← Book details Me Zanyi Da Ita Part Complete 2 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 21 OF 25

Sashe 21

Me Zanyi Da Ita Part Complete 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Tsaf shatu ta fito tayi masifar kyau cikin makeup d’in da dressing d’in da aka yi mata pink lace ne da touches d’in maroum a jiki hakn yasa aka saka mata head maroum dinkin ya zaunu daram a jikinta duk da dai ‘kwailace inji Imran amma fa
Komai yaji don tafi waccen matar tasa muciya da zani 😂. Tafiyar da za tayi ma sai da Nahna ta koya mata sai zabga’kamshin turare take. Suka fita da su Hafsa don mommah da Hajiya mama dama ba zuwa za suyi ba. Ta windown bedroom d’insa ya hangosu, don haka da sauri ya ajiye babbar rigarsa da hularsa a saman gado ya fice da key d’in mota a hannunsa. A tsaye ya tarar dasu murmushin dole yayi yana duban Hafsa don ya san Nahna bala’i ce da wayonta sarai ba zata yarda da rainin hankalinsa ba. “small mom mu d’anyi magana ma na” bin sa tayi tana murmushi ganin yarda yake kallon shatu ita tunaninta mamakin kyan da tayi yake. “Waye zai kaiku ne?” Ya fad’a yana kallon Hafsa “wallahi Ammar muke jira wai ya tafi shiryawa” “okey ita wannan ku bani aronta zan kawo ta da kaina” Hafsa ta kalleshi “mhmn mhnn faof Big son kada ka jefa ni a trouble don Na sanka trouble maker ne”. Dariya yayi sosai “nothing will happen insha Allah kada kiji komai wannan jaririyar ma kawai dai kin sanni da kishi apart from that ma yanzu duka responsibility d’inta yana kaina tunda an shafa ko ba haka ba?” Hafsa ta ta’be baki “ni dai da ka barta” zuwa yayi yaja hannun shatu yana murmushi “muje ke” shatu tayi ‘ko’karin janye hannunta ta kasa ya matse shi gam ya kuma yi mamakin jin wani irin taushi a hannun kamar audiga. “Alhamdulillah” ya furta bayan ya shiga part d’insa ya tarar gayyar abokansa sun fita, turjewa shatu ta fara yi ya jata da sauri har suna had’e jikinsu ya tura ta bedroom dinsa jin ana bud’e bedroom d’in Ammar.suna shiga ya tura ta saman kujera yana murmushi “ba dai nace ba zaki ba ance sai kin je yanzu ai sai naga ta yarda zaki.” Turo baki tayi alamar zata yi shagwa’bar da ta saba, ya matsa kusa daf da daf da ita yana mata kallon cikin ido “wallahi kika fara min kuka anan sai kin gane kurenki ba dai ba kya jin magana ba? Sai in ga mai fita dake ai har da wani zuwa ayi miki shafe-shafe kayan haushi kawai in dai don ni kika yi to ba kiyi kyau ba look at your mouth kamar gidan tsutsa.” Shiru tayi masa zuciyarta Na ‘kuna yanzu duk wannan kwalliyar a banza aka yi kenan? Nocking d’in da ake ne Yasa shi saurin zira rigarsa don ya san shaheedah ce ya gyara hula yana fesa turare Ta mudubi yake yi mata dariyar mugunta ganin yarda ta ‘bata fuska ‘kiris take jira ta fashe amma taurin kai ba zai bari tayi kuka ba. Tana kallo ya bud’e bedroom d’in ya zare key d’in da sauri ya fita ya kulle ya rufe ta baya da key yana murmushin mugunta. Shaheedah da take tsaye ta zata ita yakewa murmushin ganin kyan da ta zuba.
Tayi kyau sosai cikin black dressing ya kama hannunta suka fita.to su shatu za’ayi dinner a d’aki kenan,yana fita shatu tasa kuka ta tuge d’an kwalin da sar’kar kuka take sosai kamar me gashi tana ta buga ‘kofa amma ba wanda ya jita hakan yasa ta zauna gefen gado,ga mararta ta fara ciwo ta kuma san period ne tunda tun last month dama ta fara,Allah yasa dama da pant d’inta da pad a jaka don mommah ta gaya mata in dai ta ga date d’inta yazo to ta dinga fita da shirinta,tana ji mararta na ta motsi ta zuba tagumi kawai.

Gurin dinner ya had’u an cika kamar me kowa yayi kyau an ci kuma an sha ana ta spray d’in kud’i, Hafsa da Nahna kuwa sai neman shatu suke ba ita ba labarinta, haka yasa hafsa taje kusa da Imran tana tambayarsa,murmushi yayi yace tace fa ba zata iya zuwa ba bata jin dad’i tana d’aki na.” Hafsa bata kawo komai ba ta juya jikinta a sanyaye tana tantamar zancen Imran a zuciyarta.

Ita kuwa shatu tana can ri’ke da mara ba tayi aune ba ta fara bleeding tana mi’kewq taga tayi masa staining bed sheet waro ido tayi a hankali tace “Na shiga uku” sai kuma ta ‘kyal’kyale da dariya “Allah ya ‘kara ni nace ya kulleni kuma wallahi ba zan wanke ba” kuma sosai yayi staining. Ta shiga toilet ta zame pant da under skirt d’inta ta yar a wajen sannan ta wanke jikinta a toilet seat d’in shima ko flurshing ba tayi ba ta gyara jikinta tsaf Ta fito tana dariyar mugunta.”Alhamdulillah nagode maka period da kazo yanzu.”
Ta koma saman bed d’in tayi kwanciyar ta daga d’ayan side d’in ‘kamshin turarensa da sanyin a.c ya gauraye ta lumshe ido barci tuni ya fara fisgarta.

Mommah sai da ta ga kowa ya fice Dada ma ta shiga d’akin da suka sauka tayi shirin

*🤍ME ZAN YI DA ITA?*🤍

NAZEEFAH SABO NASHE

FREE📚
08033748387
-22

Mommah sai da ta ga kowa ya fice Dada ma ta shige masaukinta tayi shirin barci ta kwanta sannan Ta samu Hajiya mama da zancen tariyar shatu kamar yarda su kawu sa’idu suka bu’kata “Hajiya mama kin ji bu’katar da suka zo da ita na son shatu ta tare nan da one week.” Hajiya mama da sauri ta kalleta “wani irin zance ne wannan ina ce dake mu kayi zancen nan kika tabbatar min baki saka nan da sahekara biyar ma zata tare ba,su waye suka zo da wannan batun nifa bana son mutane su ga muna tauyewa yarinyar nan ha’kkinta a fara zaton don marainiyace don haka ni ban amince ba na tabbata kuma Babanku ma ba zai amince ba.” mommah tayi ‘kasa da kai tace “wallahi Hajiya mama nima yanzu na fiki da na sanin aurennan ji nake kamar na warwareshi ban da kawu sa’idu ne ma yazo da maganar da tuni na gama solving d’in problem d’in to shi mutum ne kaifi d’aya da baya canja magana, shi ya gayawa Dahda yace a gaya min a bisa umarninsa yarinya ta tare ko nan da one week ne ba na son yaga kamar na nuna masa bai isa da yarinyar ba.” Hajiya mama ta girgiza kai kafin taja ajiyar numfashi tace “Tir’kashi ana wata ga wata yanzu shatu mai zata je ta aiwatar a gidan auren shekara sha hud’u da watanni ai an daina yayin wannan auren,wallahi dama da kinyi shawara dani tun a farkon fari ma ba za’a yi wannan auren ba yanzu mai gari ya waya? Kin san dai babu dalilin da zamu bad’awa wannan dattijon arzikin ‘kasa a ido dole mu amince da abinda yace tunda dai kina gani ranar shi yazo ya siya miki ‘yanci a gidannan dole mu amince Allah yasa haka shi yafi zama alheri a gareta,ikon Allah kenan idan banda haka ga iyayenta nan su hafsa ko maganar aurar dasu ba’a fara ba sai ita jaririya a kansu to Allah ne kad’ai ya san lamarin da ya ‘boye a bayan hakan sai mu bita da fatan alheri,amma ko nan gaba idan zaki aiwatar da abu ki dinga neman shawara don aikin mai shawara baya ‘baci kuma ko bakomai ba za’a zo ana dana sani ba Allah ya shige musu gaba yasa ace gwara da aka yi.” Murya can ‘kasa mommah tace “ameen ai insha Allahu ma zan ja kunnensa kada ya sake ya d’ora mata nauyin auratayya har zuwa san da za ta gama ko da secondary ne” murmushi mama tayi a zuciyarta tace “kayya ban da yaran zamani duk da dai aure ne aka yi shi ba da son junansu ba.” momma ta gyara zama tace”kuma da dada zan had’a ta su tare har zuwa san da
Zamu ga kamun ludayin zamannasu,Sannan ga babansu ua bada ten million yace a siya mata kayan d’aki suna cikin account d’ina.” “Kash ai da bai wahalar da kansa ba addarsu,kuma tabbas Na san Babanku fad’a zaiyi amma shikkenan kiyi masa godiya ai hannun ba zai ‘ki dad’i ba mu ma za muyi namu ‘ko’karin don Babanku yace kallon shatu yake kamar maryam gatan da maryam ba ta samu ba shi zai mayar kan shatu, zan kira shi nima da safe nayi masa godiya gobe sai ku fara shiga kasuwa da ‘yan uwanki ku siya mata kaya Na gani Na fad’a kayan da ko gidan waye za’a kai ba’a ji kunya ba zan wa Babanku waya anjima kad’an shima ya bada abin da zai bayar.” Momma tayi godiya ta mi’ke ta tafi wajen dahda don shima bai je dinner ba yace ba zai iya wannan rashin kunyar ta ‘ya’yan zamani ba. Hajiya mama kuwa d’an kwanciya tayi da niyyar cikin dare za ta tashi tayi nafiloli Ta sake ro’ka musu zaman lafiya da zuri’a d’ayyiba don ita macece mai ibada kuma kullum addu’arta akan zuri’arta take.

Sai ‘karfe d’ayan dare dinner ta tashi duk da ango ya gaji amma kasancewar amarya tana ta girgizar rawa yasa dole ba’a tashi ba.rawa ce ta rashin kunya take ta yinta kamar yarda amaren zamani suke yi abin har mamaki ya dinga bawa jama’a musamman ango da abokansa. Da ya gaji ne ma ya mi’ke ransa a ‘bace ya fisgi Hannunta suka fice daga hall d’in dinnerr.zuciyarsa a cunkunshe da ba’kin ciki kasancewarsa mutum mai kishi, bai san ba abinda mutane suke kallo a jikinta ba.
Tun a mota kuwa ya dire mata kwandon masifa kamar zaici babu. Ita dai tayi shiru don ta san ta ‘bata masa rai. Yana packing kuma kallonta bai yi ba ya bud’e motar ya fita.jikinta a salu’be ita ma ta fito daga motar tana kallo ya shige part d’insu ta san ko ta bishi ba zai saurareta ba don haka ta wuce cikin gida da niyyar ta kira shi a waya ta bashi ha’kuri,tunda dai ta lura har lokacin aikin su bai kammalu ba.
Chapter 21 · 0% Book details