Chapter 1️⃣
Kuluwa Yar Balai Part 1 Complete Hausa Novel · about 5 min read
Yara ne wajan guda goma sha biyar suna sanye da uniform green and white na primary school, kowace da duwatsu manya manya a hannunta yana tafe suna bin bayansa shima yana sanye da uniform irin nasu, sai da suka bari ya shiga lungu ɗaya daga cikin yaran mai suna Kuluwa ta fito ba zata wuce shakara goma sha huɗu ba, sauran harda ƴan mata suna da yawa dan za su iya fin sha biyar.
Kuluwa ta ɗaga dutsen hannunta tana cewa.
"Labbaikallahumma labbaik." Ta jefa mishi sauran ma suka fara jifanshi suna faɗin.
"Labbaikallahumma labbaik."
Ruwan duwatsu suke yi tako ina da ƙyar wani tsoho ya tare su yana musu faɗa.
"Wallahi kaci albarcin baba." Kuluwa ta faɗa tana nuna tsohon da ya hana su.
Tayi ƙwafa ta tafi sauran suka take mata baya kamar ƙudaje.
Har ta nufi hanyar gida ta dawo da baya gidan Asabe dilalliya ta nufa, kamar mutumiyar kirki tayi sallama ta duƙa ta gaisheta sannan ta ce.
"Baba lami ce ta aiko ni ki bata wake mudu biyar zata aiko miki da kuɗin jibi idan Allah ya kaimu."
Asabe kamar ba zata bayar ba amman tayi shahada ta auna ta bata waken cike da gargadin kar ya wuce jibin.
"Ta ce idan bata aiko miki dashi ba wai kizo da kanki, zata iya mantawa." Kuluwa ta faɗa tana ɗaukar waken ta fita tana dariya.
Tana tafe tana tunanin inda zata ɓoye waken, tazo wucewa shagon wani mai siyar da hatsi kawai ta yanke shawarar ta siyar ta amshi kuɗin ko ba zata yi komai da kuɗin ba, aiko ta shiga shagon ta duƙa har ƙasa ta gaishe shi sannan ta fara hawaye tana cewa.
"Dan Allah ka taimaka mun ka sai waken nan in samu in kai, mahaifiyata asibiti." Mai shago yaji tausayinta, yanda yake siyarwa a shago haka ya siya, ta amsa tayi godiya ta nufi hanyar gida tana shiga zauren gidan, ta cire jakan makarantar ta wurga tsakar gida ta koma.
Gidan Fatu ta nufa tayi mata gaisuwa cike da mutunci sannan ta ce mata.
"Mama ta ce ki bata shinkafa mudu uku zata aiko miki da kuɗin, idan Baba ya dawo anjima."
Fatu ta fara masifa ita bata san bayar da bashi, Kuluwa ta lalaɓata har da cewa.
"Anjima idan bata kawo kuɗin ba tazo ta amsa komun dare."
Fatu ta bayar da shinkafa mudu uku Kuluwa ta ɗauka ta fita.
"Na rantse da Allah Mama da Baba lami kun shiga uku, tunda kuka shigo sabgata shegu munafukai."
Kuluwa ta nufi gida tayi sallama babu kowa a tsakar gida, ta lalaɓa ta shiga kitchen ta yi mishi mugun ɓoyo, sannan ta fito ta shiga ɗaki ko sallama ba tayi ba.
"Kakus iyayen jaraba." Kuluwa ta faɗa tana hararan tsohowar dake kaɗa, lagwanin risho.
Kaka tayi banza da ita Kuluwa ta fara buɗe kwanoni ganin bata samu komai ba, ta miƙe ta fita tayi sallama tana tura baki, kaka ta amsa sallamar tana cewa.
"Kowa ya tuba dan wuya ba lada."
Kuluwa ta zumɓura baki tana hararanta kaka ta janyo kwanon kusa da ita Kuluwa bata lura dashi ba ɗazun, dambune yasha mangyada da wake Kuluwa sai da taci ta ƙoshi sannan tayi sallah, ta sanja kaya ta kalli kaka ta ce.
"To zamu fita neman na kai, zaman gida bana masu isashen lafiyar ƙafa bane."
Kaka tayi banza da ita Kuluwa tayi hanyar waje tana tafiya tana buɗe ƙafa.
Har ta fice daga gidan kaka bata daina kallanta ba, ta yanko kwanan gidan su Ummi ta haɗu da wata budurwa taci kwalliya tana tafe tana yanga haka kawai Kuluwa taji ranta ya ɓaci.
"Shegiya mai ƙatan kai da leɓe kamar na alade." Kuluwa ta faɗa tana ɗauke kai budurwan ranta ya ɓaci, ta nufi Kuluwa tana zuwa gab da ita Kuluwa ta kauce budurwan ta faɗa kwata mai warin tsiya.
Kuluwa dariya harda hawaye tana ta tsokanar mutane har ta ƙarasa gidan su Ummi, tana zuwa ta buga ƙofar gidan babu jimawa Ummi ta fito suka yi gaba.
"Ina muka nufa.' Ummi ta faɗa.
"Gidan su Maimuna." Kuluwa ta faɗa tana dariya.
Suka shiga gidan suka gaishe da mahaifiyar Maimuna, suka zauna suna tunanin yanda zasu janyo Maimuna waje su daka.
Aka zuba musu shinkafa da miya suka zauna suka cinye tas, da zasu tafi Maimuna ta rako su waje Kuluwa ta rufe mata baki da ƙasa suka yi mata dukan tsiya, sannan suka ruga da gudu Kuluwa tana cewa.
"Gobe ma ki ƙara gulma ta a hadda wallahi sai kin fi haka dakuwa, kuma ki cewa babarku bata iya abinci ba."
Kuluwa sai bayan magrib ta dawo gida tayi sallah sannan ta fara kuka.
"Kuluwa zan ci mutuncin ki wallahi, kinje kin gama yawon neman magana zaki zo ki ta sani a gaba kina kuka."
"Yanzu kin daina ƙaunata kakus Allah sarki Mamana." Kuluwa ta faɗa tana yiwa kaka gwallo.
"Yi shiru dan Allah ki faɗa mun waye ya taɓa ki a daren nan, wallahi sai naci mutuncinshi dan Allah ki daina kuka haba kululun kakanta."
Kuluwa ta share hawayen ƙaryan data ƙirƙiro ta ce.
"Baba na nake san gani dan Allah ki barni inje."
"Kuluwa dare ya yi." Kaka ta faɗa cike da rarrashi.
"Shike nan kaka idan na mutu a daren nan dan Allah ki ce mishi ya yafe mun, kema ki yafe mun dan Allah." Kuluwa ta faɗa tana fashewa da kuka babu hawaye.
"Mutuwa kuma tashi maza kije, Allah ya kiyeye hanya amman ko zan rakaki ne saboda dare ya yi." Kaka ta faɗa tana fatan Kuluwa ta amince suje tare.
"Gwara muje tare dake yanda bom ɗin zai fi tashi da sauri." Kuluwa ta faɗa a hankali.
"Mai kike ce." Kaka ta faɗa ganin bakin Kuluwa yana motsi.
"Babu komai kakata dan Allah ki yi sauri mu tafi, kar mutuwar tazo a daren nan banga Baba na ba."
Da sauri kaka ta saka hijjab ta karkace ba tare data lura ba, Kuluwa ta kulle ƙofar gidan suka nufi gidan mahaifinta.
Dalilin da yasa Kuluwa take san zuwa gida, saboda tana san tayi kallan rigima tsakanin Fatu da Mama, domin ta san yau akwai gagarumin yaƙi a gidan mahaifinta, shi ya sa take san zuwa ta yi kallo ƙarin abin farin ciki kaka data biyota.
Banyi alƙawarin typing kullum ba, sannan bana typing ranar juma'a.*KULUWA*
*(Ƴar bala'i)*
Group 👇
https://chat.whatsapp.com/LSKW0PJdQ6Z2S2wltDG6oT
Channel 👇
https://whatsapp.com/channel/0029Vb6Kd5SFnSz8T3XpQ22g
*ALLAHUMMA SALLI ALA SAYYADINA MUHAMMAD WASSALIM*
Written by ✍️
*Jagabar Jajirtattu*
(Ta Batulu)
Kuluwa ta ɗaga dutsen hannunta tana cewa.
"Labbaikallahumma labbaik." Ta jefa mishi sauran ma suka fara jifanshi suna faɗin.
"Labbaikallahumma labbaik."
Ruwan duwatsu suke yi tako ina da ƙyar wani tsoho ya tare su yana musu faɗa.
"Wallahi kaci albarcin baba." Kuluwa ta faɗa tana nuna tsohon da ya hana su.
Tayi ƙwafa ta tafi sauran suka take mata baya kamar ƙudaje.
Har ta nufi hanyar gida ta dawo da baya gidan Asabe dilalliya ta nufa, kamar mutumiyar kirki tayi sallama ta duƙa ta gaisheta sannan ta ce.
"Baba lami ce ta aiko ni ki bata wake mudu biyar zata aiko miki da kuɗin jibi idan Allah ya kaimu."
Asabe kamar ba zata bayar ba amman tayi shahada ta auna ta bata waken cike da gargadin kar ya wuce jibin.
"Ta ce idan bata aiko miki dashi ba wai kizo da kanki, zata iya mantawa." Kuluwa ta faɗa tana ɗaukar waken ta fita tana dariya.
Tana tafe tana tunanin inda zata ɓoye waken, tazo wucewa shagon wani mai siyar da hatsi kawai ta yanke shawarar ta siyar ta amshi kuɗin ko ba zata yi komai da kuɗin ba, aiko ta shiga shagon ta duƙa har ƙasa ta gaishe shi sannan ta fara hawaye tana cewa.
"Dan Allah ka taimaka mun ka sai waken nan in samu in kai, mahaifiyata asibiti." Mai shago yaji tausayinta, yanda yake siyarwa a shago haka ya siya, ta amsa tayi godiya ta nufi hanyar gida tana shiga zauren gidan, ta cire jakan makarantar ta wurga tsakar gida ta koma.
Gidan Fatu ta nufa tayi mata gaisuwa cike da mutunci sannan ta ce mata.
"Mama ta ce ki bata shinkafa mudu uku zata aiko miki da kuɗin, idan Baba ya dawo anjima."
Fatu ta fara masifa ita bata san bayar da bashi, Kuluwa ta lalaɓata har da cewa.
"Anjima idan bata kawo kuɗin ba tazo ta amsa komun dare."
Fatu ta bayar da shinkafa mudu uku Kuluwa ta ɗauka ta fita.
"Na rantse da Allah Mama da Baba lami kun shiga uku, tunda kuka shigo sabgata shegu munafukai."
Kuluwa ta nufi gida tayi sallama babu kowa a tsakar gida, ta lalaɓa ta shiga kitchen ta yi mishi mugun ɓoyo, sannan ta fito ta shiga ɗaki ko sallama ba tayi ba.
"Kakus iyayen jaraba." Kuluwa ta faɗa tana hararan tsohowar dake kaɗa, lagwanin risho.
Kaka tayi banza da ita Kuluwa ta fara buɗe kwanoni ganin bata samu komai ba, ta miƙe ta fita tayi sallama tana tura baki, kaka ta amsa sallamar tana cewa.
"Kowa ya tuba dan wuya ba lada."
Kuluwa ta zumɓura baki tana hararanta kaka ta janyo kwanon kusa da ita Kuluwa bata lura dashi ba ɗazun, dambune yasha mangyada da wake Kuluwa sai da taci ta ƙoshi sannan tayi sallah, ta sanja kaya ta kalli kaka ta ce.
"To zamu fita neman na kai, zaman gida bana masu isashen lafiyar ƙafa bane."
Kaka tayi banza da ita Kuluwa tayi hanyar waje tana tafiya tana buɗe ƙafa.
Har ta fice daga gidan kaka bata daina kallanta ba, ta yanko kwanan gidan su Ummi ta haɗu da wata budurwa taci kwalliya tana tafe tana yanga haka kawai Kuluwa taji ranta ya ɓaci.
"Shegiya mai ƙatan kai da leɓe kamar na alade." Kuluwa ta faɗa tana ɗauke kai budurwan ranta ya ɓaci, ta nufi Kuluwa tana zuwa gab da ita Kuluwa ta kauce budurwan ta faɗa kwata mai warin tsiya.
Kuluwa dariya harda hawaye tana ta tsokanar mutane har ta ƙarasa gidan su Ummi, tana zuwa ta buga ƙofar gidan babu jimawa Ummi ta fito suka yi gaba.
"Ina muka nufa.' Ummi ta faɗa.
"Gidan su Maimuna." Kuluwa ta faɗa tana dariya.
Suka shiga gidan suka gaishe da mahaifiyar Maimuna, suka zauna suna tunanin yanda zasu janyo Maimuna waje su daka.
Aka zuba musu shinkafa da miya suka zauna suka cinye tas, da zasu tafi Maimuna ta rako su waje Kuluwa ta rufe mata baki da ƙasa suka yi mata dukan tsiya, sannan suka ruga da gudu Kuluwa tana cewa.
"Gobe ma ki ƙara gulma ta a hadda wallahi sai kin fi haka dakuwa, kuma ki cewa babarku bata iya abinci ba."
Kuluwa sai bayan magrib ta dawo gida tayi sallah sannan ta fara kuka.
"Kuluwa zan ci mutuncin ki wallahi, kinje kin gama yawon neman magana zaki zo ki ta sani a gaba kina kuka."
"Yanzu kin daina ƙaunata kakus Allah sarki Mamana." Kuluwa ta faɗa tana yiwa kaka gwallo.
"Yi shiru dan Allah ki faɗa mun waye ya taɓa ki a daren nan, wallahi sai naci mutuncinshi dan Allah ki daina kuka haba kululun kakanta."
Kuluwa ta share hawayen ƙaryan data ƙirƙiro ta ce.
"Baba na nake san gani dan Allah ki barni inje."
"Kuluwa dare ya yi." Kaka ta faɗa cike da rarrashi.
"Shike nan kaka idan na mutu a daren nan dan Allah ki ce mishi ya yafe mun, kema ki yafe mun dan Allah." Kuluwa ta faɗa tana fashewa da kuka babu hawaye.
"Mutuwa kuma tashi maza kije, Allah ya kiyeye hanya amman ko zan rakaki ne saboda dare ya yi." Kaka ta faɗa tana fatan Kuluwa ta amince suje tare.
"Gwara muje tare dake yanda bom ɗin zai fi tashi da sauri." Kuluwa ta faɗa a hankali.
"Mai kike ce." Kaka ta faɗa ganin bakin Kuluwa yana motsi.
"Babu komai kakata dan Allah ki yi sauri mu tafi, kar mutuwar tazo a daren nan banga Baba na ba."
Da sauri kaka ta saka hijjab ta karkace ba tare data lura ba, Kuluwa ta kulle ƙofar gidan suka nufi gidan mahaifinta.
Dalilin da yasa Kuluwa take san zuwa gida, saboda tana san tayi kallan rigima tsakanin Fatu da Mama, domin ta san yau akwai gagarumin yaƙi a gidan mahaifinta, shi ya sa take san zuwa ta yi kallo ƙarin abin farin ciki kaka data biyota.
Banyi alƙawarin typing kullum ba, sannan bana typing ranar juma'a.*KULUWA*
*(Ƴar bala'i)*
Group 👇
https://chat.whatsapp.com/LSKW0PJdQ6Z2S2wltDG6oT
Channel 👇
https://whatsapp.com/channel/0029Vb6Kd5SFnSz8T3XpQ22g
*ALLAHUMMA SALLI ALA SAYYADINA MUHAMMAD WASSALIM*
Written by ✍️
*Jagabar Jajirtattu*
(Ta Batulu)