← Book details Me Zanyi Da Ita Part Complete 2 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 10 OF 25

Sashe 10

Me Zanyi Da Ita Part Complete 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Shatu tayi saurin matse dariyar da take son kamata, ta sake jijjiga ‘kasan gadon , cikin murya mai amo sosai tace “ Baki ga komai ba tsohuwa sai kin bud’e ido kin ganki a gaban sarkin aljannu yana bada umarnin a shanye jininki a yar da gawarki a daji namun daji su cinye ba dai ba kya jin magana ba mun ce ki fita daga harkar hadizatu kin ‘ki hahhhhhahhhha yau zamu sha jini ku ‘karaso maza ku d’auketa kada ku sauketa sai a dajin sarki ‘kuraizu hahhhhhahhha.” Ta sake tuntsirewa da shegiyar dariya hajja kuwa tuni ta sume tun bayan da Ta ‘kwallara wata ‘kara da duk gidan ya amsa bayan taji an jijjiga gadon da ‘karfi. Imran ne ya fara fitowa kafin su mommah suma su fito kowa yana Duban d’akin hajja inda ‘karar take fitowa. Imran baiyi wata wata ba ya bud’e d’akin da sauri ya ‘karasa gun hajja da ya gani a san’kame akan gado, ya fara jijjigata sai dai ba alamar numfashi a tare da ita, idanunsa ne ya sauka akan tsinkakken abin hannun shatu da sauri ya zaro ido bayan ya d’au abin hannun yana dudduba inda zai ganota, bai ga alama ba ya zira abin hannun a aljihunsa. Momma kuwa da sauri ta ‘karaso tana dubata a gigice take sosai hakan yasa murya na rawa take cewa “ Imran kira doctor she is unconscious “ Imran ya mi’ke yayi saurin shiga toilet nan ma bai ga shatu ba, ruwa ya d’ebo ya zubawa hajja a jikinta ,da sauri ta kawo ajiyar zuciya ihu take tana fad’in kada ku tafi dani bijahil kudrati na daina shiga sabgar dijama innalillahi.” Kowa d’akin tsit yayi yana kallonta, Imran ya kamata “ Tashi Hajja ba wani aljannu da izinin ubangiji koma akwai zan binciko su” Hajja ta mi’ke jikinta sai ‘bari yake fad’i take “muje d’akinka imran tunda manga baya nan a can zan kwana ni da d’akinnan har abada anan matattarar aljannun gidannan suke.” Ammar da yake gefe ya tuntsire da dariya sannan yace “ Hajja rannan fa cewa kika yi kunyi fad’a dasu har kin ‘konasu to yau me yasa kika kasa.” Shiru tayi tana dube-dube “ kai Ammar ka iya bakinka yanzu d’akin nan taf yake da jinnu kafin kaima su dawo kanka muje lmrana” jikinta rawa yake sosai Imran ya fita da ita daga d’akin.
‘Dakin mommah ya nufa da ita da sauri taja tunga ta tsaya “ ina zaka kaini Imran?” Fuska a had’e yace d’akin mommah mana wani abu ne?” Hajja taja baya kafin tace “ma’ana so kake naje d’akin su samu nayi su dagargazani d’akinka zaka kaini dama manga na nan ne sai ba kwana a d’akinsa gobe kuwa jirgin asuba zan bi zuwa garinmu ba zan sake kwana a gidan manga baseries kuyi min bukin na tikitin jirgi.” Ammar yace “kice ba zaki zo bikin bros ba?” Kallonsa tayi sai kuma tayi ‘kwafa ta dam’ki hannun Imran “muje d’akinnaka” Imran ya’bata fuska Kafin yace “ Ni fa hajja ba’a shigar min d’aki ni kad’ai nake amfani dashi for goodness sake ya zanyi dake idan kin so shiga toilet ki dai canja shawara idan ba zaki shiga d’akin mommah ba sai dai a kaiki d’akin amarya” “To kaini can d’in ita ‘yar banza ma ko fitowa ba tayi ba duk wannan budirin da ake.” Shi dai baiyi magana ba ya jata ya kaita part d’in amarya . Yace “sai ki buga mata ni zan tafi na kwanta” ya juya da sauri ta cakumoshi ganin labulai na motsi, tsaki yayi sai kuma ya hau dukan’kofar amarya tana fitowa ya bar hajja yayi saurin fita so yake yaje ya rutsa yarinyar can.

Ko da ya shiga d’akin ganinta yayi kwance akan gadon hajja tana ta tuntsira dariya, ko kad’an bata damu ba da taga ‘kofar d’akin a rufe da key bata da hanyar fita ta san kuma dole goben asirinta zai tonu. Tsit tayi bayan ganinsa a tsaye kamar wanda aka turo fuskarsa a had’e kamar hadarin kaji. Gadon ya’karasa ya janyo jelar gashinta sai gashi ta mi’ke tsaye tsam, fuskarta babu alamar tsoro ko kad’an. Ji yayi kamar ya mammaketa ya ja bakinta ya murd’e duk da taji zafi bata nuna masa ba sai ma ‘bata fuska da tayi “kece aljannar da ke tsorata Hajja kenan to yau asirinki ya tonu kuma sai na gayawa kowa abinda kika aikata har dahda so kike ki kashe masa uwa kenan?” Turo baki tayi tana masa kallon ‘kasa-‘kasa, ba tare da tayi magana ba, ya sake janta ta durgo daga kan gadon sai gata a gabansa, kallon mamaki yake mata ganin yarda sam ba tsoro ko kad’an a tare da ita ya rasa irin yarinyar nan ko dai da gaske tana da ala’ka da jinnu tunda ance rayuwar daji tayi. “Wato ke baki tsorata ma da laifin da kikayi ba, ji yarda kike kallona da idanu kamar na mayu d’auke idonki a kaina before i nock your head, yau a toilet za kiyi spending darenki wuce Muje.” Ta’be baki tayi an gaya masa tana tsoron kwana a toilet ne balle wannan toilet d’in nasu na ‘yan gayu ita tsoronta d’aya kada ya gayawa wannan Almasifatun Babannasu da ko idonsa bata son gani razana ta suke. Ya turata toilet d’in har zai kashe fitila da yake switch d’in a waje yake sai ya fasa ya rufe toilet d’in da key ya fice daga bed room yana mamakin taurin zuciyar shatu.

Da asubar fari yazo ya bud’eta ba don komaiba sai don baya son ya shafawa mommah black paint dole zai bar hajjan a zuwan jinnun gaske ne. Tana barci a kwamin wanka ya sameta hankalinta kwance. Tsayawa yayi yana kallon al’ajabi yarda take barci peacefully a cikin toilet idan shine ai an kasheshi baya jin zai kwana da lafiya. Ya daddage ya d’aka mata duka, ta d’anyi saurin bud’e idonta tana ganin shine ta saki murmushin mugunta don tayi targeting sai ta rama wallahi nan kwana kusa kuwa. Ta zuro’kafafunta ta fita. Shi kuma yabi bayanta. Sai da yaga ta shiga d’akinsu sannan yaja ‘kofar part d’in hajja ya fice masallachi.

Ana idar da sallahr asuba Hajja ta fito main parlour ta zauna, ko tunanin d’aukan kayan ta bata yi ba. Imran yana shigowa daga masallachi yayi arba da ita dariya taso ‘kwace masa sai dai da yake ba ma’abocin dariyar bane sai ya gimtse “ wai meye haka hajja tafiya ba shiri” ya fad’a yana jingina da bango. “ mi’kewa hajja tayi tana gyara sandarta kafin ta sake gyara glass d’in idonta ta kafeshi da ido kafin tace “ko ubanka manga bai isa yace sai na sake kwana a gidannanba aljannu na neman kassarani maza-maza muje ka kaini tashar jirgi.”Ransa a ‘bace ya juya sai kuma yace”ai dai kya yi sallama da mutanen gidan.” Ya shige sashen mommah Hajja tayi saurin bin bayansa “muje ka wani bar ni anan nifa tsoron gidannan nake ji” shatu da take la’be a window ta tuntsire da dariya da sauri hajja ta dam’ki hannun sa “kaji ko wallahi har yau suna gidannan ko baka ji abinda naji ba” hararar shatu yayi tayi saurin sakin labilan. Nahna da take zaune tana azkar ta kalli shatu “ ke lafiyarki kuwa?” Shatu taso bata da labari sai kuma ta gintse tace “zo kiga tsohuwar nan anty nahna zo kiga yarda take rawar d’ari duk tabi ta ma’kal’kale yah Imran” Nanah tace “Allah ya shiryeki shatu ko dai ke kike tsorata ta?” Da sauri shatu ta girgiza kai. Suna kallo su mommah suka rakata su kayi mata sallama.

Kashegari kuwa budurwar Imran ce ta bayyana a gidan tazo hutu a cewarsu wajen uwarta daga abuja fara ‘kal da ita har yellow take sai dai a tsaye take tsam kamar sanda shatu da take jikin window inda ta saba la’be, tana ta kallon yarda Imran yake rawar ‘kafa da budurwarsa ta kuwa ta’kar’kare tace “Muciya da zani” kasancewar parlourn ba hayaniya ba wanda bai ji furucinta ba sai da maganar ta fito tayi saurin toshe bakinta tana kallon Imran da suka yi four eyes da ita ransa a matu’kar ‘bace.....”

To fah! Shatu danger

*🤍ME ZAN YI DA ITA?*🤍

NAZEEFAH SABO NASHE

FREE📚
08033748387
-13

Da sauri shatu ta ruga part d’in mommah, shima Imran yayi saurin mara mata baya, yau kam ba mai hanashi cin kwal uban shatu, a bayan mommah ya ganta tana ta dariya ‘kasa-Kasa, kamar mayunwacin zaki haka ya bita zai cafkota, mommah tayi saurin ri’keta tana furta “kai lafiya uban mai tayi maka?” Cikin ‘bacin rai yace mommah please ki rabu dani in jibgi yarinyar nan, habibteey fa take tsokana wai muciya da zani” dariya ce taso kufcewa mommah tayi saurin rufe baki wanda hakan ya sake ‘kular da Imran yayi kukan kura ya kamota mari lafiyayye ya sauke mata. Da sauri mommah ta janye ta ranta a matu’kar ‘bace “ wai meye haka ne Imran kasheta zaka yi akan wata habibty to wai ma da tace mata muciya da zani sunanta ne? Ko kuwa an canja mata suna ne ta koma muciya ina ce dai ba sunan mutum bane muciya?” Ransa a ‘bace yake sake kallon mommah kafin yayi ‘kwafa wallahi da ita take kuma zaki gane baki da wayo” Mommah ta’kunshe dariyarta ita da nahna da shigowarta kenan tace “a’a Imran kaso kanka sai dai kuma idan tsarguwa kayi ni ban ga abin damuwa ba indai ba habibteeyn taka tayi kama da muciyar da zani bace” Hafsa da Nahna suka tuntsire da dariya. Tsaki Imran yayi ya juya ya fice zuciyarsa cike da sake tsanar shatu.

Bai ganta ba a parlourn hakan ya nuna masa ta shiga sashen mahaifiyarta don haka direct d’akinsa ya nufa yana danna waya nemanta yake, sai dai sai rejecting calls dinsa take.
Chapter 10 · 0% Book details