← Book details Kuyanga Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 2 OF 17

Sashe 2

Kuyanga Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Tace "To walh koma meye Nikam Bazan taba barin Wani bayan Yarima ya mulki garinnan ba inba shiba dan haka koma meye za,a yi masa shine dai gaba

Yadaga mata hannu "ya isa meye na tada hankali da kuka indai wannan maganar mulki ce Allah ketsara komai bamu zamu tsara ba tafiya turai kuma Yaje yaita tafiya Nadaina hanashi tunda bakya so inhana din duk randa yagaji da zuwa yadaina Amma kusan da sani zanbashi mata nan ba dadewa ba
Har zatayi magana kuma saita fasa tunda bazata ari bakin yariman ba tasan halinsa sarai shima bazai so Auran hadiba.

Ta mike tafuce batareda ta gaya masa cewar da "yar rakiya zai tafiba wannan tafiyar tasan Sarkin bazai bariba

*****
Ana gobe zai tafin Ummah tasa aka kira mata *KUYANGA*

Koda tazo ckn biyayya ta durkusa gabanta tana jiran umarni domin tayi tsammanin aiki aka kirata tayi

Ummah tace mata "Kuyanga Zeenatu ko?

Ta daga kai sama

"To kifara shiri daga yau gobe zaku tafi turai keda yarima zakijene domin kiringa hidimta masa komai nashi kece basai yace ba indai aikin wahalane kada kibari yayi Har sai ranar da yaga damar dawowa zaku dawo tashi kije.

*KUYANGA* Tace "Angama Ranki yadade.

Ta mike tafuce daga dakin fulanin

Koda takoma sashinsu zama tayi a inda suke zama da MAHBUB Ta zabga tagumi tashiga tunanin wai itace zataje turai tabdijan lallai zataji dadin Rayuwa zata canza tawaye tunda tashigo gidan sarki tun tana karama bata taba futa wajen gari ba sai gashi abin farin ciki zata keta hazo

TO ABIN BAKIN CIKIN FA? wata xuciyar ta tambayeta tare dayi mata tunin abinda zatajeyi turai dakuma tuni da wanda zataje din

Take fuskarta tacanza daga walwala zuwa Damuwa

Zuciyarta tahau bugawa to shin wane irin zama zasuyi Alhalin halinsa bame kyau bane?ance yana shan giya ance yana neman mata zance ya yadu agidan dan dai ana boyewane kada aji abakin mutum a hukuntashi.

Jitayi antabata afurgice tadago kanta saitaga ashe MAHBUB ne abokinta abokin sha,awararta

Takalleshi kawai yau babu dariyar datakeyi masa

Yazauna kusa da ita yafahimci akwai damuwa yau kenan

Yacire mata tagumin da tayi yace " *ZEENAH*! Haka yake ce mata

Takalleshi akaro na biyu tasunkui dakai

Yace mata "meya faru naganki ckn damuwa anyi miki wani abin ne bayan nabarki anan din?

Ta dago ahankali tace "Bayan barinka nan gurin aka aiko kirana daga Fulani

Koda naje kiran saitake gayamin wai infara shiri gobe Yarima zaiyi koma Turai dani xai tafi domin hidimta masa da koma kuma inmun tafi ba ranar dawowa harsai inyagaji yadawo dankansa

MAHBUB yadafe kirjinsa tareda Rintse idanu yana kiran sunan Allah

Tabbas yashiga tashin hankali domin ayau yashiga halin dabai taba shiga ba arayuwarsa tunda yazo duniya

Yana bude idonsa kwalla nabiyo baya yace mata "ZEENAH tafiyarki Turai tana daidai da tafiyar farin cikina nackn gidannan Domin kece me deban kewa akoyaushe kuma ke nake kallo nake jin dadi koda ina ckn jin Yunwa ke nake kallo naji nakoshi kinsan da cewa Nadade ina son.....

Yayi shiru yana goge kwallar datake gudu akuncinsa

Yakalleta ido da ido yace "ZEENAH bantaba gaya miki Sirrin zuciyata ba saiyau, yauma dole ce zata saka domin naga zakiyi nisa dani Walh ZEENAH zaman da nake dake bana abokantaka bace Na SO Ne zallah dan Allah kisoni koda bazamui Aure ba kice kema kina sona ko naringa tuno kalmar inajin Dadi

*KUYANGA* Taji wani yarrr!ajikinta taringajin shigar wani abu tundaga tafin kafarta har zuwa kwanyarta tabbas Tafahimci wannan abun dayake shigarta bakomai bane illah Son MAHBUB ada itakam tadaukeshi aboki amini amma ayau saitaji yanayin yajuye mata da So

Tabbas tana sonsa itama bayama data tuno zasuyiwa juna nisa saitaji xcyrta ta karye hawayen da basu zubo ba saigashi sunxubo ganin nasa ma sunzubo din

Tace ahankali " MAHBUB meyasa baka gaya min tuntuniba meyasa kaboye sai yau da muka makarowa juna zaka fada yanzu gashi zanyi maka nisa

Yace "Duk nisan da zakiyi indai kina sona to tamkar muna tare ne kedai kitaimaka ki furta min ko naji dadi.

Takalleshi tayi murmushi tasadda kanta akasa tace

"INA SONKA MAHBUB."!

yai ajiyar zuciya tareda yin hamdala ga Allah yace "nagode naji dadi ki rikemin Alkawari ki rike amana kikuma kula inkun tafi bamu da ikon kanmu ZEENATU akarkashin ikon Sarki da Matansa da "YA"YANSA muke bamu isa muyi musu da Umarninsu ba sai yadda sukayi damu amma kada kiyi biyayya da aikin zalinci kada kisake acuceki kikasance me addu,a aduk inda kike kikuma zamo me kamun kai aduk inda kika tsinci kanki domin kada ayi miki cutar da zata karya miki Lagon Rayuwarki.

Taja ajiyar zuciyar Zuciyar xuciya tace "Naji na amince nakuma gode da Shawararka ya masoyina .

.

Ya mike yace mata "maza tashi kije kifara shiri indare yayi kizo muhadu anan dan muyi sallamar karshe

Tayi murmushi tace " sallamar karshe kamar wanda xan mutu inmunje can

Yayi murmushi yace " ba haka nake nufiba, nasan wataqila da sassafe zaku tafi kinga ai zaifi kyau mukadaita mu dade tare mukara yin wata hirar soyayyar ko?

Tagyada kai tana dariya

Ya daga mata gira tareda kanne ido yana kallonta

Harya tafi yabar gun bata daina kallon saba tabbas MAHBUB yahadu rashin gata ne da yanayi yasa cikar kamalarsa bata fito ba harsai ankura ido ake hanga atattare dashi

Ta girgiza kai kawai takara gaba tabar gun tayi dakinsu

Tana shiga Taga Aminiyarta ZULAI

Zulaihat tace "Hhhmmm inata nemanki ai saikuma nahangoki acan lambun soyayya.

*KUYANGA* Tayi dariya tareda dukan kafadar Zulai tace "harkin sakawa gurin zaman namu lambun soyayya lallai Zulaihat ke "yar sa ido ce.

"Ba wani sa,ido gaskiyace ba lambun soyayyar bane?

"Eh bashi bane, to ai ba soyayyar akeba.

Cewar *KUYANGA* Tana dariya

Zulaihat tace "kifadawa keya yarinya kowa yafahimceku ingaya miki duk wanda yaga yanda kuke tabbas zaigano ckn mintina batareda yasha wuya ba.

"Hhhmmm to inma soyayyar akeyi saime? Ko bamu daceba.

Zulai takama baki tace "ho! Ni na isa ince baku daceba aji haushina to walh bari kiji kundace da MAHBUB tamkar danjunanku akayoku ina kuma Son tarayyarku.

Zama *KUYANGA* Tayi kusa da ita tace " Zulai gobe zanketa hazo fa.

Da sauri Zulaihat takalleta da alamar tambaya tace "hazo kuma?kamar yaya?

Nan Ta zayyano mata komai nagame da Rakiyar da Zatai wa Yarima Turai

Zulaihat tace "wayyo Allah na inama ni aka zaba.

*KUYANGA* Tace "tabdijan !kenan har wani son tarayya kike yi da Yarima?mutumin dakowa yasan halinsa marasa kyau. To walh ni ckn bakin ciki nake ahalin yanzu da har aka zabeni

Zulai tace "Dan dai zakiyiwa MAHBUB nisa ne amma aikinsan zaki huta zakuma kisami hutu da Aikin gidannan ZEENATU kifa tuna mubayine bayinma kaskantattu wadanda ba,a san inda iyayanmu sukeba ko suna raye?ko sun mace Allah shiyasani mudai muntsinci kanmune agidan nan

Dan Allah kikwantar da hankalinki inkinje domin Allah ne yazabeki domin kihuta kedai kiyi biyayya dama ke me biyayyarce kowa yasani bakida surutu magana bata dame kiba inba sabo kikayi da mutum ba basawa ba hanawa dan haka ki ajiye soyayyar MAHBUB anan zuwa sanda zaki dawo kwacigaba

*KUYANGA* Tace "to inma ban ajiyeba yazanyi bayan askiyazo gaban goshi gobe nefa zantafin dole inyi hkr da komai dama saiyau yabayyana min abinda ke ransa

Zulai tace "hhhmmm keda bakida gano abu da wuri aisaiyau kika ji kika gane amma ai kowa yagane manufarku tabbas muna muku fatan Alkairi kedashi.

*KUYANGA* Tace "mungode.

Nan *KUYANGA* Tahau shirya kayanta ckn wani Dan akwatin karfe me kyau dashi tana Ninka kaya tana sakawa tana ayyanota A turai shin ko wane Zama zasuyi insunje……… ???

*muje zuwa fans*
[7/23, 10:28 AM] Ummi Tandama: 📿 *KUYANGA* 📿

*_🌈KAINUWA WRITERS ASSOCIATION_*
```{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}```

https://www.Facebook.com/kainuwawritersassociation

*Dis Page i Dedicated to My Best friend Hauwa,u* *(UMMU ALEESHA wa WALEED)*

*Nabilancy Luv* 💘
(Auntyn S&S)

10-15

Da Sassafe tagama kintsawa misalin Bakwai na safiya Aka aiko kiranta daga Fulani

Tana shiga Sashin Fulanin ta tararta atsaye Yarima na kusa da ita da akwatinsa babba guda daya da alamar zai dade din domin fam yacika akwatin da duk abinda yasan zai bukata duk da acan gidan nasa akwai kayansa na sawa

UMMAH Ta daka masa Yaji ta sa anyo masa dambun nama ta soya masa gyada me gishiri duk abinda tasan dai yana matuqar So ta tanadar masa taxuba masa ckn Akwatin

Yana ganin *KUYANGA* Da akwatin yahau kallonta fuska ba fara,a yace "ke wannan akwatin irin na mutanen da kumafa? Kina nufin dashi zaki bini? Kinsan kuwa Turai ?Bafa Me dile bace, maza jeki canzoshi kokuma kitafi ba kaya inmunje xan nasiya miki wasu kawai

UMMAH tayi murmushi tace "Yi mata hakuri Yarima ta canzo kasan sai ahankali kayi mata uzuri taje ta canzo kayan kokuma inshiga innema mata cikin akwatina na

Yahau girgiza kai yana duba agogon hannunsa

"Barshi UMMAH saura mintina Jirginmu yatashi saima munyi wuta ahanyar zuwa Airport din don karmu makara

Yakalli *KUYANGA* Yace "ke ajiye kayanki anan muje da najikinki inmunje zansai miki wasu kiringa sanyawa.

Ckn ladabi tace "to shikenan.

Ta ajiye akwatin karfen nata agefe tabi bayansa UMMAH tana musu Addu,u,a da fatan Alkairi

Wasu bayi maza ne suka kai masa akwatin nasa har ckn mota aka zura a boot *KUYANGA* Ta shige gidan baya

Motar natafiya zata fuce agidan Sarautar saitaji wani iri aranta tabbas zatayi kewar MAHBUB yau ranar zata zamo mata ranar bakin ciki tunda ta taso kullum suna tare gashi yau zasuyiwa juna nisa kamar ance ta dago kanta kuwa tana dagowa takalli bayanta saita hangoshi ta glass yana dago mata hannu

Ta zura hannunta tahau daga masa itama

Ashe Yarima yana hangosu ta mirro amma baiyi maganaba yai shiru

a Airport kuwa da sukaje Dakyar ta iya daga kafa tahau matattakalar jirgi saida ta rintse idonta

Jirine ma yaso kadata Allah yaso ya kula yai saurin rikota tayo luuu jikinsa yatarota yamannata ajikinsa yahau da ita ahankali

Yasan arina tunda yasan ba taba hawa tayiba

Koda suka shiga ckn jirgi akusa da juna suka zauna

Kujerarsa na kusa da tata

Idonta akasa bata iya hada ido dashi don kunyar abinda yafaru da kuma biyayya
Chapter 2 · 0% Book details