Chapter 4️⃣
Kuluwa Yar Balai Part 1 Complete Hausa Novel · about 5 min read
Sai da suka fita ƙofar gida Ummi ta ce.
"Yanzu ina muka nufa.?"
"Akwai gidajen da akayi biki shekaran jiya, zo muje cin kayan gara." Kuluwa ta faɗa tana tafiya.
Suna tafe suna yarfe hannu kamar masu lalura, idan kayi musu kallo ɗaya zaka ɗauka ƴaƴan aljannu ne fuska yasha powder ana tafe ana fari da ido.
Zun zo wucewa majalisar matasa Kuluwa ta gyara tafiya ana tafe kamar za karye, mai rake yazo wucewa Kuluwa ta tsayar dashi tana tambayarsa nawa nawa.
Mai rake yaga ciniki ya washe baki ya faɗa musu kuɗin, Kuluwa ta kwashi guda huɗu manyan ciki tayi mishi fari da ido.
Mai rake ya tsaya yana kallan ikon Allah suka yi gaba suna mishi fari da ido, ganin za su yi nisa ya tura keken raken yasha gabansu.
"Kuɗin rake na."
Kuluwa ta kalleshi sama da ƙasa ta watsar ta ce.
"Ka godewa Allah yau kasuwar ka zata yi albarka, tunda har ka haɗu damu wallahi yau sai ka siyar da raken nan duka."
Mai rake ya ƙura mata ido shi sai yanzu ya ƙare musu, gabansa ya faɗi lokacin da suka haɗa ido da Ummi kwalliya ne yanda ka san na mutanen ɓoye.
Mai rake yaji tsoron ko aljannu ya haɗu dasu gashi gari ya fara duhu, ya duƙar da kai Kuluwa ta ƙara diɓo guda biyu, Ummi data fahimci ya tsorata ta kalli Kuluwa tayi mata alama.
"Idan na koma duniyar mu zan cewa Baba na ya ƙara maka jari." Kuluwa ta faɗa tana gwallo manyan idanunta, ma sha Allah gashi idanun yasha kwalli.
Shi dai mai rake ya sunkuyar da kai ya ƙasa ya kasa motsawa, gaba ɗaya jikinsa rawa yake yi.
Kuluwa ta daka mishi tsawa.
"Bamu guri zamu wuce, idan kuma zaka bimu bismillah."
Mai rake ya faɗi ya fashe da kuka yana ta rarraba ido, ya kasa magana domin gaba ɗaya ya gama tsorata.
Kuluwa tayi gaba da rake a hannu, suna tafe suna shan rake har suka ƙaraso inda za suje, gidan yasha penti da gani saban gidane suka shiga suna rafka sallama.
Babu kowa a tsakar gidan suka shiga suna cigaba da sallama, wata mata ce ta leƙo tana tambayar su waye, taci kwalliya tana ta zuba ƙamshi, daga gani ka san amarya ce.
Kuluwa ta harareta sannan ta ce.
"Daman yaya ne ya matsa sai mun zo mun gaisheki."
Amarya ta yamutsa fuska tana faɗin.
"Ku shigo."
Kuluwa tayi dariya tana cewa.
"Zaki ci ubanki yarinya Kuluwa ce yau a gidanki."
A saman kujera ta zauna ta ɗaura ƙafa ɗaya kan ɗaya suka zauna a ƙasa kamar munafukai, suka gaisheta da ƙyar ta amsa tana tauna cingom.
"Aunty zamu sha ruwa."
Kuluwa ta fada tana tunanin abinda zata yi.
"Aiko ruwan gidan ya ƙare." Amarya ta faɗa cike da jan aji.
Kuluwa ganin amarya ta hanasu cin cin ranta ya ɓaci.
"Aunty wannan da kike gani ƙanwar budurwan yaya ne." Kuluwa ta faɗa tana na nuna Ummi.
Amarya ta zabura ta mulmulo zagi ta maka,
Ummi ta fashe da kuka tana cewa.
"Yanzu haka yana gidan mu gurin yayata, shi ne na samu ƙawata na faɗa mata lokacin ta gama shiri zata zo nan gidan, sai ta roƙeni in rakota domin ta faɗa miki, kuma wallahi auranta zai yi ni kuma yanda ki kai mana sai naji kin burgeni ba zan yarda aci amanarki ba."
"Inalillahi wa'inna ilaihir raji'un, dan Allah dagaske kuke yi.?" Amarya ta faɗa tana wurgar da cingom ɗin bakinta.
Kuluwa zata yi magana ta fara shaƙuwa tana dafe ƙirji.
"Na shiga uku." Ummi ta faɗa tana jijjiga Kuluwa.
"Mai ya sameta.?" Amarya ta faɗa gabanta yana faɗuwa.
"Tana da laluran aljannu kuma idan suka taso mata sai taci kaza, kuma wallahi idan bata ci kaza ba duk mun shiga uku." Ummi ta faɗa cikin kuka.
Amarya ta shiga kitchen kamar zata faɗi, plate ta fito dashi ta koma drinks ta kwaso guda huɗu ta ajiye, Kuluwa ta miƙe zuruf ta buɗe plate ɗin ta fara cin kaza hannu baka hannu ƙwarya daman yunwa take ji, kana ganinta ka san babu sukuni amarya tana raɓe a gefe tayi tagumi.
"Aunty babu cin cin ne.?" Ummi ta faɗa amarya ta koma kitchen.
Ummi ta ɗauke rabin kazar ta naɗe a zaninta, drink ta ɗauka guda ɗaya ta shanye ta ajiye robar.
Amarya ta fito hannunta ɗauke da plate cike da cin cin dublan alkaki, cike da mamaki take kallan Kuluwa ta cinye kazar ansha lemu guda biyu, ta kalli Ummi ta ganta a zaune a inda ta barta.
Kuluwa ta maƙale murya ta ce.
"Aunty mungode da kika taimaki goɗiyar mu, munji daɗi kuma zamu taimaka miki."
Amarya tayi shiru tana tunanin yanda mijinta yake ce mata daga ita babu ƙari.
"Tabbas mijinki yana da budurwa kuma sai kinyi da gaske zaki iya raba su, lallai ki bincike kayansa zaki samu bayanan da kike nema." Kuluwa ta faɗa tana fari da ido, idan kaga yanda take yi zaka rantse aljannun gaske ne.
"Karki faɗa mishi goɗiyar mu tazo gidan nan, domin zai hanata taimakonki." Kuluwa ta faɗa tana zaro ido, amarya tayi baya da sauri.
Tayi atishawa sau uku sannan ta kalli Ummi tana faɗin.
"Tashi muje gida ana kirana."
Ummi tayi murmushi ta ɗauko leda a saman fridge, ta juye duka abinda basu ci ba ta kalli amarya ta ce.
"Karki manta da abinda aka faɗa miki."
"Mai ya faru.?" Kuluwa ta faɗa tana ɗaure fuska.
"Babu komai." Ummi ta faɗa tana ƙunshe dariya, amarya ta ƙara musu cin cin tayi musu godiya suka tafi.
Sai da suka yi nisa da gidan suka ringa dariya kamar mahaukata.
"Kin samu kaza kamar wata mayya." Ummi ta faɗa tana dariya.
"Ai dalilin da yasa nayi mata haka saboda na fahimci marowaciyya ne, kin ga data ji maganar kishiya harda kaza ta bayar." Suna tafe suna dariya.
Duk da yamma tayi basu fasa zuwa gidan ɗayan amaryan ba.
Ummi tana riƙe da leda Kuluwa ita ce a gaba.
Banyi alƙawarin typing kullum ba.
Ta Batulu ce............✍️*KULUWA*
*(Ƴar bala'i)*
Channel 👇
https://whatsapp.com/channel/0029VaBJBOr8vd1H4qb9rd1a
Group 👇
https://chat.whatsapp.com/HDAsWBYpkZP5YJSNFPR5I8
*JAJIRTATTU WRITER'S ASSOCIATION*
Allahumma salli ala sayyadina Muhammad wassalim.
"Yanzu ina muka nufa.?"
"Akwai gidajen da akayi biki shekaran jiya, zo muje cin kayan gara." Kuluwa ta faɗa tana tafiya.
Suna tafe suna yarfe hannu kamar masu lalura, idan kayi musu kallo ɗaya zaka ɗauka ƴaƴan aljannu ne fuska yasha powder ana tafe ana fari da ido.
Zun zo wucewa majalisar matasa Kuluwa ta gyara tafiya ana tafe kamar za karye, mai rake yazo wucewa Kuluwa ta tsayar dashi tana tambayarsa nawa nawa.
Mai rake yaga ciniki ya washe baki ya faɗa musu kuɗin, Kuluwa ta kwashi guda huɗu manyan ciki tayi mishi fari da ido.
Mai rake ya tsaya yana kallan ikon Allah suka yi gaba suna mishi fari da ido, ganin za su yi nisa ya tura keken raken yasha gabansu.
"Kuɗin rake na."
Kuluwa ta kalleshi sama da ƙasa ta watsar ta ce.
"Ka godewa Allah yau kasuwar ka zata yi albarka, tunda har ka haɗu damu wallahi yau sai ka siyar da raken nan duka."
Mai rake ya ƙura mata ido shi sai yanzu ya ƙare musu, gabansa ya faɗi lokacin da suka haɗa ido da Ummi kwalliya ne yanda ka san na mutanen ɓoye.
Mai rake yaji tsoron ko aljannu ya haɗu dasu gashi gari ya fara duhu, ya duƙar da kai Kuluwa ta ƙara diɓo guda biyu, Ummi data fahimci ya tsorata ta kalli Kuluwa tayi mata alama.
"Idan na koma duniyar mu zan cewa Baba na ya ƙara maka jari." Kuluwa ta faɗa tana gwallo manyan idanunta, ma sha Allah gashi idanun yasha kwalli.
Shi dai mai rake ya sunkuyar da kai ya ƙasa ya kasa motsawa, gaba ɗaya jikinsa rawa yake yi.
Kuluwa ta daka mishi tsawa.
"Bamu guri zamu wuce, idan kuma zaka bimu bismillah."
Mai rake ya faɗi ya fashe da kuka yana ta rarraba ido, ya kasa magana domin gaba ɗaya ya gama tsorata.
Kuluwa tayi gaba da rake a hannu, suna tafe suna shan rake har suka ƙaraso inda za suje, gidan yasha penti da gani saban gidane suka shiga suna rafka sallama.
Babu kowa a tsakar gidan suka shiga suna cigaba da sallama, wata mata ce ta leƙo tana tambayar su waye, taci kwalliya tana ta zuba ƙamshi, daga gani ka san amarya ce.
Kuluwa ta harareta sannan ta ce.
"Daman yaya ne ya matsa sai mun zo mun gaisheki."
Amarya ta yamutsa fuska tana faɗin.
"Ku shigo."
Kuluwa tayi dariya tana cewa.
"Zaki ci ubanki yarinya Kuluwa ce yau a gidanki."
A saman kujera ta zauna ta ɗaura ƙafa ɗaya kan ɗaya suka zauna a ƙasa kamar munafukai, suka gaisheta da ƙyar ta amsa tana tauna cingom.
"Aunty zamu sha ruwa."
Kuluwa ta fada tana tunanin abinda zata yi.
"Aiko ruwan gidan ya ƙare." Amarya ta faɗa cike da jan aji.
Kuluwa ganin amarya ta hanasu cin cin ranta ya ɓaci.
"Aunty wannan da kike gani ƙanwar budurwan yaya ne." Kuluwa ta faɗa tana na nuna Ummi.
Amarya ta zabura ta mulmulo zagi ta maka,
Ummi ta fashe da kuka tana cewa.
"Yanzu haka yana gidan mu gurin yayata, shi ne na samu ƙawata na faɗa mata lokacin ta gama shiri zata zo nan gidan, sai ta roƙeni in rakota domin ta faɗa miki, kuma wallahi auranta zai yi ni kuma yanda ki kai mana sai naji kin burgeni ba zan yarda aci amanarki ba."
"Inalillahi wa'inna ilaihir raji'un, dan Allah dagaske kuke yi.?" Amarya ta faɗa tana wurgar da cingom ɗin bakinta.
Kuluwa zata yi magana ta fara shaƙuwa tana dafe ƙirji.
"Na shiga uku." Ummi ta faɗa tana jijjiga Kuluwa.
"Mai ya sameta.?" Amarya ta faɗa gabanta yana faɗuwa.
"Tana da laluran aljannu kuma idan suka taso mata sai taci kaza, kuma wallahi idan bata ci kaza ba duk mun shiga uku." Ummi ta faɗa cikin kuka.
Amarya ta shiga kitchen kamar zata faɗi, plate ta fito dashi ta koma drinks ta kwaso guda huɗu ta ajiye, Kuluwa ta miƙe zuruf ta buɗe plate ɗin ta fara cin kaza hannu baka hannu ƙwarya daman yunwa take ji, kana ganinta ka san babu sukuni amarya tana raɓe a gefe tayi tagumi.
"Aunty babu cin cin ne.?" Ummi ta faɗa amarya ta koma kitchen.
Ummi ta ɗauke rabin kazar ta naɗe a zaninta, drink ta ɗauka guda ɗaya ta shanye ta ajiye robar.
Amarya ta fito hannunta ɗauke da plate cike da cin cin dublan alkaki, cike da mamaki take kallan Kuluwa ta cinye kazar ansha lemu guda biyu, ta kalli Ummi ta ganta a zaune a inda ta barta.
Kuluwa ta maƙale murya ta ce.
"Aunty mungode da kika taimaki goɗiyar mu, munji daɗi kuma zamu taimaka miki."
Amarya tayi shiru tana tunanin yanda mijinta yake ce mata daga ita babu ƙari.
"Tabbas mijinki yana da budurwa kuma sai kinyi da gaske zaki iya raba su, lallai ki bincike kayansa zaki samu bayanan da kike nema." Kuluwa ta faɗa tana fari da ido, idan kaga yanda take yi zaka rantse aljannun gaske ne.
"Karki faɗa mishi goɗiyar mu tazo gidan nan, domin zai hanata taimakonki." Kuluwa ta faɗa tana zaro ido, amarya tayi baya da sauri.
Tayi atishawa sau uku sannan ta kalli Ummi tana faɗin.
"Tashi muje gida ana kirana."
Ummi tayi murmushi ta ɗauko leda a saman fridge, ta juye duka abinda basu ci ba ta kalli amarya ta ce.
"Karki manta da abinda aka faɗa miki."
"Mai ya faru.?" Kuluwa ta faɗa tana ɗaure fuska.
"Babu komai." Ummi ta faɗa tana ƙunshe dariya, amarya ta ƙara musu cin cin tayi musu godiya suka tafi.
Sai da suka yi nisa da gidan suka ringa dariya kamar mahaukata.
"Kin samu kaza kamar wata mayya." Ummi ta faɗa tana dariya.
"Ai dalilin da yasa nayi mata haka saboda na fahimci marowaciyya ne, kin ga data ji maganar kishiya harda kaza ta bayar." Suna tafe suna dariya.
Duk da yamma tayi basu fasa zuwa gidan ɗayan amaryan ba.
Ummi tana riƙe da leda Kuluwa ita ce a gaba.
Banyi alƙawarin typing kullum ba.
Ta Batulu ce............✍️*KULUWA*
*(Ƴar bala'i)*
Channel 👇
https://whatsapp.com/channel/0029VaBJBOr8vd1H4qb9rd1a
Group 👇
https://chat.whatsapp.com/HDAsWBYpkZP5YJSNFPR5I8
*JAJIRTATTU WRITER'S ASSOCIATION*
Allahumma salli ala sayyadina Muhammad wassalim.