← Book details Kuyanga Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 12 OF 17

Sashe 12

Kuyanga Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

"Au dama ackn gidan nanma akwai wanda take soyayya dashi ? Ashe haka tazama yarinyar to da alama ma cikin agida tayishi kenan

Yarima yadago da sauri yadubi mahaifiyarsa da jajayen ido yace "A,a UMMAH tunjiya Dana dawo nagaya miki cewar Wannan cikin fa nawa ne kada ki kakabawa wani makaskanci mana jini na karba.... " Dakata!

Ta dakatar dashi da daga murya ranta abace

"Wai bazaka daina kiran cikin jikin *KUYANGA* da sunan mallakin kaba,walh inkai ka karba to ni ban karb'aba domin bazan yarda da shege ace shine jikanaba jikanma ajikin baiwa Allah yakiyaye dama ajikin wata baturiyar ne ko " yar sarauta da sauki

Yarima yace " Amma ai u UMMAH shi .mahaifina
yakarba ballantana ke da kike mace kikafi sona.

Tace "Dan babanka yakarba be dameniba domin yakarbane da wata manufa aransa tunda bayason azageshi bakuma yaso Dan daza,a haifa yatashi yarasa madafa amma nasan ba har zuci yakarba

" kidaina fadar haka UMMAH.

"Saina fada din kaida bakasan inda yake mk ciwo ba baka ma damu da kyautar kujerar sarauta da Aka baiwa LAMIDO ba

Yarima yace "Ni wannan kam baya gabana fatana dai ayanzu *KUYANGA* zeenatu ta Amince da abinda nazo dashi sbd Allah yajabceni da kaunarta UMMAH kitaimaka kiyi wani Abun walh sonta nakeyi sosai har cikin raina

UMMAH ta maka masa wata harara tace "Shima LAMIDOn daya Amsa yana sonta zai Auretan nasan badan Allah yayiba a to.

Yarima ya shiga tunani

Kai Yadafe don kan nasa ke bugawa dolene yasamo mafita akan MAHBUB Domin irin kalamin dayaji tana watsa masa na soyayya tabbas su yake muradin yaji wataran tagaya masa

Toshin ta wace hanyar? Ta Yaya?

Yakasa samo amsar tambayar domin kansa yakulle Dole saiya nutsu

UMMAH bacin ran abinda Yarima yaxo mata dashi baisa tasami nutsuwa ckn rantaba tabbas dolene tasami mafita akai rana zafi inuwa quna knn domin wannan shine ana wata ga wata can Hukuncin da sarki ya yanke nabaiwa LAMIDO sarauta nacinta arai saigashi Yarima yazo mata da wani batu wai yana son *KUYANGA* to tawace hanyar ma zaisameta Alhalin LAMIDO yakarba kowa yashaida hakan lokaci kawai ake jira

Yarima yadago dakansa yaga mahaifiyarsa ta hada kai da guiwa
.yasauko kasa Yakama kafafunta yana fadin

"UMMAH kitaimaka mini kije ga mai martaba kinemamin yafiya sannan kifada masa batuna na karbar cikin *KUYANGA* da zanyi kice nayi nadama sharrin shaidanne inasonta yadaina fushi dani

Wani dunqulelen abune yatsayewa UMMAH a maqoshi na takaici da bakin ciki

Taki jinin jin Kalmar nan dayake furtawa na son *KUYANGA* dayake fada mata yanayi domin ita ji takeyi tana kara tsanarta ma tunda itace tazamo silar rushewar Burinta ayau,tayi nadamar amincewa da tayi tun farko daya yatafi da ita kasar waje tasan da bata yarda sun tafin ba da tuni hakan bata faruba tunda gashi akan Yariman yak'ita yaki cikin ne LAMIDO yashirya manaqisa yakarba don abashi sarauta kuma anbashin kamar yadda sukeso kuma bazata taba bari suji Dadin yin mulkinba indai daranta saita zame musu masifa a ckn gidan

Wannan tunanin tane

UMMAH dai taga Yarima da Gaske yakeyi domin shirin kuka yake mata akan bukatarsa

Dabara ce tafado mata tace masa "kwantar da hankalinka shalele zansan abinyi agun Takawa

Yace " to agun ZEENATUN fa?

Tahade rai

Yamarairaice mata Taga dai da Gaske ne lamarin nasa saitahau tunanin anya kuwa ba Wani abun akaiwa D'an nataba mutumin dayaqi Abu futuk kuma cikin "yan kwanaki saiya haukace akai

Lamarin Allah nefa UMMAH 😃Allah yakara inji fans 😂

Takama hannayensa itama ckn marairaita tace masa "YARIMA kai D'ane D'an fari abin so aduk wani gidan sarauta baikamata ka lanjare a son BAIWA ba kafi karfin Auren *KUYANGA* ajinka da kimarka da izzarka na Dan sarki zai ragu inhar ka Auri *KUYANGA* inaso kayi hakuri kabarta ni dakaina zansamo maka ko ackn gidan sarautar mune akwai mata masu kyau adangina mahaifina kafin ya mutu yayi sarki yanzu babban yayana shine sarkin garinmu kasan da haka Babbar masarautace datafi wannan munada mata kyawawa yan boko wayayyu sai wacce kazaba babu me kinka walh kanada cikar da namiji kaidin gwarzone me tattare da mazan taka gaka kyakkyawa kafi LAMIDO kyau da kwarjini Meye naka na damuwa da Baiwa Alhalin kafi karfinta shi din dayace abashi ita ya Aura kabarsu dama da ita yadace

Yarima yakyabe fuska yace " UMMAH bazaki ganebane

Tace "tayakuwa zangane kaki amsar batuna

Dayaga da Gaske takeyi baxata sakkoba saiya rushe mata da kuka yasan lagontane bata son damuwarsa balle ganin hawayensa

Nan take kuwa ta rude tace masa yayi shiru zata duba lamarin yaje zuwa gobe kafin tasan abinyi

Yana Fita ta aika aka nemo mata jakadiya

Jakadiya na zuwa tagurfana gabanta

" gaisuwa nakeyi Uwar dakina barka da warhaka gani ckn ladabi mezan miki ?nasan bukatace babba tasa kk kirani

UMMAH tagyada kai tace "tabbas kuwa jakadiya domin Yarima yaxo min da banzan zance wai yanzu shi *KUYANGA* yakeso kuma ya amince da cikin jikinta nasane

Jakadiya tadafe kirji tace " wannan Abu bai Dadin jiba kamar Wanda akai masa surkulle

UMMAH TACE "Maza kije kishirya kije min gurin GOGAL matsafiya kice inaso acire masa son yarinyar ckn kwana daya

Da sauri jakadiya tace " angama uwar dakina.

UMMAH takawo kudi tabata jakadiya tafuce da sauri

Amma kafin ta tafi gurin matsafiyar tasu dake bayan gari saida tafaki ido tashige Sashin MAMAH Takai musu Gulmar wai ga Yarima can yarikicewa Mahaifiyarsa waishikam yanzun *KUYANGA* Yakeso kuma ya amince cikin jikinta nasane

FAATU DA MAMAH sunyi mamakin wannan Abu sunkuma Daukeshi arainin hankali yariman yazo dashi sunsan kuma TAKAWA bazai daukaba

Yo muma ba dauka zamuyi ba 😡

Muje zuwa
[8/3, 11:13 AM] Ummi Tandama: 📿 *KUYANGA* 📿

*_🌈KAINUWA WRITERS✍🏻 ASSOCIATION_*🤝🏻
```{United we stand and succeed;Our ambition is entertain & motivate the mind of readers}```

https://www.Facebook.com/kainuwawritersassociation

*Nabilancy Luv* 💘
(Auntyn S&S)

*wannan shafin Sadaukarwace ga Binta kabir Auntyn Yasmin Mrs ibrahim R/k quarters* 👍🏼👍🏼 Kawata inayinki Ina godiya da tayani posting a grps

70-75

JAKADIYA tana isa cikin Dajin tayita shiga cikin Ko tsoro babu atare da ita haka har tazo gindin wani tsauni ta haye daf !daf!!daf!!! Ta nufi wata babbar bishiyar Kuka dake kan katon Dutsen

Tana isa ga bishiyar saita cire takalmanta ta tsaya gaban bishiyar tana fadin "Gafaranku dai manya da kanana na fadar GOGAL ga jaririya tazo tazo Neman taimako da cin Albarkaci ayi min iso gurin Hakima mandiya shugabar matsafa

Wani kuka taji yana tashi na muryoyin yara daga ckn bishiyar taitaji harna tsahon minti talatin can kuma taji shiru sai kuma ga amsa kuwwar Babbar murya tana fadin

" SANNUNKI DA ZUWA HATSABIBIYAR JAKADIYA GAMANDI ME HADA WANDA TASO

Jakadiya ta hadiyi yawu domin kirarin nan bai mataba tasaba yi matashi

,"Barkanki da isowa GOGAL

Cewar Jakadiya

GOGAL da ba,a ganinta saijin muryarta ta jikin bishiyar tace da jakadiya

"NAji zuwanki angayamin tunkina afarkon daji nasan meke tafe Uwar Dakinki ta aikoki akan Acirewa D'anta son da yakewa *KUYANGA* Daga zuciyar sa ko?

Jakadiya tace " E kwarai hakan yake.

Jakadiya taci gaba da cewa "Hakan data tsara nikuma incanza salon abun yazamo amaimakon ancire masa son yarinyar saidai ma akara masa don ya axabtu sosai

Yakasa sakat yashiga damuwa akanta sakamakon yanda yasaka yarinyar adamuwa

Wata bunsurar dariya aka sheke da ita dg jikin bishiyar kukar

Daga can kuma akace da jakadiya " ko baki fadaba hakan za,ayi domin Baxan iya cire wannan soyayyar dake ransaba na duba naga ajiyar Allah ce ban isa in girgizata ba Dan haka zankara da Dora aikinki da kika bukata domin nima ayaune zanrama abinda YARIMA yataba yiwa Jikana yafita rangadi suka hadu ahanya YARIMA yabuge minshi da doki yafadi ko kulaminshi YARIMA baiyiba harya suma agun

Jakadiya tahau gyada kanta

Tana mamakin jin wannan labari na GOGAL duk da tasan zai aikata din

Jakadiya tahau godiya tareda ajiye kudin da uwar dakinta tabata agindin bishiyar ta mike da niyyar tafiya

Sai taji ana mata magana da muryar tsohuwa ta jikin bishiyar

"Kema kibi lamuranki na gidan nan a sannu domin a irin zaqewar da kikeyi wataran zaki girbi kashinki ahannu domin akwai abinda zaki aikata zaija miki babban aiki da kuma danasani HAHAHAHA

Aka rufe da katuwar dariya

Jakadiya na kyarma tace " Ataimaka agayamin ko mene wannan Abu da zaijamin danasani don inkiyaye

Dariyar dai akaci gaba dayi mata babu wani Karin bayani

Tana kallo kudin data ajiye yabace sundauke

Difff! Taji anmata tasan bakuma xasu karace mata kanxil ba shiyasa ta tafi da baya kamar yadda ta saba

*******

Yarima Yana kwance akan makeken Gadonsa yanata juyi yakasa controlling din kansa akan soyayyar *KUYANGA* Da take azabtar dashi arai

Hotonta ke masa gixo alokacin dayake kanta a time din suna Turai

Tabbas Yanda takeda tarin baiwa bazai iya barin taba saiyayi yanda yayi ya mallaketa baxai taba barin LAMIDO ya Aure taba

Can kuma saiya mike da sauri ayau saiya ganta kota halin kakane koda zai karya billensa yashiga ckn gidan bayin bazaiji wani Abu aransaba Sontane yaja

Yazira kaya ajikinsa dama dagashi sai gajeran wando da singilet

Yafito farfajiyar gidan yatsaya yana karewa kowa dake wucewa kallo duk Wanda zai wuce ta kusa dashi saiya kawo masa gaisuwa

Da ka kawai yake amsawa

Sarkin gida ya hango agurin ajiyar dokuna yana baiwa wani farin doki da LAMIDO kefuta dashi abinci

Matsawa yayi kusa da Sarkin gidan tareda kwalla masa kira

Da sauri yabar abinda yakeyi yataho gurin Yariman

Ya mika gaisuwa tareda tsayawa ckn ladabi agefen yarima yanajiran abinda zaice masa

Yarima yace "Sarkin gida Inaso kaje ka kiramin *KUYANGA* Zeenatu

Sarkin gida yace " Tana tareda MAHBUB acan bayan Gamji da suka saba zama

Yarima yadaka masa tsawa yace "To intana tareda wani bazatazo ba ko Yaya?shi wanin yafinine ?mijin tane ko waye dinta?

Sarkin gida yahau fadin " kayi hkr ba nufina kenan ba sanar maka nayi dai bata gida agarceni bari aje can akirata

Yatafi da sauri inda yasan zaisametan

Yarima yahau cizar yatsa jin wai tana can tareda MAHBUB tabbas dole yadau mataki akan wannan Bawan dazai kawo masa tsaiko

Yananan har lokacin da Sarkin gida yadawo tareda ita tana biye dashi sanye take da zurmemen hijab harkasa

Yaringa kare mata kallo na yanda take tafiya anutse kanta akasa

Gabantane yake faduwa domin batasan dame yazo mataba
Chapter 12 · 0% Book details