Chapter 2️⃣
Kuluwa Yar Balai Part 1 Complete Hausa Novel · about 5 min read
Tun daga zauren gidan take jin hayaniyya Kuluwa tayi dariya, Mallam Sani yana zaune ya dafe kai Mama da Fatu suna zagin juna, Kaka tayi sallama Kuluwa ta nufi gurin mahaifinta.
"Alhamdulillahi gwara da Allah ya kawo ki, ɗazun ubanwa ya aiko ki karɓan shinkafa mudu uku." Fatu ta faɗa a fusace.
Babu tsoro ko shakka Kuluwa ta ce.
"Bani bace wallahi." Fatu ta saki baki da hanci tana kallanta.
Tashin hankali Mama ta mumulo zagi ta maka ta nufo gurin Kuluwa, Mallam Sani ya dakatar da ita yana cewa.
"Akwai ƙamshin gaskiya a maganar yarinyar nan, saboda ni ba shinkafa na ce ki dafa ba amman saboda neman masifa irin naki, kinje kin ciyo bashin jama'a to wallahi ba zan biya kuɗin ba."
Kuluwa tana lafe ajikin mahaifinta tana yiwa Mama gwallo a fakaice.
"Ku dai wallahi ba zaku taɓa hankali ba, mutane babu Allah a ransu, yaushe Kuluwa tazo gidan bansaniba?." Kaka ta faɗa rai a ɓace.
Baba lami dake ƙunshe dariya ta ce.
"Nima yau kwatakwata banga Kuluwa a gidan nan ba, hasalima ta kwana biyu bata zo gidan ba."
"To baƙar munafuka nayi magana dake ne.?" Mama ta faɗa kamar zata dake ta.
"Daga faɗar gaskiya sai ki dawo kaina, to Allah ya baki haƙuri yanzu sai ki fito musu da kuɗin shinkafar da kika dafa." Baba lami ta faɗa tana dariya.
Fatu dai tayi tsaye tana jiran a bata kuɗin ta.
Ƙarshe yaron Mama ya biya kuɗin yana hararan Kuluwa domin ya san halinta.
"Wallahi sai kin yi nadamar abinda kika aikata mun, munafuka mai baƙin hali irin na uwarta."
"Inalillahi wa'inna ilaihir raji'un, Mallam Sani gidanka ya haramta a gareni." Kaka ta faɗa tana fashewa da kuka.
Mallam Sani ya dakawa Mama tsawa ta bar gurin tana yin ƙwafa.
"Yanzu a gidanka har matattu ake zagi kuma kana gani ka kasa ɗaukar mataki, wallahi ka zama taɓaɓɓe wanda bai da iko a gidansa." Kaka ta faɗa tana share hawaye da gefen zani.
Da ƙyar Kaka tayi shiru Mallam Sani ya rakasu har gida yana ƙara bata haƙuri.
Lokacin da Kuluwa tazo kwanciya ta ringa ihu tana cewa.
"Dan Allah ki yi haƙuri ba zan ƙara ba." Kaka a zaune ta kwana tana yi mata addu'o'i, Kuluwa idan taga Kaka ta fara gyangyaɗi sai ta zabura tana cewa gata nan zata kamani.
Zuwa ƙarfe biyu bacci ya ɗauke Kuluwa daga nan Kaka ta samu ta kwanta, cike da tunanin irin rashin mutuncin da zata yiwa Mama gobe.
Ƙarfe shida Kuluwa tayi sallah Kaka ta miƙa mata Qur'ani ta ce.
"Maza Kulun majadun ƴar gatan Kaka, fara mai farar aniya zinariya mai haska gida."
Kuluwa da farko ta fara ɓata fuska tana tunanin abinda zata aikata, wanda zai hana ta zuwa hadda amman jin kirarin da take mata.
Yasa ta karɓa Qur'anin tana rausaya jiki tana fari da ido kamar mai tashin aljanu.
"Maza kije ƴar albarka bana so ki makara." Kaka ta faɗa tana miƙa mata hamsin kuɗin wata.
Kuluwa ta amsa ta tafi tana rangwaɗa gata babu ƙiba 😂
Tana zuwa taga an tare makara ta ƙarewa mallamin kallo yana sanye da babbar riga, kuma gashi mallamin mugune bai da mutunci, ya tsani Kuluwa saboda rashin jin maganarta akwaita da ƙoƙari neman magana tsokana, babu wanda ta ƙyale harta mallaman sun san da zamanta, gashi bata ƙaunar abinda zai taɓa mata lafiyar jiki.
Wani tsumma ta gani a kusa da ita ya dunƙule kamar maciji, tayi murmushi ta ɗauka ta ɓoye a cikin hijjab ganin layin yaƙi zuwa kanta yasa ta yanke shawarar ta watsa gurin kawai kowa ya yi ta kansa.
"Wayyo Allah maciji maciji." Kuluwa ta faɗa tana jefa musu tsumman data ɗauka, tashin hankali gaba ɗaya kowa ya watse Mallam yazo guduwa babbar rigarsa ta yarda dashi.
"Mallam maciji a bayanka." Kuluwa ta faɗa tana zurawa da gudu cikin makarantar, Mallam ya fara rarrafe yana raba ido ya kasa tashi.
Koda ta shiga makarantar abinda take faɗi kenan.
"Maciji jama'a akawo ɗauki." Gaba ɗaya ta har gitsa makarantar, yara suna ta ihu wasu suna haurawa ta window suna guduwa, wasu kuma toilet ɗin makarantar suke shigewa.
Ummi ta dafa Kuluwa ta ce.
"Daman ina tunanin yanda zan watsa makarantar ne sai gaki kin zo."
"Dallah rufa mun baki munafuka matsoraciyya kawai." Kuluwa ta faɗa tana hararan Ummi.
Ganin akwai sauran mutanen da suke zaune acikin aji yasa ta fashe da kuka ta buɗe murya ta ce.
"Inalillahi wa'inna ilaihir raji'un macizan sun ƙara yawa." Haka ta ringa bin ajujuwa tana dirawa ta window, ƙarshe dai kowa ya yi takansa daman mallamai huɗu ne kuma kowa ya yi takansa, Mallam da rarrafe ya fita get ɗin makarantar duk ya haɗa zufa.
Suka nufi hanyar gida yara taga suna dambe ɗaya jibgegiya ɗaya siririya mai ƙibar tana ta dukan siririyar, ta miƙawa Ummi Qur'ani ta shiga tsakiyar su ta ɗibo ƙasa ta raba biyu, hagu dama ta kallesu ta ce.
"Gana tsiya gana arziki." Yarinyar da ake duka ta zubar dana arziki ɗayan kuma ta cakumi hijjab ɗin Kuluwa.
Kuluwa ta kwace hijjab ɗinta hamsin ɗin da Kaka ta bata shi ta miƙawa siririyar ta ce.
"Na sai faɗar." Yarinyar tasha ƙasa ta daku tana dafe hamsin ta zura da gudu.
Kuluwa taji anyi sama da ita.
Ta Batulu ce........ ✍️
Likes comments sune ƙwarin gwiwar marubuci.*KULUWA*
*(Ƴar bala'i)*
Group 👇
https://chat.whatsapp.com/EEiLcD9ZnpbFRLSjSOZozT
Channel 👇
https://whatsapp.com/channel/0029Vb6Kd5SFnSz8T3XpQ22g
*JAJIRTATTUN MARUBUTA WRITER'S ASSOCIATION*
Ban yarda a juya mun labari ta kowace irin siga ba, duk wanda na samu ya juya mun labari ba zan lamunci hakan ba.
"Alhamdulillahi gwara da Allah ya kawo ki, ɗazun ubanwa ya aiko ki karɓan shinkafa mudu uku." Fatu ta faɗa a fusace.
Babu tsoro ko shakka Kuluwa ta ce.
"Bani bace wallahi." Fatu ta saki baki da hanci tana kallanta.
Tashin hankali Mama ta mumulo zagi ta maka ta nufo gurin Kuluwa, Mallam Sani ya dakatar da ita yana cewa.
"Akwai ƙamshin gaskiya a maganar yarinyar nan, saboda ni ba shinkafa na ce ki dafa ba amman saboda neman masifa irin naki, kinje kin ciyo bashin jama'a to wallahi ba zan biya kuɗin ba."
Kuluwa tana lafe ajikin mahaifinta tana yiwa Mama gwallo a fakaice.
"Ku dai wallahi ba zaku taɓa hankali ba, mutane babu Allah a ransu, yaushe Kuluwa tazo gidan bansaniba?." Kaka ta faɗa rai a ɓace.
Baba lami dake ƙunshe dariya ta ce.
"Nima yau kwatakwata banga Kuluwa a gidan nan ba, hasalima ta kwana biyu bata zo gidan ba."
"To baƙar munafuka nayi magana dake ne.?" Mama ta faɗa kamar zata dake ta.
"Daga faɗar gaskiya sai ki dawo kaina, to Allah ya baki haƙuri yanzu sai ki fito musu da kuɗin shinkafar da kika dafa." Baba lami ta faɗa tana dariya.
Fatu dai tayi tsaye tana jiran a bata kuɗin ta.
Ƙarshe yaron Mama ya biya kuɗin yana hararan Kuluwa domin ya san halinta.
"Wallahi sai kin yi nadamar abinda kika aikata mun, munafuka mai baƙin hali irin na uwarta."
"Inalillahi wa'inna ilaihir raji'un, Mallam Sani gidanka ya haramta a gareni." Kaka ta faɗa tana fashewa da kuka.
Mallam Sani ya dakawa Mama tsawa ta bar gurin tana yin ƙwafa.
"Yanzu a gidanka har matattu ake zagi kuma kana gani ka kasa ɗaukar mataki, wallahi ka zama taɓaɓɓe wanda bai da iko a gidansa." Kaka ta faɗa tana share hawaye da gefen zani.
Da ƙyar Kaka tayi shiru Mallam Sani ya rakasu har gida yana ƙara bata haƙuri.
Lokacin da Kuluwa tazo kwanciya ta ringa ihu tana cewa.
"Dan Allah ki yi haƙuri ba zan ƙara ba." Kaka a zaune ta kwana tana yi mata addu'o'i, Kuluwa idan taga Kaka ta fara gyangyaɗi sai ta zabura tana cewa gata nan zata kamani.
Zuwa ƙarfe biyu bacci ya ɗauke Kuluwa daga nan Kaka ta samu ta kwanta, cike da tunanin irin rashin mutuncin da zata yiwa Mama gobe.
Ƙarfe shida Kuluwa tayi sallah Kaka ta miƙa mata Qur'ani ta ce.
"Maza Kulun majadun ƴar gatan Kaka, fara mai farar aniya zinariya mai haska gida."
Kuluwa da farko ta fara ɓata fuska tana tunanin abinda zata aikata, wanda zai hana ta zuwa hadda amman jin kirarin da take mata.
Yasa ta karɓa Qur'anin tana rausaya jiki tana fari da ido kamar mai tashin aljanu.
"Maza kije ƴar albarka bana so ki makara." Kaka ta faɗa tana miƙa mata hamsin kuɗin wata.
Kuluwa ta amsa ta tafi tana rangwaɗa gata babu ƙiba 😂
Tana zuwa taga an tare makara ta ƙarewa mallamin kallo yana sanye da babbar riga, kuma gashi mallamin mugune bai da mutunci, ya tsani Kuluwa saboda rashin jin maganarta akwaita da ƙoƙari neman magana tsokana, babu wanda ta ƙyale harta mallaman sun san da zamanta, gashi bata ƙaunar abinda zai taɓa mata lafiyar jiki.
Wani tsumma ta gani a kusa da ita ya dunƙule kamar maciji, tayi murmushi ta ɗauka ta ɓoye a cikin hijjab ganin layin yaƙi zuwa kanta yasa ta yanke shawarar ta watsa gurin kawai kowa ya yi ta kansa.
"Wayyo Allah maciji maciji." Kuluwa ta faɗa tana jefa musu tsumman data ɗauka, tashin hankali gaba ɗaya kowa ya watse Mallam yazo guduwa babbar rigarsa ta yarda dashi.
"Mallam maciji a bayanka." Kuluwa ta faɗa tana zurawa da gudu cikin makarantar, Mallam ya fara rarrafe yana raba ido ya kasa tashi.
Koda ta shiga makarantar abinda take faɗi kenan.
"Maciji jama'a akawo ɗauki." Gaba ɗaya ta har gitsa makarantar, yara suna ta ihu wasu suna haurawa ta window suna guduwa, wasu kuma toilet ɗin makarantar suke shigewa.
Ummi ta dafa Kuluwa ta ce.
"Daman ina tunanin yanda zan watsa makarantar ne sai gaki kin zo."
"Dallah rufa mun baki munafuka matsoraciyya kawai." Kuluwa ta faɗa tana hararan Ummi.
Ganin akwai sauran mutanen da suke zaune acikin aji yasa ta fashe da kuka ta buɗe murya ta ce.
"Inalillahi wa'inna ilaihir raji'un macizan sun ƙara yawa." Haka ta ringa bin ajujuwa tana dirawa ta window, ƙarshe dai kowa ya yi takansa daman mallamai huɗu ne kuma kowa ya yi takansa, Mallam da rarrafe ya fita get ɗin makarantar duk ya haɗa zufa.
Suka nufi hanyar gida yara taga suna dambe ɗaya jibgegiya ɗaya siririya mai ƙibar tana ta dukan siririyar, ta miƙawa Ummi Qur'ani ta shiga tsakiyar su ta ɗibo ƙasa ta raba biyu, hagu dama ta kallesu ta ce.
"Gana tsiya gana arziki." Yarinyar da ake duka ta zubar dana arziki ɗayan kuma ta cakumi hijjab ɗin Kuluwa.
Kuluwa ta kwace hijjab ɗinta hamsin ɗin da Kaka ta bata shi ta miƙawa siririyar ta ce.
"Na sai faɗar." Yarinyar tasha ƙasa ta daku tana dafe hamsin ta zura da gudu.
Kuluwa taji anyi sama da ita.
Ta Batulu ce........ ✍️
Likes comments sune ƙwarin gwiwar marubuci.*KULUWA*
*(Ƴar bala'i)*
Group 👇
https://chat.whatsapp.com/EEiLcD9ZnpbFRLSjSOZozT
Channel 👇
https://whatsapp.com/channel/0029Vb6Kd5SFnSz8T3XpQ22g
*JAJIRTATTUN MARUBUTA WRITER'S ASSOCIATION*
Ban yarda a juya mun labari ta kowace irin siga ba, duk wanda na samu ya juya mun labari ba zan lamunci hakan ba.