← Book details Kuyanga Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 16 OF 17

Sashe 16

Kuyanga Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Da kuwa taje ga sarki tagaya masa ko uffan baice mataba shiru yayi mata dole tabar maganar yariman ta tafi

Amma ta qudurci yin aikin Asiri atsakaninsu domin janyo soyayyar yariman azuciyar sarkin

Yarima Yana dira akasar waje Allah yahadashi da wata bakar fata Ta nuna tana muradinsa azahiri bama tasan shidin Dan sarki bane saida taga alamomi a Dan zaman da sukayi na mintina a Airport

Hindu "Yar Minister ce a jahar Kaduna mahaifinta me kudine sananne Alh Khalid Baffanyo

"Yar boko ce gata da jijji da kai da dagawa Amma yau sai Allah ya damketa duk yanda take wulakanta samari a garinsu sai gashi ayau Allah yasa mata Soyayyar Saurayin da batasan asalin saba tashi guda

Dayake yariman ma na mamajo ne tuni ya afka cikin sonta shima taringa kanainaya da kissa don yasota takuma yi sa,a

Har rakiyarta yanema gidansa takuma bishi

Saidataje gidansa ta tabbatar shidin Dan babban gidane ta gane dawa take tare Domin tafahimci da alamar Dan gatane kamar yadda take yar gatan babanta

Saida suka kadaita sannan yahau tambayarta meya kawota England ?

Tace masa tazo Hutu ne gun kawunta Wanda shiya riketa alokacin datayi karatunta acan

Takuma gaya masa asalinta da matsayin data taka na aiki domin tana aiki da Ministry of Health itace Director asashen kula da Asibitocin Shiyyar Su

Ya jinjina kai yace " Ina sonki zaki Aureni?

Da zakuwa tace "Kwarai kuwa inhar da Gaske kake na amince maka amma kada ka yaudareni bani da dadi

Yayi dariya yace " nima ba Dadin gareniba.

Tayi dariya kawai

Aranar ta tayashi kwana agidan sunyi romance amma basu zarta nan ba don ya ayyana aransa ita zai aura takwanta masa

Aranar sun tsaida magana zaizo nanda sati biyu Kaduna yagaida iyayanta zai kuma tura magabatansa

Tunda suka tsaida magana da Hindu shikenan soyayya ta dinke atsakaninsu akullum suna tare awaya ba dare ba rana

Shaquwa sukai sosai in basuji muryar juna ba basajin dadi

Tana daga Kaduna amma kowa nata yasan da Fara soyayyarta da yarima

Iyayanta harsun San da sunansa domin ta gaya musu tuni

Dama ita kadai suka Haifa itace shalele sunaji da ita basa son bacin ranta

Yarima yakasa sakat tuni yahado kayansa sai Nigeria

Amaimakon yadiro Kano saiya zarce Kaduna

Kai tsaye yabi kwatancen d tayi masa

Ta aika da mota aka daukoshi aka kaishi gidan

Yaji Dadin tarbar da tayi masa da yan gidan

Yai mamakin ganin shankwamen gidansu kamar gidan Gwamna ga tarin motoci kamar ana saidasu

Akaita kawo masa gaisuwa ma,aikatan gidan aka cika gabansa da kayan ciye ciye

A main falour aka saukeshi

Mahaifiyarta taje takuma yaba da zabin diyar tata

Saida yajira mahaifinta Alh baffanyo yadawo suka gaisa ckn mutunci

Dayake mutumne wayyaye tuni yace yabashi ita yakuma bashi sati yaturo magabatansa

Yarima yai na,am

Sunyi soyayya kafin yatafi da yamma yai mata sallama yabi jirgi yataho Kano

Yaringajin kamar karsu rabu tamkar Wanda tayi masa asiri yaringaji

Ransa Dari qal yasami Matar Aure yasan yanzu dole maimartaba zai sauko inyaji zaiyi Aure

Muje zuwa fans
[8/12, 10:51 AM] Ummi Tandama: 📿 *KUYANGA* 📿

*_🌈KAINUWA WRITERS✍🏻 ASSOCIATION_*🤝🏻
```{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}```

https://www.Facebook.com/kainuwawritersassociation

*HAPPY SALLAH*
Eid⁠-Mubarak to all the muslims all around the world. May Allah SWT grant us the ability to make the most of this years.

*Nabilancy Luv* 💘
(Auntyn S&S)

95-100

Da Isar yarima gida kai tsaye gun mahaifiyarsa ya nufa

Tayi mamakin zuwansa bai sanar mata ba

Yana murmushi yace "UMMAH dawowar gaggawace tasameni adalilin Matar Aure dana gamu da ita

UMMAH da mamaki tace " Matar Aure kuma yarima ?a INA?

Yagyara zama yazayyane mata komai

Tahau gyada kai tana jin farin ciki aranta domin jin yarinyar yar masu dashine kuma hakan yayi mata arai tafiso shima yariman yayi Aure kamar yadda LAMIDO zaiyi domin Aure yana karawa mutum martaba da kima a idon Al,umma abin tinkahon tane ace tayi suruka Yar babban gida ba "yar Bayi ba dama

Tasawa abin albarka tareda karfafa masa guiwa " na amince maka kayi Aure adaidai wannan lokaci Yarima domin makiya suji kunyar abinda ake shirin maka tunda nasan duk don abakanta maka aka shiryi Auren su balle anga kafito da maitarka karara ka watsar dasu zuwa gaba mushirya kutunguila akansu inhar Aka nada LAMIDO sarautar domin baxamu barsuba

Ya gyada kai yace "Nima akwai shirin Dana shirya akan LAMIDON, UMMAH saidai zan ajiye komai agefe sai bayan nayi Auren tukunna amma kiyi kokari Takawa ya karbi abin da muhimmanci ahada ayi tareda na LAMIDON domin iyayan yarinyar da Gaske suke asatinnan zasu Zuba idon ganina

UMMAH tace " kada kaji komai Aure fa kamar anyi Angama

******
Koda UMMAH tajewa da Mai martaba wannan zance Murna ma yayi domin yasan yin Auren Yariman kamar wata hanyace zatazo masa ta shiriya don haka saiya nuna amincewarsa da gaggawa tareda tsayar mata da maganar zai tura aje akai kudin Aure tareda tsaida musu rana daidai Dana LAMIDO

Taji dadi tayi masa godiya takoma yiwa Yariman Albishir

Da farin ciki yakwana jin antsaida masa ranar Aure sati uku masu zuwa

Yaiwa Amarya Hindu albishir

Ai ihu taringayi Dan dadi da farin cikin data tsinci kanta aciki

Tuni ta gayawa iyayanta tamkar suma sungaji da itan saigashi suma suna murnar

Ackn Satin kuwa Mai martaba ya Aiko batun nan Aure

Galadima ne da Liman Amintattun Sarki sukaje kai kudin Aure Dubu Dari biyar

Da kwatance suka sami gidan domin mahaifin Hindu fitaccene babu Wanda baisan Gidan Minista ba a A T/wada Kaduna

Anbasu an amince musu nanda sati ukun Dayake kanin mahaifinsa ne da Yayan mahaifin nata da Amininsa suka karbesu agidan Ministan

Anbasu tukuici me tsoka tareda karramawa domin da tsaraba aka rakosu da zasu koma

Kaji da cake da lemuka da turarika da shaddoji haka aka zubasu a but din motarsu

Koda suka koma suka rattabasa sarki abinda suka gano cewar iyayan yarintafa Sunada mutumci da Halin girma

Sarki yaji dadi yasawa abin Albarka

Zancen Auren yarima da LAMIDO yazagaya gari anata irgen kwanakin dasuka rage sbd irin shagulgulan da aka shiryi yi sbd nad'in da za,aiwa LAMIDO na zama sarki da zaiyi

Lefe ma yarima A England yatafi yahado

Shiko LAMIDO dayaje gun *KUYANGA* tambayarta yayi

"Gimbiya!

Takalleshi da murmushi kan fuskarta tana murza zoben hannunta da MAHBUB yabata kafin yarasu

Tace ahankali
" Harna zama gimbiyar ?ai naga Gimbiya Matar Sarkice wacce yakeso kuma

Yayi murmushi dama shidin ma,abocin murmushine yace "Zeenatu kenan ai kamar kinzamane Tunda saura kwanaki daga lokacin da Aka daura mana Aure nima naxama Sarki Kema kinzama Gimbiya tunda aranar za,ai Nadi

Ta gyada kai tanajin annashuwa aranta da kuma sonshi ackn zcyrta

Shima hakan yakeji aransa agame da itan

Yakatse shirun nata dacewa " Awace kasa kikeso ahado miki lefe?

Takama baki "Ni na isa? Wacece ni tab ahado anan

Yasha mur! Yace " keko kika isa kuma ke me matsayice da kima don haka daga yau kidaina ma daukar kanki maqasqanciya agidannan domin kintashi daga *KUYANGA* kindawo *GIMBIYA ZEENATU*

Tayi murmushi ita kanta sunan yayi mata dadi

Yaci gaba da fadin"kinaji ko zamuje Sudan ko Dubai inhado miki komai acan nida Abokina Safwan tare mukai karatu dashi acan mahaifinsa ne liman na gidannan tare TAKAWA ya biya mana zaizo kugaisa

Takawa yana sonki Zeenatu ki godewa Allah jarabtar da Allah yayi mk arayuwa tazame miki riba da ci gaba domin ayau yakirani yakaramin kudi akan Wanda yabamu na siyayya nida yarima yace ke tadabance inyi miki siyayya mekyau

Yakarasa maganar yana kallon kyakykyawar fuskarta yana murmushi

Itama murmushin takeyi tana fadin "Naji dadi nagode ayiwa takawa godiya

Yace " To ni zankoma

Tayi masa yar rakiya da baifi taku biyar ba ta koma tana waigensa

LAMIDO ya burgeta tabbas yanada aji ga iya magana da kalami duk macen dayace yanaso dole ta amsa domin shi din abin sone

Tana shiga Daki tafada akan gado tana fara,a

Zulaihat tabita da kallo tana fadin "Yarinya tashiga kogin soyayya tafito

Dafatan kinyo iyo kinkamo kifi?

*KUYANGA* tayi murmushi tareda tashi tazauna tana fadin "Zulaihat kifaye ma nakamo ba kifiba tabbas LAMIDO yatafi dani kamar yadda nima natafi dashi

Allah nake godewa da yabani wannan baiwar ta zama matarsa gashi Yace Takawa yana sona yakara masa kudi akan Wanda yabasu da yarima na soyayyar lefe

Mahaifiyarsa kawai nakeji bansaniba ko itama tana sona kamar yadda Sarkin ke sona?

Zulaihat tace "Hhhhmm Zeenatu kenan aike abar soce itama banajin zataki sonki tunda ta tako har gidannan tazo miki barka da gaisuwa Dan haka kigodewa Allah kawai

" Allah nagode maka.cewar *KUYANGA*

Zulaihat tace "Ga magunguna can inji Iya Sha,awa tace kada kiyi sake da kowanne masu kyaune akwai nasha da nono dakuma nasha da Zuma anjima zata kawo miki na tsugunno

*KUYANGA* takama baki " oh maganin mata kuma tun yanzun?

Zulaihat tace "Eh aishine daidai hakan kinga abin xaifi kamaki Sosai

" Hhhmmm Allah dai yasa ba daci

Zulaita tace "koma me gareshi haka zakisha tunda kinsan Halin tsoffin nan insuka bada Abu ba,ashaba fada zasuyi suce suna mana gata muna gocewa

*KUYANGA* Tayi murmushi tadauki magungunan tafara hada wa xatasha

******
Yarima yadauki wayarsa yalalubo nambar abokinsa SAHABI da suka Dade basuyi wayaba

Acan bangaren SAHABI yana ganin kiran Yariman yayi murmushi yadaga yana fadin" Dama kana da nambata kamance dani

Yarima yace "inada ita mana fushi nayi dakai na abinda kayimin amma yanzu na huce Dan haka Ina gayyatarka Aurena karshen wata

SAHABI yayi murmushi yace " Allah yasanya Alkairi nima Auren zanyi nanda sati mezuwa kafin nakama

Yarima yace "Shegen kaya wato banda nakira bazanjiba kenan ?lallai na yarda karikeni aranka SAHABI

SAHABI yace " ba haka bane yarima Aurenne ba Wanda nakeso ba Hadani akai da yarinyar diyar kanin mahaifina ce ita ke sona

Dariya yarima yabushe masa yace "sunmin daidai walh domin insun kyaleka " yar talakawa zaka dauko musu banza me sakaran ra,ayi

Sahabi yace "kai " yar INA zaka aura?

Yarima yabashi labarin Hindu da yanda suka hadu a Airport a England

SAHABI yace "Hhhmmm to bagiringirin ba dai tayi mai

Yarima yace " oho dai nafika tunda ni Auran Soyayya zamuyi

"Nima bawai kinta nakeba tunda yar 'uwa tace

Ina Zeenatu naji ance abinda ta Haifa yarasu
Chapter 16 · 0% Book details