BABI NA GOMA SHA BIYU Fiye da sati biyu
Duk Kyan Takalmi Part 1 Complete Hausa Novel · about 29 min read
dr shuraim bai kira aisha farida ba, itama
bata kira shi ba. Don haka sai ta fara shiga
kokonto anya kuwa dr shuraim yana sonta?
Da yana sonta ai ba zai share ta haka ba,
wata kila tausayinta kawai yake yi ba
soyayya ba. Jikinta yayi sanyi, ta fara shiga
damuwa, bata da walwala abubuwa suka
taru suka yi mata yawa. Kowa ya kalle ta sai
ya tambaye ta me yasa ta rame. Taci gaba
da daurewa tana ta addua tana neman agaji
daga Ubangiki Mai kowa, Mai komai. Son dr
shuraim ya zame mata tamkar ruwan
shanta, ya zame mata abincin cinta, kuma
mayafin lullubarta. Duk da daurewa da tayi,
sai da ta kai ta kasa cigaba da daurewa
saboda ji take tamkar zuciyarta zata yi
bindiga ta fashe don kunci. Tsananin son dr
shuraim da kuma rashin abida abokiyar
shawararta, itace mai bata shawara da
kwantar mata da hankali. Tasan da tana
nan da tuni ta fada mata abin da ya kamata
tayi nan gaba. Ranar talata bayan yaya
hussaini ya fita aiki, yara sun tafi
makaranta, sai ita kadai a gida. A kwance
take a daki ba tare da tana jin dadin
kwanciyar ba. Ta yanke shawarar tunda ga
dan kudi a hannunta bari ta harhada tayi
musu danwake, ta kai musu asibiti ko Allah
Zai sa ta dace ya ganta ya tuno da ita don
tana tunanin ya manta da ita ne. Tayi
zumbur ta miike ta shiga shirye shiryen yin
dan wake. Kafin karfe goma na safe ta
gama tsab, ta zubawa yara na su a flask. Ta
shiga tayi wanka ta fito ta dauki fiye da
mintina talatin tana kwalliya.
Wata sabuwar atamfarta ta saka diamond
mai kore da ja, aka dinka mata riga da skirt
matsattsu, ta sami bakin gyale da bakin
takalmi ta saka. Sai dai kash! Ta juya ta
sake juyawa ta dubi jikinta sosai, sai taji ba
zata iya fita a haka ba. Ta san shi kansa dr
shuraim din ma ba burge shi zatayi ba. Don
haka ta ajiye gyalenta ta dauko bakin
hijabinta sabo dal ta siya kwanan nan naira
dubu daya irin wanda ake siyarwa a dinke
mai hannaye kamar riga. Ya shiga da
takalminta mai dan tsini. Ta kullo kofar
dakunan bayan ta debowa yara kayan
makarantar islamita da flaski din abincinsu
ta mika dakin uwani taroke ta arziki idan
yaran sun dawo ta basu abincin su ci su
sauya kaya idan lokacin islamiya yayi su tafi.
Tace itama ba dadewa zatayi ba, zata kai
wa marar lafiya abinci a sibiti. Uwani ta
amsa mata cike da fara'a gami da alkwarin
zata aiwatar da abin da ta umurce ta, ta
hada ta yiwa marar lafiyar adduar samun
sauki. Aisha ta dauki kwandon da ta saka
flask din abinci da plates da cokula, bayan
yaji dakakke a 'yar roba, da 'yar robar
mangyada. Tana tafe cikin nutsuwa har ta
fito daga lokonsu ta sami adaidaita sahu
nan da nan ta haye. Ita kanta tasan tayi
kyau, ko ba a fada mata. Jama' da dama
sun dasa don samari suna ta binta sun kai
su uku sunayi mata magana. Suna sonta
bata kula su ba. Kuyi hakuri an riga an bada
ni. Amsar da take ba su kenan.
Tana isa cikin asibitin malam ta doshi
ofishin dr lukman, sai taji kirjin ta ya fara
dukan uku uku, don fargabar abinda zata
tarar daga dr shuraim. Tana hawa kan
barandar ofishin sai ta hango dr shuraim da
wasu dattijai maza su uku sun tunkaro ta,
ma'an suna fitowa ita kuma tana shiga. Sai
taji wani mummunan faduwar gaba. Ya
tsura mata ido sosai yana kallonta, har sai
ta taji kunya ta sunkuyar da idanuwanta
kasa. Suka wuce ita ma ta wuce, ta juyo a
hankali zata dube shi, shima ya juyo sai
gaba dayansu suka gaggauta juyawa da
sauri. Ta shiga fargaba saboda ta dimauce,
bata gaishe shi ba, kuma ya kamata ta
gaishe shi din. Don haka ne ma yake ta
kallonta har da waiwaye. Abin da zuciyarta
ke zayyano mata kenan. Jikinta a sanyaye
ta shiga ofishin dr lukman, taci sa'a yana
nan shi da abokinsa dr mohd. Bayan ta
gaishe su, sai ta ajiye kwandon abinci a
gaban dr lukman. Tace ga danwake nayi
muku. Yayi farin ciki, yayi godiya sosai. Dr
mohd ta dubi dr lukman yace lukman zaka
bani 'yar kanwar nan taka kuwa? Ina sonta
tun ranar da na fara ganinta. Kirjin aisha
farida ne ya burededen dukan uku uku har
ta fara dana sanin zuwanta nan a yau. Ana
wata sai ga wata, yanzu idan dr shuraim
yaji ko da wasa dr mohd ya furta yana
sonta, ai bar masa zaiyi ba zai kara nuna
alamar so ba. Ta tsunduma cikin wannan
dogon tunani, sai da dr lukman ya ambaci
sunanta ta dawo da hankalinta gare su.
Yace kanwata kinji wai in bashi ke? Tayi
murmushin karfin hali tayi shiru. Dr mohd
yaci gaba da kallonta, kallo mai cike da so
da kauna. Ta sunkuyar da kanta kasa, tana
mai tsananin jin kunya hade da bacin rai. Dr
lukman yayi dariya ya daki kafadarsa yace
kai da kake min tsiya wai ba kanwata bace,
bamuyi kama ba, sai inga wanda zai baka
'yar. Dr mohd yayi dariya yace yi hakuri
don Allah, yaya na daina. Yana rufe bakinsa
sai dr shuraim ya shigo. Nan da na hankalin
aisha farida ya sake tashi. Ta fara addua
kada Allah Ya sa acigaba da zancen soyayyar
nan. Tayi sauri ta sulalo daga kan kujera ta
gaishe shi. Ya amsa cike da far'a, sannan
yaci gaba da kallonta. Can yace lukman
dama kanwarka ce na hadu da ita a baranda
nake mata kallon sani, amma ban gane ta
ba. Naga ta sauya. Aisha farida ta dube shi
a kunyace ta sunkuyar da kai. Dr lukman
yace me ka ga tayi? Ta sake yin kyau ko? Ai
an gama makaranta ana hutawa a gida. Dr
mohd yace kai fa lukman yaya ne ka bari in
fadi da bakina mana, sai kace tayi kyau, kai
yayan kwabo ne ko? Su biyu suka tuntsire
da dariya yayin da dr shuraim ya tsaya cak!
Ya dubi dr mohd ya juya ya dubi dr lukman
ya juyo ya dubi aisha farida nan da nan taji
zuciyarta na dukan uku uku. Daga dukkan
alamu dr lukman ma baiji dadi da dr mohd
ya fadi haka a gaban dr shuraim ba, domin
yana kyautata zaton dr shuraim yana son
aisha farida, furatwa ne kawai baiyi ba.
Dr shuraim ya gaggauta daukar ajiyarsa a
loka ya fice da sauri. Aisha farida ta kame a
zaune, yayin da numfashinta yake kokarin
daukewa gaba daya, babu wanda yake
magana a tsakanin su biyun, dr mohd ne
kadai yake surutunsa. Haushi da tsanarsa
suka bayyana a fuskar aisha farida. Ta
dauke shi a matsayin tamkar mutumin da
ya dauko wuka mai kaifi ya dubi cikinta ya
burma mata, ma'ana ya kashe ta. Domin ya
rugurguza mata walwalar rayuwarta duniya
da lahira. Dr mohd yayi ajiyar zuciya, ya
dubi aisha farida yace bani lambar wayarki
aisha umar. Ta dago da sauri ta dube shi,
duba na takaici ba tare da ta iya furta
kalma gida daya ba. Dr lukman yayi sauri
yace ita zaka tambaya ko ni yayanta zaka
tambaya na ba izini ka karba? Ita ma na
umurce ta ta baka? Tayi murmushin karfin
hali ta mike tsaye a sanyaye ta yi musu
sallama zata tafi. Dr mohd ya nemi ta kara
zama suyi hira, tace gidan babu kowa sai ita
kadai, don haka take so ta koma da wuri.
Dr lukman ya ciro naira dubu daya ya mika
mata, yace tayi kudin mota. Tace ya bari ba
zata karba ba, tana kudin motarta. Dr
mohd ya zabura yace ka bari kawai zan
bata ko kuma ma marasa lafiyan da suke
jirana suyi hakuri sai na kai matata gida
sannan zandawo. Dr lukman yace wannan
kyautata ce ta daban a matsayin na
yayanta, kai da ita kuma daban. Kuma
wallahi sai kin karba kinji ma na rantse.
Aisha farida ta saka hannu biyu ta karba
gami da yin godiya, cikin sassanyiyar
murya. Dr mohd yace Allah sarki, kaji
yarinya mai ladabi, gaskiya nifa da gaske
nake. Lukman zanje in kai ta gida in dawo
muyi maganar gaskiya ba wasa nake ba.
Tayi wuf! Ta fice da sauri don bata so ya
biyo ta, shima ya fita da sauri ya biyo
bayanta ta, ya umurce ta ta jira shi su tafi
tare. Wani babban tashin hankalin kuma sai
ya tura kofar ofishin dr shuraim ya leka sai
ga dr shuraim a zaune a kan kujerarsa yana
danna laptop. Ya dagi da kyawawan
idanuwansa ya dubi dr moh sannan ya sake
daga ido ya hango aisha farida a gefensa.
Sai ya sunkuyar da kai, yaci gaba da danne
dannensa. Amma daga kallon fuskarsa
kasan zuciyarsa a bace take. Dr mohd yace
abokina zo muyi rakiya, wancan dan iskan
lukman yaki yace shi a dole babban yaya
ne. Ya girgiza kai yace nima yaya ne, ba
zanje ba. Kaje sai ka dawo. Aisha farida tayi
wuf! Ta bar wajen, tafiya take ba tare da
tasan inda take jefa kafarta ba. Kawai wani
lungu ta samu ta dinga kutswa cikin asibitin
maimakon ta nufi bakin gate sai tayi ciki.
Kafin dr mohd ya waiwayo sai yaga wayam!
Bata nan. Ya fito da sauri ya dudduba
hanyar gate ba ta nan. Ya duba kudu da
arewa, babu ita babu dalilinta. Sai ya cika
da mamaki, ya shiga kokonto da wasi wasi
don haka ya koma ciki da sauri don ya
shaidawa yaya lukman. Dr lukman yayi
dariya yace kunyarka takeji, kuma tana da
tarbiya bata so a ganta da namiji , ni nasan
halin kanwata. Dr mohd ya takura sai an
kitay a waya yaji inda take. Aisha farida ta
isa ofishin matron maryam ta iske bata nan,
sai sababbin dalibai da aka turo daga
makarantarsu. Yawancinsu ma duk sun
santa. Bayan sun gaisa ta tambaye su
matron sai suka ce ta fita. Aisha ta jawo
kujera ta zauna tana huci, nan da na suka
hau tambayarta bata da lafiya ne? Tace
gajiya ce kawai, tana so ta huta sannan ta
tafi. Bata rufe bakinta ba sai wayarta ta dau
kara. Ta bude 'yar karamar jakar da ta saka
kudin motarta da wayar ta zaro wayar,
sunan dr lukman ne ya bayyana. Sai taki
amsawa har ta katse. Tana katsewa ya sake
kira, don haka ta tabbatar kiran yana da
amfani, sai ta amsa. Tambayar da ya fara
mata itace kina ina? Tayi inda inda sannan
tace ina cikin adaidaita sahu hanyar
komawa gida. Yace toh shikenan. Allah Ya
kaiki gida lafiya. Ya kashe wayar tana jiyo
muryar dr mohd amma bata gane abin da
yake cewa ba. Anan zan dakata mu hadu a
DUK KYAN TAKALMI 3 kuji yadda zata
kasance. Daga 'yar uwarku JUT.
See Translation
January 10, 2015 at 7:26pm · Public
35
DUK KYAN TAKALMI 3* 1
Tayi ajiyar zuciya mai karfi.sannan ta
kwantar da kanta akan teburin da yake
gabanta don ta rasa abun da yake yimata
dadi innalillahi wa inna ilahi raji`un,ta ke ta
ambato,sai da ta dauki tsawon mintina 20
bata iya dago waba,ta mike tsaye da kyar
yayin da idanuwanta suka yi ja,alhalin kuma
ita ba kuka takeyi ba daliban dai har yanxu
tambayarta sukeyi,anya kuwa lafia? tace
lafia kalau kawai dai gajiya ce. Tayi musu
sallama tabar musu sako su gaishe da
metron maryam sannan ta tafi,ta cikin
lunguna ta kurkurda ta fito gate,tana fitowa
taci sa`a ta sami A dai- daita sahu babu
kowa a ciki,don haka tayi wuf ta shigo
batare da ta fada masa inda zai kai ta ba
balle suyi cinikin kudin da zai karba,tana
shiga ta zauna tana daga kanta, sukayi ido
hudu da dr shuraim cikin tsaleliyar motarsa
discussion continues,shi ma kallonta yake yi
alokacin da yake kokarin tsallakawa titi,ta
sunkuyar da kanta da sauri,yayin da
shikuma ya tsaya cak yana kallonta,daga
dukkan alamu yana mamaki da ya ganta
yanxu,mai adaidaita sahu yaja ya tafi yayin
da aisha farida ta rike kai,saboda nauyin da
taji kan yanayi mata sai da mai adaidaita
sahu yayi da gaske sannan ta bashi amsa, ta
fada masa inda zai kaita tana shiga gida
sallan azahar kawai tayi ta shiga lungun ta
kwanta ba tare da ta san a duniyar da take
ba,taji dadi da ganin yara a zaune a dakin
uwani,sunci abinci suna hutawa,don haka
tace suyi zamansu a nan zatayi aiki idan
lokacin makarantar islamiyya yayi su
tafi,saboda kawai bata son damu da
magana cikin wanan hali da ta riski kanta
Allah sarki soyayya ruwan zuma tayini tana
duban numbr dr shuraim,sai taga kamar shi
take gani,koda yaushe kunnenta da
idanuwanta ta suna yi mata gizau,taga
kaman shine yake kiranta da zaran an
kirata,idan taga bashi bane sai ranta ya baci
tana so takirashi amma tana tsoro kada ya
wulakantata kuma bata ma san abun da
zata ce masa ba idan takira din. washegari
ta tashi acikin bacin rai kaman yanda ta yini
a jiya ta yankewa kanta shawarar gara ta
hada ta kaura shagamu kawai tayi
rayuwarta acan ,idan sakamakonsu na exm
ya fito ta karbi takardunta taje can ta nemi
aiki a asibitin garinsu shi yafi mata
sauki,saboda son dr ya zamar mata annoba
musamman idan tana ganinsa. wayarta tayi
kara alokacin da take wanke-wanke ta arto
da gudu ta dauka tana addu`a Allah ya sa
dr ne,sai taga wata bakuwar no ce,ta yi
sauri ta danna,muryar wani kamillan
mutum taji ya ambaci sunanta,aisha umar
ce ko? ta amsa eh,nice" yace dr mohd ke
magana!
Ta sulale ta zauna,yayin da takaici ya
lullube xuciyarta,ta gaishehsi taja bakinta
tayi shiru tana sauraronsa,yace sai kika
gudu kuma ko tsorona kike ji? ta kame a
zaune,domin tana jiyo muryar dr lukman da
dr shuraim a gefensa,hankalinta ya tashi
har abada sai hawaye ya surnano daga
idanuwanta bata iya bashi amsa ba,yace ki
kwatanta min gidanku zan zo,tayi shiru can
tace ai zan shigo asibitin gobe zan karbi
kwanukan da na kawo muku,yace kash
gobe ai bana gari sai dai ki zo jibi tana jiyo
muryar dr lukman yana cewa to ka fasa
tafiyar mana idan da gaske kake yin son? dr
shuraim kuwa bai sake furta komai ba yana
gefe guda yana kallonsu,tayi sauri ta katse
wayar ta rushe da kuka,tayi sauri takira
wayar shagamu gidansu abida,lambar
mamarta,bugu daya ta dauka ta gaisheta,ta
shaida mata aisha farida ce daga
kano,kasancewarta tsohuwa ba iya karanta
suna tayi ba. Goggo tace ai na gane
muryarki yar baba,kamar yadda wasu suke
kiranta da haka,ina anti abida,ya jikin nata?
goggo ta amsa,mungode Allah,amma dai
jikin abida to sai yadda Allah yayi,gata nan
yanzun nan tace a tashe ta zaune ta gaji da
kwanciya,aisha farida ta fashe da
kuka,goggo ma ta fashe da kuka,aisha tace
a bawa abida wayar,goggo tace sai dai in
kara mata wayan a kunne,bata iya daga
hannunta, bazata iya rike wayar ba. Muryar
abida ce ke karkawa tace farida maiyasa
kike kuka? zan samu lafiya da izinin
Ubangiji. Aisha ta matse hawaye tace, anti
abida so nake ayi wa yara hutu na taho
shagamu na dinga ganinki bana jin dadin
gidan nan
Bana jin dadin kanon, duniyar ma gaba daya
ta isheni,Allah ya baki lafia. Hawaye ya
surnano da idon abida, tace bana so ki
kaura shagamu,har sai kin cika burinki akan
dr, Farida ta fashe da kuka tace anti bana
jin zan cika wannan burin nawa,domin
yanxu wani abokinsa ne yake sona,mai suna
dr mohd kuma har dr shuraim din ya
sani,nasan zai hakura ya bar wa dr mohd ni
kuma bana son dr mohd din,shuraim nake
so. Yanxu haka suna tare,kuma agaban dr
din yayi min waya,abida ta cije baki saboda
tsananin ciwon da yake addabarta,tace
kada ki damu duk irin abunda zai faru ki
zubawa sarauta Allah ido,ki gode masa kici
gaba da addu`a,kanwata duk irin wannan
wata hikimar Allah ce wacce ba ki sani ba,ki
ci gaba da nemawa zuciyarki abun da take
so har sai kin cika burinki,ina yimiki fatan
alheri. Farida ta katse wayar ta rusa kuka
ita kadai a daki ta fada a bayyane,wayyoh
abidata wayyoh shuraim,inna lillahi wa inna
ilaihi raji`un, Allah ka taimake ni ka cikamin
burina,ka karbi adduoina guda biyu,kaba wa
abida lafia ka bani dr. Tayi kuka tayi addua
har muryarta ta ddisashe,yau ma dai yara
sun sha wahala har karfe 2 basu ci abincin
rana ba,don bata iya dorawa da wuri ba.
kuyi hakuri ku yafemun yara ni kadai nasan
halin da nake ciki inji farida lokacin d take
cuu-cukun xuba musu abinci bayan da ta
tabbatar sun galabaita. Faruk ya dubeta
yace anti aisha meyasa kullun kike kuka? ko
mamarmu ta mutu ne? Hawaye ya surnano
da idonta tayi saurin ta dukar da kanta
kkasa don kada ya gane kukan zata sakeyi
ta girgiza kai tace mamanku bata mutuba ta
samu sauki,na muku alkawari ranan asabar
zansaka kati a wayata inkiramuku ita daya
bayan daya kuyi magana da ita zakuji
muryarta radau taji sauki sosai. sai taga sun
hada ido sunhadu sunyi daria suka hau
murna bayan tabasu abinci sunaci a tsakar
gida tashiga daki tarufe tashige lungu
tadinga kuka tana addua ya Allah kana sane
da halin danake ciki kasa abida ta warke
nasani baka barin wani dan wani yaji dadi
Allah ka duba kananan yaranta har hudu ka
tashi kafadunta,suna tanbayata mamarsu
yaya zance musu idan tarasu Allah kada
kabarsu sutashi a marayu kaman ni,Allah
kabani mijin danake so dr, insan dadin aure
dan idan na auri wani bashiba farin cikina
ragaggenai. Ya Allah kafini sanin abunda
yafi Alkhairi a rayuwata Allah nagode maka
kaciga da taimakona da kai kade na dogara,
adduoin da Aisha farida keta zubawa kenan
a wannan yinin,bata iya fitowo tayi hira da
yan gidan ba,har sai da ta tabbatar
magruba ta karato yaya husaini ya kusa
dawowa sannan ta fito,ta fara cukuncukun
dora abincin dare. Washegari jummaa ta
shirya da wuri ta fita,karfe tara a cikin
asibiti tayi mata,kasancewar juma`a ce don
kada a rufe hanya,ta isa ofishin dr.lukman
sai taji a kulle wata kila bai iso ba,tunda bai
isoba tasan dr shuraim bai karaso ba.
Amma dai taja jikinta ofishin ta tsaya,ta
karanta sunansa ta sake karantawa sai taji
sanyi a ranta,ko sunansa ta gani a rubuce
dadi takeji ,ta lumshe ido,tasa hannu a
hankali ta rike hannun kofar,sai taji tamkar
ta shafi hannunsa ta san tabbas ya taba da
hannunsa,ta murda da wasa don tana da
tabbacin a kulle take,bai karasoba kwatsam
sai taga kofa a bude har ma ta wangale sai
ga dr radau a zaune akan kujera suna hada
ido taji tamkar ta zura da gudu don fargaba,
tayi wuki-wuki da ido tana kallonsa cike da
mamaki yayin da shima haka har tsawon
lokaci suna kallon juna. Shigo mana inji shi,
ta fara tafiya a hankali kanta a sunkuye a
kasa cike da kunya,sai yanxu ta dubi kayan
da ta sako a jikinta,birkideden hijabi ne har
kasa yana jan kasa,shi ma mai hannu ne
kaman riga ake sakashi,maroon color sai ta
saka takalmi shima kalar hijabin mai dan
tsini,yayin da fuskarta bayan hoda bata kara
komai ba,babu kwalli balle jagira,don bata
saka ran zata hadu da shi ba.niyyarta tazo
ta kwashi kwanunkanta tayi wa asibitin
sallama daman tasan dr mohd baya nan yau
shi yasa ta garzayo dan bata son su hadu.
Sai kallonta yake tundaga sama har
kasa,har saida ta karaso gabansa ta durkusa
har kasa ta gaishe shi yace tashi tashi ki
hau kujera ki zauna, ta tashi a hankali ta
zauna kan kujerar har yanxu kanta a
sunkuye yake a kasa,har zuwa lokaci mai
tsawo batayi maganaba shima haka danne
dannensa kawai yakeyi a laptop.
Can ta dago ta dube shi sai taga ya dago da
sauri ya dube ta,tayi murmushi tace yaya
lukman be karaso bane?? naje ofc dinshi a
kulle,ya gyada kai kawai bai yi magana ba
sai taji hankalinta ya tashi,ta tabbatar yana
jin haushinta ta yunkura ta mike tace,bari
in jirashi a waje ya girgiza kai ba tare da ya
kalleta ba,yace ba damuwa ki zauna a nan
har yazo,ta koma ta zauna yayin da taji dan
sanyi a ranta,taci gaba da sunkayar da kai,
idan ya dago ya dubeta sau daya, sai yaci
gaba da kallon laptop dinsa. Kamar daga
sama taji ya ambaci sunan ta,ta dago da
luhu-luhun idonta ta dubeshi ta amsa cikin
nutsuwa. Ya tsaya cak da abunda yakeyi
yace lafiyarki kalau,ko akwai abunda yake
damunki ne? tayi murmushin karfin hali mai
kayatarwa,tace lafiata kalau dr. Yace bawan
da yataba gayamiki kin rame kwanan nan?
ta sake murmushi ba tare da tasan amsan
da zata bashi ba, yace don wa kike dafa
abincin nan da kike kawowa? Shi kansa
yasan ta firgita da jin wannan
tambaya,domin ta dago da sauri ta dubeshi
ta tabbatar yau wulakancinsa yau ya motso
kanta ,taji hankalinta ya tashi,sai kwalla
tacika mata ido,ya sake maimaita
tambayarsa, hakika amsa yake bukata kuma
ya xuba mata ido,ta runtse ido tayi shiru.
Can ta dago ta dubeshi tace saboda kai da
dr lukman nake kawowa. Yayi daria yace
harda ni ba saboda lukman kawai ba? to
mun gode kuma munji dadin abincki sai dai
ina rokonki ki daina wahala da mu,kada ki
kara kawowa. Kallo na rashin fahimta take
yimasa,har sai da ya gane haka. Yayi ajiyar
xucia yace bana so naga mace na
wahala,macen ma mai suna mai daraja irin
naki AISHA FARIDA. Sai taji dadi ya rufeta
tasa hannu ta sosa goshinta saboda
kunya,tayi murmushi tace dr ba damuwa ni
ba ya damuna,in har zaku ci,ya girgiza kai
yace kiji maganata,ki daina kawowa in
muna so zamuyi miki waya ki kwatanta
mana gidan mu zo mu dauka,ba sai kinxo
ba kinji ko? nan da nan ta amsa da to,in
sha Allah zanyi amfani da abunda kafada.
Yace yawwa na gode yaya mai jiki,ta
langwaba da kai,tace tana can shagamu
tana fama har yanxu bana jin tana samun
sauki, sai ta fara kwalla. Ya tsaya cak ya
daina abinda yake,yana dubanta yace ban
taba ganin randa zan ganki ba kya kuka
ba,farida waya gaya miki ke kadai kike da
matsala a duniya,mu me yasa bama kuka
kullum? Waye ya shagwabaki kike yawan
kuka? tasa hannu ta matse hawaye,tayi dan
murmushi tace ba kowa....yace kidena
kuka ni kukan yaro ma bana so balle babba
kuma mace,baki san duk sanda naga
hawaye a idonki ba ,idan kika tafi damuna
yake a xucia ba? to ni haka nake a
rayuwata,matsalar wani matsala tace,ki
fadamun ko akwai abinda yake damunki a
rai,sai in baki shawara nima abokin lukman
ne.
Tayi dariya ta girgiza kai tace babu komai
idan ma akwai ina fadawa Allah ya kawo
mun sauki. Yace wannan yayi kyau ko meye
damuwarki ki fadawa Allah. Kuka da saka
damuwa a rai matsala zaki jawowa lfyrki,mu
likitoci bama son haka. Musamman
bangaren yayanki lukman kwakwalwa suna
hana mu2m yawan 2nani da damuwa. Ki
kiyaye kina karamarki zaki cuci rayuwarki a
banza. Ta gyada kai tace naji likita ngd.
Yace shigarki tayi min kyau ta burgeni. Sai
taji tmkr ba shi yake magana ba. Ta kalle
shi ya kalleta, shima ya gane ta shiga
mamaki. Sai yai murmushiyace,kina burge
ni fa, i lyk ur style. Dgwar ajiyar zuciya yaji
taja, har yanzu kallonsa takeyi kawai. Yace
zaki jira ni in tashi daga aiki na mayar dake
gida? Wannan karon ma sake zaro ido tayi
ta dube shi cike da mamaki. Yayi dry yace,
ba kya bani amsa fa, me yasa kike
mamamki ne? Tayi mrmshin krfn hali tace,
to. Yace ki jirani a nan ofishin bayan sallar
juma'a sai na dauke ki a motata mu
fita,idan na kaiki gidana kika gani muka dan
huta bayan magruba sai muje in mayar
dake gidanku nima naga gdnku. Ko ban zo
ba ke saiki zo gidana 2nda ni kadai ne a
gdn kema kuma antinki bata nan, babu
wanda zaisa miki ido. Yau dr. Lk ba zai xo
ba,tare suka yi tafiya da dr. Mohd saini
kadai kinga sai kiyi zamanki a ofishina ki jira
har bayan sallar juma'a ko? Kuma dk
abunda zai faru a tsakaninmu bana si ki bari
wani ya sani har lk sirri ne. Ta zazzare ido
tana dubansa,taga shi ko a jikinsa
maganarsa yakeyi kansa a tsaye. Sai taji a
ranta ta tsani kanta, kuma t tsani
rayuwarta. Ashe dan iska ne bata sani
ba,har take yabonsa? Sai taji gaba daya ya
sure mata taji daman bata sanshi ba,bata
taba ganinsa a raywrta ba. Ya dubeta duba
na kurilla yayi mrmushi ya daga mata gira
yace,baby kin amince dani? Zan kawo miki
canji a rayuwa. Soyayya da jindadi ga dukiya
mai yawa. Dn Allah ya dora min sonki a lkc
guda kece baki sani ba,kina da kyau,gaki da
diri,kinfi sauran mata. Taji tmkr ya caka
mata wuka a kahin zuciya ta fada a
zuciyarta, innalillahi wa'inna ilaihir rahi'un!
Dr shuraim me yasa halinka ya zama haka?
Wayyo Allah na dama ace yadda kake da
kyau kanada kyawun halyya a boye kmr
yadda a zahiri kake kamilalle mai rukon
addini
Ya katse 2naninta yace, bari inje clinic ona
da patient zan bar miki ofishin ki bude firij
akwai fruits da juices kisha wanda kike so.
Ya dauki laptop dinsa ya fice yayin da ta
bishi da kallo harya fita. Ta dafe kirji ta
zabura ta mike tsaye sai taji jiri ya kwasheta
ta koma ta zauna ta rushe da kuka. Ta fada
a bayyane, Allah ka fini sanin dalilin daya sa
na tsinci kaina a cikin irin wannan rayuwa.
Ina abida? Abida ko zo kiji halin da nake
ciki. Tayi kuka ta gaji,ta dubi ko ina a cikin
ofishin babu abnda take hangowa a cikin
lokokinsa daga manyan littafan likitoci dai
kur'anai izifi sittin-sittin. Ta daga ido ta
dubi bango taga gaba daya firem ne a
rubuce da sunan Allah da manzonsa. Ta
dubi kasa sallayar sallarsa a lungu da carbi
dan yayi sallah yake ja. Sai taji ranta ya
sake baci,ta fada a ranta. Dr shuraim ya
zama babban munafuki a addini a fili yana
nunawa shina Allah ne,fasikancu ne kuma a
boye. To ashe duk 'yan matan nan da yake
wulakantawa dk sai daya gama lalata su
tukunnan sannan ya koresu? Ka cuci kanka,
ka cuci kyakkyawar hallitarka. Allah ka yaye
min son fasikin mu2m a rayuwata. Ta sake
rushewa da kuka,tayi zumbur ta mike ta
bude kofar ta leko taga bayanan, sai ta fito
ta jawo kfr ta rufo. Tana tafe tana waiwaye
waiwaye. Abin mamaki sai taga ofishin dr lk
a bude har wani dalibi ya kwankwasa ya
tura kfr ya shiga. Ta sake tabbatarwa dr S
makaryaci ne,makiri,azzalumi,yayi niyyar
cutarta. Tayi kmr ta shiga ofishin ta dibi
kwanukanta, in yaso tayi sallama dasu har
abada. Sbd abokin fasiki shima in ba a yi
sa'a ba fasikin ne. Sai taji ranta kawai har
kwanukan bata so,suje su rike. Tayi wuf! Ta
fice da sauri tfy take ko waiwaye bata yi
burinta kawai ta ganta a cikin adaidaita
sahu.
UK KYAN TAKALMI 3* 2
Tazo fita ta get kenan sai taji wayarta ta
dau
ruri tayi sauri ta dauko 'yar jakarta,ta duba
sai taga sunan dr. Lk ta danna a sanyaye sai
yace, Aisha Farida kina inane? Ta dafe kirji
tayi shiru can tace ina gida. Yace ashe bake
bace wata na gani a cikin asibiti kmr ke sak!
Ta gifta. Sai ya katse wayar, ta tsaya cak!
Ta
dubi hanyr ofishinsa ta dubi hnyr waje.
Yayin data dinga shawarwarin inda zataje.
Taji kmr ta koma ofishinsa ta shaida masa
abun da abokinsa yayi mata,sai taga meye
amfanin shaida masa din? Watakila ma
bakinsu 1. Dn haka tayi tfyrta. Tana cikin a
dai daita sahu tana sharbar hawaye ta
sauka
a unguwarsu ta gangara gida, dk wanda ya
hadu da ita a hnya saiya tmbyeta farida lfy?
Tace bani da lfy. Sbd sunga kuka takeyi
haikan, kuma tfy take kmr zata fadi. Ta
kunshe fuska a cikin hijab, ta shiga gida dn
bata son mutanen gida su gane tana kuka.
Ta bude daki ta shiga sai ta yaye hijabin ta
urgar ta dora kannu aka ta rusa kuka mai
sauti. Tayi sauri tasa hannu ta kunshe
bakinta, dn kada 'yan gidan su jiyota. Ta
drkushe kasa tana fadin, Allah ngd maka
daka bayyana min waye dr.S 2nda wuri.
Allah ka yaye min sonsa, ka masanya min
da wanda yafi shi alkhairi. Ashe abida tayi
gsky data ce in rike addu'a, Allah shi yasan
dai-dai idan bawa yana son abu yaga Allah
bai bashi ba. Bai sani ba ko abun ba
alkhairi
bane a gareshi. Na rasa Dr S,na rasa ka har
abda, na hakura da kai. Bana sonka, bana
marmarin in sake haduwa dakai a
rayuwata. Ta jawo wayarta ta nemo sunan
goggon mahaifiyar abida,dk da tasan halin
da abida ke ciki,amma babu yadda zatayi
ne, dole ita din zata fadawa don in bata
fada ba zuciyarta zata iya fashewa a yau.
Ina anti abida? AF ta tmbyi goggo ko
gaisuwa babu. Lfy? Ta tmbya cike da
damuwa. Jikinta zan tmbya,kuma ina so a
bata waya mu gaisa. Inji AF. Goggo tace
bana so kuna maganr nan, dn kuka naga
tanayi, ban san me kike fada mata ba.
Marar lfy baya son damuwa fa farida. Ta
jiyo muryar abida tana cewa, googgo ki
kawo min wayar, bakiu san abn da zata
fada min ba. Farida bata da kowa a duniya
saini. Idan da sauran nmfashi na a duniya
ban mu2 ba,ai zan saurari matsalolinta.
Goggo taje ta karawa abida waya a kunne.
Abida ta ambaci sunanta sai AF ta rushe da
kuka. Tace anti ashe Dr.S dan iska ne? Wai
zai kaini gdnsa mu huta. Abida tayi dariya
tace,kada ki yanke hukunci,kibi a hnkl. Ba
gsky bane, kici gaba da addu'a kanwata.
Takaici ya sake bullowa daga cikinzuciyar
AF
da taji amsar abida, saita katse wayar.
Karar shigowar sako ne ya shigo wayarta.
Ta
duba da sauri sunan Dr.Lk ne nan da nan ta
cika da mamaki. Tana kokarin budewa ta
karanta sai wani sakon ya shigo. Ta duba
taga sunan Dr.S ne,ta gyara zama ta mike
kafa yayinda hawaye ya hadu da gumi suka
damalmale mata fuska, ta dora hannu aka
ta fasa kuka. Taji hnklnta ya tshi dn bai
kamata ta zama haka ba a wajensu dr.lk
ba,
abn arzikin data keyi musu bai dace su
saka
mata da tsiya ba. Me tayi musu a rayuwa
da zasu hada aki su cuce ta. Ashe son da
Dr. Mohd yace yana yi mata dk tsokana
ce,yaudarata sukeyi kenan? Zuciyarta tana
duka 3 3 a lkcn da zata bude sakonnin dn
fargabar abnda zata karanta. Sai
idanuwanta sikayi dusu dusu har bata gani
sosai sbd tsananin kuka. Ta bude na frko ta
karanta,sai ta dafe krji yayin da ta bude na
2 ta karanta,sai ta damko wuyanta dan
mamaki,kuma sakonnin iri daya ne babu ko
digo daya daya bambanta. Ta zabura ta
mike tsaye ta sake karanta dukka 2n hakika
abn data gani dazu shine ba gizo
idanuwanta keyi ba,gsky ne.
Kin ci jarabawa Aisha Umar,fito muna kofar
gidanku". Abinda Allah ya nuna mata kenan
a cikin wayarta(kunji ta fa sai kace wani
wahayi wai Allah ya nuna mata lols) sako
daga Dr.S da Dr.Lk,dukka abu daya suka
rubuta mata. Ta cika da mamaki sai tayi
sauri ta jawo wani tsohon zaninta ta
fafface
ta goggoge fuskrta tayi wasai,sannan ta
goggoga 'yar hoda ta sake saka hijabnta.
Hannunta sai karkarwa yake ta sala
takalminta ta fito a nutse tana sanda. Bata
tabbatar da abunda suka rubuto mata ba
ko gske ne,amma dao gara taje ta duba. Da
fitarta Dr. S I ta fara hangowa tayi sauri ta
sake duban na kusa dashi, Dr. Lk ne,sai
taga sun dubi junansu sun kyalkyale da
dariya. Ta snkyr da kanta kasa ta karaso
gabansu ta durkusa ta gaishe su. Dr. Lk
yace,srkn kuka, kin daina kukan ne? Dr.S
yace,farida kin bar min ofishina a bude har
an yashe ni. Tay ajiyar zuciya,ta grgza kai
ba tareda tasan abnda zata fada ba.
"Kin ci jarabawa Aisha Umar,fito muna
kofar
gidanku". Abinda Allah ya nuna mata kenan
a cikin wayarta(kunji ta fa sai kace wani
wahayi wai Allah ya nuna mata lols) sako
daga Dr.S da Dr.Lk,dukka abu daya suka
rubuta mata. Ta cika da mamaki sai tayi
sauri ta jawo wani tsohon zaninta ta
fafface
ta goggoge fuskrta tayi wasai,sannan ta
goggoga 'yar hoda ta sake saka hijabnta.
Hannunta sai karkarwa yake ta sala
takalminta ta fito a nutse tana sanda. Bata
tabbatar da abunda suka rubuto mata ba
ko gske ne,amma dao gara taje ta duba. Da
fitarta Dr. S I ta fara hangowa tayi sauri ta
sake duban na kusa dashi, Dr. Lk ne,sai
taga sun dubi junansu sun kyalkyale da
dariya. Ta snkyr da kanta kasa ta karaso
gabansu ta durkusa ta gaishe su. Dr. Lk
yace,srkn kuka, kin daina kukan ne? Dr.S
yace,farida kin bar min ofishina a bude har
an yashe ni. Tay ajiyar zuciya,ta grgza kai
ba tareda tasan abnda zata fada ba.
"kinsi jarabawa farida". Inji dr.S. Dr.Lk
kuma yace wlhy abokina gwadaki yayi
muna
zazzaune a cikin motata a lkcn da kika fito
kika nufi get shiyasa nayi miki wannan
wayar. Niyyarmu mu dauko ki mu dawo
dake gida,sai yace gara mu biyo ki a baya
muga gidanku. Ta sake yin dgwr ajiyar
zuciya ta dago da sauri ta dubi Dr.S sai yayi
mata mrmshi ma kayatarwa. Taji sanyi a
cikin zuciyarta,farin ciki marar misaltuwa ya
tabbata a zuciyarta. Ji take tmkr anyi mata
albishir zata shiga aljanna. Dr.S yace yanzu
ke in aka ce miki haka nake zaki yarda? Ina
da kyakkyawan zato a kanki saina ke so in
tabbatar da hakan, dn haka ni da abokina
muka shirya jarabawa muka baki. Allah
cikin
ikonsa sai kika cinye dukka. Mrmshi takeyi
har yanzu,bata ce komai ba, mun baro aiki
da yawa muka taho a yi hkr a gafarce mu
idan munyi laifi da muka shiryo wannan
gwaji,sbd mun saka ki kuka da yawa. Ta
rufe ido tayi dariya tace, bakuyi laifi ba
yayana. Dr.Lk yace,idan akwai yaro yazo ya
biyo mu mota ya karbar miki kwandon ki
mun taho miki dashi. Tace, to bari in shiga
gida in turo yaro ngd sai anjimanku.
Kallonta kawai Dr. S yakeyi harta shige ciki.
Ya grgza kai yace, lk nan ne gidansu da
gaske? Innalillahi wa inna ilaihi raji'un.
Yanzu daman a irin wannan gidan take
rayuwa? Dr Lk yace, da alama kuwa gidan
haya ne basu kadai bane dn ina nan a tsaye
ina ganin mata iri iri suna leko mu. A cike
gidan nan yake, irin hayar nan ta dakuna
birjik,bandaki daya. Yanzu a cikin bakin
gidan nan daman ake dafa mana dambu da
danwake muke ci? Dr.Lk yace, to bakin
gida, bakar tukunya ce? Ai kanwata tana da
tsafta,a tsaftace abincinta. Kai fa a ni'ima
kake shiyasa baka san ana wahala ba a
kasar nan. Dr.S yace, gsky ana wahala aini
ban taba shigowa lungun nan ba 2nda Allah
ya halicce ni. Ai bansan irin wannan gidan
farida take ba, daban zargeta ba don tana
hawa acaba. Alla srki ashe rashi ne yake
sakata hawa acaba.
Bai rufe baki ba saiga wani
dakwalkwalallen
yaro hancinsa fal da majina yace, wai gani
inji Aisha Farida kuna kirana. Dr S ya dubi
yaron ya juya ya dubi Dr.Lk sai suka tun
tsire da dariya. Dr.S ya ce Allah mai
halitta,yaro Allah yasa kayi ilimi ka fita fili
ka rabuda irin wannan rayuwa. Ya kama
hannunsa yace, zo muje abokina,yaya
sunanka? Yaro yace,sunana Dahiru. Dr. S
yana tafe yana sake waiwayawa yana
duban
gidan su Aisha Farida,yana sake kallom
unguwar da kwatoci, baya ga sauro da
kudaje suna ta shawagi. Dr. S ya dorawa
Dahiru kwando aka ya bashi naira #500
suka shiga mota suka tafi. Har suka isa
asibiti Dr. S bai fasa jajantawa wadannan
bayin Allah ba, musamman abar kaunarsa
AF. Yaji ya sake tausaya mata, ya kara
sonta,kuma ya kudiri niyyar taimakonta.
AF ta shiga gida zuciyarta cike da frn
ck,harma ta kasa fasalta irin frn ckn data
tsinci kanta a yau. Tana shiga daki ta cire
hijabi ta dauki waya ta kirasu abida aka ci
sa'a knwrta maimuna ce ta dauka. Byn sun
gaisa sai tace tabwa anti A zasuyi mgna.
Maimuna ta karawa Abida a kunne. Abida
tace AF ya ake ciki? Tayi dry tace, Anti A
ngd wa Allah ngd miki. Yanzu Dr.s yabar kfr
gdn nan shida Dr.lk ashe mgnr nan daya
fada min so yake ya gwasa ni yagani 'yar
iska ce ni? Yace naci jarabawa. Abida tayi
mrmshi tace, naji a jikina Dr.s m2mn kirki
ne, ko byn raina ki zama mai kyakkyawan
zato a kansa. AF taji jiknta yayi sanyi
tace,zaki ji sauki anti,ki daina fdr haka.
Ngd. Abida tayi mrmshi tace, yanzu zaki
wuce mataki na 4 zaki taka mataki na 5
shine ki nuna masa tsantsar soda kulawa.
Idan ya gasgata kina sonsa sbd Allah sima
zai soki a zuciyarsa,yasoki harma ya fara
2nanin yadda zaki kasance a matsayin
matarsa, ku zauna din-din-din. AF taja dgwr
ajiyr zuciya tace, to antina ngd,Allah ya baki
lfy. Abida tace Amin.
bata kira shi ba. Don haka sai ta fara shiga
kokonto anya kuwa dr shuraim yana sonta?
Da yana sonta ai ba zai share ta haka ba,
wata kila tausayinta kawai yake yi ba
soyayya ba. Jikinta yayi sanyi, ta fara shiga
damuwa, bata da walwala abubuwa suka
taru suka yi mata yawa. Kowa ya kalle ta sai
ya tambaye ta me yasa ta rame. Taci gaba
da daurewa tana ta addua tana neman agaji
daga Ubangiki Mai kowa, Mai komai. Son dr
shuraim ya zame mata tamkar ruwan
shanta, ya zame mata abincin cinta, kuma
mayafin lullubarta. Duk da daurewa da tayi,
sai da ta kai ta kasa cigaba da daurewa
saboda ji take tamkar zuciyarta zata yi
bindiga ta fashe don kunci. Tsananin son dr
shuraim da kuma rashin abida abokiyar
shawararta, itace mai bata shawara da
kwantar mata da hankali. Tasan da tana
nan da tuni ta fada mata abin da ya kamata
tayi nan gaba. Ranar talata bayan yaya
hussaini ya fita aiki, yara sun tafi
makaranta, sai ita kadai a gida. A kwance
take a daki ba tare da tana jin dadin
kwanciyar ba. Ta yanke shawarar tunda ga
dan kudi a hannunta bari ta harhada tayi
musu danwake, ta kai musu asibiti ko Allah
Zai sa ta dace ya ganta ya tuno da ita don
tana tunanin ya manta da ita ne. Tayi
zumbur ta miike ta shiga shirye shiryen yin
dan wake. Kafin karfe goma na safe ta
gama tsab, ta zubawa yara na su a flask. Ta
shiga tayi wanka ta fito ta dauki fiye da
mintina talatin tana kwalliya.
Wata sabuwar atamfarta ta saka diamond
mai kore da ja, aka dinka mata riga da skirt
matsattsu, ta sami bakin gyale da bakin
takalmi ta saka. Sai dai kash! Ta juya ta
sake juyawa ta dubi jikinta sosai, sai taji ba
zata iya fita a haka ba. Ta san shi kansa dr
shuraim din ma ba burge shi zatayi ba. Don
haka ta ajiye gyalenta ta dauko bakin
hijabinta sabo dal ta siya kwanan nan naira
dubu daya irin wanda ake siyarwa a dinke
mai hannaye kamar riga. Ya shiga da
takalminta mai dan tsini. Ta kullo kofar
dakunan bayan ta debowa yara kayan
makarantar islamita da flaski din abincinsu
ta mika dakin uwani taroke ta arziki idan
yaran sun dawo ta basu abincin su ci su
sauya kaya idan lokacin islamiya yayi su tafi.
Tace itama ba dadewa zatayi ba, zata kai
wa marar lafiya abinci a sibiti. Uwani ta
amsa mata cike da fara'a gami da alkwarin
zata aiwatar da abin da ta umurce ta, ta
hada ta yiwa marar lafiyar adduar samun
sauki. Aisha ta dauki kwandon da ta saka
flask din abinci da plates da cokula, bayan
yaji dakakke a 'yar roba, da 'yar robar
mangyada. Tana tafe cikin nutsuwa har ta
fito daga lokonsu ta sami adaidaita sahu
nan da nan ta haye. Ita kanta tasan tayi
kyau, ko ba a fada mata. Jama' da dama
sun dasa don samari suna ta binta sun kai
su uku sunayi mata magana. Suna sonta
bata kula su ba. Kuyi hakuri an riga an bada
ni. Amsar da take ba su kenan.
Tana isa cikin asibitin malam ta doshi
ofishin dr lukman, sai taji kirjin ta ya fara
dukan uku uku, don fargabar abinda zata
tarar daga dr shuraim. Tana hawa kan
barandar ofishin sai ta hango dr shuraim da
wasu dattijai maza su uku sun tunkaro ta,
ma'an suna fitowa ita kuma tana shiga. Sai
taji wani mummunan faduwar gaba. Ya
tsura mata ido sosai yana kallonta, har sai
ta taji kunya ta sunkuyar da idanuwanta
kasa. Suka wuce ita ma ta wuce, ta juyo a
hankali zata dube shi, shima ya juyo sai
gaba dayansu suka gaggauta juyawa da
sauri. Ta shiga fargaba saboda ta dimauce,
bata gaishe shi ba, kuma ya kamata ta
gaishe shi din. Don haka ne ma yake ta
kallonta har da waiwaye. Abin da zuciyarta
ke zayyano mata kenan. Jikinta a sanyaye
ta shiga ofishin dr lukman, taci sa'a yana
nan shi da abokinsa dr mohd. Bayan ta
gaishe su, sai ta ajiye kwandon abinci a
gaban dr lukman. Tace ga danwake nayi
muku. Yayi farin ciki, yayi godiya sosai. Dr
mohd ta dubi dr lukman yace lukman zaka
bani 'yar kanwar nan taka kuwa? Ina sonta
tun ranar da na fara ganinta. Kirjin aisha
farida ne ya burededen dukan uku uku har
ta fara dana sanin zuwanta nan a yau. Ana
wata sai ga wata, yanzu idan dr shuraim
yaji ko da wasa dr mohd ya furta yana
sonta, ai bar masa zaiyi ba zai kara nuna
alamar so ba. Ta tsunduma cikin wannan
dogon tunani, sai da dr lukman ya ambaci
sunanta ta dawo da hankalinta gare su.
Yace kanwata kinji wai in bashi ke? Tayi
murmushin karfin hali tayi shiru. Dr mohd
yaci gaba da kallonta, kallo mai cike da so
da kauna. Ta sunkuyar da kanta kasa, tana
mai tsananin jin kunya hade da bacin rai. Dr
lukman yayi dariya ya daki kafadarsa yace
kai da kake min tsiya wai ba kanwata bace,
bamuyi kama ba, sai inga wanda zai baka
'yar. Dr mohd yayi dariya yace yi hakuri
don Allah, yaya na daina. Yana rufe bakinsa
sai dr shuraim ya shigo. Nan da na hankalin
aisha farida ya sake tashi. Ta fara addua
kada Allah Ya sa acigaba da zancen soyayyar
nan. Tayi sauri ta sulalo daga kan kujera ta
gaishe shi. Ya amsa cike da far'a, sannan
yaci gaba da kallonta. Can yace lukman
dama kanwarka ce na hadu da ita a baranda
nake mata kallon sani, amma ban gane ta
ba. Naga ta sauya. Aisha farida ta dube shi
a kunyace ta sunkuyar da kai. Dr lukman
yace me ka ga tayi? Ta sake yin kyau ko? Ai
an gama makaranta ana hutawa a gida. Dr
mohd yace kai fa lukman yaya ne ka bari in
fadi da bakina mana, sai kace tayi kyau, kai
yayan kwabo ne ko? Su biyu suka tuntsire
da dariya yayin da dr shuraim ya tsaya cak!
Ya dubi dr mohd ya juya ya dubi dr lukman
ya juyo ya dubi aisha farida nan da nan taji
zuciyarta na dukan uku uku. Daga dukkan
alamu dr lukman ma baiji dadi da dr mohd
ya fadi haka a gaban dr shuraim ba, domin
yana kyautata zaton dr shuraim yana son
aisha farida, furatwa ne kawai baiyi ba.
Dr shuraim ya gaggauta daukar ajiyarsa a
loka ya fice da sauri. Aisha farida ta kame a
zaune, yayin da numfashinta yake kokarin
daukewa gaba daya, babu wanda yake
magana a tsakanin su biyun, dr mohd ne
kadai yake surutunsa. Haushi da tsanarsa
suka bayyana a fuskar aisha farida. Ta
dauke shi a matsayin tamkar mutumin da
ya dauko wuka mai kaifi ya dubi cikinta ya
burma mata, ma'ana ya kashe ta. Domin ya
rugurguza mata walwalar rayuwarta duniya
da lahira. Dr mohd yayi ajiyar zuciya, ya
dubi aisha farida yace bani lambar wayarki
aisha umar. Ta dago da sauri ta dube shi,
duba na takaici ba tare da ta iya furta
kalma gida daya ba. Dr lukman yayi sauri
yace ita zaka tambaya ko ni yayanta zaka
tambaya na ba izini ka karba? Ita ma na
umurce ta ta baka? Tayi murmushin karfin
hali ta mike tsaye a sanyaye ta yi musu
sallama zata tafi. Dr mohd ya nemi ta kara
zama suyi hira, tace gidan babu kowa sai ita
kadai, don haka take so ta koma da wuri.
Dr lukman ya ciro naira dubu daya ya mika
mata, yace tayi kudin mota. Tace ya bari ba
zata karba ba, tana kudin motarta. Dr
mohd ya zabura yace ka bari kawai zan
bata ko kuma ma marasa lafiyan da suke
jirana suyi hakuri sai na kai matata gida
sannan zandawo. Dr lukman yace wannan
kyautata ce ta daban a matsayin na
yayanta, kai da ita kuma daban. Kuma
wallahi sai kin karba kinji ma na rantse.
Aisha farida ta saka hannu biyu ta karba
gami da yin godiya, cikin sassanyiyar
murya. Dr mohd yace Allah sarki, kaji
yarinya mai ladabi, gaskiya nifa da gaske
nake. Lukman zanje in kai ta gida in dawo
muyi maganar gaskiya ba wasa nake ba.
Tayi wuf! Ta fice da sauri don bata so ya
biyo ta, shima ya fita da sauri ya biyo
bayanta ta, ya umurce ta ta jira shi su tafi
tare. Wani babban tashin hankalin kuma sai
ya tura kofar ofishin dr shuraim ya leka sai
ga dr shuraim a zaune a kan kujerarsa yana
danna laptop. Ya dagi da kyawawan
idanuwansa ya dubi dr moh sannan ya sake
daga ido ya hango aisha farida a gefensa.
Sai ya sunkuyar da kai, yaci gaba da danne
dannensa. Amma daga kallon fuskarsa
kasan zuciyarsa a bace take. Dr mohd yace
abokina zo muyi rakiya, wancan dan iskan
lukman yaki yace shi a dole babban yaya
ne. Ya girgiza kai yace nima yaya ne, ba
zanje ba. Kaje sai ka dawo. Aisha farida tayi
wuf! Ta bar wajen, tafiya take ba tare da
tasan inda take jefa kafarta ba. Kawai wani
lungu ta samu ta dinga kutswa cikin asibitin
maimakon ta nufi bakin gate sai tayi ciki.
Kafin dr mohd ya waiwayo sai yaga wayam!
Bata nan. Ya fito da sauri ya dudduba
hanyar gate ba ta nan. Ya duba kudu da
arewa, babu ita babu dalilinta. Sai ya cika
da mamaki, ya shiga kokonto da wasi wasi
don haka ya koma ciki da sauri don ya
shaidawa yaya lukman. Dr lukman yayi
dariya yace kunyarka takeji, kuma tana da
tarbiya bata so a ganta da namiji , ni nasan
halin kanwata. Dr mohd ya takura sai an
kitay a waya yaji inda take. Aisha farida ta
isa ofishin matron maryam ta iske bata nan,
sai sababbin dalibai da aka turo daga
makarantarsu. Yawancinsu ma duk sun
santa. Bayan sun gaisa ta tambaye su
matron sai suka ce ta fita. Aisha ta jawo
kujera ta zauna tana huci, nan da na suka
hau tambayarta bata da lafiya ne? Tace
gajiya ce kawai, tana so ta huta sannan ta
tafi. Bata rufe bakinta ba sai wayarta ta dau
kara. Ta bude 'yar karamar jakar da ta saka
kudin motarta da wayar ta zaro wayar,
sunan dr lukman ne ya bayyana. Sai taki
amsawa har ta katse. Tana katsewa ya sake
kira, don haka ta tabbatar kiran yana da
amfani, sai ta amsa. Tambayar da ya fara
mata itace kina ina? Tayi inda inda sannan
tace ina cikin adaidaita sahu hanyar
komawa gida. Yace toh shikenan. Allah Ya
kaiki gida lafiya. Ya kashe wayar tana jiyo
muryar dr mohd amma bata gane abin da
yake cewa ba. Anan zan dakata mu hadu a
DUK KYAN TAKALMI 3 kuji yadda zata
kasance. Daga 'yar uwarku JUT.
See Translation
January 10, 2015 at 7:26pm · Public
35
DUK KYAN TAKALMI 3* 1
Tayi ajiyar zuciya mai karfi.sannan ta
kwantar da kanta akan teburin da yake
gabanta don ta rasa abun da yake yimata
dadi innalillahi wa inna ilahi raji`un,ta ke ta
ambato,sai da ta dauki tsawon mintina 20
bata iya dago waba,ta mike tsaye da kyar
yayin da idanuwanta suka yi ja,alhalin kuma
ita ba kuka takeyi ba daliban dai har yanxu
tambayarta sukeyi,anya kuwa lafia? tace
lafia kalau kawai dai gajiya ce. Tayi musu
sallama tabar musu sako su gaishe da
metron maryam sannan ta tafi,ta cikin
lunguna ta kurkurda ta fito gate,tana fitowa
taci sa`a ta sami A dai- daita sahu babu
kowa a ciki,don haka tayi wuf ta shigo
batare da ta fada masa inda zai kai ta ba
balle suyi cinikin kudin da zai karba,tana
shiga ta zauna tana daga kanta, sukayi ido
hudu da dr shuraim cikin tsaleliyar motarsa
discussion continues,shi ma kallonta yake yi
alokacin da yake kokarin tsallakawa titi,ta
sunkuyar da kanta da sauri,yayin da
shikuma ya tsaya cak yana kallonta,daga
dukkan alamu yana mamaki da ya ganta
yanxu,mai adaidaita sahu yaja ya tafi yayin
da aisha farida ta rike kai,saboda nauyin da
taji kan yanayi mata sai da mai adaidaita
sahu yayi da gaske sannan ta bashi amsa, ta
fada masa inda zai kaita tana shiga gida
sallan azahar kawai tayi ta shiga lungun ta
kwanta ba tare da ta san a duniyar da take
ba,taji dadi da ganin yara a zaune a dakin
uwani,sunci abinci suna hutawa,don haka
tace suyi zamansu a nan zatayi aiki idan
lokacin makarantar islamiyya yayi su
tafi,saboda kawai bata son damu da
magana cikin wanan hali da ta riski kanta
Allah sarki soyayya ruwan zuma tayini tana
duban numbr dr shuraim,sai taga kamar shi
take gani,koda yaushe kunnenta da
idanuwanta ta suna yi mata gizau,taga
kaman shine yake kiranta da zaran an
kirata,idan taga bashi bane sai ranta ya baci
tana so takirashi amma tana tsoro kada ya
wulakantata kuma bata ma san abun da
zata ce masa ba idan takira din. washegari
ta tashi acikin bacin rai kaman yanda ta yini
a jiya ta yankewa kanta shawarar gara ta
hada ta kaura shagamu kawai tayi
rayuwarta acan ,idan sakamakonsu na exm
ya fito ta karbi takardunta taje can ta nemi
aiki a asibitin garinsu shi yafi mata
sauki,saboda son dr ya zamar mata annoba
musamman idan tana ganinsa. wayarta tayi
kara alokacin da take wanke-wanke ta arto
da gudu ta dauka tana addu`a Allah ya sa
dr ne,sai taga wata bakuwar no ce,ta yi
sauri ta danna,muryar wani kamillan
mutum taji ya ambaci sunanta,aisha umar
ce ko? ta amsa eh,nice" yace dr mohd ke
magana!
Ta sulale ta zauna,yayin da takaici ya
lullube xuciyarta,ta gaishehsi taja bakinta
tayi shiru tana sauraronsa,yace sai kika
gudu kuma ko tsorona kike ji? ta kame a
zaune,domin tana jiyo muryar dr lukman da
dr shuraim a gefensa,hankalinta ya tashi
har abada sai hawaye ya surnano daga
idanuwanta bata iya bashi amsa ba,yace ki
kwatanta min gidanku zan zo,tayi shiru can
tace ai zan shigo asibitin gobe zan karbi
kwanukan da na kawo muku,yace kash
gobe ai bana gari sai dai ki zo jibi tana jiyo
muryar dr lukman yana cewa to ka fasa
tafiyar mana idan da gaske kake yin son? dr
shuraim kuwa bai sake furta komai ba yana
gefe guda yana kallonsu,tayi sauri ta katse
wayar ta rushe da kuka,tayi sauri takira
wayar shagamu gidansu abida,lambar
mamarta,bugu daya ta dauka ta gaisheta,ta
shaida mata aisha farida ce daga
kano,kasancewarta tsohuwa ba iya karanta
suna tayi ba. Goggo tace ai na gane
muryarki yar baba,kamar yadda wasu suke
kiranta da haka,ina anti abida,ya jikin nata?
goggo ta amsa,mungode Allah,amma dai
jikin abida to sai yadda Allah yayi,gata nan
yanzun nan tace a tashe ta zaune ta gaji da
kwanciya,aisha farida ta fashe da
kuka,goggo ma ta fashe da kuka,aisha tace
a bawa abida wayar,goggo tace sai dai in
kara mata wayan a kunne,bata iya daga
hannunta, bazata iya rike wayar ba. Muryar
abida ce ke karkawa tace farida maiyasa
kike kuka? zan samu lafiya da izinin
Ubangiji. Aisha ta matse hawaye tace, anti
abida so nake ayi wa yara hutu na taho
shagamu na dinga ganinki bana jin dadin
gidan nan
Bana jin dadin kanon, duniyar ma gaba daya
ta isheni,Allah ya baki lafia. Hawaye ya
surnano da idon abida, tace bana so ki
kaura shagamu,har sai kin cika burinki akan
dr, Farida ta fashe da kuka tace anti bana
jin zan cika wannan burin nawa,domin
yanxu wani abokinsa ne yake sona,mai suna
dr mohd kuma har dr shuraim din ya
sani,nasan zai hakura ya bar wa dr mohd ni
kuma bana son dr mohd din,shuraim nake
so. Yanxu haka suna tare,kuma agaban dr
din yayi min waya,abida ta cije baki saboda
tsananin ciwon da yake addabarta,tace
kada ki damu duk irin abunda zai faru ki
zubawa sarauta Allah ido,ki gode masa kici
gaba da addu`a,kanwata duk irin wannan
wata hikimar Allah ce wacce ba ki sani ba,ki
ci gaba da nemawa zuciyarki abun da take
so har sai kin cika burinki,ina yimiki fatan
alheri. Farida ta katse wayar ta rusa kuka
ita kadai a daki ta fada a bayyane,wayyoh
abidata wayyoh shuraim,inna lillahi wa inna
ilaihi raji`un, Allah ka taimake ni ka cikamin
burina,ka karbi adduoina guda biyu,kaba wa
abida lafia ka bani dr. Tayi kuka tayi addua
har muryarta ta ddisashe,yau ma dai yara
sun sha wahala har karfe 2 basu ci abincin
rana ba,don bata iya dorawa da wuri ba.
kuyi hakuri ku yafemun yara ni kadai nasan
halin da nake ciki inji farida lokacin d take
cuu-cukun xuba musu abinci bayan da ta
tabbatar sun galabaita. Faruk ya dubeta
yace anti aisha meyasa kullun kike kuka? ko
mamarmu ta mutu ne? Hawaye ya surnano
da idonta tayi saurin ta dukar da kanta
kkasa don kada ya gane kukan zata sakeyi
ta girgiza kai tace mamanku bata mutuba ta
samu sauki,na muku alkawari ranan asabar
zansaka kati a wayata inkiramuku ita daya
bayan daya kuyi magana da ita zakuji
muryarta radau taji sauki sosai. sai taga sun
hada ido sunhadu sunyi daria suka hau
murna bayan tabasu abinci sunaci a tsakar
gida tashiga daki tarufe tashige lungu
tadinga kuka tana addua ya Allah kana sane
da halin danake ciki kasa abida ta warke
nasani baka barin wani dan wani yaji dadi
Allah ka duba kananan yaranta har hudu ka
tashi kafadunta,suna tanbayata mamarsu
yaya zance musu idan tarasu Allah kada
kabarsu sutashi a marayu kaman ni,Allah
kabani mijin danake so dr, insan dadin aure
dan idan na auri wani bashiba farin cikina
ragaggenai. Ya Allah kafini sanin abunda
yafi Alkhairi a rayuwata Allah nagode maka
kaciga da taimakona da kai kade na dogara,
adduoin da Aisha farida keta zubawa kenan
a wannan yinin,bata iya fitowo tayi hira da
yan gidan ba,har sai da ta tabbatar
magruba ta karato yaya husaini ya kusa
dawowa sannan ta fito,ta fara cukuncukun
dora abincin dare. Washegari jummaa ta
shirya da wuri ta fita,karfe tara a cikin
asibiti tayi mata,kasancewar juma`a ce don
kada a rufe hanya,ta isa ofishin dr.lukman
sai taji a kulle wata kila bai iso ba,tunda bai
isoba tasan dr shuraim bai karaso ba.
Amma dai taja jikinta ofishin ta tsaya,ta
karanta sunansa ta sake karantawa sai taji
sanyi a ranta,ko sunansa ta gani a rubuce
dadi takeji ,ta lumshe ido,tasa hannu a
hankali ta rike hannun kofar,sai taji tamkar
ta shafi hannunsa ta san tabbas ya taba da
hannunsa,ta murda da wasa don tana da
tabbacin a kulle take,bai karasoba kwatsam
sai taga kofa a bude har ma ta wangale sai
ga dr radau a zaune akan kujera suna hada
ido taji tamkar ta zura da gudu don fargaba,
tayi wuki-wuki da ido tana kallonsa cike da
mamaki yayin da shima haka har tsawon
lokaci suna kallon juna. Shigo mana inji shi,
ta fara tafiya a hankali kanta a sunkuye a
kasa cike da kunya,sai yanxu ta dubi kayan
da ta sako a jikinta,birkideden hijabi ne har
kasa yana jan kasa,shi ma mai hannu ne
kaman riga ake sakashi,maroon color sai ta
saka takalmi shima kalar hijabin mai dan
tsini,yayin da fuskarta bayan hoda bata kara
komai ba,babu kwalli balle jagira,don bata
saka ran zata hadu da shi ba.niyyarta tazo
ta kwashi kwanunkanta tayi wa asibitin
sallama daman tasan dr mohd baya nan yau
shi yasa ta garzayo dan bata son su hadu.
Sai kallonta yake tundaga sama har
kasa,har saida ta karaso gabansa ta durkusa
har kasa ta gaishe shi yace tashi tashi ki
hau kujera ki zauna, ta tashi a hankali ta
zauna kan kujerar har yanxu kanta a
sunkuye yake a kasa,har zuwa lokaci mai
tsawo batayi maganaba shima haka danne
dannensa kawai yakeyi a laptop.
Can ta dago ta dube shi sai taga ya dago da
sauri ya dube ta,tayi murmushi tace yaya
lukman be karaso bane?? naje ofc dinshi a
kulle,ya gyada kai kawai bai yi magana ba
sai taji hankalinta ya tashi,ta tabbatar yana
jin haushinta ta yunkura ta mike tace,bari
in jirashi a waje ya girgiza kai ba tare da ya
kalleta ba,yace ba damuwa ki zauna a nan
har yazo,ta koma ta zauna yayin da taji dan
sanyi a ranta,taci gaba da sunkayar da kai,
idan ya dago ya dubeta sau daya, sai yaci
gaba da kallon laptop dinsa. Kamar daga
sama taji ya ambaci sunan ta,ta dago da
luhu-luhun idonta ta dubeshi ta amsa cikin
nutsuwa. Ya tsaya cak da abunda yakeyi
yace lafiyarki kalau,ko akwai abunda yake
damunki ne? tayi murmushin karfin hali mai
kayatarwa,tace lafiata kalau dr. Yace bawan
da yataba gayamiki kin rame kwanan nan?
ta sake murmushi ba tare da tasan amsan
da zata bashi ba, yace don wa kike dafa
abincin nan da kike kawowa? Shi kansa
yasan ta firgita da jin wannan
tambaya,domin ta dago da sauri ta dubeshi
ta tabbatar yau wulakancinsa yau ya motso
kanta ,taji hankalinta ya tashi,sai kwalla
tacika mata ido,ya sake maimaita
tambayarsa, hakika amsa yake bukata kuma
ya xuba mata ido,ta runtse ido tayi shiru.
Can ta dago ta dubeshi tace saboda kai da
dr lukman nake kawowa. Yayi daria yace
harda ni ba saboda lukman kawai ba? to
mun gode kuma munji dadin abincki sai dai
ina rokonki ki daina wahala da mu,kada ki
kara kawowa. Kallo na rashin fahimta take
yimasa,har sai da ya gane haka. Yayi ajiyar
xucia yace bana so naga mace na
wahala,macen ma mai suna mai daraja irin
naki AISHA FARIDA. Sai taji dadi ya rufeta
tasa hannu ta sosa goshinta saboda
kunya,tayi murmushi tace dr ba damuwa ni
ba ya damuna,in har zaku ci,ya girgiza kai
yace kiji maganata,ki daina kawowa in
muna so zamuyi miki waya ki kwatanta
mana gidan mu zo mu dauka,ba sai kinxo
ba kinji ko? nan da nan ta amsa da to,in
sha Allah zanyi amfani da abunda kafada.
Yace yawwa na gode yaya mai jiki,ta
langwaba da kai,tace tana can shagamu
tana fama har yanxu bana jin tana samun
sauki, sai ta fara kwalla. Ya tsaya cak ya
daina abinda yake,yana dubanta yace ban
taba ganin randa zan ganki ba kya kuka
ba,farida waya gaya miki ke kadai kike da
matsala a duniya,mu me yasa bama kuka
kullum? Waye ya shagwabaki kike yawan
kuka? tasa hannu ta matse hawaye,tayi dan
murmushi tace ba kowa....yace kidena
kuka ni kukan yaro ma bana so balle babba
kuma mace,baki san duk sanda naga
hawaye a idonki ba ,idan kika tafi damuna
yake a xucia ba? to ni haka nake a
rayuwata,matsalar wani matsala tace,ki
fadamun ko akwai abinda yake damunki a
rai,sai in baki shawara nima abokin lukman
ne.
Tayi dariya ta girgiza kai tace babu komai
idan ma akwai ina fadawa Allah ya kawo
mun sauki. Yace wannan yayi kyau ko meye
damuwarki ki fadawa Allah. Kuka da saka
damuwa a rai matsala zaki jawowa lfyrki,mu
likitoci bama son haka. Musamman
bangaren yayanki lukman kwakwalwa suna
hana mu2m yawan 2nani da damuwa. Ki
kiyaye kina karamarki zaki cuci rayuwarki a
banza. Ta gyada kai tace naji likita ngd.
Yace shigarki tayi min kyau ta burgeni. Sai
taji tmkr ba shi yake magana ba. Ta kalle
shi ya kalleta, shima ya gane ta shiga
mamaki. Sai yai murmushiyace,kina burge
ni fa, i lyk ur style. Dgwar ajiyar zuciya yaji
taja, har yanzu kallonsa takeyi kawai. Yace
zaki jira ni in tashi daga aiki na mayar dake
gida? Wannan karon ma sake zaro ido tayi
ta dube shi cike da mamaki. Yayi dry yace,
ba kya bani amsa fa, me yasa kike
mamamki ne? Tayi mrmshin krfn hali tace,
to. Yace ki jirani a nan ofishin bayan sallar
juma'a sai na dauke ki a motata mu
fita,idan na kaiki gidana kika gani muka dan
huta bayan magruba sai muje in mayar
dake gidanku nima naga gdnku. Ko ban zo
ba ke saiki zo gidana 2nda ni kadai ne a
gdn kema kuma antinki bata nan, babu
wanda zaisa miki ido. Yau dr. Lk ba zai xo
ba,tare suka yi tafiya da dr. Mohd saini
kadai kinga sai kiyi zamanki a ofishina ki jira
har bayan sallar juma'a ko? Kuma dk
abunda zai faru a tsakaninmu bana si ki bari
wani ya sani har lk sirri ne. Ta zazzare ido
tana dubansa,taga shi ko a jikinsa
maganarsa yakeyi kansa a tsaye. Sai taji a
ranta ta tsani kanta, kuma t tsani
rayuwarta. Ashe dan iska ne bata sani
ba,har take yabonsa? Sai taji gaba daya ya
sure mata taji daman bata sanshi ba,bata
taba ganinsa a raywrta ba. Ya dubeta duba
na kurilla yayi mrmushi ya daga mata gira
yace,baby kin amince dani? Zan kawo miki
canji a rayuwa. Soyayya da jindadi ga dukiya
mai yawa. Dn Allah ya dora min sonki a lkc
guda kece baki sani ba,kina da kyau,gaki da
diri,kinfi sauran mata. Taji tmkr ya caka
mata wuka a kahin zuciya ta fada a
zuciyarta, innalillahi wa'inna ilaihir rahi'un!
Dr shuraim me yasa halinka ya zama haka?
Wayyo Allah na dama ace yadda kake da
kyau kanada kyawun halyya a boye kmr
yadda a zahiri kake kamilalle mai rukon
addini
Ya katse 2naninta yace, bari inje clinic ona
da patient zan bar miki ofishin ki bude firij
akwai fruits da juices kisha wanda kike so.
Ya dauki laptop dinsa ya fice yayin da ta
bishi da kallo harya fita. Ta dafe kirji ta
zabura ta mike tsaye sai taji jiri ya kwasheta
ta koma ta zauna ta rushe da kuka. Ta fada
a bayyane, Allah ka fini sanin dalilin daya sa
na tsinci kaina a cikin irin wannan rayuwa.
Ina abida? Abida ko zo kiji halin da nake
ciki. Tayi kuka ta gaji,ta dubi ko ina a cikin
ofishin babu abnda take hangowa a cikin
lokokinsa daga manyan littafan likitoci dai
kur'anai izifi sittin-sittin. Ta daga ido ta
dubi bango taga gaba daya firem ne a
rubuce da sunan Allah da manzonsa. Ta
dubi kasa sallayar sallarsa a lungu da carbi
dan yayi sallah yake ja. Sai taji ranta ya
sake baci,ta fada a ranta. Dr shuraim ya
zama babban munafuki a addini a fili yana
nunawa shina Allah ne,fasikancu ne kuma a
boye. To ashe duk 'yan matan nan da yake
wulakantawa dk sai daya gama lalata su
tukunnan sannan ya koresu? Ka cuci kanka,
ka cuci kyakkyawar hallitarka. Allah ka yaye
min son fasikin mu2m a rayuwata. Ta sake
rushewa da kuka,tayi zumbur ta mike ta
bude kofar ta leko taga bayanan, sai ta fito
ta jawo kfr ta rufo. Tana tafe tana waiwaye
waiwaye. Abin mamaki sai taga ofishin dr lk
a bude har wani dalibi ya kwankwasa ya
tura kfr ya shiga. Ta sake tabbatarwa dr S
makaryaci ne,makiri,azzalumi,yayi niyyar
cutarta. Tayi kmr ta shiga ofishin ta dibi
kwanukanta, in yaso tayi sallama dasu har
abada. Sbd abokin fasiki shima in ba a yi
sa'a ba fasikin ne. Sai taji ranta kawai har
kwanukan bata so,suje su rike. Tayi wuf! Ta
fice da sauri tfy take ko waiwaye bata yi
burinta kawai ta ganta a cikin adaidaita
sahu.
UK KYAN TAKALMI 3* 2
Tazo fita ta get kenan sai taji wayarta ta
dau
ruri tayi sauri ta dauko 'yar jakarta,ta duba
sai taga sunan dr. Lk ta danna a sanyaye sai
yace, Aisha Farida kina inane? Ta dafe kirji
tayi shiru can tace ina gida. Yace ashe bake
bace wata na gani a cikin asibiti kmr ke sak!
Ta gifta. Sai ya katse wayar, ta tsaya cak!
Ta
dubi hanyr ofishinsa ta dubi hnyr waje.
Yayin data dinga shawarwarin inda zataje.
Taji kmr ta koma ofishinsa ta shaida masa
abun da abokinsa yayi mata,sai taga meye
amfanin shaida masa din? Watakila ma
bakinsu 1. Dn haka tayi tfyrta. Tana cikin a
dai daita sahu tana sharbar hawaye ta
sauka
a unguwarsu ta gangara gida, dk wanda ya
hadu da ita a hnya saiya tmbyeta farida lfy?
Tace bani da lfy. Sbd sunga kuka takeyi
haikan, kuma tfy take kmr zata fadi. Ta
kunshe fuska a cikin hijab, ta shiga gida dn
bata son mutanen gida su gane tana kuka.
Ta bude daki ta shiga sai ta yaye hijabin ta
urgar ta dora kannu aka ta rusa kuka mai
sauti. Tayi sauri tasa hannu ta kunshe
bakinta, dn kada 'yan gidan su jiyota. Ta
drkushe kasa tana fadin, Allah ngd maka
daka bayyana min waye dr.S 2nda wuri.
Allah ka yaye min sonsa, ka masanya min
da wanda yafi shi alkhairi. Ashe abida tayi
gsky data ce in rike addu'a, Allah shi yasan
dai-dai idan bawa yana son abu yaga Allah
bai bashi ba. Bai sani ba ko abun ba
alkhairi
bane a gareshi. Na rasa Dr S,na rasa ka har
abda, na hakura da kai. Bana sonka, bana
marmarin in sake haduwa dakai a
rayuwata. Ta jawo wayarta ta nemo sunan
goggon mahaifiyar abida,dk da tasan halin
da abida ke ciki,amma babu yadda zatayi
ne, dole ita din zata fadawa don in bata
fada ba zuciyarta zata iya fashewa a yau.
Ina anti abida? AF ta tmbyi goggo ko
gaisuwa babu. Lfy? Ta tmbya cike da
damuwa. Jikinta zan tmbya,kuma ina so a
bata waya mu gaisa. Inji AF. Goggo tace
bana so kuna maganr nan, dn kuka naga
tanayi, ban san me kike fada mata ba.
Marar lfy baya son damuwa fa farida. Ta
jiyo muryar abida tana cewa, googgo ki
kawo min wayar, bakiu san abn da zata
fada min ba. Farida bata da kowa a duniya
saini. Idan da sauran nmfashi na a duniya
ban mu2 ba,ai zan saurari matsalolinta.
Goggo taje ta karawa abida waya a kunne.
Abida ta ambaci sunanta sai AF ta rushe da
kuka. Tace anti ashe Dr.S dan iska ne? Wai
zai kaini gdnsa mu huta. Abida tayi dariya
tace,kada ki yanke hukunci,kibi a hnkl. Ba
gsky bane, kici gaba da addu'a kanwata.
Takaici ya sake bullowa daga cikinzuciyar
AF
da taji amsar abida, saita katse wayar.
Karar shigowar sako ne ya shigo wayarta.
Ta
duba da sauri sunan Dr.Lk ne nan da nan ta
cika da mamaki. Tana kokarin budewa ta
karanta sai wani sakon ya shigo. Ta duba
taga sunan Dr.S ne,ta gyara zama ta mike
kafa yayinda hawaye ya hadu da gumi suka
damalmale mata fuska, ta dora hannu aka
ta fasa kuka. Taji hnklnta ya tshi dn bai
kamata ta zama haka ba a wajensu dr.lk
ba,
abn arzikin data keyi musu bai dace su
saka
mata da tsiya ba. Me tayi musu a rayuwa
da zasu hada aki su cuce ta. Ashe son da
Dr. Mohd yace yana yi mata dk tsokana
ce,yaudarata sukeyi kenan? Zuciyarta tana
duka 3 3 a lkcn da zata bude sakonnin dn
fargabar abnda zata karanta. Sai
idanuwanta sikayi dusu dusu har bata gani
sosai sbd tsananin kuka. Ta bude na frko ta
karanta,sai ta dafe krji yayin da ta bude na
2 ta karanta,sai ta damko wuyanta dan
mamaki,kuma sakonnin iri daya ne babu ko
digo daya daya bambanta. Ta zabura ta
mike tsaye ta sake karanta dukka 2n hakika
abn data gani dazu shine ba gizo
idanuwanta keyi ba,gsky ne.
Kin ci jarabawa Aisha Umar,fito muna kofar
gidanku". Abinda Allah ya nuna mata kenan
a cikin wayarta(kunji ta fa sai kace wani
wahayi wai Allah ya nuna mata lols) sako
daga Dr.S da Dr.Lk,dukka abu daya suka
rubuta mata. Ta cika da mamaki sai tayi
sauri ta jawo wani tsohon zaninta ta
fafface
ta goggoge fuskrta tayi wasai,sannan ta
goggoga 'yar hoda ta sake saka hijabnta.
Hannunta sai karkarwa yake ta sala
takalminta ta fito a nutse tana sanda. Bata
tabbatar da abunda suka rubuto mata ba
ko gske ne,amma dao gara taje ta duba. Da
fitarta Dr. S I ta fara hangowa tayi sauri ta
sake duban na kusa dashi, Dr. Lk ne,sai
taga sun dubi junansu sun kyalkyale da
dariya. Ta snkyr da kanta kasa ta karaso
gabansu ta durkusa ta gaishe su. Dr. Lk
yace,srkn kuka, kin daina kukan ne? Dr.S
yace,farida kin bar min ofishina a bude har
an yashe ni. Tay ajiyar zuciya,ta grgza kai
ba tareda tasan abnda zata fada ba.
"Kin ci jarabawa Aisha Umar,fito muna
kofar
gidanku". Abinda Allah ya nuna mata kenan
a cikin wayarta(kunji ta fa sai kace wani
wahayi wai Allah ya nuna mata lols) sako
daga Dr.S da Dr.Lk,dukka abu daya suka
rubuta mata. Ta cika da mamaki sai tayi
sauri ta jawo wani tsohon zaninta ta
fafface
ta goggoge fuskrta tayi wasai,sannan ta
goggoga 'yar hoda ta sake saka hijabnta.
Hannunta sai karkarwa yake ta sala
takalminta ta fito a nutse tana sanda. Bata
tabbatar da abunda suka rubuto mata ba
ko gske ne,amma dao gara taje ta duba. Da
fitarta Dr. S I ta fara hangowa tayi sauri ta
sake duban na kusa dashi, Dr. Lk ne,sai
taga sun dubi junansu sun kyalkyale da
dariya. Ta snkyr da kanta kasa ta karaso
gabansu ta durkusa ta gaishe su. Dr. Lk
yace,srkn kuka, kin daina kukan ne? Dr.S
yace,farida kin bar min ofishina a bude har
an yashe ni. Tay ajiyar zuciya,ta grgza kai
ba tareda tasan abnda zata fada ba.
"kinsi jarabawa farida". Inji dr.S. Dr.Lk
kuma yace wlhy abokina gwadaki yayi
muna
zazzaune a cikin motata a lkcn da kika fito
kika nufi get shiyasa nayi miki wannan
wayar. Niyyarmu mu dauko ki mu dawo
dake gida,sai yace gara mu biyo ki a baya
muga gidanku. Ta sake yin dgwr ajiyar
zuciya ta dago da sauri ta dubi Dr.S sai yayi
mata mrmshi ma kayatarwa. Taji sanyi a
cikin zuciyarta,farin ciki marar misaltuwa ya
tabbata a zuciyarta. Ji take tmkr anyi mata
albishir zata shiga aljanna. Dr.S yace yanzu
ke in aka ce miki haka nake zaki yarda? Ina
da kyakkyawan zato a kanki saina ke so in
tabbatar da hakan, dn haka ni da abokina
muka shirya jarabawa muka baki. Allah
cikin
ikonsa sai kika cinye dukka. Mrmshi takeyi
har yanzu,bata ce komai ba, mun baro aiki
da yawa muka taho a yi hkr a gafarce mu
idan munyi laifi da muka shiryo wannan
gwaji,sbd mun saka ki kuka da yawa. Ta
rufe ido tayi dariya tace, bakuyi laifi ba
yayana. Dr.Lk yace,idan akwai yaro yazo ya
biyo mu mota ya karbar miki kwandon ki
mun taho miki dashi. Tace, to bari in shiga
gida in turo yaro ngd sai anjimanku.
Kallonta kawai Dr. S yakeyi harta shige ciki.
Ya grgza kai yace, lk nan ne gidansu da
gaske? Innalillahi wa inna ilaihi raji'un.
Yanzu daman a irin wannan gidan take
rayuwa? Dr Lk yace, da alama kuwa gidan
haya ne basu kadai bane dn ina nan a tsaye
ina ganin mata iri iri suna leko mu. A cike
gidan nan yake, irin hayar nan ta dakuna
birjik,bandaki daya. Yanzu a cikin bakin
gidan nan daman ake dafa mana dambu da
danwake muke ci? Dr.Lk yace, to bakin
gida, bakar tukunya ce? Ai kanwata tana da
tsafta,a tsaftace abincinta. Kai fa a ni'ima
kake shiyasa baka san ana wahala ba a
kasar nan. Dr.S yace, gsky ana wahala aini
ban taba shigowa lungun nan ba 2nda Allah
ya halicce ni. Ai bansan irin wannan gidan
farida take ba, daban zargeta ba don tana
hawa acaba. Alla srki ashe rashi ne yake
sakata hawa acaba.
Bai rufe baki ba saiga wani
dakwalkwalallen
yaro hancinsa fal da majina yace, wai gani
inji Aisha Farida kuna kirana. Dr S ya dubi
yaron ya juya ya dubi Dr.Lk sai suka tun
tsire da dariya. Dr.S ya ce Allah mai
halitta,yaro Allah yasa kayi ilimi ka fita fili
ka rabuda irin wannan rayuwa. Ya kama
hannunsa yace, zo muje abokina,yaya
sunanka? Yaro yace,sunana Dahiru. Dr. S
yana tafe yana sake waiwayawa yana
duban
gidan su Aisha Farida,yana sake kallom
unguwar da kwatoci, baya ga sauro da
kudaje suna ta shawagi. Dr. S ya dorawa
Dahiru kwando aka ya bashi naira #500
suka shiga mota suka tafi. Har suka isa
asibiti Dr. S bai fasa jajantawa wadannan
bayin Allah ba, musamman abar kaunarsa
AF. Yaji ya sake tausaya mata, ya kara
sonta,kuma ya kudiri niyyar taimakonta.
AF ta shiga gida zuciyarta cike da frn
ck,harma ta kasa fasalta irin frn ckn data
tsinci kanta a yau. Tana shiga daki ta cire
hijabi ta dauki waya ta kirasu abida aka ci
sa'a knwrta maimuna ce ta dauka. Byn sun
gaisa sai tace tabwa anti A zasuyi mgna.
Maimuna ta karawa Abida a kunne. Abida
tace AF ya ake ciki? Tayi dry tace, Anti A
ngd wa Allah ngd miki. Yanzu Dr.s yabar kfr
gdn nan shida Dr.lk ashe mgnr nan daya
fada min so yake ya gwasa ni yagani 'yar
iska ce ni? Yace naci jarabawa. Abida tayi
mrmshi tace, naji a jikina Dr.s m2mn kirki
ne, ko byn raina ki zama mai kyakkyawan
zato a kansa. AF taji jiknta yayi sanyi
tace,zaki ji sauki anti,ki daina fdr haka.
Ngd. Abida tayi mrmshi tace, yanzu zaki
wuce mataki na 4 zaki taka mataki na 5
shine ki nuna masa tsantsar soda kulawa.
Idan ya gasgata kina sonsa sbd Allah sima
zai soki a zuciyarsa,yasoki harma ya fara
2nanin yadda zaki kasance a matsayin
matarsa, ku zauna din-din-din. AF taja dgwr
ajiyr zuciya tace, to antina ngd,Allah ya baki
lfy. Abida tace Amin.