Sashe 18
Me Zanyi Da Ita Part Complete 2 Complete Hausa Novel · about 7 min read
Aliyu ne ya dafa Imran yana dariya “Amma lallai guy d’in nan ka raina mana hankali yanzu dama mutum biyu zaka aura baka gaya mana ba” Abdul ya girgiza kai yana murmushi yace “wonderful ni bama wannan ba how comes kai da baka son hayaniya ka auri mata biyu ina cika bakin da kake mana na cewa mace d’aya ta isheka?” Yana jinsu duk suna surutunsu ya kasa furta komai zallar tunani da zuciyarsa ta tafi,sai zufa yake tunani yake wacece ita wacece ma wata Aysha da aka d’aura masa aure bai sani ba, tabbas ashe kuwa tayi shirin zama bazawara don sam bai ga dalilin da zai sa ya amince da mace har biyu ba. Koma waye ya bawa dahda wannan gurguwar shawarar. Tsawon lokaci zuciyarsa ta kasa hasasho masa shatu ce yarinyar gaba d’aya zuciyarsa ma bata hasasho masa shatu ba tunani yake a cikin ‘ya’yan abokan dahda da suka mayance masa cewa suna sonsa aka d’auki d’aya aka bashi. Bai cewa abokansa komai ba duk da surutan da suke masa, burinsa yaga dahda ko Ammar amma ba d’aya da ya gani,hakan yasa dole suka shiga motocinsu suka tafi masauki.Imran dai ya zama tamkar mutum mutumi.
Amarya shaheedah kuwa a bakin yayyenta maza da suka dawo dga d’aurin aure ta samu labari.shaheed da ya shigo a rud’e ne ya dafa ta murya can ‘kasa yace “How comes shaheedah duk cika bakin da kike yi ba zaki zauna da kishiya ba sai gashi ko tarewa ba kiyi ba angonki ya auri wata zai had’a ta dake.” Shaheedah da bata d’au zancen serious ba ta zabga masa harara “God forbid don Allah shaheed ka daina wannan wasan bana son sa as per as am alive ko kallon ‘yan mata ba zan bar habibi yayi ba balle kishiya over my death body” shaheed murmushi yayi kafin khalil ‘kaninta yace “ai kuwa kin makaro don kuwa mata biyu aka d’aurawa aure da habibinnaki ke da wata Aysha.” Da sauri shaheedah ta mi’ke tana kallonsu “please don Allah kuce min wasa kuke?what a nonsense?” Khalil da shaheed suka sake tabbatar mata haka nan sauran mutane da suka je d’aurin aurenma suka tabbatar mata,dalilin da yasa ta yanke jiki ta fad’i, tuni nmufashinta ya d’auke,hakan yasa da sauri aka rufu akanta ana ‘ko’karin ceto ranta.
‘Yan kano kuwa tuni labari ya riski zainab ta hanyar mutane masu sanar da ita fad’uwar shaheedan da dalilin fad’uwarta ta.cikin tsananin mamaki take cewa “mata biyu a haba dai ba kuji da kyau ba idan kuwa hakan ya tabbata tabbas duk wacce tayi ‘ko’karin zama kishiyar shaheedah tayi shirin riskar ba’kin cikin da zai zama ajalinta wallahi.” Da sauri ta mi’ke ta nufi General parlour inda Hajja take.tun kafin ta furta komai hajja ta tabbatar da ba lafiya ba don yanayinta ya nuna ‘karara. Da sauri Hajja ta mi’ke da niyyar ta jata su samu sirri don ganin dada a zaune da itama ta kasa ta tsare, amma ina zainab tuni ta furta abin da ya ri’ke mata ma’kogaro “Hajja da gaske ne? Da gaske ne Imran mata biyu aka aura masa da wata wai Aysha wacece ita?” Gaba d’aya gurin zaro ido su kayi, musamman Hajja da maganar tayi mata dirar mikiya, da sauri ta girgiza kai “wannan ba gaskiya bane ba yarda za’ayi manga ya zartar da wannan hukuncin bai gaya min ba sharri ne da surutu irin na d’an Adam” zainab ta girgiza kai “Hajja babu fa batun sharri a wannan zancen it’s true naji a bakunan da ba zasu min ‘karya ba kuma sun halarci d’aurin auren ga shaheedah canma ance ta sume daga kin zancen.” Hajja ta ja ta zauna ja’bar a kujera “To wacece yarinyar aka ce miki idan kuwa zancennan ya tabbata tabbas manga zai ga ‘bacin raina kuma Imran dole ya saketa koma wacece zancen banza zancen wofi kenan, ki kwantar da hankalinki kamar tsumma a randa.” Mommah dake zaune murmushi kawai take zubawa ta tabbata yau gidannan akwai show idan har suka san wacece amaryar.tana kallonsu suka shige d’aki bayan hameedah ta tunatar dasu zancen a sirri ya kamata ayi shi.Mommah ta ta’be baki a zuciyarta tace “oho dai burina ya gama cika.”
Kowa burinsa Dahda ya dawo yaji ya gaskiyar lamarin yake.ko su Hajiya Mama mommah bata gayawaba ta ja bakinta tayi shiru tana jiran kowa yaji labarin kamar dirar mikiya tunda ta lura har yanzu basu san da shatunta aka d’aura aure ba.
Shi kuwa Imran yana can asibiti ya tasa shaheedah gaba da kallo da take ta kuka bayan farkowarta,ta kuma tabbatar da lamarin gaskiya ne.sai ga Imran ya ‘bige da jinya madadin hotunan d’aurin aure da suka ci burin aiwatarwa,irin dai wanda ake yayi a social media d’innan.
Kukan take sosai da har ya ‘karawa Imran zazzafan ciwon kai,ya kama kannasa ya ri’ke tun yana rarrashin ta da yi mata rantsuwar ta kwantar da hankalinta koma wacece idan ya tabbatar da auren sakinta zai yi kuma da gaske yake.amma ina shaheeda bata ji shi ba,hakan yasa kawai ya kama hannunta yana murzawa alamar rarrashi idanunsa a lumshe. Haushi ma lamarin ya bawa abokansa yanda take kuka kamar a kanta aka fara kishiya.Tsawon lokaci sannan aka sallamesu bayan ta gama shan drip.ana komawa gida Abbanta yace ta bari ta warware a kaita. Suna ke’bewa da Imran tace yace kawai a kaita please Imran anty na nake son gani kawai ko zuciyata tayi sanyi.” Tausayinta yasa Imran gayawa wata ‘kanwar babanta cewar a kaita kawai ta ‘karasa warwarewa a gidanta.
Haka kuwa aka yi babu ‘bata lokaci aka tafi airport dama sun yi booking jirgi.amarya dai ta tafi fuska ‘kozai-‘kozai fuska ko kwalliya babu duk da burin da aka ci na budiri a wannan ranar.
Ana kaita ko ta kan mommah da danginta ba abi ba duk da tunasarwar da dangin ubanta suke musu amma Hajja ‘kememe ta’ki yarda tace “ku shige da ita d’akinta mai aka yi aka yi wata dijah balle danginta wa ya san surkullen da suka yiwa manga ya d’aura masa aure da wata yarinyar.ku kaita gurin uwarta ni ina nan ina jiran shigowar manga tunda ya’ki d’aga waya ta.”hakan yasa ba wanda ya sake bi ta kan uwar miji duk da al’ada ta shar’anta a bata damarta a kai mata matar d’anta. Hakan sam bai damu mommah ba tunda burinta ya cika.
Shi kuwa ango Imran yana cikin d’akinsa zuciyarsa sai suya ta keyi shi mamakinsa d’aya dama ana yiwa namiji auren dole? Yana jiyo abokansa suna ta dariyar shegantkarsu.
SHIGOWAR DAHDA**************
Yana dawowa ya tarar Hajja da jama’arta baje a parlourn,gefe d’aya ga Dada da tata jama’ar,zancen dai ya san ake hakan yasa bai san lokacin da murmushi ya ku’buce masa ba ya san sarai za’a rina,Dijah ta jawo masa rigima yau,da bai san yarda zaiyi solving d’inta ba. ya dur’kusa ya gaida su Dada sannan ya ‘karasa gefen hajja ya zauna, Da kyar take amsa gaisuwar da yake mata tana gama amsa gaisuwar ta d’ora da “meye gaskiyar labarin da naji game da aure biyu da akace an d’aurawa Imrana,wacece yarinyar da har ni ban isa kayi shawara dani ba?” Manga waigawa Yayi yaga Dijah bata wajen don haka ya ciro wayarsa ya kira ta yana kallon hararar da Hajja take masa ya cigaba da kiran Imran shima a waya,so yake su hallara duk ayi komai a gabansu. Tsawon mintuna mommah ta shigo da su Hajiya mama, sai ga Imran shima ya shigo jikinsa a sanyaye, ya zauna a gefen mommah, haka nan zainab da su shaheedah su hameedah suma duk suka bayyana.
Sannan manga ya gyara zama ya fara da “kamar yarda kuka saka Imran da shaheedah soyayya har suka amince da junansu suka ‘kaunar junansu haka ita ma Dijah mahaifiyarsa ta bu’kaci son a had’a Auren Imran da shatu yarinyar wajenta.........
Idanu waje kowa yake kallonsa cikin tsananin mamaki.Imran kuwa zama yayi kamar statue yayi masa ‘kuri da ido kawai yana tunani shatu shi aka aura ma Shatu,shatun dai da ya sani ‘kazama shi kuwa mai zai yi da ita a yanzu ba sai anjima ba zai saketa wallahi yaushe zai iya wannan abin kunyar mai zai cewa mutanen da yake cikawa baki yana fad’in mai zai yi da ita? Ita kuwa shaheeda tuni ta zube a jikin hameedah ta ma kasa kuka sai sakin ajiyar zuciya take.
Imran murya na rawa ya fara ro’kon Dahda “please dahda wallahi bana sonta ko kad’an kada kuyi min haka zaku sa min attack wallahi don Allah ka amince Na sake ta.” “Wallahi Imran ka sake Na saki shatu sai dai ka sake uwa don wallahi sai na zare ka daga cikin ‘ya’yana Na gaya maka kada ma ka fara attempting zancen saki idan kuwa haka ta faru zan nuna wa kowa bad side d’ina wallahi an kaini ‘karshe” sosai kuwa yake kallonta saboda yarda take maganar da gaske take daga ‘kasan zuciyarta take fitowa, ranta a ‘bace idanunta kuwa yayi jajir.
Sai ji su kayi Hajja ta saki dariya muryarta a sama tace “Ai kuwa ba ki isa ba dijah ni kuma zan nuna miki nice uwar manga ko ki amince ya sake ta ko kuma ni na saka manga ya sake ki.......
*🤍ME ZAN YI DA ITA?*🤍
NAZEEFAH SABO NASHE
FREE📚
08033748387
-20
ELEGANT ONLINE WRITERS.....
Amarya shaheedah kuwa a bakin yayyenta maza da suka dawo dga d’aurin aure ta samu labari.shaheed da ya shigo a rud’e ne ya dafa ta murya can ‘kasa yace “How comes shaheedah duk cika bakin da kike yi ba zaki zauna da kishiya ba sai gashi ko tarewa ba kiyi ba angonki ya auri wata zai had’a ta dake.” Shaheedah da bata d’au zancen serious ba ta zabga masa harara “God forbid don Allah shaheed ka daina wannan wasan bana son sa as per as am alive ko kallon ‘yan mata ba zan bar habibi yayi ba balle kishiya over my death body” shaheed murmushi yayi kafin khalil ‘kaninta yace “ai kuwa kin makaro don kuwa mata biyu aka d’aurawa aure da habibinnaki ke da wata Aysha.” Da sauri shaheedah ta mi’ke tana kallonsu “please don Allah kuce min wasa kuke?what a nonsense?” Khalil da shaheed suka sake tabbatar mata haka nan sauran mutane da suka je d’aurin aurenma suka tabbatar mata,dalilin da yasa ta yanke jiki ta fad’i, tuni nmufashinta ya d’auke,hakan yasa da sauri aka rufu akanta ana ‘ko’karin ceto ranta.
‘Yan kano kuwa tuni labari ya riski zainab ta hanyar mutane masu sanar da ita fad’uwar shaheedan da dalilin fad’uwarta ta.cikin tsananin mamaki take cewa “mata biyu a haba dai ba kuji da kyau ba idan kuwa hakan ya tabbata tabbas duk wacce tayi ‘ko’karin zama kishiyar shaheedah tayi shirin riskar ba’kin cikin da zai zama ajalinta wallahi.” Da sauri ta mi’ke ta nufi General parlour inda Hajja take.tun kafin ta furta komai hajja ta tabbatar da ba lafiya ba don yanayinta ya nuna ‘karara. Da sauri Hajja ta mi’ke da niyyar ta jata su samu sirri don ganin dada a zaune da itama ta kasa ta tsare, amma ina zainab tuni ta furta abin da ya ri’ke mata ma’kogaro “Hajja da gaske ne? Da gaske ne Imran mata biyu aka aura masa da wata wai Aysha wacece ita?” Gaba d’aya gurin zaro ido su kayi, musamman Hajja da maganar tayi mata dirar mikiya, da sauri ta girgiza kai “wannan ba gaskiya bane ba yarda za’ayi manga ya zartar da wannan hukuncin bai gaya min ba sharri ne da surutu irin na d’an Adam” zainab ta girgiza kai “Hajja babu fa batun sharri a wannan zancen it’s true naji a bakunan da ba zasu min ‘karya ba kuma sun halarci d’aurin auren ga shaheedah canma ance ta sume daga kin zancen.” Hajja ta ja ta zauna ja’bar a kujera “To wacece yarinyar aka ce miki idan kuwa zancennan ya tabbata tabbas manga zai ga ‘bacin raina kuma Imran dole ya saketa koma wacece zancen banza zancen wofi kenan, ki kwantar da hankalinki kamar tsumma a randa.” Mommah dake zaune murmushi kawai take zubawa ta tabbata yau gidannan akwai show idan har suka san wacece amaryar.tana kallonsu suka shige d’aki bayan hameedah ta tunatar dasu zancen a sirri ya kamata ayi shi.Mommah ta ta’be baki a zuciyarta tace “oho dai burina ya gama cika.”
Kowa burinsa Dahda ya dawo yaji ya gaskiyar lamarin yake.ko su Hajiya Mama mommah bata gayawaba ta ja bakinta tayi shiru tana jiran kowa yaji labarin kamar dirar mikiya tunda ta lura har yanzu basu san da shatunta aka d’aura aure ba.
Shi kuwa Imran yana can asibiti ya tasa shaheedah gaba da kallo da take ta kuka bayan farkowarta,ta kuma tabbatar da lamarin gaskiya ne.sai ga Imran ya ‘bige da jinya madadin hotunan d’aurin aure da suka ci burin aiwatarwa,irin dai wanda ake yayi a social media d’innan.
Kukan take sosai da har ya ‘karawa Imran zazzafan ciwon kai,ya kama kannasa ya ri’ke tun yana rarrashin ta da yi mata rantsuwar ta kwantar da hankalinta koma wacece idan ya tabbatar da auren sakinta zai yi kuma da gaske yake.amma ina shaheeda bata ji shi ba,hakan yasa kawai ya kama hannunta yana murzawa alamar rarrashi idanunsa a lumshe. Haushi ma lamarin ya bawa abokansa yanda take kuka kamar a kanta aka fara kishiya.Tsawon lokaci sannan aka sallamesu bayan ta gama shan drip.ana komawa gida Abbanta yace ta bari ta warware a kaita. Suna ke’bewa da Imran tace yace kawai a kaita please Imran anty na nake son gani kawai ko zuciyata tayi sanyi.” Tausayinta yasa Imran gayawa wata ‘kanwar babanta cewar a kaita kawai ta ‘karasa warwarewa a gidanta.
Haka kuwa aka yi babu ‘bata lokaci aka tafi airport dama sun yi booking jirgi.amarya dai ta tafi fuska ‘kozai-‘kozai fuska ko kwalliya babu duk da burin da aka ci na budiri a wannan ranar.
Ana kaita ko ta kan mommah da danginta ba abi ba duk da tunasarwar da dangin ubanta suke musu amma Hajja ‘kememe ta’ki yarda tace “ku shige da ita d’akinta mai aka yi aka yi wata dijah balle danginta wa ya san surkullen da suka yiwa manga ya d’aura masa aure da wata yarinyar.ku kaita gurin uwarta ni ina nan ina jiran shigowar manga tunda ya’ki d’aga waya ta.”hakan yasa ba wanda ya sake bi ta kan uwar miji duk da al’ada ta shar’anta a bata damarta a kai mata matar d’anta. Hakan sam bai damu mommah ba tunda burinta ya cika.
Shi kuwa ango Imran yana cikin d’akinsa zuciyarsa sai suya ta keyi shi mamakinsa d’aya dama ana yiwa namiji auren dole? Yana jiyo abokansa suna ta dariyar shegantkarsu.
SHIGOWAR DAHDA**************
Yana dawowa ya tarar Hajja da jama’arta baje a parlourn,gefe d’aya ga Dada da tata jama’ar,zancen dai ya san ake hakan yasa bai san lokacin da murmushi ya ku’buce masa ba ya san sarai za’a rina,Dijah ta jawo masa rigima yau,da bai san yarda zaiyi solving d’inta ba. ya dur’kusa ya gaida su Dada sannan ya ‘karasa gefen hajja ya zauna, Da kyar take amsa gaisuwar da yake mata tana gama amsa gaisuwar ta d’ora da “meye gaskiyar labarin da naji game da aure biyu da akace an d’aurawa Imrana,wacece yarinyar da har ni ban isa kayi shawara dani ba?” Manga waigawa Yayi yaga Dijah bata wajen don haka ya ciro wayarsa ya kira ta yana kallon hararar da Hajja take masa ya cigaba da kiran Imran shima a waya,so yake su hallara duk ayi komai a gabansu. Tsawon mintuna mommah ta shigo da su Hajiya mama, sai ga Imran shima ya shigo jikinsa a sanyaye, ya zauna a gefen mommah, haka nan zainab da su shaheedah su hameedah suma duk suka bayyana.
Sannan manga ya gyara zama ya fara da “kamar yarda kuka saka Imran da shaheedah soyayya har suka amince da junansu suka ‘kaunar junansu haka ita ma Dijah mahaifiyarsa ta bu’kaci son a had’a Auren Imran da shatu yarinyar wajenta.........
Idanu waje kowa yake kallonsa cikin tsananin mamaki.Imran kuwa zama yayi kamar statue yayi masa ‘kuri da ido kawai yana tunani shatu shi aka aura ma Shatu,shatun dai da ya sani ‘kazama shi kuwa mai zai yi da ita a yanzu ba sai anjima ba zai saketa wallahi yaushe zai iya wannan abin kunyar mai zai cewa mutanen da yake cikawa baki yana fad’in mai zai yi da ita? Ita kuwa shaheeda tuni ta zube a jikin hameedah ta ma kasa kuka sai sakin ajiyar zuciya take.
Imran murya na rawa ya fara ro’kon Dahda “please dahda wallahi bana sonta ko kad’an kada kuyi min haka zaku sa min attack wallahi don Allah ka amince Na sake ta.” “Wallahi Imran ka sake Na saki shatu sai dai ka sake uwa don wallahi sai na zare ka daga cikin ‘ya’yana Na gaya maka kada ma ka fara attempting zancen saki idan kuwa haka ta faru zan nuna wa kowa bad side d’ina wallahi an kaini ‘karshe” sosai kuwa yake kallonta saboda yarda take maganar da gaske take daga ‘kasan zuciyarta take fitowa, ranta a ‘bace idanunta kuwa yayi jajir.
Sai ji su kayi Hajja ta saki dariya muryarta a sama tace “Ai kuwa ba ki isa ba dijah ni kuma zan nuna miki nice uwar manga ko ki amince ya sake ta ko kuma ni na saka manga ya sake ki.......
*🤍ME ZAN YI DA ITA?*🤍
NAZEEFAH SABO NASHE
FREE📚
08033748387
-20
ELEGANT ONLINE WRITERS.....