Sashe 16
Me Zanyi Da Ita Part Complete 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Kafin doctor yazo haukane kawai ba suyi ba sai da Ammar ya shigo ya sanar dasu shigowar doctor sannan Imran ya kalli shaheeda ransa a ‘bace yace “Go and cover your body ko kunya baki ji” wani kallo ta watsa masa kafin tayi magana doctor ya shigo da sauri Imran ya dafa kansa ya jata ya turata d’aki yana tsaki. Ko da ta shiga d’aki hijab kawai ta zira ta sake fitowa a guje. Doctor ya gama dubasu sannan ya fito da allura ya fara yi musu don dama dahda yayi masa bayanin ciwon. Sai kusan ‘karfe 4:00 na dare sannan abin ya lafa musu amma fa sunji jiki duk jiknnan yayi luhu-luhu balle idonsu.basu koma d’akunansu ba don suna tunanin tabbas aljannun ne tun da a d’akin da hajja take sauka suka sauka yau kam sun gasgata zancen hajja. Jin shigowar su mommah yasa shatu shiga d’aki da sauri tana tuntsira dariya. Amma mamakinta d’aya me yasa Imran bai tona mata asiri ba karo na biyu kenan yana kamata da irin wannan.shi kansa Imran tunda ya shiga d’aki yake smilling shi kad’ai ya lura yarinyar nan comedian ce ta bugawa a news.
Da safe ma basu koma d’akin ba a sashen amarya suka koma zama suna sake la’antar mommah don a cewarsu aljannu take turo musu ai kuwa indai sune su zuba su da ita gida dai baza su barshi ba sai sun kai kwanakin da suka ‘kayyadewa kansu tunda a goben zasu tafi abuja kai lefe. Hameedah tana sake girgiza ‘kafa ranta a matu’kar ‘bace tace “wallahi wannan matar muka ‘kyaleta nan gaba raba mu za tayi da yaya manga gaba d’aya dole mu tashi tsaye a kanta mu har a gaya mana malamai mu da
Muku jinin barebari.” Falmata ma cewa tayi”wallahi kuwa naga alama kuma lefe tayiwa kanta tunda hajja tace mu kai kada ma mu nemi danginta wallahi kaiwa zamuyi ke kuma shaheedah sai kin dage sosai duk abinda muka kawo miki kada kiyi wasa dashi munyi al’kawarin sai mun dasa mata ninkin ‘bacin ran da ta sakawa manga sai mu zuba mu gani tana ji tana gani Imran sai dai ta hange shi daga ness” gaba d’aya suka saka shewa har da amarya zainab. Fanna na gyara zama tace mai yafi wannan takaici ace d’anka yana auren ‘yar kishiyarka kuma zainab ke kin samu d’a daga sama kamar yarda uwarta ta samu manga daga sama suke juya mana shi son ransu.” Dariya suka ‘kara yi.
Ko da ta gama shirin school tana fitowa general parlour ta gansu murmushi ta saki ta fara wa’kar ado gwanja ta casss. A harzu’ke suke kallonta,Hameedah ta mi’ke da sauri tana jifanta da wani irin kallo “ke don uwraki da wa kike?” Shatu rausayar da kai tayi gefe kafin tace “kawai don ina wa’kata sai ki zageni” fitowar Imran da Ammar kenan sunyi shirin fita su ka ji hameedah tana wallahi sai na sake jibgarki kamar yarda nayi miki jiya shegiya mai idon aljannu.” Imran waro ido yayi yana kallon hameedah mamaki fal ransa lalle bata san sharrin yarinyar nan ba bata san itace gayyar aljannun da suke wajigasu ba, har shatu ta karkace zata yi rashin kunya Ammar ransa a ‘bace ya jata “wuce ki tafi school tun d’azu driver na jiranki kin tsaya jan magana.” Baki ta zun’buro irin na shagwa’ba “Yaya Ammar uwata fa ta zaga.” Harara ya zuba mata “kin wuce ko sai na mangareki tayi ta zaginki ma yana tsiro ne? Oya maza-maza wuce school kafin na sameki a wajen” sum sum ta wuce har taje ‘kofa ta juyo da ‘karfi tace “an fad’a d’in a sosa cass a sosa iya da razor.” Imran bai san sanda murmushi ya ku’buce masa Ammar kuwa darawa yayi sosai yace “kai shatu danger” hameedah kuwa ‘kwafa tayi tana zabgawa Ammar harara.
Kashegari kuwa suka isa abuja dangin baban shaheeda suka kai lefe ba tare da dangin mommah ko d’aya ba duk da kuwa suna cikin abujar. Haka suka dawo da sha tara ta arziki duk da suma ba lefen wasa suka kai ba lefene na gaske na gani a fad’a na kuma d’orawa a instagram,a yayata a duniya. Biki kuwa aka saka shi sati uku cif don suma dangin uban shaheedahn a shirye suke tsaf kuma masu farcen susa ne tabbas kuwa za’ayi biki na kece raini. Bayan sun dawo kano da kwana d’aya suka wuce maiduguri hannayensa dam’ke da sha tara ta arziki. Mommah ba tace musu Komai ba duk da ta tambayi Hajiya mama kuma ta tabbatar mata ba a gaya musu kai lefen ta basu ha’kuri. Hajiya mama ta girgiza kai a cikin wayar tace”Lala lala dijah ke zan bawa ha’kuri kiyi ha’kuri da jarrabawar da Allah yayi miki ta fitinannun dangi miji kina zaune ubangiji zaiyi miki sakayya suma fa mata ne kuma sun haifi mata ki zuba musu ido yanzu ubangiji ai tun a duniya yake sakayya ba kayi ba ma anyi maka ina ga kayi kiyi ha’kuri kullum shine abinda zan iya ce miki.” Hawaye ya zubowa mommah sai dai ba ta nunawa hajiya mama kuka take ba tayi godiya ta kashe wayar a zuciyarta tace “akwai ranar ‘kin dillaci ranar da zata cusa musu nasu ‘bacin ran dole ne su girbi abinda suka shuka d’a dai nata ne kuma ba zata bari su juya shi kamar yarda suke muradi ba.
*****************
A hankali awanni suka yi ta shigewa suna zama kwanaki daga kwanaki kuwa,har satittikan biki suka zo gidan a hargitse yake kowa sai shiri yake ana ji da lamarin bikin to ba dole ba ta kowane side jikan farko kuma d’an gaban goshi ake yiwa Aure,tun ana saura sati biki dahda yasa shaheedah dole ta koma gidan babanta duk da ba haka suka so ba uwarta taso ta tsaya ta cigaba da banka mata mallakin mallaka sai dai dole ta tafi. Hajja ma ana saura satin tazo ta tare a part d’in dahda daga gefe a babban parlournsa akwai wani bedroom and toilet anan ta baje danginta kuma suna d’aki mai Aljannu.
Mutanen katagum ma sun hallara ciki kuwa har da Dada tsohuwa mai ran ‘karfe. Tuni mommah ta fara gyara d’iyarta tsaf fatarta ta goge a spa haka nan an yi mata saloon gashin nnan an jawo shi tsahonsa har da na Mamaki.
Suna dawowa daga spa a gajiye suka tarar Hajiya mama tazo ita ma da ‘yan uwanta na yola ga Hafsa da Nahna da sauri shatu ta rungume uncle Hisham shi kuwa duk da nauyin da tayi masa haka ya shiga wulwulata yana fad’in a cafe a cafe ‘yar gidan mommah mai mommah ke baki ne kika yi wani fresh har glowing kike?” Kayan dad’i” ta furta tana murmushi har hushiryarta ta fito. Still Ammar yayi yana kallonta har bakinsa ya gaza shiru yace “mommah ‘karin gashi kika kaita aka yi mata da wankin fata?” Gaba d’aya gurin ba wanda baiyi dariya ba Hafsa tace “Ammar ko dai kana ciki ne a d’aura gobe da kai kawai.” Girgiza kai yayi “Ina ni ina rigimar shatu ni ‘kabilar ibira ma zan aura sun fi iya kula da miji” shatu ma harara ta zabga masa Allah ya kiyaye ma in aureka kayi fari da yawa ni nafi son irin Yaya Imran wanda baya magana sosai kai kuwa surutu kamar parrot.” Dariya sosai parlorn duka suka ganin Imran yana tahowa yana ware ido alamar yaji zancenta sarai. Tamke fuskarsa yayi ya zuba kallonsa akan shatu da tayi saurin jan gyale ta rufe fuskarta alamar kunya tsaki “kada ma ki saka rai da samun irina ke ai irinki Ammar d’in ne ya dace dake sai kuje ku haifi parrots d’in”Dada tsohuwa ta ta’be baki “Yo Allah na tuba kada dai inga mutum yazo yana ‘yar murya kana ganin yarinya zankad’aziyya wanke hannu ka ta’ba da mai matarka ta ka tafi ta to ku ku zama shaida ko nan gaba kada Imran yazo yace a bashi balarabiyar nan.” Tsaki yaja yana mi’kewa “MAI ZAN YI DA ITA? Ni kuwa God forbid gayyar ‘kazanta da surutun tsiya Ina da mata ta ‘yar gayu ta bugawa a jarida.” Ran shatu ne ya ‘baci tun da take bata ta’ba jin haushin kalamansa ba sai yau hawaye ya fara bin fuskarta.
[8/30, 9:26 PM] +234 706 428 6235: *🤍ME ZAN YI DA ITA?*🤍
NAZEEFAH SABO NASHE
FREE📚
08033748387
-18
ELEGANT ONLINE WRITERS
Sosai take hawayen saboda kalaman Imran sun ‘bata mata rai. Momma ta jata jikinta da sauri tana jifan Imran d’in da harara “fice min daga nan tunda burinka ya cika ka saka shatu kuka yo itama su’butar baki Tayi idan banda haka mai za tayi da kai a haife ka haifeta tunda ka ninka shekarunta.” Ficewa yayi ba tare da yace komai ba Allah ya tsari gatari da saran shuka” ya raya a zuciyarsa.
Ana gobe kamu masu tafiya abuja suka dinga dandazon tafiya dangin mommah dai ba suje ba a cewarsu bikin namiji suke zo ba ruwansu da dangin mace sun san ma kun sunje wula’kanci zasu sha,gida ya d’ad’e ba kowa daga mommah sai danginta suke Ta tsara yarda bikinsu zai kasance.Juma’a ne d’aurin aure don haka ranar asabar za suyi dinner lahadi suyi bud’ar kai ango ma alhamis d’in zasu wuce da abokansa da suka zo daga wurare da dama wasu ma ba ‘yan ‘kasar nan bane.
Da safe ma basu koma d’akin ba a sashen amarya suka koma zama suna sake la’antar mommah don a cewarsu aljannu take turo musu ai kuwa indai sune su zuba su da ita gida dai baza su barshi ba sai sun kai kwanakin da suka ‘kayyadewa kansu tunda a goben zasu tafi abuja kai lefe. Hameedah tana sake girgiza ‘kafa ranta a matu’kar ‘bace tace “wallahi wannan matar muka ‘kyaleta nan gaba raba mu za tayi da yaya manga gaba d’aya dole mu tashi tsaye a kanta mu har a gaya mana malamai mu da
Muku jinin barebari.” Falmata ma cewa tayi”wallahi kuwa naga alama kuma lefe tayiwa kanta tunda hajja tace mu kai kada ma mu nemi danginta wallahi kaiwa zamuyi ke kuma shaheedah sai kin dage sosai duk abinda muka kawo miki kada kiyi wasa dashi munyi al’kawarin sai mun dasa mata ninkin ‘bacin ran da ta sakawa manga sai mu zuba mu gani tana ji tana gani Imran sai dai ta hange shi daga ness” gaba d’aya suka saka shewa har da amarya zainab. Fanna na gyara zama tace mai yafi wannan takaici ace d’anka yana auren ‘yar kishiyarka kuma zainab ke kin samu d’a daga sama kamar yarda uwarta ta samu manga daga sama suke juya mana shi son ransu.” Dariya suka ‘kara yi.
Ko da ta gama shirin school tana fitowa general parlour ta gansu murmushi ta saki ta fara wa’kar ado gwanja ta casss. A harzu’ke suke kallonta,Hameedah ta mi’ke da sauri tana jifanta da wani irin kallo “ke don uwraki da wa kike?” Shatu rausayar da kai tayi gefe kafin tace “kawai don ina wa’kata sai ki zageni” fitowar Imran da Ammar kenan sunyi shirin fita su ka ji hameedah tana wallahi sai na sake jibgarki kamar yarda nayi miki jiya shegiya mai idon aljannu.” Imran waro ido yayi yana kallon hameedah mamaki fal ransa lalle bata san sharrin yarinyar nan ba bata san itace gayyar aljannun da suke wajigasu ba, har shatu ta karkace zata yi rashin kunya Ammar ransa a ‘bace ya jata “wuce ki tafi school tun d’azu driver na jiranki kin tsaya jan magana.” Baki ta zun’buro irin na shagwa’ba “Yaya Ammar uwata fa ta zaga.” Harara ya zuba mata “kin wuce ko sai na mangareki tayi ta zaginki ma yana tsiro ne? Oya maza-maza wuce school kafin na sameki a wajen” sum sum ta wuce har taje ‘kofa ta juyo da ‘karfi tace “an fad’a d’in a sosa cass a sosa iya da razor.” Imran bai san sanda murmushi ya ku’buce masa Ammar kuwa darawa yayi sosai yace “kai shatu danger” hameedah kuwa ‘kwafa tayi tana zabgawa Ammar harara.
Kashegari kuwa suka isa abuja dangin baban shaheeda suka kai lefe ba tare da dangin mommah ko d’aya ba duk da kuwa suna cikin abujar. Haka suka dawo da sha tara ta arziki duk da suma ba lefen wasa suka kai ba lefene na gaske na gani a fad’a na kuma d’orawa a instagram,a yayata a duniya. Biki kuwa aka saka shi sati uku cif don suma dangin uban shaheedahn a shirye suke tsaf kuma masu farcen susa ne tabbas kuwa za’ayi biki na kece raini. Bayan sun dawo kano da kwana d’aya suka wuce maiduguri hannayensa dam’ke da sha tara ta arziki. Mommah ba tace musu Komai ba duk da ta tambayi Hajiya mama kuma ta tabbatar mata ba a gaya musu kai lefen ta basu ha’kuri. Hajiya mama ta girgiza kai a cikin wayar tace”Lala lala dijah ke zan bawa ha’kuri kiyi ha’kuri da jarrabawar da Allah yayi miki ta fitinannun dangi miji kina zaune ubangiji zaiyi miki sakayya suma fa mata ne kuma sun haifi mata ki zuba musu ido yanzu ubangiji ai tun a duniya yake sakayya ba kayi ba ma anyi maka ina ga kayi kiyi ha’kuri kullum shine abinda zan iya ce miki.” Hawaye ya zubowa mommah sai dai ba ta nunawa hajiya mama kuka take ba tayi godiya ta kashe wayar a zuciyarta tace “akwai ranar ‘kin dillaci ranar da zata cusa musu nasu ‘bacin ran dole ne su girbi abinda suka shuka d’a dai nata ne kuma ba zata bari su juya shi kamar yarda suke muradi ba.
*****************
A hankali awanni suka yi ta shigewa suna zama kwanaki daga kwanaki kuwa,har satittikan biki suka zo gidan a hargitse yake kowa sai shiri yake ana ji da lamarin bikin to ba dole ba ta kowane side jikan farko kuma d’an gaban goshi ake yiwa Aure,tun ana saura sati biki dahda yasa shaheedah dole ta koma gidan babanta duk da ba haka suka so ba uwarta taso ta tsaya ta cigaba da banka mata mallakin mallaka sai dai dole ta tafi. Hajja ma ana saura satin tazo ta tare a part d’in dahda daga gefe a babban parlournsa akwai wani bedroom and toilet anan ta baje danginta kuma suna d’aki mai Aljannu.
Mutanen katagum ma sun hallara ciki kuwa har da Dada tsohuwa mai ran ‘karfe. Tuni mommah ta fara gyara d’iyarta tsaf fatarta ta goge a spa haka nan an yi mata saloon gashin nnan an jawo shi tsahonsa har da na Mamaki.
Suna dawowa daga spa a gajiye suka tarar Hajiya mama tazo ita ma da ‘yan uwanta na yola ga Hafsa da Nahna da sauri shatu ta rungume uncle Hisham shi kuwa duk da nauyin da tayi masa haka ya shiga wulwulata yana fad’in a cafe a cafe ‘yar gidan mommah mai mommah ke baki ne kika yi wani fresh har glowing kike?” Kayan dad’i” ta furta tana murmushi har hushiryarta ta fito. Still Ammar yayi yana kallonta har bakinsa ya gaza shiru yace “mommah ‘karin gashi kika kaita aka yi mata da wankin fata?” Gaba d’aya gurin ba wanda baiyi dariya ba Hafsa tace “Ammar ko dai kana ciki ne a d’aura gobe da kai kawai.” Girgiza kai yayi “Ina ni ina rigimar shatu ni ‘kabilar ibira ma zan aura sun fi iya kula da miji” shatu ma harara ta zabga masa Allah ya kiyaye ma in aureka kayi fari da yawa ni nafi son irin Yaya Imran wanda baya magana sosai kai kuwa surutu kamar parrot.” Dariya sosai parlorn duka suka ganin Imran yana tahowa yana ware ido alamar yaji zancenta sarai. Tamke fuskarsa yayi ya zuba kallonsa akan shatu da tayi saurin jan gyale ta rufe fuskarta alamar kunya tsaki “kada ma ki saka rai da samun irina ke ai irinki Ammar d’in ne ya dace dake sai kuje ku haifi parrots d’in”Dada tsohuwa ta ta’be baki “Yo Allah na tuba kada dai inga mutum yazo yana ‘yar murya kana ganin yarinya zankad’aziyya wanke hannu ka ta’ba da mai matarka ta ka tafi ta to ku ku zama shaida ko nan gaba kada Imran yazo yace a bashi balarabiyar nan.” Tsaki yaja yana mi’kewa “MAI ZAN YI DA ITA? Ni kuwa God forbid gayyar ‘kazanta da surutun tsiya Ina da mata ta ‘yar gayu ta bugawa a jarida.” Ran shatu ne ya ‘baci tun da take bata ta’ba jin haushin kalamansa ba sai yau hawaye ya fara bin fuskarta.
[8/30, 9:26 PM] +234 706 428 6235: *🤍ME ZAN YI DA ITA?*🤍
NAZEEFAH SABO NASHE
FREE📚
08033748387
-18
ELEGANT ONLINE WRITERS
Sosai take hawayen saboda kalaman Imran sun ‘bata mata rai. Momma ta jata jikinta da sauri tana jifan Imran d’in da harara “fice min daga nan tunda burinka ya cika ka saka shatu kuka yo itama su’butar baki Tayi idan banda haka mai za tayi da kai a haife ka haifeta tunda ka ninka shekarunta.” Ficewa yayi ba tare da yace komai ba Allah ya tsari gatari da saran shuka” ya raya a zuciyarsa.
Ana gobe kamu masu tafiya abuja suka dinga dandazon tafiya dangin mommah dai ba suje ba a cewarsu bikin namiji suke zo ba ruwansu da dangin mace sun san ma kun sunje wula’kanci zasu sha,gida ya d’ad’e ba kowa daga mommah sai danginta suke Ta tsara yarda bikinsu zai kasance.Juma’a ne d’aurin aure don haka ranar asabar za suyi dinner lahadi suyi bud’ar kai ango ma alhamis d’in zasu wuce da abokansa da suka zo daga wurare da dama wasu ma ba ‘yan ‘kasar nan bane.