Sashe 12
Me Zanyi Da Ita Part Complete 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Da ta dawo kuwa samu tayi duk gidan suna part d’insu Imran wai bashi da lafiya ta’be baki tayi ta samu abinci kawai ta fara ci ita ina ruwanta da ciwonsa mutum sai shegiyar tsaftar tsiya har da wani amai da ciwo. Taci ta ‘koshi sannan tayi wanka ta zira da wando tana fitowa ta tarar da mommah ta shigo. Mommah ta bud’e mata hannu tana welcoming d’inta tare da furta”oyoyo autar mommah ya school d’in” ta d’aga kai “
Ba laifi mommah amma fa sai an jawa ‘yan class d’in kunne bana son rashin kunya don naji suna ce min wai ra’kumi a cikin ‘yan tsaki to yau dai nayi musu na ba’kunta gobe kuwa wallahi na jaki zasu ci” Mommah murmushi tayi ta dafa ta “ba’a fad’a a makaranta baby na kada ki kula kowa kin ji’yar albarka kiyi karatunki kawai ki koma gida shine abinda ya kaiki kinji?” Murmushi tayi ta d’aga kai shigowar nahna ce yasa mommah ta tuna ruwan tea zata dafawa Imran kuma ya ro’keta don Allah da kansa zata kawo masa don yanzu tsoron ta’ba komai na gidan yake da zai iya ma da kansa zai shiga kitchen d’in ya dafa to jiri yake ji saboda tun safe ba abinda ya shiga cikinsa.Momma ta girgiza kai “kinga kuwa nahna shaf na manta abinda nazo yi bari in tashi” Nahna tana dariya tace “ya kuwa ce da kanki yakeso ki dafa masa kuma kina juyewa in kawo masa ni ban san me ya sameshi ba” mommah tace “mhmn rabu da Imran haka yake idan yana cuta sangarta ce dashi zan ga yarda matarsa zata yi da ‘kyan’kyaminsa wallahi abin yana damuna sai kace wani mai cutar tsafta.” Da kanta ta dafa tea d’in ta bawa Nahna ta kai masa.
Yana ganinta ya mi’ke zaune da kyar yana ri’ke kansa ya jingina da bangon gadon a hankali ya motsa bakinsa muryarsa ta fito “please mommah ce ta dafa kuma kina tsaye a wajen? Ibilishiyar yarinyar nan kuma bata wajen ko?” Nahna ta girgiza kai tana dariya ta tabbatar masa mommah ce ta dafa da kanta. Ta zuba ta mi’ka masa yana sipping a hankali. Lokacin shaheeda ta murd’a ‘kofa ta shigo kallo d’aya tayiwa nahna ta d’auke kai hannunta d’auke da cooler ta nufi gefen gadon ta zauna cike da kwainane sai zabga ‘kamshi take ta zauna a gefensa tana jan yatsun ‘kafarsa “am sorry Habibi ya jikin?” Nahna ta kai idonta kan hannun sai kuma ta ta’be bakinta da sauri ta fice tana mamakin rashin kunya irinta ‘yan matan yanzu sam basa iya tsare mutuncin kansu shi yasa ko auren aka yi mazan basa ganin mutunci su.shaheeda ta sake kallonsa tana murmushi “ Habibi in zuba maka abincin?” Da sauri ya girgiza kai, ta kuwa had’e rai a hankali tace “kai habibi I cooked it with my own hand fa please kaci kaji?” Cikin muryar shagwa’ba take gaya masa hakan ya sake narkar da zuciyarsa yana jifanta da wani kallo ya matsu ya matsu sosai ya auri shaheeda shi kad’ai irin son ta da yake dan’kare a zuciyarsa yana jiran lokacin da Zai amayar dashi.ta zuba a plate ta zauna tana bashi a hankali cikin sigar jan hankali.
Mommah ce ta tilasta shatu sai taje dubashi, ta mi’ke tana zun’bura baki a zuciyarta take tunanin ita mommah bata san itace silar ciwon bane ta tabbata yanzu idan taje sai ya huce haushin abinda tayi masa. Hafsa ce cikin fad’a tace “Ba zaki tashi kije ba sai na ‘bata miki rai baki san d’an uwanki bane shi duk duniya baki da kamarsa fa shi da Ammar.” Mi’kewa tayi ta fita niyyarta idan ta fita ta la’be ta dawo tace taje, sai dai a rashin sa’arta Nahna ta mi’ke tace “Bari muje na san halinta yanzu ta ‘buya tace taje.” Ta tura ‘kofar bed room d’in a hankali bayan ta shiga parlourn hakan yasa Nahna saurin juyawa ta koma. Ita kuwa shatu mummunan gamo tayi shaheeda ce a gefen Imran tana ta shafa masa fuska wai tausa take masa ta shige jikinsa sosai kamar me. Da sauri shatu ta runtse ido tayi saurin juyawa shi kuwa Imran motsin da yaji ne yasa shi saurin mi’kewa sai yaga fitar shatu da sauri ya janye jikinsa yana wa shaheeda wani irin kallo “sau nawa zan gaya miki bana son irin wad’annan abubuwan bafa wayewa bace yanzu kinsa yarinya ‘karama ta gammu a haku me kikeso tace mai kike so tayi zargi a zuciyarta?” Shaheeda marairaice masa fuska tayi “Haba habibi meye a cikin hakan kawai fa tausa ne amma tunda baka so insha Allah na daina Allah ya kaimu lokacin da zaka zama halal d’ina in nuna maka pure love da ba surki amma waccen yarinyar mai take zuwa yi har bed room d’inka?” Runtse ido yayi yana tunanin lamarin yarinyar baya ko son ganin fuskarta tsoronta lamarinsa yake bashi don haka dole ya samarwa kansa lafiya ya fita sabgarta kafin tayi abinda zai kaishi lahira burinsa ma lokacin bikinsa yayi ya tattara ya bar gidan ba sai ta ganshi bama balle ta hukunta shi da ‘kazantarta.
A ranar Dahda ya dawo amarya aka shiga giringid’ishin kama miji mommah dai ko gurinsa bata jeba balle taga abinda zai ‘bata mata rai, sai da ya gaji da kansa ya shiga part d’inta tana zaune da kwalliyarta ta tsadaddiyar atamfa ta kashe d’auri parlorn nan sai ‘kamshin turaren wuta yake yi. Murmushi ya sakar mata “uwargida ran gida barka da hutawa ni nazo gaisheki tunda ba’a nemansa” murmushin ta saki itama bayan ta gama saurararsa tace “hakan da kayi shine abinda ya kamata ka bi cikakkiyar sunnar manzon Allah ya hanya?” “Alhamdulillah” ya furta yana sauke nauyayyiyar ajiyar zuciya ya tabbata da itace da girki da tuni ta kai masa ruwan wanka ta kuma taimaka masa da tausa da lafiyayyen girkinta tana zuba masa tana murmushi ba dole dijah ta sace zuciyarsa shi kad’ai ya san wacece dijah ya kuma tabbatar ba zai samu kofa kwafinta bane balle wacce ta kaita. “Na biya wajen hajja wai me ya faru ne ta tabbatar min da aljannu a cikin gidannan wai ba zata sake zuwa ba” yana murmushi ya fad’a mommah ma dariyar tayi tace”Ba mamaki da aljannun a d’akin da take sauka amma mu dai bamu ta’ba gani ba” “Ni na sani na san rigimar hajja ce yanzu ba ma wannanba ta rigime min sai anyi bikin Imran nan da wata d’aya da Rabi” mommah ta saki murmushi kafin tace “Masha Allah Allah ya nuna mana me yayi saura ai ya gama gininsa Allah yasa albarka yasa abokiyar arzikinsa ce yana d’akima ba lafiya” Dahda ya mi’ke “ai naje na duba shi ina shigowa zainabu ta fad’a min Allah ya bashi lafiya yace min stress ne yayi masa yawa Imran ne akwai son kud’i baya son hutawa” mommah tana dariya tace “kyan d’a ya gaji ubansa”
*🤍ME ZAN YI DA ITA?*🤍
NAZEEFAH SABO NASHE
FREE📚
08033748387
-15
*****
Tun daga lokacin Imran ya tattara shatu ya watsar a gefe baya shiga shirginta sam ko a waje ya ganta baya zama idan kuwa yana waje tazo da sauri yake barin wajen. Hakan da yake yi kuma sosai ya fara damun zuciyar shatu bata so ba sam bata so ya daina shiga lamarinta ba haka kawai take son ta dinga ganinsa tana jin muryarsa da kuma kyakykyawan murmushinsa, hakan yasa ko da yaushe take zama a main parlour kawai don yas shigo ta ganshi taji’kamshinsa ta kuma ga kyakykyawan takunsa da yake yi tamkar a cikin izza bata san daliliba haka kawai IMRAN AHMAD MANGA yake burgeta. Ba wai soyayya take nufi ba tunda har a lokacin bata san so ba kawai dai burgeta yake tsaftarsa kallonsa tafiyarsa maganarsa komai Imran manga yayi burge shatu yake sosai har cikin zuciyarta ba mamaki hakan yana da ala’ka da zamowarsa d’an uwanta kuma jininta wanda duk duniya bata da na biyunsu. Ganin ya daina shiga shirginta itama ta tattarshi ta watsar ta kama Ammar abinta da uncle d’inta Hisham da kullum suke tare indai suna gidan.
Tuni ta mayar da hankalinta akan karatunta both islamic da boko bata wasa burinta ta zama mai ilimi ta kuma iya english kamar yarda taga su Anty hafsa suna yarawa abin yana burgeta yana sata nishad’i, hakan yasa take damun mommah da zancen ita kuma mommah ta dafa kanta tace “sha kuruminki shatun mommah zaki iya turanci da ko bature england sai ya sara miki” hakan da mommah take fad’a shi yake ‘kara mata ho’b’basa taji tana so tana kuma zakwad’i da karsashin son zamowa baturiya mai yara english ba gargada ko tuntu’ben harshe. Sosai take dagewa lamarin har tsoro yake bawa mommah ganin yarda ta mayar da karatu abokinta ko da yaushe zaka sameta da littafi na islamiyya da na boko. Tsoron mommah d’aya kada karatu ya sa ‘kwalwarta ta’buwa don haka sau tari take ‘kwace littafin ta saka mata kallo ko tace tayi barci ko na rabin sa’a ne kwanyarta ta samu hutu.
Tuni su hafsa suka tattara suka koma Abuja saboda yawan damunsu da hajiya mama take da yawa akan hutun ya isa, kullum fad’a take tana ‘karawa “ Ba hauka bane abin ku tattaro komatsanku ku dawo nima ina bu’katarku idan bikin yazo kwa koma tunda dai bata da wasu sha’ki’kan da suka wuce ku” hakan yasa dole suka tafi zuciyarsu cike da tausayin mommah ganin yarda kishiya da dangin miji suka sakata gaba. Koda suka gayawa hajiya maa murmushi kawai tayi kafin tace “haka rayuwar ta gada ba yarda bawa zai zauna ‘kalau bai jarrabeka ba idan kaga Allah baya jarrabarka ma ka binciki kanka balle d’iya mace a gidan miji taya kuke zaton zata samu aljanna a ‘bagas ai dole ne a jarrabeta ko ta’bangaren kishiya uwar miji ko dangin miji, ‘ya’yansa ko d’ungurungum mijin ma gaba d’aya babu wata mace da zata ce salin Alin tana rayuwarta ‘kalau tsakanin bawa da ubangiji godiya kawai a duk yanayin da ya tsinci kansa don haka ta godewa Allah tunda mijinta na sonta saura kuma ta barwa Allah ta sha mamakin hukuncinsa ai hukumullahi la ajabun.”
********
Ba laifi mommah amma fa sai an jawa ‘yan class d’in kunne bana son rashin kunya don naji suna ce min wai ra’kumi a cikin ‘yan tsaki to yau dai nayi musu na ba’kunta gobe kuwa wallahi na jaki zasu ci” Mommah murmushi tayi ta dafa ta “ba’a fad’a a makaranta baby na kada ki kula kowa kin ji’yar albarka kiyi karatunki kawai ki koma gida shine abinda ya kaiki kinji?” Murmushi tayi ta d’aga kai shigowar nahna ce yasa mommah ta tuna ruwan tea zata dafawa Imran kuma ya ro’keta don Allah da kansa zata kawo masa don yanzu tsoron ta’ba komai na gidan yake da zai iya ma da kansa zai shiga kitchen d’in ya dafa to jiri yake ji saboda tun safe ba abinda ya shiga cikinsa.Momma ta girgiza kai “kinga kuwa nahna shaf na manta abinda nazo yi bari in tashi” Nahna tana dariya tace “ya kuwa ce da kanki yakeso ki dafa masa kuma kina juyewa in kawo masa ni ban san me ya sameshi ba” mommah tace “mhmn rabu da Imran haka yake idan yana cuta sangarta ce dashi zan ga yarda matarsa zata yi da ‘kyan’kyaminsa wallahi abin yana damuna sai kace wani mai cutar tsafta.” Da kanta ta dafa tea d’in ta bawa Nahna ta kai masa.
Yana ganinta ya mi’ke zaune da kyar yana ri’ke kansa ya jingina da bangon gadon a hankali ya motsa bakinsa muryarsa ta fito “please mommah ce ta dafa kuma kina tsaye a wajen? Ibilishiyar yarinyar nan kuma bata wajen ko?” Nahna ta girgiza kai tana dariya ta tabbatar masa mommah ce ta dafa da kanta. Ta zuba ta mi’ka masa yana sipping a hankali. Lokacin shaheeda ta murd’a ‘kofa ta shigo kallo d’aya tayiwa nahna ta d’auke kai hannunta d’auke da cooler ta nufi gefen gadon ta zauna cike da kwainane sai zabga ‘kamshi take ta zauna a gefensa tana jan yatsun ‘kafarsa “am sorry Habibi ya jikin?” Nahna ta kai idonta kan hannun sai kuma ta ta’be bakinta da sauri ta fice tana mamakin rashin kunya irinta ‘yan matan yanzu sam basa iya tsare mutuncin kansu shi yasa ko auren aka yi mazan basa ganin mutunci su.shaheeda ta sake kallonsa tana murmushi “ Habibi in zuba maka abincin?” Da sauri ya girgiza kai, ta kuwa had’e rai a hankali tace “kai habibi I cooked it with my own hand fa please kaci kaji?” Cikin muryar shagwa’ba take gaya masa hakan ya sake narkar da zuciyarsa yana jifanta da wani kallo ya matsu ya matsu sosai ya auri shaheeda shi kad’ai irin son ta da yake dan’kare a zuciyarsa yana jiran lokacin da Zai amayar dashi.ta zuba a plate ta zauna tana bashi a hankali cikin sigar jan hankali.
Mommah ce ta tilasta shatu sai taje dubashi, ta mi’ke tana zun’bura baki a zuciyarta take tunanin ita mommah bata san itace silar ciwon bane ta tabbata yanzu idan taje sai ya huce haushin abinda tayi masa. Hafsa ce cikin fad’a tace “Ba zaki tashi kije ba sai na ‘bata miki rai baki san d’an uwanki bane shi duk duniya baki da kamarsa fa shi da Ammar.” Mi’kewa tayi ta fita niyyarta idan ta fita ta la’be ta dawo tace taje, sai dai a rashin sa’arta Nahna ta mi’ke tace “Bari muje na san halinta yanzu ta ‘buya tace taje.” Ta tura ‘kofar bed room d’in a hankali bayan ta shiga parlourn hakan yasa Nahna saurin juyawa ta koma. Ita kuwa shatu mummunan gamo tayi shaheeda ce a gefen Imran tana ta shafa masa fuska wai tausa take masa ta shige jikinsa sosai kamar me. Da sauri shatu ta runtse ido tayi saurin juyawa shi kuwa Imran motsin da yaji ne yasa shi saurin mi’kewa sai yaga fitar shatu da sauri ya janye jikinsa yana wa shaheeda wani irin kallo “sau nawa zan gaya miki bana son irin wad’annan abubuwan bafa wayewa bace yanzu kinsa yarinya ‘karama ta gammu a haku me kikeso tace mai kike so tayi zargi a zuciyarta?” Shaheeda marairaice masa fuska tayi “Haba habibi meye a cikin hakan kawai fa tausa ne amma tunda baka so insha Allah na daina Allah ya kaimu lokacin da zaka zama halal d’ina in nuna maka pure love da ba surki amma waccen yarinyar mai take zuwa yi har bed room d’inka?” Runtse ido yayi yana tunanin lamarin yarinyar baya ko son ganin fuskarta tsoronta lamarinsa yake bashi don haka dole ya samarwa kansa lafiya ya fita sabgarta kafin tayi abinda zai kaishi lahira burinsa ma lokacin bikinsa yayi ya tattara ya bar gidan ba sai ta ganshi bama balle ta hukunta shi da ‘kazantarta.
A ranar Dahda ya dawo amarya aka shiga giringid’ishin kama miji mommah dai ko gurinsa bata jeba balle taga abinda zai ‘bata mata rai, sai da ya gaji da kansa ya shiga part d’inta tana zaune da kwalliyarta ta tsadaddiyar atamfa ta kashe d’auri parlorn nan sai ‘kamshin turaren wuta yake yi. Murmushi ya sakar mata “uwargida ran gida barka da hutawa ni nazo gaisheki tunda ba’a nemansa” murmushin ta saki itama bayan ta gama saurararsa tace “hakan da kayi shine abinda ya kamata ka bi cikakkiyar sunnar manzon Allah ya hanya?” “Alhamdulillah” ya furta yana sauke nauyayyiyar ajiyar zuciya ya tabbata da itace da girki da tuni ta kai masa ruwan wanka ta kuma taimaka masa da tausa da lafiyayyen girkinta tana zuba masa tana murmushi ba dole dijah ta sace zuciyarsa shi kad’ai ya san wacece dijah ya kuma tabbatar ba zai samu kofa kwafinta bane balle wacce ta kaita. “Na biya wajen hajja wai me ya faru ne ta tabbatar min da aljannu a cikin gidannan wai ba zata sake zuwa ba” yana murmushi ya fad’a mommah ma dariyar tayi tace”Ba mamaki da aljannun a d’akin da take sauka amma mu dai bamu ta’ba gani ba” “Ni na sani na san rigimar hajja ce yanzu ba ma wannanba ta rigime min sai anyi bikin Imran nan da wata d’aya da Rabi” mommah ta saki murmushi kafin tace “Masha Allah Allah ya nuna mana me yayi saura ai ya gama gininsa Allah yasa albarka yasa abokiyar arzikinsa ce yana d’akima ba lafiya” Dahda ya mi’ke “ai naje na duba shi ina shigowa zainabu ta fad’a min Allah ya bashi lafiya yace min stress ne yayi masa yawa Imran ne akwai son kud’i baya son hutawa” mommah tana dariya tace “kyan d’a ya gaji ubansa”
*🤍ME ZAN YI DA ITA?*🤍
NAZEEFAH SABO NASHE
FREE📚
08033748387
-15
*****
Tun daga lokacin Imran ya tattara shatu ya watsar a gefe baya shiga shirginta sam ko a waje ya ganta baya zama idan kuwa yana waje tazo da sauri yake barin wajen. Hakan da yake yi kuma sosai ya fara damun zuciyar shatu bata so ba sam bata so ya daina shiga lamarinta ba haka kawai take son ta dinga ganinsa tana jin muryarsa da kuma kyakykyawan murmushinsa, hakan yasa ko da yaushe take zama a main parlour kawai don yas shigo ta ganshi taji’kamshinsa ta kuma ga kyakykyawan takunsa da yake yi tamkar a cikin izza bata san daliliba haka kawai IMRAN AHMAD MANGA yake burgeta. Ba wai soyayya take nufi ba tunda har a lokacin bata san so ba kawai dai burgeta yake tsaftarsa kallonsa tafiyarsa maganarsa komai Imran manga yayi burge shatu yake sosai har cikin zuciyarta ba mamaki hakan yana da ala’ka da zamowarsa d’an uwanta kuma jininta wanda duk duniya bata da na biyunsu. Ganin ya daina shiga shirginta itama ta tattarshi ta watsar ta kama Ammar abinta da uncle d’inta Hisham da kullum suke tare indai suna gidan.
Tuni ta mayar da hankalinta akan karatunta both islamic da boko bata wasa burinta ta zama mai ilimi ta kuma iya english kamar yarda taga su Anty hafsa suna yarawa abin yana burgeta yana sata nishad’i, hakan yasa take damun mommah da zancen ita kuma mommah ta dafa kanta tace “sha kuruminki shatun mommah zaki iya turanci da ko bature england sai ya sara miki” hakan da mommah take fad’a shi yake ‘kara mata ho’b’basa taji tana so tana kuma zakwad’i da karsashin son zamowa baturiya mai yara english ba gargada ko tuntu’ben harshe. Sosai take dagewa lamarin har tsoro yake bawa mommah ganin yarda ta mayar da karatu abokinta ko da yaushe zaka sameta da littafi na islamiyya da na boko. Tsoron mommah d’aya kada karatu ya sa ‘kwalwarta ta’buwa don haka sau tari take ‘kwace littafin ta saka mata kallo ko tace tayi barci ko na rabin sa’a ne kwanyarta ta samu hutu.
Tuni su hafsa suka tattara suka koma Abuja saboda yawan damunsu da hajiya mama take da yawa akan hutun ya isa, kullum fad’a take tana ‘karawa “ Ba hauka bane abin ku tattaro komatsanku ku dawo nima ina bu’katarku idan bikin yazo kwa koma tunda dai bata da wasu sha’ki’kan da suka wuce ku” hakan yasa dole suka tafi zuciyarsu cike da tausayin mommah ganin yarda kishiya da dangin miji suka sakata gaba. Koda suka gayawa hajiya maa murmushi kawai tayi kafin tace “haka rayuwar ta gada ba yarda bawa zai zauna ‘kalau bai jarrabeka ba idan kaga Allah baya jarrabarka ma ka binciki kanka balle d’iya mace a gidan miji taya kuke zaton zata samu aljanna a ‘bagas ai dole ne a jarrabeta ko ta’bangaren kishiya uwar miji ko dangin miji, ‘ya’yansa ko d’ungurungum mijin ma gaba d’aya babu wata mace da zata ce salin Alin tana rayuwarta ‘kalau tsakanin bawa da ubangiji godiya kawai a duk yanayin da ya tsinci kansa don haka ta godewa Allah tunda mijinta na sonta saura kuma ta barwa Allah ta sha mamakin hukuncinsa ai hukumullahi la ajabun.”
********