,ango dai ya riski matarsa sabuwa dal a leda sai muce Allah ya kawo ‘kazantar d’aki.
*************
Yafe ba.” Tana fad’a ta juya Imran shi dariya ma ta bashi ya juya kawai a zuciyarsa yace “kin san kina tsoron hakan kika yi mata aure kash ina ma bana gudun ayi min dariya da ayau zan mayar miki da shalelen taki cikakkiyar mace.”
*🤍ME ZAN YI DA ITA?*🤍
NAZEEFAH SABO NASHE
FREE📚
08033748387
-23
ELEGANT ONLINE WRITERS........
Suna shiga bed room d’in ya ja ‘kofa ya rufe, fuska a d’aure yake kallonta,ya tsareta da ido sosai kafin yace,”sakonki na jiya ya isar min, wai ke ki nuna min kin cika mace ko?har kin fara period, amma ban san ke wawuya bace sai yanzu,wa yace miki mace tana bari ma a gane tana period? Baki san abin kunya bane hakan?” Turo baki tayi kawai tana kallonsa,sai kuma a lokacin wata shahararriyar kunyarsa ta kamata,ta ji sam bata kyauta ba yanzu shikkenan ya gane mata sirrin ta? Sirrin da mommah tayi ta jan kunnenta akan kada ta bari a gani, da sauri ta runtse idonta.
Tsaki ya ja “Dama kafin na dawo ki tabbata kin fitar da ‘kazantarki daga toilet d’in ki kuma wanke min bin d’ina,and then lastly ki tabbatar kin wanke anything dake toilet d’in ya dawo kamar sabo, wawuyan yarinya kawai.” Ya fad’a yana kai mata ran’kwashi, daga haka ya fice ya kuma kulleta da key ta baya.
Sai sannan shatu ta bud’e idonta, tana sakin ajiyar zuciya, a hankali tace “Wai ni Shatu mai na aikata mutuminnan yanzu zai sake min kallon ‘kazama.” Tsaki ta ja ta shige toilet d’in, very neat ta samu toilet d’in,amma haka nan ta ‘kara wankeshi.
Momma jin shirun yayi yawa, da sauri ta danna kiransa a waya don hankalinta sam ya gaza kwanciya. Tsawon lokaci wayar tana ringing shi kuwa yana kallo yana driving ya’ki receiving call d’in sai murmushi yake, ya san mai take yiwa bata san ko bindiga aka saka masa ba zai iya aikata abinda take tunani ba.
Ji yayi text message ya shigo, ya bud’e yana murmushi had’e da ware ido kamar yarda hakan ya zame masa jiki. “Wallahi ka aikatawa yarinyar nan wani abin sai ka sani.” Dariya yayi sosai har da dukan sitiyari. A zuciyarsa yace “Ai kuwa yanzu wasan zai fara Mommah.”
********************************
Cikin kuka da tashin hankali take kallon mahaifiyrta, “Yanzu Anty duk burin da naci ya tafi a banza kenan? Yarinyar nan tarewa za tayi? Kuma ana nufin itama Imran mallakinta ne kamar yarda yake mallakina? Tana da right da komai a kansa, zata had’a jiki dashi? Komai da zaiyi min zai mata?” Cikin tashin hankali ta sake rintse ido. “Na shiga uku Anty pls kiyi wani abu mana, wallahi ji nake kamar zuciyata zata buga.” Tsaki Zainab tayi kafin tace “Ke bana son shashancin banza ki tsaya ki saurari abinda zan ce miki,ko jiya munyi waya da shuwa ta tabbatar min da ta koma gurin mutuminnan abinda ya sake ce mata kenan dole ki san yarda kika yi kika bashi maganinnan yaci a nama, a kuma ranar da yaci ake so lallai ya had’a shimfid’a da ita, yace min wallahi da zarar anyi haka kashegari zai sake ta kuma ba zai sake waiwayarta ba.” Kukan ta sake saki “Ni fa anty a sake wata shawarar wallahi ba zan amince ya shafi jikinta ba,balle har su had’a shimfid’a Imran nawa ne ni kad’ai.” Tsaki Anty tayi ta mi’ke a zuciye tace “Sai ki shirya zama da ita din-din-din a matsayin kishiya,ni dai abinda naga zan iya yi kenan shashasha ko meye abin damuwa?abin rana d’aya lokaci d’aya, kuma wallahi kika sa nayi asarar kud’ina ranki ne idan yayi dubu zai ‘baci,kin san nawa na kashe? Ban da tafiya cikin jeji da shuwa ta kwana tana yi a garinsu, to kije kiyi yarda kike so, ki bari suyi surkullensu na fulani su su mallakeshi,kin san dai yarinyar nan ta fiki komai da komai.” Runtse idonta shaheeda tayi murya na rawa tace “zan gwada Anty Allah ya bani iko.” Antyn ta dafa ta yauwa “ko ke fa idan kika yi hakan shine zaki samu kansa,ki ci karanki babu babbaka.” Shaheedah ta saki ajiyar zuciya tana dafa hannun mamanta tace “Amma Anty ta yaya zai amince ya kusanceta bayan kin san ba son auren yake ba.” Anty tayi murmushi “Yaro-Yaro ne ai ba yanzu zakiyi ba sai lokacin da muka so ta bar gidan,a lokacin dama kin tsara tafiya Abuja sai ki bashi a nama yaci,to kafin ki tafi ki tabbatar kin bashi desire tablet a cikin tea da safe mai ‘karfin gaske,idan ya bu’kace ki kice period kike ko kuma kafin maganin ya fara aiki kiyi sauri ki tafi shikkenan fa fa’kat, burinmu na farko zai cika.” Dariya shaheedah tayi ta rungume Antyn ta cikin tsananin farin ciki,hankalinta kam yanzu hundred percent ya kwanta.
Da yamma kafin a kai amarya Momma ta kira Imran, ba ‘bata lokaci yazo, tana kallonsa su biyu a
Parlourn tace “Nasiha zan maka Imran a matsayina na mahaifiyarka duk runtsi duk wuya ka kula da iyalinka,amana ce ubangiji ya dan’ka maka a hannunka, kayi adalci a tsakaninsu Imran kada kaga ita wannan yarinya ce ka cuceta ko ka zalunceta,zata tare nan da kwana shidda....” da sauri Imran ya zaro ido yace “kwana shidda Mommah ai naga tayi ‘karama.” Mommah tsaki tayi”Ni kaina ba’a son raina hakan zata faru ba ba yarda zanyi ne, sai dai ina son in ja kunnenka hakan ba yana nufin na baka lasisin kula ta bane, wallahi ban amince ba kada wata mu’amala ta had’aku,
Ka bar ta tayi karatunta please Imran.”
Ransa a ‘bace ya saki ajiyar zuciya yana tunanin mai zai kaishi kusantarta ko shi ya kawo maita duniya, gaskiya bai ji dad’in lamarin tariyar nan ba, har hakan ya gaza ‘boyuwa a
Fuskarsa,sai dai bai ce komai ba ya mi’ke ya tafi bayan ya zaro key d’in part d’in shatu na gidansa ya mi’kawa mommah kamar yarda ta bu’kata.
Tunda ya koma bedroom d’insa ya zubawa kayan da abokansa suka had’a masa na komawa gidansa kallo,idan ka ganshi zaka yi zaton kayan yake kallo,Sai dai tuni zuciyarsa ta tafi tunanin neman mafitar yarda zaiyi da auren Shatu, tunani iri-iri ya shigeshi wata zuciyar tace kawai ya saketa ya gudu da matarsa su bar ‘kasar, a duk shawarwarin wannan ce tafi tsaya masa.
Tsaf Amarya Shaheedah ta fito a cikin shigar laffaya sai zabga ‘kamshi take kai kace anyi ‘barin turare a jikinta,sanye take cikin pink d’in laffaya, ta dai rufe kanta amma idonta ko alamar kuka babu,
Burinta a yau ya cika na auran Imran, kamar yarda ta dad’e tana mafarki,yau dai ga ta a matsayin matarsa,don haka take jin kamar taje ta kai kanta ganin su masu kaiwar basa sauri sun tsaya sai zagaye suke da ita wajen ‘yan uwa.
Gida yayi kyau ya sha kayan alfarma na gani a fad’a,sai zabga ‘kamshi yake. Amarya tun daga haraba take sakin murmushi cikin laffaya.
Kowa ya yaba sannan masu kawota suka tattara suka tafi, ‘yan mata zuciyarsu cike da burin samun irin gidan ko makwafinsa.
Ango dai tunda abokansa suka fara siyan baki yake sakin tsaki,burinsa suyi su tattara su tafi,tunda ya dad’e yana jiran wannan ranar a matsayinsa na kamilin saurayi.
Abubuwan da suka faru a daren abubuwane da baza su manta su ba a kaf tarihin rayuwarsu,ango dai ya riski matarsa sabuwa dal a leda sai muce Allah ya kawo ‘kazantar d’aki.
*************