Gabatarwa
Duk Kyan Takalmi Part 1 Complete Hausa Novel · about 165 min read
Sunana Aisha farida umar, 'yar asalin jihar
katsina amma zama ya kai kakannina garin
shagamu. Anan aka haifi mahaifi har yayi
aure aurensa ya hayayyafa don haka babu
garin da muka fi sani wanda ya wuce
shagamu. Mahaifiyata ma 'yar garin
shagamu ce. Yanzu shekaruna ashirin da
uku a duniya, na fito daga dangi wadanda
suke talakawa liki. Ilahirin dangina kakaf na
wajen uwa dana wajen uba basu da hali.
Koda yake akwai daidaiku masu rufin asiri
amma ba za a kira su masu arziki ba amma
dai sunfi wasu. Wannan dalili yasa bamu
cika karatu mai zurfi ba wasu daga primary
suke tsayawa, wasu sun shiga scondary
amma talauci sai yasa a cire su basa
karasawa. Masu dan gara gara ne ma suke
kammala secondary amma fa jami'a ta
gagaresu sai dai kallo. Danginmu suna da
dimbin yawa mata da maza, yara da manya
gamu da tsofaffi tukuf tukuf Allah Ya ara
musu tsawon rai. Mahaifina yana daya daga
cikin dattijan domin ya tsufa jagof, tun tashi
na daman a tsohonsa na ganshi har ya
makance saboda tsufa. Shine babba a cikin
'yan gidansu don haka yafi kannensa tsufa
kuma yafi sauran 'yan uwansa talauci
kasancewar yafi su tara mata har guda hudu
da tulin 'ya'ya har guda arba'in da uku.
Nice 'ya ta arba'in da biyu a wajensa,
kanwata guda daya kacal mai suna
munauwara. Mu biyu ne kadai muke uwa
daya uba daya a gidan domin mahifiyarmu
ce amaryarsa, ya aure ta tana kankanuwa
yayin da yake tsohonsa. Sauran matansa
ma duka sun tsufa wasu daga cikin manyan
'ya'yansa sun girme ta suma har sun aurar
da 'ya'yansu suna da jikoki wadanda suka
fini ma. Don haka ban mori dadin uba ba,
sanda na fara wayo baya ganina kasancewar
ya makance.
Aikina shine kullum inzo dakinsa in riko
hannunsa in fito dashi kofar gida sai in
zaunar dashi akan kujerar katakonsa sannan
ni kuma in zauna a gefensa ina sauraron
hirar da sukeyi shida abokansa,
makwabtansa da 'yanuwansa tsofaffi. Ina
jin dadin sauraron tsofaffi labarai masu
al'ajabi na mutanen da. Ina fahimta sosai
kuma ina rikewa a kwakwalwata tas, babu
abinda nake mantawa harma idan suka fadi
wata kalma da ban sani ba sai in tambayesu
su bani amsa. Idan babana ya aike ni dauko
ruwa, fura ,koko ko kuma kurtun tofin
yawunsa a dakinsa sai inji duk raina ya baci
saboda za'a tsallake wani shashi daga cikin
hirar. Sai in zura da gudu don inyi sauri in
dawo kada a wuceni, idan na dawo kuwa na
sa su dole su dawo da labarin baya. Anan
na koyi iya magana mai ma'ana da jan
hankalin mai saurarona da kuma fitar da
lafazai masu girma da hikima tamkar wata
babba. Daga nan na samo suna "Farida
tsiri" inji kawayena haka suke kira na domin
duk wanda na zauna dashi zaiyi tunanin
wayona yayi yawa zan cuce sho ko zanyi
masa dubara ko in yaudare shi. Duk sanda
zanji labarin anyi gulmata bai wuce ace na
cika iyayi ba da dadin zance rai-rai-rai
kamar aku. Ko kuma ace na cika kissa da
kisisina bana fushi ko ma za'ayi min, ga tsiri
ina magana kamar wata tsohuwa wacce
taga jiya taga yau. Ina jin dadin halayena
kuma dashi nake cin ribar zaman duniya.
Zan iya zama da kowanne irin mutum ne
komai bakin halinsa da muguwar zuciyarsa,
duk sharrinsa ko alkhairinsa haka kuma duk
in da ya kai ga masifa da zafin rai zamu
zauna lafiya. Da kowacce irin kabira zan iya
zama lafiya. Da bakar fata da inyamuri,
hausa, babarbare, bafillatani, bayarabe,
ibira ne, tangale ne, mumuye ne, margi ne,
basayi ne, ba'are ne, dan niger ne ko kuwa
adon dawo ne dan bur sudan duk na san
yadda zan tafiyar dasu.
Mahaifina yana da yawan magana ba zai iya
zama shi kadai ba, ba tare da bakinsa yana
motsi ba, sai na gado sho don haka tamu
tazo daya sai mu hadu muyi tayi. Har baya
so in matsa daga gabansa don haka ban
cika zuwa makaranta ba, ko yayyena zasu
korani sai in ruga da gudu dakinsa in labe a
bayansa. Sai yace musu "inga mara kunyar
da zai shigo ya banbare aisha daga bayan,
baza taje makarantar ba nan dakin ma
makaranta ce". Aji ne mai zaman kansa don
darasi take duka na iya rayuwar zaman
duniya. Ku fada min ko a jami'a wanne
darasi ne za'a zaunar da dalibi a karanto
masa rayuwa karara balle dan primary aji
daya? To ku kyale ta ba in da zata je sai ta
ga dama sannan zata je makarantar. Dalilin
zuwanta makaranta don ta koyi rubutu ne
kawai. Idan sukaji yana fada basa karasowa
cikin dakin, su gama labe-labensu ina hango
inuwarsu ta jikin asabari sai inki fita, sai sun
gaji da jirana sannan su tafi. Idan hantsi
yayi sai inje zaure in kinkimo kujerar katako
in kai masa kofar gida, sannan in share
wajen in shimfida tabarmi a kasa wasu
tabarmin in shimfida akan wasu dakali biyu
da suke kofar gida. Sannan in dawo dakinsa
in mika masa sandarsa na riko hannunsa in
fito dashi kofar gida wajen kujerarsa, sai ya
laluba ya zauna sannan in koma gefensa in
zauna sai ya fara bani labari ko tatsuniyoyi.
Sannu a hankali sai 'yan majalisarsa su fara
bulbulowa daga gabas wasu daga yamma
wasu daga barin kudu, wasu daga arewa.
Yawancinsu kannensa ne uwa daya uba
daya, ko uba daya. Wasu kuma kakanni
suka hada, wasu makwabtaka ce ta hada ko
auratayya, wasu kuwa manyan abokansa ne
da akayi kuruciya tare. Babu wanda yake da
kasa da shekaru sittin a wajen. Anan na
samu tarbiyar girmama babba duk
kankantarsa, domin idan na gaishe su daga
tsaye ko daga zaune ba zaus amsa ba ko
kuma inji duka dal a bayana wai nayi rashin
da'a. Sai kaji sun daka mintsawa suce inzo
in durkusa har kasa sannan in gaishe su.
Tun ina jin haushin inyi kuka har na daina,
tun ina mantawa har na saba. Sannan na
koyi durkusawa har kasa idan zan mikawa
babba abu koda kuwa da kadan ya girme ni
kuma da hannu biyu. Sun hana ni mikawa
sa'ana ko yaron dana girma abu a
wulakance ko da hannun hagu. Sun
gargadeni ni da na guji wulakanta dan adam
ko da kuwa almajiri ne domin babu kyau
wulakanci da girman kai.
Anan nakoyi daubarun cin jarabawa a
makarantar boko ko kuma saurin haddace
kur'ani a makarantar allao. Sunce in zamana
mai yawan kallon bakin malamina ina
sauraro, ina ganin yadda yake fitar da
lafazinsa daga hanka, ganda, tantanin
makwallato da kuma dumbarun bakinsa. Yin
haka zai sa in dinga fitar da kalma yadda
ake bukata a fada. Kada in dinga zama a
bayan aji, ko da yaushe kujerata ta zamana
a gaban malam saboda gudun yin wasa da
yara. In zama mai yawan tambayar duk
abin da ban gane ba anan take ba sai an
wuce wajen ba. Sannan in dinga kwafar
rubutu daidai in da ban gane ba ko ban
gani ba in tambayi malam ko wani na kusa
dani wanda nasan yasan abin da yake yi.
Kada in sake in koma gida in yarda jakata
ko allona ba tare da nayi bita ba. Sunce da
zarar naci abinci na huta in samu lungu in
shiga inyi ta tilawa zanji na fahimci abin da
ban gane ba a a aji watakila saboda yunwa
ko gajiya ta hana in gane a lokacin. Suka
shawarce in yawaita yin aikin gidan
(homework) tare da yayyena wadanda suke
ajin gaba dani, kada in sake in dinga yi ni
kadai ba tare da wani ya duba min ba. Duk
abinn nan dana fada min na haddace sai dai
anan nake zubarwa saboda bana kaunar
zuwa makaranta, har gara ma makarantar
allo dan itama a kofar gidanmu take dole
inje.
Idan rana ta bude sai majalisa ta yoye, ni
kuma sai kama hannun tsohona in shiga
dashi daki sannan inje in karbo masa
abincin rana daga wajen matar da take da
girki. Tuwo ne dai na masara ko na dawa,
miyar kuka ce ko danyen karkashi. Shinkafa
sai jifa jifa ake siyowa a dafa ko kuma idan
an samu wani dan albarka cikin yayyena ko
sirkiai su kawo mana a dafe ko danye. Da
yamma sai in sake zuwa inyi shimfida in fito
dashi, 'yan majalisarmu basa tashi basa
manta lokacin sai kagansu daya bayan daya
suna bulbulowa. Duk wannan zance da
nake yi muku ina da shekara hudu ne zuwa
tara, ban cika shekara goma ba a duniya
Allah Ya karbi ran mahaifina. Mahaifina ya
rasu a ranar wata juma'a da safe. Bazan
taba manta wannan ranar ba saboda itace
ranar dana taba makara ban tashi da karfe
bakwai na safe banje wajensa ba, domin
kullum karfe bakwai a dakinsa take min.
Wannan kuwa ya faru ne a sanadiyar wata
kasala da wani yanayi da jikina yake min ba
dadi. Ni ba mai barci ba, haka ni ba ido
biyu ba. Tamkar wani abu mai nauyi aka
saka aka dirirritseni na kasa juyi. Sai dai
kuma idona a rufe ba kamar mai tunani
kamar mai mafarki domin abinda nake
nanatwa hirar da mukayi da mahaifina ce a
daren jiya kafin inzo in kwanta. Daga ni sai
shi bayan 'yan majalissa sun watse muna
labari kamar yadda muka saba. Ya laluba ya
dafa kaina yace aisha ki zama mai rikon
amana a rayuwarki yin haka zai ja miki farin
jini a wajen al'umma. Ki kiyayi munafunci,
ma'ana gulma shine yi da mutum yin haka
zai zubar miki da kima. Ki guji sata duk
rintsi kada ki taba abin wani yin haka zai
zubar miki da mutunci ke da zuri'arki gaba
daya za'a dinga yi muku gori. Ki guji yin
zina, laifi ne a wajen Allah kuma rashin
mutunci zai dasu a idon jama'a zaki zama
abar zagi, kowa ya fada miki magana, sai ki
zama ballagaza ko yaro karami ba zai
girmamaki ba. Ki kiyayi kwadayin abin wani,
ki nema naki na kanki duk kankantarsa ki
hakura kiyi amfani dashi shine zaman
lafiyarki da farin cikin rayuwarki. Kada ki
raina baiwar da Allah ya baki, kada ki dinga
ganini wadanda suka fiki. Kada zuciyarki ta
mutu kice ba zaki shiga ku fafata ba, ki
zama mai karfin zuciya da kudiri na alkhairi
kada zuciyarki ta dinga karaya. Sannan ki
zama mai godiya ga Allah a duk halin da
kika tsinci kanki na dadi ko wuya. Ki zama
mai yawan kyauta ko abinda kika mallaka
kalilan ne kada ki makale hannu kice baki
dashi, sai ranar da kika samu da yawa zaki
dinga bayarwa. Ki nemi ilimi mai yawa, na
muhammadiyya dana zamani komai wuya
domin kada a barki a baya a rayuwar duniya
da lahira. Allah Yace mu nemi ilimi a duk
inda yake domin sai munsan shi zamu
bauta masa. Allah baya karbar ibadar jahili,
har baccin mai ilimai yafi jahilin da zai
kwana yana sallah.
Sai naji mahaifiyata tana girgiza ni tana ta
ambaton sunana, idan na bude ido na dube
ta sai in koma in kwanta har sai da ta daga
ni zaune. Tace dani wanne irin bacci ne
haka har tara da rabi tayi baki je kin kaiwa
babnki koko ba, bayan kinsan baya jin dadin
jikinsa? Cikin magagin bacci nace mata yau
baba ya fita kofar gida da kansa, yayi shara
yayi shimfida da kansa. Sai ta harareni tace
karyar banza, a mafarki ko a ido biyu?
Yaushe kika ganshi ke da na tashe ki
dakyar? Sai na tuna ashe mafarki ne don
haka na mike a firgice ko sallah banyi ba na
fita kofar gida na hau shara, na fitar da
kujerarsa da tabarmi kamar kullum. Sannan
nazo na dauki koko a kwanon sha da
kudaya na duma na nufi dakin tsohona.
Wata irin al'ada ce matan gidanmu sukeyi
wai mata mai girki bata shiga dakin miji
saboda kada ayi gulmarta ace ta cika jaraba,
tsohon Allah sai anje an nanike maka,
makahon da yake ta kansa yau da lafiya
gobe babu. Kina shiga dakinsa za'a fara
lekowa ta lungu lungu ana kus kus, kina
fitowa kuwa zaki hadu da harara , zumde,
yafice da habaice habaice. Tsakanin shi
dasu gaisuwa daga bakin kofa ya fadi abinda
zai fada ki juya idan kin zuba masa abincin
ki aiki 'ya'yanki ko jikokinki su mika masa.
Daga baya ma da aka ga nice karama mai
shiga wajensa kullum sai aka dora min
alhakin kai masa abinci kullum, duk wacce
ta gama sai ta kwalla min kira inzo in kai
masa abinci.
Na shiga dakinsa sai na iske shi a lullube
kamar mai bacci, sai na zata lambo yayi ko
fushi yake yi dani dan banzo da wuri ba. Nayi
ta sallama shiru, sai nazo dai dai kunnensa na
durkusa na gaishe shi bai amsa ba, sai na
shiga yi masa bayanin abinda ya tsayar dani,
shimfida nayi har su malam shehu sun fara
zuwa. Sai naji yayi shiru bai motsa ba, sai
kawai na bude lullubin sai ga idanuwansa a
kakkafe yana kallon sama kamar mai
murmushi. Nace lallai baba kana jina ashe kayi
kasake kana kallon sama kana murmushi. Sai
bai bani amsa ba! Ni kuma sai naji raina ya
baci, sai nayi fushi na tashi na fita bakin kofar
dakin na zauna ina kumbure kumbure. Matan
gidan suka fara yimin tsiya suna cewa ke kuma
me akayi miki? Ke da baban naki ne kuma yau
ake jin kanku "yar lelensa wacce baya bari a
taba ki. Sai nace dasu yana ji ina tayi masa
magana yaki kulani, idonsa biyu yaki yi min
magana idanuwansa suna kalllon sama kamar
yana murmushi. Sai jikinsu ya fara basu tabbas
akwai wata matsala domin suma sun leka suna
gaishe shi bai amsa ba duk da dai anji motsin
alwalarsa da asuba amma baya baccin safe.
Sai matansa suka kutsa cikin dakin da sauri
kuma a gigice. Kururuwa da lafazansu ne ya
gigita ni, har yau ban kara jin mummunar
kalma a kunnena irin ta ranar ba. Suka ce
wayyo malam babu, malam ya mutu, munga ta
kanmu, ihu mun shiga uku, rumfa ta gaji da
shirgin kaya ta rushe. Ire iren kalaman da suke
fada kenan suna rusa kuka kururuwa. Sai naji
zuciyata ta hau dukan uku, na dafe kirjina na
fada a bayyane nace Innalillahi wainnailaihi
rajiun. Allah Ya jikanka baba, Allah ya sa
aljannah ce makomar ka. Allah da Ya karbi
abunSa dan yafi mu sonsa, daga gareka muka
zo kuma gare Shi zamu koma. Da ka tafi ba
kayi gaggawa ba haka mu da muka rage ba
muyi nawa ba. Sai manyan maza da mata suka
jeru a kaina suna kallona babu wanda ya kara
magana balle ihu. Mamaki marar iyaka zaka
dinga hangowa daga cikin idanuwansu. Ina
salati ina hawaye cikin natsuwa ba tare da
kwarmato ba. Sai yaya hussaini ya fashe da
kuka yace farida lallai baba ya shigar dake
makaranta, ya saka ki a aji ya koyar dake
darussan dako a jami'a ba za koya miki ba.
Baba yayi gaskiya da yake hana ki tafiya daga
wajensa har sai da kika koya ilimi wanda zai
isheki zaman duniya da lahira. Ya juya ya duba
iyayensa da 'yan uwansa yace wannan abinda
farida ta fada ya zama darasi a wajenku,
wa'azi ne, nasiha ce zuwa gare mu. Ihu da
kwarmato da dora hannu aka kuna fadin mun
shiga uku, ina zamu saka kanmu? Gatanmu ya
fadi. Dawa zamu zauna a duniya? Rumfa ta
gaji da shigi ta rushe. Dukka sabo ne, bata ne,
jahilci ne, azaba kuke karawa mamaci. Tabbas
idan ka saba da abu ranar da zaka rabu dashi
akwai ciwo, kuka wajibi idan akayi mutuwa
amma ba'a son ihu da kururuwa. Kamata yayi
ayai ta karanta innalillahi wainna ilaihi rajiun
sannan ayiwa mamaci fatan samun aljannan.
Ku dubi karamar yarinya nan farida itace kusan
wacce tafi kowa kankanta a cikin gidan nan
amma ita kadai ce tayi abinda ya dace , itace
wacce tafi mu shakuwa dashi, tafi mu sonsa,
kuma itace tafi mu nuna masa kaunar da take
yi masa shine data yi masa addua. Muyi koyi
da ita don tafi mu ilimi, tafi mu sanin ya
kamata. Sai suka daina ihu suka koma suna
ambaton sunan Allah. Yaya hussaini ya tashe
ni tsaye yasa gefen rigarsa ya goge min
hawaye. Yace ki daina kuka 'yar karamar
kanwata, kowa yasan ke aka yiwa mutuwar
nan sai kuma kika fi kowa yin tawakkali haka
Allah yake so. Ina mai yi miki albishir Allah ba
zai bari ki wahala ba, da izininsa ba zakiyi
kaskantaccen maraici a rayuwarki ba, duk da
kin rasa mahaifinki a lokacin da kike da
karancin shekaru saboda baki mance da
Ubangijinki ba wanda shine gatan ki. Allah
Yana tare da duk wanda yasan da Shi kuma
wanda yake neman taimakonsa. Farida nayi
miki alkawari zan dauki nauyinki, zan rike ki
amana har izuwa ranar da zan aurar dake
saboda wannan tawakkalin da kika nuna, zan
rike ki tamkar 'yar dana haifa ta cikin. Wacce
hakkin cinta, shanta, suturarta, tarbiyyarta,
iliminta da suka wajaba a kaina har zuwa ranar
da zan aurar da ita sannan nauyinta ta koma
hannun mijinta. Ki shiga ciki wajen baba kiyi
masa sallama, kiyi masa irin adduar da kika yi
masa yanzu ta neman gafara da rahamar
Ubangiji. Mutuwa ce kadai ta raba kaunar dake
tsakaninku. Na juya da sauri na shiga wajen
tsohona, durkusa a gabansa setin kunnensa na
tofa masa kulhuwallahu ahad uku, sannan nayi
masa adduar samun aljanna da neman hasken
kabari. Nayi masa fatan Allah ya sa ya tashi a
cikin gafartattun bayi a cikin alummar manzon
Allah (SAW). Sannan mahifiyata ta jawo
hannuna muka fito waje, cikin kuka mai tsanani
tace dani farida na yafe miki duk abin da kika
yi min. Allah yayi miki albarka a rayuwarki ta
duniya da lahira. Alhamdulillahi nayi dace da
'ya ta gari, mai jin kan iyayenta. Ina fatan nima
zakiyi min irin wannan adduar idan na riga ki
tafiya. Muna zazzaune a tsakar gida maza
suka shiga sukayi masa wanka, suka hada shi
suka fita da shi akayi masa sallah. Aka dauke
shi aka tafi dashi gidansa na karshe, gidan da
ba'a fitowa unguwa, gidan da ba'a leke, gidan
da ba'a jiyo motsinka balle a gaishe ka ka
amsa wato kabarinsa. Bakina bai gushe da
karanta masa kulhuwallahu ba da inna
a'adaina kalkausar har karshe. Shi ya bani
adduar yace ita ake so a dinga karantawa
mamaci. Da akayi sadakar bakwai sannan aka
watse, lokacin mutuwa ta dawo min sabuwa fil,
idan aka tashe mu daga bacci za'a tura mu tafi
makarnatar boko sai in nufi dakinsa zan buya
sai in ga a rufe sannan in tuna ashe ya rasu,
dole a tura keyata zuwa makaranta raina baya
so, da yamma ma sai a tura ni makarantar
allo. Ina tuna nasihohin da tsohona da
abokansa sukayi min na dabarun samun
nasarar karatu, sai nake bin duk yadda suka
umurce ni sai naga ina ganewa kuma ina cin
jarabawa don haka saina fara jin dadin
makarantun da nake zuwa, na dawo ina zuwa
makaranta da kaina ba sai an tura ni dole ba.
Ranar asabar da lahadi muna zuwa makarantar
allo da safe da yamma amma ranar alhamis da
juma"a da yamma ba ma zuwa koina don babu
makarantar allo, sai na fitar da kujeran babana
in shimfida tabarmi kamar yadda na saba. Sai
inga tsofaffin nan suna zuwa daya bayan daya
suna zuwa suka taru kamar yadda suka saba
da, don har sun daina taruwa tun bayan da ya
mutu. Baba ahmadu ne ya maye kujerar
babana shine babba ina gefensa koda yaushe,
duk sanda suka kalle ni sai inga suna hawaye
suna tausayina da alama suna tunawa da
yayansu, abokinsu, amininsu, makwabcinsu,
abin kaunarsu. Zaman majalisar yakoma ranar
alhamis da juma'a ne kawai da yamma. Kuma
munci gaba da hirarrakin mu kamar yadda
muka saba. Bayan rasuwar mahaifinmu da
shekara guda yaya hussaini yayi aure, ya auri
'yar kanin babanmu mai suna abida dai dai
lokacin daya sami dan karamin aiki a union
bank, da certificate dinsa na secondary a
matsayin masinja a branch na kano dan haka
kano ya kauro damu. Da zamu tafi mahifiyata
ta hada min kayana kakaf tana kuka ina kuka,
kanwata munauwara ma tana kuka, 'yan gidan
kacokan suka fito suna mana fatan Allah Ya
kiyaye hanya da fatan Allah Ya bamu zaman
lafiya, Ya hada mu da abokan arziki a can.
Muka tare masu babura biyu muka hau da
jakunkunan kayanmu muka nufi tasha, muka
hau doguwar mota mai zuwa kano. Kano ta
dabo tumbin giwa, mai mata da motoci ko da
me kazo an fika. Rabona da shagamu kenan
har yau ban sake komawa da sunan zama ba
sai dai inje da sunan ziyara. A wata unguwa a
cikin kano mai suna sharifai zauran tudu, yaya
hussaini daman ya kama mana haya tun kafin
muzo, a gida mai dakuna bakwai muka kama
dakuna biyu. Don haka mutane ne da yawa a
cikin gidan, bandakin daya ne kacal, kicin daya
da tsakar gida daya ake amfani dasu mata da
maza, yara da manya. Abunka da gidan yawa,
kazanta ba'a magana. Gashi daman gidan ya
tsufa ya farfashe ba gyara sai warin bola da
kwata kowa kyashi ya hana shi gyarawa. Idan
ka share cikin dakinka da kofar dakinka ka
gama shara babu wanda zai share tsakar gidan
da zaure balle kofar gidan. Ga gida a lungu ko
mota bata shiga lokon, ga wata tafkekikyar
kwalbati da ta cinye fadin lungun, kowa a
tattakure babu sakewa, yara basa iya wasan
guje guje su more sboda matsi. Haka kowacce
mace ta baza kayan san'arta a cikin gida, cikin
zaure ko kofar gida saboda sai an taimakawa
mazan rayuwar zata tafi dai dai. Daman mazan
da yawansu buga buga sukeyi, wani sai ya
dawo gida babu abinda ya samo, da dan kudin
sana'ar natar za'a yi cefane kuma ta bawa
yaranta kudin makaranta. A gidan ma har gara
yaya hussaini tunda yana daukar albashi duk
tsiya dai karshen wata zai samu duk da dai dan
albashin bashi da yawa kuma rabin kudin a
acaba yake tafiya, kafin wata ya kare sai anci
bashi dole kafin a biya an jigata. Duk da haka
dai munfi sauran, muna dan cancanawa dai
muna rayuwa. Ni da abida muka fara sana'a,
muna soya wainar fulawa a kofar dakinmu,
kuma ana saya ba laifi duk da cinikin naira
biyar biyar ne, duk da haka muna samun na
sayan maggi, gishiri, a ciki ake bani kudin
makaranta da kudin dinkin tsummokaran mu
idan sun yayyage. A makarantar bokon cikin
unguwa aka saka ni, kamar sauran yaran
unguwar haka aka saka ni a makarantar allo da
yamma ta islamiya da daddare. Bana fashin
zuwa makarantar kullum saboda ina tsoron
yaya hussaini sosai, baya yi min wasa koda
yake matarsa ma baya sakar mata fuska ,
mutum ne mai zafin zuciya. Lallaba shi muke
kamar kwai. A daki daya nake zaune babu
komai a ciki daga 'yar karamar katifa sai 'yar
jakar kayana ta buhu a gefe ko ledar daki ba'a
shimfida ba sai tsurar ragargajejjen siminti da
wani yagulallan labule. Dakin su abida da
mijinta ne mai labule mai kauri, an shimfida
leda a kasan da katuwar katifa sai akwatin
kayansu a gefe. Kayan kitchen da danyan
abinci suna dakina wasu a dakinsu. Haka muke
rayuwa amma muna farin ciki saboda mun
sami ci gaba fiye da a garinmu tunda daman
can a cikin talauci aka haife mu. Bayan
kaurowar mu da shekara daya mahaifiyata ta
tara kudin motarta da guzurinta tazo ganina
sabida tun kaurowarmu bamu je shagamu ba,
saboda matsalar tattalin arziki sai ita tazo dan
taga yadda muke rayuwa don koda yaushe
magana ta takeyi don tana sona sosai har fiye
da 'yar autarta. Nayi murna matuka da ganinta
har ita ta fini murna, yaya hussaini da matarsa
ma sunyi murna da ganinta kuma sunji dadin
tsarabar da ta kawo mana. Ni da abida atamfa
dai dai ta kawo mana, yaya hussaini ta kawo
masa yadi, sannan ta kawo mana doya,
dankali, ayaba da lemo jifgi guda. Allah cikin
ikonsa cikin daren data zo muna kwance da ita
a dakina ciwon ciki ya turnuke ta kafin in
bugawa yaya kofa ya fito don a kai ta asibiti
rai yayi halinsa. Ummata ta mutu a gabana ina
kallonta ban isa in hana ta tafiya ba, Ubangiji
ya nemi kayanSa. Sai na tuna wasiyyat da ta
bar min cewar idan ta riga ni mutuwa inyi mata
addua kamar yadda na yiwa mahaifina. Nayi
mata addua sosai kuma ban manta ambaton
innalillahi wa'innalialhir rajiun ba har gari ya
waye. Sai dai nayi kuka mai yawa saboda na
kara wayo na san zafin mutuwar sosai ba
kamar da ba, na tausayawa kaina sai nafi
tausayin kanwata munauwara. Gata karama ita
kadai ta rage babu uwa, babu uba, babu ni 'yar
uwarta. Nasan a gidanmu 'yan ubanci akeyi
kowa yana tattalin 'yan dakinsu, nasan sai dai
dangin mahaifiyta ne zasu dauke ta suma
kuma duka kanwar ja ce, talauci ne tsagoronsa.
Rashin kudin motar da za'a kai gawarta
shagamu shi ya hana yaya ya kai ta can a
binne sai kawai ya buga waya ya sanar dasu
wannan mummunan labari. Sun kuwa gigice da
jin haka sai suka yanke shawara gara wasu su
taho kanon ayi jana'iza a binne ta anan. Allah
Ya rubuto anan kasarta take. Da suka iso sai
akayi mata sallah aka binne ta. Kafin kwana
bakwai wasu daga cikin danginmu sai da suka
zo kano sukayi gaisuwa sannan suka koma,
wasu da yawa basu sami damar zuwa ba, da
yake a can ma ana zaman makokin don ba
kowa yake da kudin zuwa ba. Da akayi albashi
ni da yaya hussaini da matarsa mukaje
shagamu don yin gaisuwa da kuma zancen
abinda ta bari. Baiwar Allah bata da komai
daman mijinta bai bar mata komai ba, dan
matan basu samu gida ba! Basu samu gona
ba. Ko mu 'ya'yan kudi kadan aka bamu da
akayiwa gidan da gona kudi wani yayanmu ne
ya saya dan ba zai rabu ba. Daga ragargajejjen
gadonta sai tsumokaren kayanta aka ajiye
mana shine gadonmu. Na kasance marainiya
babu uwa ba uba, sai ni sai halina sai kuma
yayana hussaini da matarsa sai Allah. Kuma
ina godiya ga Allah a kowanne lokaci don ban
mantawa da nasihohin da mahaifina yayi min
ta karshe. Allah yana ganina, kuma Yana
taimakona, Bai bari na tagayyara ba. Babbar
baiwar da Allah ya min itace daya bani jama'a,
masu sona suna da yawa a duniya, mata da
maza. Yara da manya kowa yana yabon
halayyata koda kuwa an kushe ni sai kaji ana
yabona. Na godewa Allah Shine gatana shine
majibancin al'amurana. Aisha farida ta rushe
da kuka hade da hawaye mai radadin fita.
Hawaye ne yake ta kwaranya tamkar an bude
ruwa a famfo. Barrister Mu'azzam ya juya ya
dubi abokinsa barrister nuruddeen shima ya
kalle shi sannan suka juya su dukka suka sake
duban aisha farida, suka cigaba da mamakin
wannan yarinya mai surutu da zazzakar murya,
ga iya magana tana fitar da kalamai dalla dalla
a jejjere tamkar wacce wani ya labe yake rada
mata. Wannan itace fadi ba'a tambaye ki ba,
amma fa sunji dadin sauraron labarinta, yayi
ma'ana kuma sun karu da abubuwa da yawa
na game da zamantakewar rayuwa. Sannan sun
tausaya mata, ta cancanci a tausaya mata
domin rayuwarta tana cike da abubuwan ban
tausayi. Daga ganin ta a kidme take a dimauce
ta fado musu ta gaishe su, kafin su amsa ta
sami kujera ta zauna ta hau basu labari. Yau
ne rana ta farko da suka fara ganinta a
rayuwarsu itama haka, farida batasan wacce
irin damuwa bace ta hana su zama a gidajensu
suka fito a cikin daren nan suka zauna a wajen
shakatawa mai suna "fish park" dake
nassarawa GRA. Barrister muazzam ya zaro
dan karamin handkerchief fari kal daga gaban
aljihun rigarsa (suit) ya mika mata ba tare da
yayi magana ba, ta dago da jajayen idanuwanta
tana gogewa wani sabon hawaye fil yana
bulbulowa daga idanuwanta. Barrister
muazzam ya mika hannu a sanyaye kan teburin
dake gabansu ya dauko wani kwalin lemo ya
tsiyaya a cikin kofuna biyun da suke gabansu
ya mika mata, sai ta karba sannan tayi godiya
ta fara kurba a cikin nutsuwa yayin da shima
ya dauki daya kofin ya kwankwadi lemon a
cikin kofin ya mikawa abokinsa shima ya karba
ya fara sha ba tare da wani daga cikinsu yace
uffan ba. Sai aisha farida ta fara tunanin ko
kurame ne bata sani ba tazo ta hau su da
surutu, saboda tun sanda ta zo ta zauna ana
fiye da mintuna talatin babu wanda yayi ko tari
a cikinsu har yanzu sai kallonta kawai sukeyi
da ido. Ta kurbi lemo ta ajiye kofin akan teburi
ta sharce hawaye da hankicin dake hannunta
tayi murmushi. Tace bayin Allah shin baku
magana ne, ko kurame ne?
Kallonta kawai suke yi har yanzu babu wanda
ya tanka mata, su kalleta su juya su kalli
junansu. Sai taji hankalinta ya tashi, tayi ajiyar
zuciya tace yaya sunanku? Barista nuruddeen
ya dubi barr muazzam ya kifta masa ido
alamar kada yayi magana. Suka ci gaba da
sauraronta tana ta magana ita kadai, sai taji ta
zama tamkar wata mahaukaciya wacce bata
san ma abinda take yi ba, taji duk ta tsani
rayuwarta, sai ta tashi a sanyaye ta juya zata
tafi. Barr muazzam yaji tausayinta sai yace
aisha farida meyasa zaki tafi? Ta juyo da sauri
ta dube shi sai ta girgiza kai tace kuyi hakuri
ban san na takura muku ba, na shiga masifa,
na shiga kunci har na dimauce ban san dalilin
da yasa nazo wajenku na dinga zazzago muku
labari baku tambaye ni ba. Na ganku
kammalallu dan haka na zata zaku karbe ni
hannu bibibuy , kuba bani shawara dan ban san
abinda zanyi ba anan gaba. Barr muazzam
yace dawo ki zauna, shirun da mukayi miki don
bamu sanki ba kuma bamu san manufarki ba
kinsan duniya abar tsoro ce bai kamata nan da
nan ka yarda da mutumin da baka taba gani
ba. Kuncin rayuwar kuwa mun fiki shiga shine
ya fito damu nan ko Allah zaisa muji dan
sanyi. Ta dawo ta zauna a sanyaye ya yin da
take tuhumar kanta da laifin rashin hankali,tana
jin haushin kuskuren data tafka daga ganin
mutane bata san su ba kawai ta zo ta zauna ta
hau basu labari,ta fadi sirrinta bayan ba'a
tambaye ta ba,lallai dole suyi mata kallon wata
sakarya. Ta tambayi zuciyarta shin ko cutar
tabin hankali ce ta kama brain din ta domin
sanda ma ta fara magana bata sani ba.
Mu'azzam ne ya ktse tunanin da take yi ya ce
"ni sunana Barr Mu'azzam,abokina kuma Barr.
Nuruddin. Mecece takamaimiyar matsalarki?
Menene dalilin da ya fito da ke daga gidanku
zuwa nan a cikin daren nan? Naga ba tare da
mijinki ku ka zo sayan kifi ba kamar yadda
nake ganin wasu ma'auratan hausawanmu na
yi? Me kika fito nema? Wanne irin taimako kike
nema daga garemu? Kina so mu saya miki kifi
ne ko kuwa kudin mota ki ke nema? Ta yi
murmushi ta ce "gaskiya ne,na cancanci a
tambaye ni domin ban yi kama da mai kamun
kai ba. A rude na shigo nan dan yau ne rana ta
farko dana taba zuwa nan,ban san inda zan
nufa ba sai na hango ku kawai na ji a raina
tamkar naga yayyena,wadanda zasu iya
taimakona shine na taho wajen ku ko Allah zai
sa ku kwace ni daga mugun dan sandan da
yake shirin cutar da rayuwata. Barr nuruddin ya
dubi abokinsa ya tsuke fuska ya ce "kai kada fa
ka yayumo mana ruwan dafa kanmu,ka bar
yarinyar nan ta kama gabanta. Me yasa ka
dawo da ita har ta yi niyyar tafiya? Ka cika
kwashe- kwashe kamar baka san irin yan
matan nan ba ne yan club? Idan ba yar club ba
wacce budurwar kirki ce zata baro gidan
iyayenta ta shigo wajen nan da dare? Ka duba
ka ga nisan unguwarsu tun daga cikin gari
zuwa nan? Zuwa ta yi ta tsara mu ko daya
daga cikinmu zai dauke ta. Ke yarinya ki kama
gabanki mu ba irinki bane,je ki can ki sami yan
uwanki irin ki. Shawarar da zan baki kuma ita
ce ki koma skul ki taimaki lyf din ki don yawan
duniya ba riba sai asara,akamr yadda kika ce
mahaifinki ya yi maki wasiyya kafin ya rasu"
aisha farida tayi dariya maimakon ta ji haishi
sai ta gyada kai tace "gaskiya ne yayana na ji
dadin shwararka kuma zan dauka insha Allah
zanyi amfani da ita. Sai nauyi da kunya ya
kama barrista mu'azzam ya ji kamar ya nutse
a cikn kasa saboda baranbaramar da abokinsa
yake yi,baya kara,ba kunya balle jin nauyi yake
maganarsa,ya harare shi yace haba nuraddin
kai fa mtsalata da kai kwaba mahgana babu
taunawa. Ka bari ka ji uzurinta idan ka gama
jin inda ta nufa sai ka yanke mata hukunci.
Kamar ba lauya ba ai sai ka gama sauraron
labarinta tun daga farko har karshe sannan ka
gama jero mata tambayoyi ta gama amsawa
ka kula da inda ta nufa sannan ka yi mata
nasiha ba fada ba. Yanzu da a kotu muke sai
ka fadi a sharia dan kawai kana jin haushin ka
sai ka huce akan yar mutane,to ba ita ta kar
zomon ba ko rataya ba'a bata ba.
Posted by Bashir Sani Mahmud on 22 Aug 2017
Aisha farida tayi karfin hali tace ba damuwa, ai
laifina ne dan banyi kama da mai kamun kai
ba, tunda ba'a tambaye ni ba nazo na fara yi
muku surutu, nasan ba'a son mace marar
kamun kai. Barr muazzam ya girgiza kai yace
zuwanki nan ba laifi bane dan kin zo kin zauna
a kusa damu, kujeru ne a jejjere kowa zai iya
zuwa ya zauna. Da kika zo kika same mu kinyi
mana sallama duk da tun kafin mu amsa har
kin zauna. Daman kamata yayi ki gabatar
mana da kanki kuma kinyi hakan sai dai kika
zarce da bamu labari shine abinda ya daure
mana kai kenan. Kallon junan da kikaga muna
yi ina tunanin ya sanki ne, shima yana tunanin
ko na sanki ne. Aisha bani labarin takamaiman
abinda ke damunki, muma nan da kika ganmu
matsala ce take addabarmu, ki saki jiki ki fada
mana mu dake sai mu taimaki juna da
shawarwari. Barr nuruddeen ya fusata ya mike
tsaye ya dubi abokinsa yace malam in ka gama
kazo ka same ni a cikin mota mu tafi, dan ba
zan iya zama ina sauraron wannan shirmen
naku ba. Bansan sanda ka zama marar aji ba,
daga haduwa da 'yar tasha sai ka hau hira da
ita kai ma kana baza sirrinka, idan taji
matsalar ka me wannan zatayi maka? Itama
bata san yadda zatayi da kanta ba balle ta
bawa wani shawara. Kada ka sake ka ambaci
sunana a cikin labarinku kai dai ka fadi taka
matsalar. Ya juya a fusace ya tafi bai daina
fada ba yana tafe yana magana yana wurwurga
hannu har ya fice daga cikin gate din. Aisha
farida da barr muazzam suka bishi da kallo har
sai da suka daina hango shi. Ta sunkuyar da
kanta kasa sai hawaye ya fara zubowa daga
idanuwanta. Kada ki yi kuka aisha, ki mayar da
komai ba komai ba. Kece fa kika gama bani
labarin cewa zaki iya zama da kowanne irin
mutum a duniya. Inji brr muazzam. sai tayi
murmushi ta shiga goge hawayenta tace ko
kusa ban damu ba, banji haushi ba. Kawai dai
abokinka yayi min kallon ballagar mace, 'yar
tasha, 'yar club, karuwa kenan. Shine mutum
na farko a rayuwata daya taba jifata da
wadannan munanan sunaye, saboda bai sanni
ba, sai dai ina fatan ya sanni nan gaba. Barr
muazzam yace yi hakuri kanwata, ki cigaba da
bani labarin rayuwarki, ina jin dadin sauraronki.
Haqiqa Aisha farida,labarinki yakai maqura
gurintausayi,nayi kuka sosai,rabena da
irinkukannan yaukimani wata takwas
kenan.tunrasuwar yayata,ayau nafisa mamawa
kinsani cikintausayin ki,maganardanakeyi
yanzuhaka nakasa tsayarda hawayendake
zuba'a idona. kitaimaka kibani lbrin cigabanki
da daukakardakikasamu kozansamisukuni
yau...wallah nafisa natausayamiki sosai. BABI
NA BIYU Da na karasa makarantar primary sai
yaya hussaini ya kaini wata makaranta a wajen
sabongari na zana jarabawar common entrance
ta shiga makarantar federal. Allah cikin ikonsa
sai naci jarabawa aka turani makarantar da na
zaba wato FGC kano. Yayi min sayayya iya
karfinsa ya kaini, ya bibbiya dukka kudaden
makarantar da aka bukata, ya dawo gida ya
barni a can. Nayi kuka saboda rashin sabo,
gashi bansan kowa ba a makarantar amma
daga baya na saba da dalibai 'yan uwana sai
na fara jin dadin rayuwar makarantar. Jama'a
na sona saboda yadda nake da fara'a, ladabi
da son aiki bana kiwa don haka kowa yana son
ya jani a jiki saboda ina da matukar tsafta. Na
yi suna a makarantar nan da nan malamai ma
suka sanni saboda kwazona da wayo, ga iya
magana. Na gama aji uku hutun da zamu shiga
aji hudu aka cireni, abu ya ci tura hidimomu
sun karu, yayana ba zai iya cigaba da yi min
siyayya ba da biyan kudin makaranta ba
kasancewar shima ya hayyayyafa. A jejjere ba
kakkautawa abida take haihuwa, 'ya'yanta na
farko ma 'yan biyu ne maza abubakar da umar,
sai ta haifi mace mas'uda ga wani cikin a
jikinta ko yaye ta goyen bata yi ba. Ga kudin
haya ya karu, cefane ya karu, farashin abinci
ya karu, gashi an kara kudin makaranta ya
kusa ninka na da ma. Daman duk sanda zan
koma makaranta sai ya ciyo bashi kafin ya
harhada ni in tafi. Ya kira ni daki ya zaunar da
ni yayi min bayanin halinda ake ciki, sai ya bani
hakuri cewar zai mayar dani makarantar
gwamnati ta ;yan mata dake shekara. Dole na
koma makarantar shekara naci gaba da karatu,
daga aji 4 na fara, sai na zama zakaran gwajin
dafi nafi kowa kokari saboda dana sami horo a
FGC a wajen yaran kabilun da basa jin hausa
da yaran hausawan da suka sami horon turanci
tun daga primary. Ajin kimiya na shiga (science
class) har Allah ya kaini aji shida aka bani
shugabar dalibai, duk wata gasa ko muhawara
ta turanci tsakaninmu da wasu makarantun ni
nake tsayawa makarantarmu, idan bana nan
babau abinda yake tafi dai dai. Shugabar
makarantar mu tana alfahari dani, kullum tana
kwatance dani saboda kokarina. Da muka
gama makarantar ita da malamai sai da sukayi
takaicin rashina saboda ba'a sami madadina
ba. Bayan gama makarantata da wata uku
yayana ya harhada 'yan kudadensa ya bani
kudin mota da guzuri na zuwa shagamu,
saboda duksanda yake zuwa shi da matarsa da
'ya'yansa ina makaranta ba'a zuwa dani.
Tsofaffin abokan hirata har sun gaji da
tambayata wasu ma sun mutu, haka wasu
daga cikin yayyena sun murmutu duk banje ba.
Ina samun wasikun kanwata munauwara akai
akai duk sanda ta sanda ta sami mai zuwa sai
ta bayar an kawao min, ta shaida min cewar
an cire ta daga makaranta tana secondary aji 3
anyi mata aure saboda rashin kudi. Ni kadai
yaya hussaini ya saka a mota zuwa shagamu,
dana isa garin shagamu a tasha na hau acaba
zuwa gidanmu, ban manta hanya ba. Da yawan
'yan gidanmu basu shaida ni ba sai daga baya
suka gane ni, sunga na girma nayi kyau. Duk
da rashin wadatar da muke ciki a kano sai
naga na fisu kyawun gani, cikakkiyar lafiya da
gogewa. Na zagaya dangi na kusa dana nesa
har sai da naji kafafuwana zasu gutsire saboda
yawansu. Na ziyarci gidan kanwata dake agege
a lagos anan take aure, rayuwarta abin tausayi,
gida ne irin na haya mai dauke da dakuna fiye
da ashirin, yare kala kala kamar hausawa,
yarbawa, igbo, da wasu yaruka daban daban.
Bandaki daya ne kacal, tunda asubahi ake fara
layin shiga bandaki. Mijinta iliyasu shima dan
shagamu ne amma a lagos yake facin taya, ita
kadai ce sana'arsa. 'Ya'yansu biyu a lokacin.
Saboda tausayin halinda na same ta kusan
dukka kayana na sakawa na bata kyauta,
sannan na hada mata mayafai, sarkokina,
takalmana, guda dai dai na rarrage. Duk
kudaden dana samu na bata dukka kudin mota
na komawa ta kano kadai na ware. Muka sha
kuka tare da nazo tafiya, kukan da muke na
tunawa da iyayenmu ne da kuma kukan
rabuwa, don munsan zamu dade kafin mu sake
haduwa. Na dawo kano jakata kwalam babu
komai duk na rabar da kyana kuma da masu
kyan na tafi dasu. Tsummokaran, tsofaffin,
yagaggun kadai na bari a gida. Haka nazo na
dinga karancin kaya duk sun ragargaje dan
haka na daina zuwa taron biki ko gidan
kawayena. Abida tayi ta min fada tace nayi
garaje ai ba'ayin haka tun da nasan ban ajiye
wasu ba a lufge kuma bani da mai dinka min
wasu ai bai kamata in rabar ba. Idan fita ta
kama ni dole sai dai in ari kayan abida in saka
inje, ina dawowa in cire mata. Abinka da
cakudi, zaman saka ido, kowa yana kula da
shige da ficenka. Gulmammaki iri iri bayan
zumde da yafice zaka ga anayi mana, abin ya
kai har su dinga kiran 'ya 'yan abida suna
bugun cikinsu suna tambayarsu wai ina kayana
suka ga ina arar na abida? Irin wannan gutsiri
da tsomar sai da ta wuce kan matan gida ta
koma wajen mazansu, su kuma suka
tseguntawa yayana hussaini, suka ce masa bai
dace in dinga arar kayan abida ina fita kofar
gida ina tsayawa da samari ba, ina yawo da
kawayena a gari. Idan ba an lura ba in a
duhune sai a zaci abida ta fara bin maza.
Sukayi ta zuba masa bayanan da dole
hankalinsa yayi matukar tashi, ransa yayi
mummunan baci. Ya shigo dakina ransa a bace
ya iske ni a kwance yace min in kira abida
itama ta shigo nan dakin yana da magana da
ita. Mukazo muka durkusa a gabansa muna
karkarwa saboda yadda muka ga ransa a bace
gashi mutum ne mai zafin zuciya. Ya umarci
abida ta fada masa gaskiya kada ta kuskura
tayi masa karya akan abinda zai tambayeta,
haka nima ya gargadeni kafin ya yi mana
tambayoyin. Muka yi masa alkawarin zamu
fada gaskiya, ba zamuti karya ba. Cike da
fargaba mai tsanani muke sauraron abinda zai
fada mana. Ya cewa abida da gaske ne aisha
farida tana aron kayanki ta saka ta fita yawo a
gari? Sai abida ta dafe kirji tace Innalillahi
wainna ilaihir rajiun! Ya daka mata tsawa mai
firgitarwa yace baki bani amsa ba. Nan da nan
ta fara hawaye, jikinta na karkarwa tace eh
haka ne. Sai ya kai mata mari har sai da ta
fadi kasa, ya fada cikin fushi yace to ta hada
kayanta ta tafi gidansu. Na rushe da kuka na
dinga rokarsa ya yafe mata ba laifinta bane
nice na tambaye ta. Nima din ya yafe min na
daina daga yau. Sai ya rufe ni da duka yana
duma, yana tattaka ni da kafa tamkar zai kashe
ni. Munafukan matan gidan ne suka zo suka
kwace ni dakyar, ransa yayi matukar baci sai
fada yake yana zaginmu wai sai mun harhada
kayanmu mun bar masa gidansa. Ana bashi
hakuri tamkar zuga shi akeyi dakyar ya haukra
ya kyale mu amma tun daga lokacin baya raga
mana, komai mukayi sai ya hantare mu, sai
harara koda yaushe. Sai na daina fita koina ,
koda yaushe ina fama da dinkin yaga da zare
da allura. Abida ta iske mijinta a dakinsu ta
ajiye masa abinci sannan ta durkusa ta gaishe
shi. Ya amsa dakyar cikim fushi, bata damu ba
ta zauna a kusa dashi ta dauko muhuci ta fara
yi masa firfita. Sai yayi mata tsawa yace ta
bari baya so, ta tashi ta fita ta bashi waje.
Cikin lallausar murya tana zubar da hawaye
tace ka yafe mana laifukan da muka maka,
munyi kuskure, fushin da kake yi damu ya
hanamu sukuni, bama jin dadin rayuwarmu,
rayuwa tayi mana kunci. Dan ban fada maka
bane halin da ake ciki kada ranka ya baci, ashe
dana fada maka ma zaifi sauki. Aisha farida ce
ta rabar da kayan sakwarta kakaf a shagamu
saboda tausaya musu da tayi, ta gansu cikin
tsumma, shine ta dawo bata da kaya sai
yagaggu. Dan haka bata iya fita wajen
kawayenta shine nake bata aron kayana ta
saka tana dawowa take cirewa, bansan abinda
'yan gulma suka fada maka ba har ya jawo
ranka ya baci ka dauki mataki cikin fushi. Sai
yayi shiru yana sauraronta can yace ai duk
laifinki ne, meyasa ba zaki fada min halin da
ake ciki a cikin gidana ba har sai da wasu suka
fada min a waje? Kinsan irin zaman da mukeyi
da 'yan gidannan, zaman saka ido ne, duk
shige da ficen mu akan idonsu. Ashe gaba daya
lungunnan gulmar ku ake yi shiyasa raina ya
baci. A take ya bata naira dubu biyu yace ta
bani inje in sayo atamfofi guda biyu 'yan naira
dari takwas takwas inyi dinkin dari bibbiyu.
Abida mace mai hakuri da tsananin wayo, ta
iya zama da mijinta duk zafin zuciyarsa, tabbas
macen da bata da hakuri da wayo ba zata iya
zama dashi ba, sai gashi da kansa yayi
nadamar aninda yayi mana, sai yaji kunya yazo
yana lallaba mu. DUK KYAN TAKALMI 5
Saurayina guda daya nake kulawa mai suna
musbahu, lungun mu daya dashi kowa yasan
mu tare, yana sona sosai nima haka saboda
yana kula dani. Tun sanda na gama sakandire
yake so ya aiko gidanmu ayi zancen aure sai
aka sami matsala daga gidansu, mahaifiyarsa
bata sona 'yar kanwarta take so ayi musu
auren gida, shi kuma ni yake so ya
aura.mahaifiyarsa ta tsane ni haka kawai, ko a
hanya na gaishe ta bata amsawa shiyasa na
daina zuwa gidansu don da ina zuwa wajen
kanwarsa jamila kawata ce ajinmu daya a
shekara. Musbahi ma yaji labarin duka dana
sha saboda aron kaya, sai naga ya siyo min
leshi guda daya da atamfa ya hada min da
naira dari biyar kudin dinki, sannan yayi min
fada in daina boye masa sirrina saboda yadda
yake sona a ransa, matsalata ai matsalarsa ce.
Yace duk sanda na shiga matsala in fada masa
ko bashi da kudi zai ciyo bashi yayi min komai
in dai baifi karfinsa ba. Yaci gaba da bani
hakuri akan halinda yake ciki shi da
mahaifiyarsa, ita ta hana shi ya turo gidanmu
zancen aurenmu. Ya umarce ni da mu dage da
addu'a Allah Ya karkato da zuciyar
mahaifiyarsa kaina taji tana sona ayi auren
dani. Sakamakon jarabawar mu na sakandire
ya fito naci credit takwas, geography ne kadai
naci pass shima dan a ranar da muka yi
jarabawar bani da lafiya. Sai misbahu yace idan
ya sami kudi zai saya min form din jamb in
wuce jami'a. Sai nace ba zan iya karatu a
jami'a ba saboda 'ya'yan masu kudi ne sukeyi,
bani da mai bani kudin mota da kudin sayan
handout, gashi dole sai an saka sutura masu
kyau. Sai shima ya gasgata zancena yaga
shima bashi da halin da zai dauki nauyin duk
wadannan sabida dan abinda yake samu ba
mai yawa bane. Duk da wasu lokutan sukan
sami ayyuka da yawa suna samun kudi a
business center yake aiki, suna typing a
computer, suyi kalandu ko meme. Sai yace to
zai samo min management in fara, nan ma
nace bana so nafi son inyi schl of nursing
saboda ba ruwana da neman kayan sakawa,
suna da uniform, sai yace shikenan zai binciko
yaji duk yadda akeyi a shiga amma in fara jin
ra'ayin yayana. Yayana ya amince da
shawararmu kuma yaji dadi musamman da
musbahu yazo har kofar gidanmu ya sa akayi
masa sallama da yayana hussaini ya kara yi
masa bayani. Yace zai taimaka min da wata
dawainiyar kudin makarnatar sai ya amince
yayi masa godiya. Musbahu da yayana ne suka
hada gwiwa suka bani duk kudaden da ake
bukata na shiga makarantar koyar aikin jinya
ta malam aminu kano dake unguwar court
road. Karatun shekara uku ne a shekara ta uku
ne muke zuwa asibiti koyar aiki don haka
karatu na yi tayi haikan, ban taba samun
matsala ba cinye jarabawata nake yi koda
yaushe. A asibitin malam aminu kano ake horar
damu koyar aiki (attachment). Ina zuwa
kkullum daga unguwarmu sharifai zuwa court
rd akan acaba saboda idan nace zan hau bus
zan bata lokacina zanyi in makara. Kudin
acabana kit da kit babu canji wata rana ko
purewater zan sha sai dai kawayena su saya
min. Duk da idan za'a je sayan abinci ko shan
lemo sai in gudu bana binsu saboda kullum sai
dai su saya min, ni kuma na fara jin kunya sun
gane bani dashi. Kawata khadija sani ismail
kadai wacce bata gajiya da taimakona kuma
duk sanda tace muje cin abinci naki zuwa ko
na sulale na gudu sai ranta ya baci, har tayi
fushi dani. Sai inyi tayi mata bayanan karya in
kirkiro uzurin dana je nayi ba guduwa nayi ba
sai ta ki yadda tasan karya nakeyi. Ba ita nake
ji ba, sauran kawayenmu nakeji don suna nuna
min bakin hali daga baya kuma in dinga jin
kananan maganganu cewar na cika san banza
kullum bana fitar da kudina ina sayawa kaina
abu balle in sayawa wani, sai dai ni kullum a
saya min. Rashin sani yafi dare duhu, kallon
kitse sukeyi wa rogo. Hakika ni mai yawan
tsafta ce in kula da fararen kayan makaranta
ta, kullum tsaf dani, ina kalkale jikina tas a
wanke ga karin guga. Gani nafi duk 'yan ajin
mu kokari yawanci ni nake basu amsa. Khadija
bazata iya rabuwa dani ba dan bata da kokari
sai dai gata, tunda iyayenta suna da hali. Duk
wasu manyan littattafai na karatu (text book)
babanta yana saya mata duk tsadarsu, sai nafi
morarsu don ni ce mai hazakar karatun ba ita
ba. Da taimakon Allah da taimakon khadija sani
nake cin jarabawa dan ba zan iya sayan
littattafan nan masu tsada ba. Badan Allah Ya
sa na iya kitos ba ina yiwa makwabta, da wata
rana ma ba zanje makaranta ba saboda duk
ranar da yaya hussaini ya tashi bashi da kudi
sai yace in hakura kada inje makaranatar randa
ya samu naje. Ni kuma bana so inyi fashi, da
kudin kitson nake harhadawa in tafi duk da
kitso a unguwar bashi da tsada, kan manya
naira talatin ko arba'in, na yara kuwa naira
ashirin ko goma ne. Ban taba fadawawa
kawayena sirrina ba, duk da yawan kawayen da
nake dasu a ajinmu mata da maza, sai dai ayi
hayaniya wasa da dariya a watse, ina taka
tsantsan da harshena a koda yaushe. Babu
wanda a cikinus ya san yadda gidanmu yake,
basu taba zaton haka nake rayuwa ba, sai dai
sun fahimci wani abu akwai wasu matsaloli
wanda ba zasu boyu ba. Suyi ta zargi da sake
sakensu a ransu su kadai, ni dai bazasu ji daga
bakina ba kuma ba zasu iya tara ta su
tambaye ni ba. Ni daman bana zuwa gidan
kowa balle azo gidanmu, mu hadu a abkin gate
ne mu rabu idan an tashi. Bana jin dadin
rayuwata a wannan bangaren saboda bani da
wata takamaimiyar kawa ko masoyin da zan
amayar musu da radadin da zugin matsalolin
da suke addabata. Kawata guda daya, itace
aminiyata, yayata, masoyiyata wato matar
yayana abida. Muna zama ni da ita mu raba
dare ko mu yini muna tattauna matsalolinmu,
koda yaushe ina samun nutsuwa da kwarin
gwiwa idan abida ta bani hakuri akan talaucin
da na tsinci kaina da shawarwari, sai inji sanyi
a raina, tawakkali ya kama zuciyata sai inji ta
tuno min da nasihohin da mahaifina yayi min a
baya. Idan nayi haka sai in dawo da walwalata,
ni burina guda daya ne shine in gama karatuna
in fara aiki in taimaki kaina, in taimaki 'yan
gidanmu. Babbar matsalar ma da tafi damuna
shine zaman cakudi a gidanmu, cikin tsagoron
kazata da cinkosa, babban burina ba wuce inga
mun bar gidan nan da umguwar mu canja gida
ko haya ce dai mu kama gidan da muke mu
kadai. Dakina daya da yara, ga dakin dan
karami mun cunkushe gashi su dukka yaran
abida fitsarin kwance sukeyi dan haka sun ruba
katifar sai zarni take dan haka na hakura da
katifar na bar musu. Na koma kwana akan
tabarma, idan na tashi da safe sai inyi salla
akai in nada in jingine a lungu sai zan sake yin
wani sallar sannan in shimfida. Har yanzu
kayana a jakar bagco yake a gefen shimfidata,
rayuwata ba irin na 'yan matan 'yan boko bace,
tamkar a kauye nake ba'a birni ba. Ko inyi
tunanin shiga hanyar banza, ban taba sha'awar
makalewa gidan kawaye ba ko arar kayan
kawa, na rike talaucina na kama kaina bana
sha''awar kayan wani. Daga makaranta sai
gida, a gidan ma nafi zama a daki kullum ina
karatu. Idan kaga na fito aiki nazo taya abida,
wankan 'ya'yanta , tsarkinsu ko aikin girki. Sai
'yan gidanmu da sauran 'yan unguwa suka
shiga yimin shaidar girman kai ne dani dan ni
'yar boko ce, basa ganin fara'ar da nake yi
musu. Kullum ina gaishe su ko basu ganni ba,
tabbas mutum ba'a iya iya masa, saboda dan
Adam ya kasance mai butulci ne. BABI NA UKU
Wata rana ranar litinin da misalin karfe daya na
rana muna cikin a sibiti, a bangaren marasa
lafiya muke wadanda aka kwantar dasu
sakamakon wasu kurajen da suka feso a
jikinsu. Muna biye da ma'aikaciyar jinya matron
maryam tana nunnana mana yadda ake aiki,
domin neman karin bayani sai tace bari ta
hada mu da kwararren likita wanda ya kware a
bangaren fata. Ta tura wani daki ta shiga
muma muka bita a baya da alama dakin
daukan darussa ne sabida naga kujeru ne zalla
da allo makale a jikin bangon. Kamar yadda
naji ta ambaci sunansa, dr shureim imran. Mun
iske shi tsaye a tsakiyar ajin tare da wasu
daliban likitoci guda 3 maza biyu, mace daya
da alama sunzo sunyi masa tambayoyi ne akan
wasu abubuwan da basu gane ba. Bayanai
yake yi musu cikin harshen turanci kai kace
baturen america ne, kalmomin kimiyyar
(botanical names) da yake ta ambato yana
jerowa layi layi da ka ba tare da yana duba
littafi ba, kai kace shine ya lakaba musu sunan
don ya haddace. Muna sake kutsawa cikin
ofishin yayin da zazzakar muryarsa, daddada
take sake shiga kunnuwanmu sai duk muka
kagu mu isa gabansa don mu kalli fuskar mai
muryan nan daddada. Kasancewar kofar ta
cushe muna shiga don muna da yawa, ga
dalibai likitoci nan suna kokarin fitowa sun
gama daukar darasin. Kowa ya kagu yayi ido
hudu da mai daddadar muryar nan, keyarsa
kawai na fara hangowa daga nesa sai na
tabbatar bakar fata ne dan uwana saboda ban
hango jan kunne ba da farin gashi irin na
turawa ba. Bakin gashi ne tattaura irin namu
na hausawa, sai dai gashin a gyare yake yana
shekin mai kuma ya kwanto lambar zuwa
karshen keyarsa. Kansu babu hula, yana sanye
da bakaken kaya riga da wando (suit), farar
riga mai dogon hannu daga ciki, ya daure
wuyansa da jan kyalle wato necktie. Dana
matso ciki sai na fara hango gefen fusakarsa,
wata lafiyayyiyar fata na fara hangowa mai
dauke da launi mai tsananin kyau. Irin kalar da
take tsada a duniya wato hasken duhu
(chocolate color). Ko dana sake samun daman
na matso kuda dashi sai ga gefen fuskarsa tar
ina gani wato idonsa daya da gefen hancinsa,
sai kawai naji wata mummunar fadywar gaba
ta far min ni ma bansan dalili ba har wadanda
ke kusa dani zasu iya jiyo karar ajiyar zuciya
danayi. Tunda nake a rayuwata ban ta ba ganin
irin wadannan dara daran idanuwan ba masu
tsananin haske daga ciki, da bakar kwayar ido
mai tsananin baki, aka zagaye idon da wasu
gashin ido da gashin gira masu yawa da
tsananin baki, ya gyara su sunyi kira mai kyau
suna sheki. A nutse ya waiwayo da kyakkyawar
fuskarsa gaba daya ya dube mu, bani kadai ba
duk wata 'ya mace da take wajen sai dataji a
ranta dama ace wannan kadarar mallakarta ce.
'Yan uwansa maza ma sai da suka raya a
ransu dama ace sune shi, ga kyau ga ilimi.
Ashe a da dana ke hango gefen fuskarshi ban
hango komai ba, kyau mai sunan kyau sai ka
kalle shi gaba dayansa daga kafarsa zuwa
kansa. Dogon mutum ne sosai ma kyawun
sura, bashi da kiba da yawa, haka bashi da
rama. Yayi kama da irin bakaken turawan nan
da ake kira african American, hukuncin da na
yanke masa kenan dan ko kusa baiyi kama da
'yan nigeria ba! Tabbas ruwa biyu ne suka
hadu suka same shi bakar fata da farar fata.
Saurayina guda daya nake kulawa mai suna
musbahu, lungun mu daya dashi kowa yasan
mu tare, yana sona sosai nima haka saboda
yana kula dani. Tun sanda na gama sakandire
yake so ya aiko gidanmu ayi zancen aure sai
aka sami matsala daga gidansu, mahaifiyarsa
bata sona 'yar kanwarta take so ayi musu
auren gida, shi kuma ni yake so ya
aura.mahaifiyarsa ta tsane ni haka kawai, ko a
hanya na gaishe ta bata amsawa shiyasa na
daina zuwa gidansu don da ina zuwa wajen
kanwarsa jamila kawata ce ajinmu daya a
shekara. Musbahu ma yaji labarin duka dana
sha saboda aron kaya, sai naga ya siyo min
leshi guda daya da atamfa ya hada min da
naira dari biyar kudin dinki, sannan yayi min
fada in daina boye masa sirrina saboda yadda
yake sona a ransa, matsalata ai matsalarsa ce.
Yace duk sanda na shiga matsala in fada masa
ko bashi da kudi zai ciyo bashi yayi min komai
in dai baifi karfinsa ba. Yaci gaba da bani
hakuri akan halinda yake ciki shi da
mahaifiyarsa, ita ta hana shi ya turo gidanmu
zancen aurenmu. Ya umarce ni da mu dage da
addu'a Allah Ya karkato da zuciyar
mahaifiyarsa kaina taji tana sona ayi auren
dani. Sakamakon jarabawar mu na sakandire
ya fito naci credit takwas, geography ne kadai
naci pass shima dan a ranar da muka yi
jarabawar bani da lafiya. Sai misbahu yace idan
ya sami kudi zai saya min form din jamb in
wuce jami'a. Sai nace ba zan iya karatu a
jami'a ba saboda 'ya'yan masu kudi ne sukeyi,
bani da mai bani kudin mota da kudin sayan
handout, gashi dole sai an saka sutura masu
kyau. Sai shima ya gasgata zancena yaga
shima bashi da halin da zai dauki nauyin duk
wadannan sabida dan abinda yake samu ba
mai yawa bane. Duk da wasu lokutan sukan
sami ayyuka da yawa suna samun kudi a
business center yake aiki, suna typing a
computer, suyi kalandu ko meme. Sai yace to
zai samo min management in fara, nan ma
nace bana so nafi son inyi schl of nursing
saboda ba ruwana da neman kayan sakawa,
suna da uniform, sai yace shikenan zai binciko
yaji duk yadda akeyi a shiga amma in fara jin
ra'ayin yayana. Yayana ya amince da
shawararmu kuma yaji dadi musamman da
musbahu yazo har kofar gidanmu ya sa akayi
masa sallama da yayana hussaini ya kara yi
masa bayani. Yace zai taimaka min da wata
dawainiyar kudin makarnatar sai ya amince
yayi masa godiya. Musbahu da yayana ne suka
hada gwiwa suka bani duk kudaden da ake
bukata na shiga makarantar koyar aikin jinya
ta malam aminu kano dake unguwar court
road. Karatun shekara uku ne a shekara ta uku
ne muke zuwa asibiti koyar aiki don haka
karatu na yi tayi haikan, ban taba samun
matsala ba cinye jarabawata nake yi koda
yaushe. A asibitin malam aminu kano ake horar
damu koyar aiki (attachment). Ina zuwa
kkullum daga unguwarmu sharifai zuwa court
rd akan acaba saboda idan nace zan hau bus
zan bata lokacina zanyi in makara. Kudin
acabana kit da kit babu canji wata rana ko
purewater zan sha sai dai kawayena su saya
min. Duk da idan za'a je sayan abinci ko shan
lemo sai in gudu bana binsu saboda kullum sai
dai su saya min, ni kuma na fara jin kunya sun
gane bani dashi. Kawata khadija sani ismail
kadai wacce bata gajiya da taimakona kuma
duk sanda tace muje cin abinci naki zuwa ko
na sulale na gudu sai ranta ya baci, har tayi
fushi dani. Sai inyi tayi mata bayanan karya in
kirkiro uzurin dana je nayi ba guduwa nayi ba
sai ta ki yadda tasan karya nakeyi. Ba ita nake
ji ba, sauran kawayenmu nakeji don suna nuna
min bakin hali daga baya kuma in dinga jin
kananan maganganu cewar na cika san banza
kullum bana fitar da kudina ina sayawa kaina
abu balle in sayawa wani, sai dai ni kullum a
saya min. Rashin sani yafi dare duhu, KALLON
KITSE sukeyi wa ROGO. Hakika ni mai yawan
tsafta ce in kula da fararen kayan makaranta
ta, kullum tsaf dani, ina kalkale jikina tas a
wanke ga karin guga. Gani nafi duk 'yan ajin
mu kokari yawanci ni nake basu amsa. Khadija
bazata iya rabuwa dani ba dan bata da kokari
sai dai gata, tunda iyayenta suna da hali. Duk
wasu manyan littattafai na karatu (text book)
babanta yana saya mata duk tsadarsu, sai nafi
morarsu don ni ce mai hazakar karatun ba ita
ba. Da taimakon Allah da taimakon khadija sani
nake cin jarabawa dan ba zan iya sayan
littattafan nan masu tsada ba. Badan Allah Ya
sa na iya kitos ba ina yiwa makwabta, da wata
rana ma ba zanje makaranta ba saboda duk
ranar da yaya hussaini ya tashi bashi da kudi
sai yace in hakura kada inje makaranatar randa
ya samu naje. Ni kuma bana so inyi fashi, da
kudin kitson nake harhadawa in tafi duk da
kitso a unguwar bashi da tsada, kan manya
naira talatin ko arba'in, na yara kuwa naira
ashirin ko goma ne. Ban taba fadawawa
kawayena sirrina ba, duk da yawan kawayen da
nake dasu a ajinmu mata da maza, sai dai ayi
hayaniya wasa da dariya a watse, ina taka
tsantsan da harshena a koda yaushe. Babu
wanda a cikinus ya san yadda gidanmu yake,
basu taba zaton haka nake rayuwa ba, sai dai
sun fahimci wani abu akwai wasu matsaloli
wanda ba zasu boyu ba. Suyi ta zargi da sake
sakensu a ransu su kadai, ni dai bazasu ji daga
bakina ba kuma ba zasu iya tara ta su
tambaye ni ba. Ni daman bana zuwa gidan
kowa balle azo gidanmu, mu hadu a abakin
gate ne mu rabu idan an tashi. Bana jin dadin
rayuwata a wannan bangaren saboda bani da
wata takamaimiyar kawa ko masoyin da zan
amayar musu da radadin da zugin matsalolin
da suke addabata. Kawata guda daya, itace
aminiyata, yayata, masoyiyata wato matar
yayana abida. Muna zama ni da ita mu raba
dare ko mu yini muna tattauna matsalolinmu,
koda yaushe ina samun nutsuwa da kwarin
gwiwa idan abida ta bani hakuri akan talaucin
da na tsinci kaina da shawarwari, sai inji sanyi
a raina, tawakkali ya kama zuciyata sai inji ta
tuno min da nasihohin da mahaifina yayi min a
baya. Idan nayi haka sai in dawo da walwalata,
ni burina guda daya ne shine in gama karatuna
in fara aiki in taimaki kaina, in taimaki 'yan
gidanmu. Babbar matsalar ma da tafi damuna
shine zaman cakudi a gidanmu, cikin tsagoron
kazanta da cinkoso, babban burina ba wuce
inga mun bar gidan nan da umguwar mu canja
gida ko haya ce dai mu kama gidan da muke
mu kadai. Dakina daya da yara, ga dakin dan
karami mun cunkushe gashi su dukka yaran
abida fitsarin kwance sukeyi dan haka sun ruba
katifar sai zarni take dan haka na hakura da
katifar na bar musu. Na koma kwana akan
tabarma, idan na tashi da safe sai inyi salla
akai in nada in jingine a lungu sai zan sake yin
wani sallar sannan in shimfida. Har yanzu
kayana a jakar bagco yake a gefen shimfidata,
rayuwata ba irin na 'yan matan 'yan boko bace,
tamkar a kauye nake ba'a birni ba. Ko inyi
tunanin shiga hanyar banza, ban taba sha'awar
makalewa gidan kawaye ba ko arar kayan
kawa, na rike talaucina na kama kaina bana
sha''awar kayan wani. Daga makaranta sai
gida, a gidan ma nafi zama a daki kullum ina
karatu. Idan kaga na fito aiki nazo taya abida,
wankan 'ya'yanta , tsarkinsu ko aikin girki. Sai
'yan gidanmu da sauran 'yan unguwa suka
shiga yimin shaidar girman kai ne dani dan ni
'yar boko ce, basa ganin fara'ar da nake yi
musu. Kullum ina gaishe su ko basu ganni ba,
tabbas mutum ba'a iya iya masa, saboda dan
Adam ya kasance mai butulci ne. BABI NA UKU
Wata rana ranar litinin da misalin karfe daya na
rana muna cikin a sibiti, a bangaren marasa
lafiya muke wadanda aka kwantar dasu
sakamakon wasu kurajen da suka feso a
jikinsu. Muna biye da ma'aikaciyar jinya matron
maryam tana nunnana mana yadda ake aiki,
domin neman karin bayani sai tace bari ta
hada mu da kwararren likita wanda ya kware a
bangaren fata. Ta tura wani daki ta shiga
muma muka bita a baya da alama dakin
daukan darussa ne sabida naga kujeru ne zalla
da allo makale a jikin bangon. Kamar yadda
naji ta ambaci sunansa, dr shureim imran. Mun
iske shi tsaye a tsakiyar ajin tare da wasu
daliban likitoci guda 3 maza biyu, mace daya
da alama sunzo sunyi masa tambayoyi ne akan
wasu abubuwan da basu gane ba. Bayanai
yake yi musu cikin harshen turanci kai kace
baturen america ne, kalmomin kimiyyar
(botanical names) da yake ta ambato yana
jerowa layi layi da ka ba tare da yana duba
littafi ba, kai kace shine ya lakaba musu sunan
don ya haddace. Muna sake kutsawa cikin
ofishin yayin da zazzakar muryarsa, daddada
take sake shiga kunnuwanmu sai duk muka
kagu mu isa gabansa don mu kalli fuskar mai
muryan nan daddada. Kasancewar kofar ta
cushe muna shiga don muna da yawa, ga
dalibai likitoci nan suna kokarin fitowa sun
gama daukar darasin. Kowa ya kagu yayi ido
hudu da mai daddadar muryar nan, keyarsa
kawai na fara hangowa daga nesa sai na
tabbatar bakar fata ne dan uwana saboda ban
hango jan kunne ba da farin gashi irin na
turawa ba. Bakin gashi ne tattaura irin namu
na hausawa, sai dai gashin a gyare yake yana
shekin mai kuma ya kwanto lambar zuwa
karshen keyarsa. Kansu babu hula, yana sanye
da bakaken kaya riga da wando (suit), farar
riga mai dogon hannu daga ciki, ya daure
wuyansa da jan kyalle wato necktie. Dana
matso ciki sai na fara hango gefen fuskarsa,
wata lafiyayyiyar fata na fara hangowa mai
dauke da launi mai tsananin kyau. Irin kalar da
take tsada a duniya wato hasken duhu
(chocolate color). Ko dana sake samun daman
na matso kusa dashi sai ga gefen fuskarsa tar
ina gani wato idonsa daya da gefen hancinsa,
sai kawai naji wata mummunar fadywar gaba
ta far min ni ma bansan dalili ba har wadanda
ke kusa dani zasu iya jiyo karar ajiyar zuciya
danayi. Tunda nake a rayuwata ban ta ba ganin
irin wadannan dara daran idanuwan ba masu
tsananin haske daga ciki, da bakar kwayar ido
mai tsananin baki, aka zagaye idon da wasu
gashin ido da gashin gira masu yawa da
tsananin baki, ya gyara su sunyi kira mai kyau
suna sheki. A nutse ya waiwayo da kyakkyawar
fuskarsa gaba daya ya dube mu, bani kadai ba
duk wata 'ya mace da take wajen sai dataji a
ranta dama ace wannan kadarar mallakarta ce.
'Yan uwansa maza ma sai da suka raya a
ransu dama ace sune shi, ga kyau ga ilimi.
Ashe a da dana ke hango gefen fuskarshi ban
hango komai ba, kyau mai sunan kyau sai ka
kalle shi gaba dayansa daga kafarsa zuwa
kansa. Dogon mutum ne sosai ma kyawun
sura, bashi da kiba da yawa, haka bashi da
rama. Yayi kama da irin bakaken turawan nan
da ake kira african American, hukuncin da na
yanke masa kenan dan ko kusa baiyi kama da
'yan nigeria ba! Tabbas ruwa biyu ne suka
hadu suka same shi bakar fata da farar fata.
Duk da tashin hankalin da na shiga da naji
bayananta sai nayi murmushin karfin hali nace
subhanallah! Bai kamata kice zaki bi kowacce
hanya ba gara ma kice zaki bishi da addua in
da alkhairi Allah ya yi. Khadija tace bawai ina
nufin zan fita daga musulunci ba akansa ba,
amma fa dole saina saka malamaina sunyi min
addua. Na fahimci maryam ahmed da mansura
mahmud suna sonsa kin san su da bin
malamai, in ban dage ba sai sun janye
hankalinsa. Gaskiya tunda nake a duniya ban
taba ganin Kyakkyawan bakar fata irinsa ba, ko
kin taba gani? Na girgiza kai nace ban taba
gani ba, amma shima yana ji da kansa dan
yasan ya hadu kuma mata suna nuna masa
haka. Ba kya ganin 'yan matan nan medical
student suna ta kawo hare harens garshi?
Khadija tace tabbas na gani, shiyasa nace sai
nayi da gaske fa. Ai mu uku ne kadai muka
amayar da maitarmu a waje, nasan mata da
yawa sun dasa a ajin fada ne kawai basu yi ba.
Kin burge ni aisha umar, sai naga kwata kwata
ba ya gabanki, ko a bayan idonki muna yabonki
don kina kama kanki bakya shiga rigimar da
tafi karfinki. Sai kawai nayi murmushi nace a
raina kallon kitse kike yiwa rogo, aini zuciyata
tuni ta kunsa min abinda zuciyoyinku basu
kunsa muku ba. Tabbas nasan burina da fatana
akan dr shurain yafi nasu. Aisha umar kalli
motar can, inji khadija yayin da ta matse 'yan
yatsunna don gigicewa. Na juya da sauri, sai
naga wata dankareriyar mota baka mai farin
gilashi. A cikin motar kuma zankadeden mutum
ne, sanye da farar riga da bakin gilashi a
fuskarsa. Ya kalle mu, muma kallonsa mukayi
sai ya kawar da kai ya fisgi motarsa da gudu
ya nufi gate din fita. Na dubi motar har da
waiwaye sannan na juyo na dubi khadija nace
motar nan ta hadu, haka mutumin da yake
cikin motar ma ya hadu. Wanene shi? Tace au
baki gane shi bane? Dr shuraim ne likitan da
muke zancensa yanzu. Dan halak yaki ambato.
Sai nace kai bashi bane, ai shi bakar suit ya
saka. Tace bakar ta saman ya cire, ya bar
farar ta ciki. Baki shaida jan neck tie din bane?
Sai nayi shiru saboda haduwarsa tafi karfin
tunanina, sama ta yiwa yaro nusa ba zai iya
tabawa ba sai dai ya daga ido ya hango. Sai
na tuna ai Allah ne ya halicce shi wanda ya
halicce ni, babu wanda yafi wani a wajensa sai
wanda yafi bauta masa don haka na daina
raina kaina. Na kudira a raina zan sake rikar
addinina yadda zan sami babban rabo a lahira,
koda kuwa ban sami wanda nake so a duniya
ba. Zuciya ta fara warwarewa daga kuncin
daya damke ta na son maso wani. Tun ina
sauraron surutun da khadija takeyi har na
daina ganewa, burina kawai in ganni a gida na
shige lungun dakina. Ina hau yamutsattsiyar
tabarmata in kudindina inyi ta aiyano ni tare da
abin kauna ta shuraim. Ina daukar jakata sai
nayi musu sallama na nufi gate din fita a
sanyaye ina tafe ina tunani. Na fita waje na
tsayar da acaba kamar kullum na haye ya kai
ni kofar gidanmu. Tun daga zauren gidanmu
nake cin karo da matan gidan suna ta
hidindimunsu na saye da sayarwa da surutin da
suke yini suna yi, ayi gulmar wannan, a zagi
waccan, yau sai suka ganni ba kamar kullum
ba. Da bayan na gaishe su sai in dan zauna ayi
barkwanci sannan in wuce cikin gida, yau babu
kanta da kyar nake magana, sauri kawai nake
yi in shige ciki. Sunyi zaton yunwa nakeji, har
suke zolayata da cewa abida ba ta nan, ba'ayi
abinci ba. Na wuce abu na, na iske abida tana
dafa a binci a risho. Tana ganina tayi kasake
tana kallona, ta san akwai damuwa tunda bata
jiyo muryata ba, bata gano murmushina ba
saboda ina da yawan dariya. Ta dube ni tace
aisha farida kalau kuwa, ko allura zakiyi wata
mara lafiya ta kwace ta tsira miki? Nayi dariya
nace haba dai ayi haka kuwa? Bana jin dadi
dai. Tace Allah ya sawake, shiga daki kihuta
kafin abinci ya dahu ki ci zaki murmure. Ina
shiga daki na cire uniform dina sai na daura
tawul na dauki kwandon wanka zan je in watsa
ruwa dan inji dan sanyi a jikina saboda na
kwaso rana.sai na ga abida ta shigo tana
dariya tace da ni "af ashe wanka zaki yi da
labari zan baki mai dadi kuma marar dadi." Na
ajiye kwandon wanka na jawo hannunta muka
zauna.Na ce bani in sha ai na fasa wanakan,me
ya faru? Ta yi dariya tace labarin musbahu
tsohon saurayinki da matarsa lubabatu zan
baki daman,aure dai yaki dadi har ya yi mata
saki daya dazun nan aka yi rigimar. Lungun
nan ya cika da mutane mahaifiyarsa dai sai a
taya ta da addua don ta cika naci,ce masa tayi
idan ya sake furta kalmar saki sai ta tsine
masa dole sai ya zauna da lubabatu tasan
akan aisha farida yake yi mata wulaqanci kala-
kala. Tayi rantsuwa tace ko bayan ranta idan
ya saki lubabtu ya aure ki Allah ya isa. Kin ji
wata kiyayya sabuwa ko? Na yi murmushin
karfin hali nace,Allah ya kyauta,ta ma daina
kokarin tsinewa danta a kaina tuntuni na yi
masa sallama nace ya bi mahaifiyarsa don ya
sami rahama. Ya na aiko min da kudi tun ina
karba sai na daina karba daga baya idan ya
aiko sai in mayar da dan aiken in ce bana so
don zaman lafiya. Abida tace haka ya fi,ai gara
da kika yi. Masa haka kin taimake shi. Ni na
dauka ma zancen kika ji tun daga zaure da na
ga kin shigo ranki a bace. Amma fa ki godewa
Allah AF saboda kin samu kyakkyawon yabo a
ung nan. Ba kiji. Yadda kowa yake yabonki
ba,ake ta tsine mata ita kuma. Kowa ya dinga
cewa me ye laifin AF har da bata so danta ya
aura? Yarinya mai nutsuwa da hankali mai ilimi
da fara'a tana gaishe da mutane. Ta zo ta
tauyewa yaro rayuwarsa ta cusa masa
dakalkalalliyar macen da ba ta da tsari. Nace
au daman an sanni da yawa a ung nan haka?
Abida tace "ji ki da Allah da neman magana
waye bai sanki ba,musamman da kika shiga
skul of nursing kina karbar haihuwa kina allura
a cikin ung sai ki ji kowacce mata tana cewa
wajen aisha likita zan je ta rubuta min magani.
A nan dai muka tashi muka rufe hirar nan
zuciyata cike da tausayin musbahu ba don
mahaifiyarsa ba ta sona ba da na aure shi mun
zauna mun rufawa juna asiri,in huta fadawa
cikin hatsarin da nake shirin jefa kaina. Bayan
na yi wanka na ci abinci sai na wartsake na
shiga cikin matan gidan muna ta hira har ma
na ji na fara mantawa da abunda yake damuna
a zuciyata. Sai da kowa ya shiga barci dare ya
fara nisawa sai tunanin Dr shureim imran yace
da wa Allah ya hada ni in ba da ke ba,sai na ji
gaba daya daya zuciyata ta kasa sukuni. Da
zarar na rufe ido sai in ganshi tamkar a zahiri.
Sai na yi ta yaki da zuciyata ina ture shi daga
tunanina.kai in takaice maka a cikin satin nan
ban gane kaina da kaina saboda tsananin
tunaninsa. Idan na je asibiti bana walwala haka
idan na dawo gida ba na jin dadin zuciyata
kada ma dare ya ji labari sai ka ga idona ya
wartsake garau na burma tunanin DR shureim
imran. Da gaske sonsa nake,so ba da wasa
ba.tun ranar kuma ban sake ganinsa ba sai dai
kullum sai khadija ta yi min labarinsa.Albishir
din da ta yi min shi ne ta sami lambar wayarsa
amma tana tsoron kira don tana ganin zai yi
mata wulaqanci. Ta shaida min ta rabawa
malamai kudi ana ta ragargaza mata addu'a ta
koina,a kalla ta raba musu zunzurutun kudi ya
kai N25,000 so take sai an gama addua tas
sannan ta kira shi dolensa ya amince. Sai na
sake jin jikina ya yi sanyi na sake yi wa
zuciyata fada da ta yi ta- ka tsan- tsan ta
daina cusa abunda zai iya kasheta.idan da
khadija. Zata lura duk sanda ta fara yi min
zancen Dr shureim sai jikin yayi sanyi kuma na
kan rasa amsar da zan bata ko shwara.
Kallonta kawai nake tsayawa ina yi yayin da
zata iya ganin hawaye yana cika min ido sai
inyi sauri in mayar da shi ina tauisayinta na fi
tausayin kaina domin na san zuciyata ta fi tata
shiha hatsari kuma ta fini sanin yadda zata yi
da kanta. Ni ko wayar ma bani da ita babu
kudin saka kati balle in saka rai ko zan karbi
lambar in kira inji dadi. Na zama na rasa
walwala ta ko abincin kirki bana iya ci na
dukufa da adduar Allah ya yaye min don sonsa
ya zame min ciwo.naji duk na tsani kaina karfi
da yaji nake fisge tunaninsa daga cikin
zuciyata.amma abu ya ci tura sai ma karuwa
yake yi. Idan naki tunaninsa karfi da yaji a ido
biyu da zarar na kwanta sai nayi mafarkinsa,
sai gani cikin dare ina kuka wiwi ina sallah da
adduar Allah Ya yaye min, Allah Ya kawo abin
da zai sa inji na tsane shi ma. Duk satittikan
nan da nayi ina jinyar sonsa ko a hanya ban
hadu dashi ba balle ma in ji dan sanyi a raina,
ina so ina kara ganin suffarsa don in kawata
tunanina domin kamanninsa suna kokarin
disashe min. Ranar talata da sassafe ina
dirowa daga kan acaba a kofar shiga gate din
asibitin aminu kano sai na yi kicibus dashi a
cikin wannan tsaleliyar motar tasa. Na
waiwaya da sauri na dube shi yayin da shi ma
yake dubana har da rage tafiya amma fa duban
da yake yi min bana kauna bane, hararata yake
yi game da nuna tsana mai yawa a bayyane.
Sai yayi tsaki ya girgiza kai ya kada sitiyarin
motarsa yayi wucewarsa. Sai na dankare a
tsaye ni ban ciro kudin mai acaba na biya shi
ba, ni banyi gaba ba balle ace mantuwa nayi.
Bani kudin mana, inji zalamamman dan acba.
Na ciro kudin na mika masa ya karba yana
shirin ya miko min canjina naira ashirin sai na
girgiza kai nace kayi min sadaka, ku taya ni
addua don bani da lafiya. Sai ya tsaya yana
kallona cike da tausayi yace to ko gida za a
mayar dake idan ba zaki iya aikin ba? Ai komai
sai da lafiya akeyi. Nayi murmushin karfin hali
nace ciwona addua yake bukata ba hutu ba, ko
shan magani. Sannan maganin ciwon yana
cikin asibitin nan, idan na koma gida ai babu
maganin a can. Yace gaskiya ne duk wani
magani yana asibiti. Allah Ya yaye miki
kowanne irin ciwo ne wannan. Na amsa da
amin nagode. Na juya a sanyaye ina tafiya
kamar kwai ya fashe min a ciki. Ina mai
matukar mamaki da takaicin kallon wulakancin
da yayi min. Na kasa tantance ni kuwa laifin
me nayi masa a rayuwata da ya tsane ni,
yaushe ma ya taba ganina banda sau daya
shima a rubibi, yaushe zai ganeni? Aisha farida
umar, karaf naji an kira sunana daga gefena.
Nayi firgigit na juyo da sauri. Khadija sani
ismail na gani ta tsaya da motarta hience 2008
ta sauke gilashin wundonta kasa, na tsallako
inda take na bude gaban motar na shiga. Ina
kokarin gaishe ta sai ta katse ni cikin murna
take magana tace albishirinki? Na kira Dr
shuraim imran jiya ya dauka, sai dai mun fara
magana yace in bashi bane wanda nake newa
wrong number ce, ya katse wayar. Sai na tura
masa sako nace ni dalibarsa ce , na kira in
gaishe shi. Kinga amsar daya bani. Sai ta miko
min wayarta, sai hannuna ya hau kakkarwa,
har sai da ta tsaya tana kallona saboda gaba
daya jikina bari yake yi. Na duba na karanta
sai naga ya runuta "thanks". Sai na lumshe ido
don dadin ganin rubutunsa da lambarsa, naji
dama nice nake yi masa waya da tura sako da
ko amsar da ya bawa khadija na samu ya bani
kadai na gama jin dadin rayuwata, ta isheni
abin farin ciki. Na bude baki nayi magana da
kyar, nace lallai kinji dadi. Tace dadi ka-n jiya
ai jar da barci da munshari don samun
kwanciyar hankalin dana ji. Dole in karawa
malamaina kudi su sake dagewa da addua
sosai. Nayi ajiyar zuciya nace ya san sunanki?
Tace bai tambaye niba, ki kyale shi sai a
hankali, dan wulakanci ne fa wannan da kike
gani. Muka isa bangaren da muke,mun bar
bangaren masu kuraje mun koma bangaren
yara. Muna shiga ciki muka iske 'yan ajinmu a
tsaitsaye kowannensu da dan littafinsa a hannu
da biro, da alama matron ta fara bayani akan
wannan yaro mai ciwon amai da gudawa. A
tsaye nake ina kallon bakin yaron a hannun
mahaifiyarsa yana tsala kuka, amma ban
fahimci bayanan matron ba, ko kadan ban san
me take cewa ba. Tunanina kawai daman ace
dana ne wannan jaririn muka haifa tare da Dr
shureim imran. Sai da ta gama bayani ta juya,
naga an bi ta duuu a baya zuwa gadon wani
yaron marar lafiya, shi kuma mai ciwon
pneumonia ne, sai na ja birki na tsaya cak na
ki bin su saboda kafafuwana da kwakwalwata
sun gaji ba zasu iya daukar abubuwa guda biyu
ba, tunanin dr shuraim imran shi yafi matsa
min, gara in yi shi shi kadai, shi yafi
muhimmanci a gareni don haka na juya na nufi
ofishinmu inda muke zama mu huta da ajiye
jakunkunan mu. Ina shiga sai naga maryam
ahmad tayi kasake a zaune akan kujera tana
matsa wayarta, fuskarta babu walwala. Nayi
mata magana sai naji da kyar take amsa min.
Na tambaya cikin damuwa maryam lafiya? Me
ke damunki? Baki da lafiya ne. Ta girgiza kai
tace lafiya kalau. Ni dai na dame ta da
tambaya lallai sai ta fada min abin dake
damunta. Ko a mafarki ban zata amsar da zata
bani ba kenan. Budar bakin ta ke da wuya tace
waye inba dr shureim ba? Sai naji gabana ya
fadi daf! Na fada a gigice me yayi miki? Sai ta
dube ni kwalla ta cika mata ido tace aisha
farida na yarda dake shi yasa zan fada miki
sirrina, na san kina da rike sirrin jama'a ba
ataba fada miki magana kin yada ba, na san
zaki bani shawarar da ta dace. Ina matukar
son dr shureim imran, har zuciyata sai naga da
in tsaya labe labe shi ma mutum ne kamar ni,
me zai hana in tunkare shi in fada maas tunda
ni bazawara ce, kunyar me zanji? Duk inda
mace ta kai na kai, ina da kyauna da ilimina da
arzikina, gani 'yar asali karewa ma 'yar
sarauta. Dazun nan na tare shi a bakin ofis
dinsa yana ganina ya bata rai na gaishe shi ya
amsa da kyar, ya bude kofar ofis dinsa ya shiga
sai na bi bayansa. Muna shiga sai ya daka min
tsawa yace lafiya? Nace nazo in gaishe shi ne.
Ya fada a fusace yace to naji sai anjima. Nace
kuma ina da magana da nake tafe da ita. Sai
yace fadi maganarki ki fita. Nace so nake mu
saba in karbi lambarka, ka karbi tawa. Ko rufe
bakina banyi ba yace bana bukatar in saba da
ke, haka bana son lambarki, sai anjima. Sai ta
fashe da kuka ta rungumeni. Bansan sanda na
dora hannu aka ba nace mun shiga uku, Allah
Ya jikaina. Maryam ta dago cike da mamaki
tace aisha farida menene? Nayi sauri na gyara
zancen nace ai da kika fada min abin da yayi
miki sai naji kama zan hadiyi zuciya in mutu,
shine nace Allah yaji kaina. Tace meye
shawararki? Shawarar da na ba wa kaina ita
nake kokarin in bata, itace tayi hakuri ta rabu
dashi, taci gaba da addua. Allah ya yaye mata
sonsa ya hadata da mai sonta wanda yafi shi.
Sai tace a'a ai ba isa ba, sai ya san ita yayi
ma wulakanci. Ai ko zata salwantar da
dukiyarta kakaf sai ta rama abinda yayi mata.
Sai tayi masa asirin da sai ya kwanta a kasa
ta murje shi da takalmin kafarta. Ban sake
magana ba na tsaya kawai ina kallonta, yayin
da naji tausayinsa ya kama ni, bana so a
wahalar min da abin kaunata. Daga nan na
kara cire ran mafarkin samun dr shuraim imran
a rayuwata. Naci gaba da jinya ina jiran ranar
ajalina domin mutuwata ce kadai zatayi min
maganin ciwon nan. DUK KYAN TAKALMI 7 Sai
ta fashe da kuka ta rungumeni. Bansan sanda
na dora hannu aka ba nace mun shiga uku,
Allah Ya jikaina. Maryam ta dago cike da
mamaki tace aisha farida menene? Nayi sauri
na gyara zancen nace ai da kika fada min abin
da yayi miki sai naji kama zan hadiyi zuciya in
mutu, shine nace Allah yaji kaina. Tace meye
shawararki? Shawarar da na ba wa kaina ita
nake kokarin in bata, itace tayi hakuri ta rabu
dashi, taci gaba da addua. Allah ya yaye mata
sonsa ya hadata da mai sonta wanda yafi shi.
Sai tace a'a ai ba isa ba, sai ya san ita yayi
ma wulakanci. Ai ko zata salwantar da
dukiyarta kakaf sai ta rama abinda yayi mata.
Sai tayi masa asirin da sai ya kwanta a kasa
ta murje shi da takalmin kafarta. Ban sake
magana ba na tsaya kawai ina kallonta, yayin
da naji tausayinsa ya kama ni, bana so a
wahalar min da abin kaunata. Daga nan na
kara cire ran mafarkin samun dr shuraim imran
a rayuwata. Naci gaba da jinya ina jiran ranar
ajalina domin mutuwata ce kadai zatayi min
maganin ciwon nan. Abida ta lura bana cikin
walwata kullum ina cikin damuwa, ta
tambayeni har ta gaji na kasa fada mata
wannan badakalar cutar da zuciyata ke fama
da ita, babu abinda nake boyewa abida amma
wannan dai ba zai fadu ba. Na gwammace a
dauki gawata a dinga tunanin fuju'an na mutu
babu ciwo ni da Ubangijina munsan abinda ya
kashe ni. Sai na shiga tunanin ko shi yasa ya
dinga hararata saboda masu irin uniform dina
ne suke damunsa ya zata nice? Haka ne ma
babu tantama ya dauka khadija da maryam ce
ni. Bansan takamaiman ofis dinsa ba, don haka
kaina tsaye na tunkari ofishin dr lukman likitan
kwakwalwa dauke da file din matron maryam
ta umurce ni da in kai masa. Ofis na uku tace
min daga hannun dama, don haka kaina tsaye
nan na kwankwasa na shiga tun kafin a bani
izini, saboda saurin da nake yi don inyi in koma
wajen daukan darasi. Abin da nagani a cikin
ofishin shi ya firgita ni har sai da kowa ya gane
na tsorata, dr shureim imran na gani a zaune a
kan kujera da laptop dinsa akan table yana
danne danne, maimakon mai ofis din dr
lukman. Wace wannan? Ya kika koma da sauri?
Wa kike nema? Tambayoyin da na jiyo ana yi
min kenan daga cikin ofishin ni kuwa tuni nayi
waje. Na rufo kofar a hankali na fara sanda zan
juya, jikina yana rawa ina gudun wulakancinsa.
Wata murya naji an kira ni, har na kai kan
barandar waje. Ina juyawa naga mai gadi ce
(security). Tace inje inji doctor. Hankalina ya
tashi kan kace kwabo na fara gumi tamkar ana
gasa ni a garwashi. Ofishin dr lukman kuwa ta
nuna amma ban ga kowa a bakin kofar ba,
kuma har yanzu kofar a rufe. Ni kaina ban san
ayoyin da nake karantawa ba har na isa bakin
kofar, na tura kofar na shiga ina mai jan dan
gajeren hijabina ina rufe rabin fuskata. Ina
sauraron yadda Allahi Zaiyi dani kuma. Nayi
sallama na shiga amma na kasa daga ido in
dube shi. Yaya kika leko kika koma? Wannan
karon kuma wata sabuwar murya naji daban ba
irin ta dazu ba, sai na dago ido da sauro na
dube shi. Dr lukman na gani zaune yana danna
laptop dinsa ba dr shureim imran bane. Sai
mamaki ya rufe ni a zahiti har ya fahimci haka,
na tabbatar son dr shureim yayi min yawa da
har ya fara yi min gizau. Nayi murmushi na
dauka ba ofishin na shigo ba shiyasa na juya.
Na matso na mika masa file din yana dubawa
ya girgiza kai yace me yasa matron zatayi min
haka, ni ba wannan nace ta aiko min ba. To
iyakacin kalmar da na fahinta kenan daga nan
na daina sauraronsa saboda dr shureim imran
na gani ya fito daga bandaki da alama alwala
yayi don jikinsa daruwa. Kallo daya nayi masa
na zazzare ido sai na sunkuyar da kai kasa
yayin da jikina ya hau rawa, zuciyata ta hau
tsalle tana oyoyo ga abincin da na dade ina
yunwarsa. Shine ma dai yayi min kallo sau biyu
ya watsar ya shige lungu ya shimfida abin
sallah. Kafin ya tayar da sallah dr lukman ya
tsokano shi da ci gaba da hirar da suke yi.
Yace wato dr shureim ka tsani ka ga 'yan
acaba kenan? Yayi dariya yace yadda naki
mutuwata haka naki inga mutum ya hau acaba
musamman mace ina takaicin wannan abu, sai
inga ba gara mutum yaje ya kwanta a sibiti ba
yace a zuke jininsa gaba daya a rabawa
marasa lafiya saboda ya mutu, gara yace a
yayyanki duk sassan jikinsa a raba sadakatul
jariya. Dr lukman ya kwashe da dariya har da
buga kafa a kasa. Yace haba dai doctor har
abin ya kai haka? Yace haka ne mana, saboda
yadda zaka ga suna kutsawa a jikin tirela. Na
fada maka fa acaba ne ya kashe san uwa na
uwa daya uba daya, kuma ina tsaye ina kallo
ya kutsa dashi karkashin tirela. Daha cewa dan
acaba kai ni can in siyo batir motarmu ta mutu
a hanya, shikenan ya warce shi sai karkashin
tirela sai gawarsu aka kwakulo. Tun daga
lokacin idan naga mutum akan acaba sai kaga
na bar abun da nakeyi na rike kai, ina taya shi
da addua har sai na daina hangensu.
Musamman mace sai inji kamar in fasa ihu ince
ga motarta nan zo ki hau na tafi da kafa.
Wadanne irin maza ne zasu bar matarsu taje
ta hau acaba, ko bashi da mota ai sai ya bata
kudin drop har inda zata je a mota. Sai a
lokacin na tabbatr da dalilin da yasa yake
hararata rannan ashe, don na sauko daga kan
acaba ne. Ya tayar da sallah, dr lukman ya
miko min file biyu da wanda nazo dashi da
wanda yayi cike cike yace in mayar mata ince
bashi ba, koren file din zata bayar. Na durkusa
na karba na fito da sauri, yayin da zuciyata ta
cika da murna saboda yau taga abinda take
muradi. Sai ya sake burge ni dana ga yana
sallah, naji dadi danaji dalilin hararar da yayi
min rannan ba tsana ta yayi ba. Sai na fara
tunanin hanyar da zanbi in shiga harkarsa ba
tare da yayi min wulkanci ba. Naci sa'a kuwa
ina zuwa nayi mata bayani sai ta miko min
koren file din da yace ta bani in kai masa. Na
taho hanya ina farin ciki hade da fargabar abun
da zanje in tarar. Na isa ofishin sai faduwar
gaban da nake ji ta karu, na fara karanta
ADDUAR WANDA YAJI TSORON MUTANE
"Allahummakfinihim bimaa shi'ita" (Ya Allah Ka
isar mini dasu da abin da kaso). Ina tura kai
sai nayi sallama. Dr lukaman ne ya amsa, har
yanzu gogan nawa yana kan abin sallah ya idar
amma yana jan carbi. Na dago ido na dube shi
a hankali, sai muka hada ido ni dashi, bansan
wanda ya fara kawar da kai gefe ba. Na matsa
lungu ina jiran dr lukman ya gama dubawa sai
da na tabbatar lungun da na shige ko ya daga
ido ba zai ganni ba. Na nutsu kai kace a gaban
sarki nake, yadda nake sanda kai kace da
kayan sata aka kamani, za'a yanke min
hukunci. Wayar dr shuraim imran ce take ruri,
kidan ringing tone din yana tashi a hankali,
wakar soyayya ce ta celen dion mai taken come
bake to me, sai ya danna amsa. Kalmar da ya
fara ambato a cikin harshen turanci ita ta
gigitani, tasa na dimauce sai na tsinci kaina
har da kwalla mai radadin fita saboda kishi.
Daga ji ba sai an fada min ba da matarsa yake
magana, wacce yake tsananin so da kauna fiye
da kowacce 'ya mace a duniya. Tunda nake a
rayuwata ban taba jin namijin bahaushe da ya
fadawa matarsa wannan kalma, ko da yake ni
'yar gargajiyace na tashi cikin 'yan gargajiya
tsakanina da matansu sai ke zo nan, dauko,
dafa, wanke, goge. Kullum sai hantara dube ki
ballagaza, kazama, kwadayayyiya. Haka na
saba ji tun tashina tsakanin miji da matarsa.
Amma dr shuraim imran yace da abar
kaunarsa, salam my dear, my heart, my life
how are you and how is your trip? Hope cool.
Duk da ban jiyo abinda zata fada ba itama da
daddadar kalma ta mayar masa. Ya juye
harshe sai turanci yake zazzagowa ya tambaya
kuna ina yanzu? Sai ta bashi amsa, banji
amsar ba sai yace ok kun bar london yanzu
kuna amsterdam? Awa nawa zaku yi transit
din? Ta fada masa, sai yace karfe goma dai dai
zaku iso kano, ni kuma karfe tara a airport zata
yi min da izinin Ubangiji. Ina kewarki, ina
babyna? Can sai naji ya fara magana cikin
muryar yara yana yiwa yaro wasa, sai na
tabbatar 'yarsa ce itama da turancin yake mata
magana. Kalmar da ya fada ta karshe daga ita
ya kashe waya itace "I love u baby, I miss u
too, I am eager to see ur beautiful face. Take
care bye". Na dinga dauki ba dadi da zuciyata
don so take ta tsinko fado kasa ta ragargaje
don tashin hankalin da ta shiga. Dr lukman ya
dube shi yayi dariya yace madam ce? Ya
lumshe ido tace madam ce ita da baby sun
taho yanzu suna amsterdam sun baro london.
Kaji matar da take makaranta shine ta bar
karatunta ta biyo ni. Dr lukman yace ah da
gaskiyarta, yaushe zata zauna a can mijinta
yana nan? Dr shureim imran yace toh ai
matsalar ba zata iya zaman bane a nan, tana
yin sati biyu a daddafe zata fara magiya inzo
mu koma london, ita ba ta zauna tayi karatunta
ba a can, ita bata bar yarinya tayi karatunta
ba. Dr lukman yace ai da ta dinga barin
yarinyar a gidan iyayenta ba suma a london din
ba gidansu yake? Sai iyayenta su rike muku
'yar kai da ita ku karaci walagiginku tsakanin
london da Nigeria. Dr shureim imran yayi dariya
yace toh ai yarinyar harta fi uwar damuwa ai
ita tace take so uwar tace sai an kawo ta ta
ganni, sai tasa uwar tayi min waya fiye da sau
goma a rana ace min ga baby tana kuka, wai
tana son magana dani. Ina daukar wayar kasan
abinda zata ce min? Daddy I miss you, sai ta
kashe waya shikenan. Su dukka suka kwashe
da dariya, dr lukman yace gaskiya ku canza
tsari, ko kai ka hakura da zaman nigeria ka
koma can ku zauna, daman a can kuka hadu.
Dr shureim imran ya rike baki yace cafdi! Ai ba
zai yiwu ba, ka manta halin babana ai ba zai
bari inyi aiki a can ba, kasan shi da kishin
kasar nan, babu dansa da bai dawo nigeria ba
yanzu. Karatu kadai ya amince muje muyi, aiki
kuwa dole mu dawo mu bautawa kasarmu, mu
taimaki alummar hausa, fulani, musulmai 'yan
uwanmu, bai damu da yawan albashin can ba.
Dr lukman yace haka ka fada min, gaskiya ya
burge ni. Ina ma za'a sami dattijan arewa
irinsa masu kishin YARENSU DA ADDININSU da
kasar nan, da kasar nan ta gyaru. Dr shureinm
yace ai kuwa sanda zanyi aure hana ni yaso yi,
dana dage ina so ni da ita ya shimfida mana
sharudda masu tsauri. Tace taji ta gani zata bi
duk abinda yace. Sharadi na farko da ya
shimfida mana shine dole ta biyo ni nigeria mu
zauna dindindin idan munje london hutu muka
yi da zarar hutu ya kare mu dawo. Sannan dole
ta bar shigar dan siket da wando ta saka
atamfa ko leshi da mayafi don shi ya tsani
english wears. Tace ta yarda yanzu ma zaman
da ya bari tana yi na dan shekaru ne saboda
karatu, ta kusa kare makarantar da zarar ta
kare yace ta hado kayanta kakaf ta kaura kasar
nan, dole anan kasar zatayi aiki ba a can ba.
Tags :
Itama kuma bata iya zaman kasar na, tsoron
sauro takeyi, ko kuda ta gani sai ta hau kuka
ta tashi da gudu. Baby kuwa tana burge ni
babu abinda ba taci, kuma babu in da bata
shiga ta zauna lafiya a kasar nan, bata
damuwa da duk wani canji kuma itama a can
aka haifeta kamar yadda aka haifi uwar a can.
Dr lukman yayi dariya yace ah wannan ita ta
biyo kakanta alhaji, komansu na gargajiya ,
babu zancen cewa ma kai ta biyo, don kai ma
bature ne. Dr shureim imran yace ai kuwa baka
san bature ba, ai ni ko a gidanmu sun san nina
biyo alhaji sak, saboda ko wajen abinci bana
cin su shinkafa, taliya , cake, macaroni da
sauransu. Idan aka ga naci irin wadannan toh
a london nake, ko abj don babu yadda zanyi.
Nifa har kwano nake bawa direbana ya dauka
ya tafi cikin gari unguwar su wani abokina
neman danwake, dambu, ko gurasa mai
kulikuli. Dr lukman ya kwace da dariya yace har
da yawon neman dambu kake sawa ayi? Lallai
dagaske kake. Ni kuma abinda ba'aci kenan a
gidana ko tuwo zasu yi sai dai suyi min
abincina daban, haba ai an wuce wannan
lokacin ina yaro in nadi dambu da tuwo, yanzu
da wayona da 'yan canjina a aljihi inci dambu?
Ko ba haka ba 'yar boko, har yanzu kina cin
dambu? Ya tambayeni, sai nayi sauri na dubi
dodona dr shuriem, domin shi nake tsoro.
Gogan nawa sai yayi dif bai sake magana ba,
yaji an dako dani a zancensu. Jikina ya sake
yin sanyi, nayi murmushi nace bana cin dambu
nima. Dr lukman yace yawwa ashe bani kadai
ne na gaji da cin tuwo ba, muna da yawa.
Daga lokacin hirar ya koma ni da dr lukman
kadai, dr shureim yaki tsoma baki. Dr lukman
yace dani ke 'yar gidan matron maryam ce,
naga kuna kama? Wannan karon ne ma naga
dr shureim ya dubeni kasa kasa, sai yayi wuf
ya mike tsaye yana nade abin sallah, ya linke
ya ajiye sannan ya shiga daura neck tie a
wuya, ya saka bakar suit dinsa. Cikin sanyi jiki
nace a'a ni ba 'yarta bace, malamata ce kawai,
muna shiri sosai. Dr lukman yaci gaba da
rubutu yana magana yace ke ba 'yar gezawa
bace kenan. Tunda matron maryam 'yar
gezawa ce. Nayi dariya nace a'a ni ba 'yar
kano nace ba ma, ni 'yar shagamu ce. Sai ya
tsaya da rubutun ya dube ni ta cikin gilashinsa
yace da gaske kike, ko kanwar yahaya umar
ce? Babban abokina ne, ajinmu daya a
sakandiren da muka yi a yobe. Sai nayi caraf
nace yayana ne, babanmu daya. Sai ya fasa
rubutun ya ajiye biro yace yanzu dan Allah
yahaya umar yayanki ne? Na gyada kai nace
yayana ne. Yace llallai kuwa naga kama, kina
cewa ke 'yar shagamu ce sai naga fuskarku iri
daya daman tun sanda na fara ganinki na rasa
wanda kika min kama. Yana ina yanzu? Yana
nan lagos yana aiki a tasha dan union ne. Yace
subhanallah! Yanzu duk kokarin nan na yahaya
umar bai cigaba da karatu ba a aikin tasha ya
kare? Kinsan fa ni dashi muka kudiri niyyar sai
munyi karatun likita. Tunda muka gama
makaranta a. Yobe na dai ganinsa, naje
gidansu a nan yobe nemansa ban same shi ba
aka ce ya koma garin babansu shagamu, ashe
dangin mahaifiyarsa ne a yobe ko? Shikenan
rabuwarmu dashi, sai dai duk sanda aka
ambaci shagamu sai na tuno shi, saboda dan
shagamu muke ce masa. Mun shaku sosai
dakinmu daya, ajinmu daya. Nayi murmushi
nace eh dangin mahaifiyarsa ne suka rike shi a
yobe, tun yana yaro, daya gama sakandire sai
ya koma gida shagamu, bai cigaba da karatu
ba kuma. Ina rufe bakin dr shureim ya shirya
tsafa, ya dauki jakar laptop dinsa ya dubi
abokinsa dr lukman. Yace ni na tafi sai kuma
gobe. Dr lukman yace aini ma na tashi, ka jira
ni yarinyar nan zan sallama kawai, ka ga ashe
ma ni kanwata ce, haba tun sanda nake
ganinta nake ganin kamar na san fuskar, ashe
kanwar abokina ne childhood frnd yahaya umar.
Ya tabe baki yace a'a ni dai nayi gaba, sai ka
taho kawai. Ya fice ya bar mu. Bai ma bada
amsar labarin da ya bashi ba saboda a kaina
ne ba zai tsoma baki ba, sai na fara dankarawa
zuciyata zagi akan ko taki ko taso sai ta rabu
da son wannan marar mutuncin. Me yayi zafi?
Dan kawai Allah yayi masa baiwa kala kala,
yayi masa farin jini, ana sonsa sai ya dinga
wulakanci, shi waye? Namiji ne fa kamar
kowanne namiji, gasu nan birjik a titi suna bin
mace tana musu yanga kafin ma ta kula su.
Suna 'yar murya suna yi mata wahala, don ta
saurare su. Haka na dinga kushe shi a zuciyata
don in samu sukuni, duk yadda zanbi in raba
zuciyata da sonsa bi nake yi don shine samun
saukina. Dr lukman ya rufe file ya bani,
tambayi lambar wayar abokinsa yayana yahaya.
Nace bani da waya, amma zan karbo masa
lambar a wajen yayana hussaini gobe zan kawo
masa. Sai yayi mamaki don nace bani da waya,
sai ya tambaye ni, yace faduwa wayar taki tayi
ne? Kuma baki hadda ce lambarsa ba? Na
amsa da eh faduwa tayi. Saboda sauri nake in
fice daga ofishin saboda abin kaunata baya
nan, daman saboda shi naji tsayuwar da nake
yi bata isheni ba tun dazu, yana barin ofishin
sai naji duk ofis din ya gindure ni. So nake in
fito inga in daya nufa, kuma da wacce irin mota
yazo yau. Nayi wa dr lukman sallama na fito
bakin barandar da sauri, na waiga kowacce
kusurwa sai ban ganshi ba, ko alamunsa babu,
sai naji haushin dr lukman ya rufe ni, da bai
bari na fito da wuri ba, gashi nan har ya tafi.
Sai zuciyata tace ke da kike yi min fada in rabu
dashi, ina ke ina takaicin don baki gan shi ba?
Nayi ajiyar zuciya mai karfi naci gaba da tafiya
maimakon inbi doguwar baranda sai na sauko
na dinga kutsawa ta kasa cikin motoci. Ban sa
ran ganinsa ba ko kadan amma dai nasan dole
ta nan ya bi, idan zai dauki motarsa ko sawun
takalmansa na taka ai naji sa'ida a raina.
Kamar daga sama naji wata murya mai shige
da tasa daga gefena, abin da yake fada kuwa
shine "wait, wait dr hidaya, na fada miki na
sake fada miki don Allah ki daina damuna da
waya cikin dare, yau matata zata zo kasar na,
bana so ki jawo mana matsala. Aiki ne ya hada
mu anan idan an tashi daga aiki to ban sanki
ba kowa ya kama gabansa. Wanne irin abu ne
haka, ina zan saka raina? A asibiti a dame ni
har gida ma kun fara bina? Yaya akayi kika
nemo gidanmu har kika ba mai gadinmu sako
ya bani? A wanne dalile zakiyi min sayayya ki
kai min gida? Zaki jefa rayuwata cikin damuwa
tsakanina da matata, da kuma iyayena. Na
dinga tafiya a hankali ina kallonsu, a tsaye suke
a jikin motarsa har ya bude mota zai shiga sai
ta tsayar dashi. Ransa a bace yake magana
cikin matsanancin fushi, sai ita ma ta fusata ta
magana cikin kuka da fada. Dr shureim in har
ni 'yar halak ce a cikin uwata da ubana na
kyale ka, har abada ba zan sake nemanka ba.
Ya fada cike da gadara yace shi yafi sauki, naji
dadi sosai kuwa. Ta juya a fusace tana sharce
hawaye, yayin da farin gilashin idonta ya fado
kasa, ido daya ya fita. Na karaso da sauri na
dauko mata na mika mata, sai ta dube ni
jajayen idanuwanta ta karba gami da ce min
thank u very much. Ta wuce da sauri. Dr
shureim ya dube ni, ya sake bude ido ya kalle
ni sosai, na tsaya cak kamar yadda yake tsaye
kyam yana dubana. Na harare shi sama da
kasa naja dogon tsaki na kada kai na wuce na
bar shi nan a tsaye bai daina kallona ba, ni dai
ban waiwaya ba. Na san ya cika da mamakina,
ni dai burina ya cika tunda na fara ramawa
kaina wulakacin da yayi min da sauran
wahallalun mata da 'yan uwana masu sonsa.
Na kudiri aniyar kallon arziki ya daina hada mu
sabida na san ba zan same shi ba kamar
sauran da suka fini haduwa, ga kyau basu
same shi ba. Kamar daga sama naji wata
murya mai shige da tasa daga gefena, abin da
yake fada kuwa shine "wait, wait dr hidaya, na
fada miki na sake fada miki don Allah ki daina
damuna da waya cikin dare, yau matata zata
zo kasar na, bana so ki jawo mana matsala.
Aiki ne ya hada mu anan idan an tashi daga
aiki to ban sanki ba kowa ya kama gabansa.
Wanne irin abu ne haka, ina zan saka raina? A
asibiti a dame ni har gida ma kun fara bina?
Yaya akayi kika nemo gidanmu har kika ba mai
gadinmu sako ya bani? A wanne dalile zakiyi
min sayayya ki kai min gida? Zaki jefa
rayuwata cikin damuwa tsakanina da matata,
da kuma iyayena. Na dinga tafiya a hankali ina
kallonsu, a tsaye suke a jikin motarsa har ya
bude mota zai shiga sai ta tsayar dashi. Ransa
a bace yake magana cikin matsanancin fushi,
sai ita ma ta fusata ta magana cikin kuka da
fada. Dr shureim in har ni 'yar halak ce a cikin
uwata da ubana na kyale ka, har abada ba zan
sake nemanka ba. Ya fada cike da gadara yace
shi yafi sauki, naji dadi sosai kuwa. Ta juya a
fusace tana sharce hawaye, yayin da farin
gilashin idonta ya fado kasa, ido daya ya fita.
Na karaso da sauri na dauko mata na mika
mata, sai ta dube ni jajayen idanuwanta ta
karba gami da ce min thank u very much. Ta
wuce da sauri. Dr shureim ya dube ni, ya sake
bude ido ya kalle ni sosai, na tsaya cak kamar
yadda yake tsaye kyam yana dubana. Na
harare shi sama da kasa naja dogon tsaki na
kada kai na wuce na bar shi nan a tsaye bai
daina kallona ba, ni dai ban waiwaya ba. Na
san ya cika da mamakina, ni dai burina ya cika
tunda na fara ramawa kaina wulakacin da yayi
min da sauran wahallalun mata da 'yan uwana
masu sonsa. Na kudiri aniyar kallon arziki ya
daina hada mu sabida na san ba zan same shi
ba kamar sauran da suka fini haduwa, ga kyau
basu same shi ba. Da na koma gida, dare yayi
sai bacci ya gagare ni, na shifa zulumi da
fargabar kallon da nyi masa. Naji kwata kwata
ban kyauta ba, tausayinsa ya rufe ni, yayin da
sabon sonsa ya tsatsafo daga cikin zuciyata.
Na dora hannu aka ina fadinn na kashe kaina
da kaina, me ya kaini yi masa wulakanci ni da
nake addua, ina saka ran zan same shi
watarana? Na shiga adduar Allah Ya sa baiji
haushina ba. Gari na wayewa na shiga
shiryawa, na tsaya na tsarawa fusakata
kwalliya yadda zanyi kyau sosai. Nayi sauri na
tare yaya hussaini zai fita aiki, nace ya bani
lambar yaya yahaya wani abokinsa likita ne ta
ke nema. Naci sa'a ya rubuta min akan wata
'yar takarda anan take ya miko min, ko karya
kumallo ban tsaya na yi ba, na fice. Allah cikin
ikonSa ina sauke kafata daya daga kan acaba
ko dayar ban sauke ba a bakin gate din asibiti,
sai ga dr shurim ya karyo zai shiga gate. Ya
galla min harara sannan ya figi motarsa ya
wuce, sai naji dariya ta subuce min, nasan
dalilin hararar da yake min bai wuce don na
hau acaba ba, ni kuwa ko a jikina. Acaba kuwa
yanzu na fara hawa tunda ya tsani yaga mace
akan acaba. Idan baya so mu hau sai ya saya
mana motar hawa ni da 'yanuwana mata masu
hawa acaba. Sai na tsinci kaina ina tafe ina
farin ciki, ko babu komai dai yanzu ya fara
sanina, hararar dana samu ma naji dadi, nafi
wadanda bai san suna raye ba. Kai tsaye
ofishinsu na bishi, kafin in isa har ya kai cikin
ofis. Ina murda kofa sai ta wangale sai gani
kicibus gabansa, bai amsa sallamata ba sosai a
ciki ciki ya amsa kamar baya so, kallo daya
yayi min ya dauke kai yaci gaba da dube duben
littafin da yake kan teburinsa , yana tsaye. Na
gaishe shi yayi kamar baiji ba, na fada cike da
gatsali dr lukman nake nema. Ya fada cike da
takaici, kuma aka ce miki nan ne ofishinsa ko?
Na fada cikin tsiwa eh a nan na ganshi jiya shi
yasa yau nazo nan nemansa. Sai ya dago da
sauri ya dubeni cike da mamaki. Can ya dukar
da idonsa kasa, yaci gaba da dube dubensa, bai
bani amsa ba. Na rike kugu nace ga sakonsa
dan Allah ko zaka ajiye masa? Ya sake dagowa
a fusace ya fada cikin fushi, ke an fada miki
nan ba ofishinsa bane, kije ki tambayi inda ofis
dinsa yake. Ko nayi miki kama da wanda zaki
bawa sako? Na murguda baki nace saboda nan
matron maryam tace min inzo in same shi jiya
shiyasa yau ma nazo. Na juya a fusace na fice
na ki rufo masa kofar sosai. Sai naga ya biyo
bayana, ya dade a tsaye yana kallona ina tafiya
har na fice daga harabar, na barshi zuciyarsa
cike da takaici. Na fara samun sa'ida a
zuciyata tunda na fara samun damar yin
magana dashi, duk da ba maganar arziki bace.
Dana dawo ofishin da rana, sai na sami dr
lukman a ofishin dr shureim baya nan. Mun
dade muna hira da abokin yayana, naki tafiya
da wuri ina saka ran ko zai dawo sai bai dawo
ba, takaici ya isheni. Na koma gida cike da
tunaninsa da sonsa zokar a cikin zuciyata, ko
rufe idona nayi suffarsa ce ke fado min. Ina
matukar son abinda ba zan samu ba, sai inyi
kuka inyi dariya ni kadai bana mantawa da
addua, ina neman agaji daga wurin Ubangijina.
Nafi adduar Allah Ya yaye min sonsa akan
adduar Allah Ya karkato da tunaninsa kaina,
saboda a ganina shi zaifi yi min sauki duk da
babu abinda ya gagari Allah. Sai inyi ta
shawagina cikin asibiti a satin nan ko Allah zai
sake hada ni da dr shureim, ban ganshi ba ko a
hanya, ni kuma bana so inje ofishinsu saboda
zai gane akwai wani abu a zuciyata. DUK KYAN
TAKALMI 9 Sai dai kash! Na rabu da karatuna
har 'yan ajinmu sun gane hankalina baya kan
abinda ake koya mana, ban ma cika tsayawa a
wajensu ba, bini bini a neme ni a rasa. Nima na
rasa kaina, duk likitan da naga ya wuce da
bakar suit sai na bishi da kallo in zata abin
kaunata ne, sai inga ashe bashi bane, raina
yayi ta baci. Matron maryam ta lura da haka
sai tayi ta tambayata, amsar dai ita ce babu
komai, idan aka dame ni ince bana jin dadin
jikina. Haka ma dai a gida amsar iri daya ce,
data makaranta ga duk wanda ya dame ni da
tambaya. Na zama tababbiya a cikin satin nan
da ban ganshi ba. Addua nake Allah Ya yaye
min amma tamkar sonsa karuwa yake a
zauciya, ban taba sanin haka dacin soyayya
yake ba a rayuwata ko a film da littafi ban taba
ganin irin abin da ya faru dani ba. Haka kawai
na fara son mutumin da bai san inayi ba.
Shiyasa a rayuwa ba a so ka cika baki akan
abu, muddin ka cika baki akan wani abu
tabbas abun nan sai kaga ya same ka. Bazan
manta ba shekaru hudu da suka wuce akwai
wata kawata ummi, ajinmu daya a shekara.
Allah Ya jarrabe ta da son wani malamin mu
mai suna abdul yasar, shima danji da kaine
kamar dr shureim. Duk sanda taje wajensa sai
yayi mata wulakanci ita kuma tazo tana kuka
tana fada min, takaici ya kama ni maimakon in
bata hakuri sai inyi ta zaginta, ina Allah wadari
da halinta. Kullum sai ince mata me akayi aka
yi da namiji? Har zata je yana wulakanta ta,
duk a cikin samarinta ma babu kassararre,
talaka, bakauye ma irinsa, duk sunfi shi
haduwa ta rabu dashi mana. Sai tace min ita
dai shi take so bata son sauran. Kuma taci
gaba da nace masa tanayi masa wahala bayan
mun gama makaranta daga karshe ya aureta.
Ranan wata asabar da hantsi na shirya naci
ado da wata atamfata shudiya, tunda ranar
babu makaranta saina zankadawa yayana da
matarsa karya nace a asibiti ake nemanmu
zamu yiwa yara allurar rigakafi, yayana ya zaro
kudin acaba naira dari biyu kamar yadda ya
saba bani kullum. Na nufi gidan ummi domin
inji hanyar da ta bi ta samu mai gidanta abar
kaunarta abdul yasar. A kofar nasarawa
gidanta yake duk da na dade banje gidan ba,
amma naci sa'a na gane, rabona da gidan tun
ranar da muka kai ta, haka da ta haihu ma a
gidansu muka same ta muka yi mata barka,
'yar unguwar zango ce. Cike da fargaba na
shiga gidan don kada ace min bata nan inyia
asarar kudin babur din da na kashe nazo, ga na
komawa gida. Sai naci karo da maigidanta a
zauren gidan. Nayi sauri na duka na gaishe da
malamina, ya amsa a gaggauce ko kallon kirki
baiyi min ba, da alama dama ya tsane ni.
Nasan dadin soyayya yasa ummi ta zazzage
masa shawarwarin da na sha bata cewar ta
rabu dashi bakauye ne, bai hadu ba. Babu
wanda ya fada min haka, na lura tun a lokacin
bikin yana kula sauran kawayenmu nice kada
baya son yiwa magana. Na wuce cikin gidan
sadan sadan don banga fuskar da zan tambaye
shi tana nan ko bata nan ba. A tsakar gida na
ganta ta buga tagumi da alama akwai damuwa
a tattare da ita. Tana ganina sai ta mike da
sauri ta rungume ni, na dauka dariya takeyi, sai
naga hawaye. Na cika taf! Na tumbatsa da
mamaki na rike ta ina tambayarta ko lafiya?
Taja ni zuwa cikin dakinta muka zauna a gfen
gado tana magana cikin kuka. Tace aisha farida
wulakancin da yassar yake min ya isheni, don
kawai yaga bazan iya rabuwa dashi bane. Nayo
shiru na kasa magana, yayin da na shiga
hankalina na fasa tambayar abin da nazo
tambaya. Ashe har yanzu da sauran rina a
kaba, ko a yanzu na auri dr shureim ashe idan
naje gidan ma wulakanci yana nan zokar.
Zuciyata ta fara yimin fada tana cewa farida ki
yi ta kanki, ki cire son dr shureim imran idan ba
kin zabi ciwon zuciya ya zama ajalinki ba. Na
tambaya cikin sanyin jiki wai ke ummi yaya aka
yi ma tun farko ya amince ya aureki bayan
baya sonki? Tace ashe ba dake muka je ba, da
maijidda lawan mukaje wajen wani malami a
kurna. Sai na dafe kirji na fada a gigice, na
shiga uku ummi! Malami kuma? Ta gyada kai
tace shine yayi min aiki yace dole sai yasar ya
zo ya aure ni ko ba a hayyacinsa ba. Kuma
yazo din ya aure ni, har nake juya shi yadda
nake so, sai bayan da na haihu ban koma ba.
Kinsan ance idan mace ta haihu duk wani sihiri
da tsarin da yake jikinta karyewa yake yi, sai
tayi sabon shiri. Kuma kin san halin malaman
zamanin nan sunfi so ka dauwama kana zuwa
wajensu kana kai musu abin da ka kwakwala
daga wajen mazan, idan ka dauke kafa bayan
bukata ta biya sai su karya maka aikin, komai
sai ya cakude dole sai ka dawo. Sannan yanzu
bani da waya, bama magana dashi ta waya,
daya fada min irin sadakar da zanyi dan duk
ranar laraba yanayi min waya yace nayi
sadakar sukari ko nono na aljanar da take kula
da soyayyar da yasar yake min, kinga na dade
banyi sadakar ba. Hankalina ya tashi, abin da
nake gani a film yazo har gida. Nace ummi
tsafi kenan fa? Tace haba dai tsafi, babban
malami ne fa ya iya jan aya, baki ga matan
manya da masu kudin garin da suke layi a
gidansa ba, talakawa irina kadan ne. Ya iya
aiki fa. Zuciyata ta fara rabuwa gida biyu, inje
ko kar inje? Amma fa jikina bari yake yi, naji
tana ambaton aljana a cikin al'amuran. Daga
karshe zuciyata ta yanke min, kawai inje ni ma
ayi min asirin da dole zaizo ya so ni ko da
daga baya asirin ya karye ai dai naci riba tunda
bani da buri a rayuwata irin in ga na same shi
yayi min magana ma kawai, balle ace yazi
gidanmu har anyi maganar aure dashi, ya aure
ni na tare gidansa, ai ba karamar riba bace a
rayuwata. Kuma idan haka ne in anyi auren ai
sai in ringa komawa wajen malamin ina kara
masa kudi yana cigaba da sona, yana fada min
abinda zan bayar sadaka ina yin sadakar yadda
son ba zai tafi daga zuciyarsa ba. Tunda kafin
lokacin bikin na gama makaranta na fara aiki,
ko da albashina na dinga biyan malam ko bai
bani kudinsa ba. Sai na gyara zama nace ummi
nima fa matsalar da take tafe dani kenan, nima
irin naki ne ta same ni. Allah ya jarrabe ni da
son wani likita a asibitin da nake attachment,
amma fa likitan yafi ni haduwa nesa ba kusa
ba, gashi daji da kai da wulakanci, har yafi
malam yasar dinki. Na rasa yadda za'ayi ya
saurareni ma balle ayi zancen soyayya. Baki ga
yadda hadaddun likitoci mata suke binsa ba
yaki sauraronsu. Kawayena biyu suke yi masa
asiri dan ya sosu amma bai kama shi ba, ina
jin ya shirya kansa asiri baya cinsa. Wani
babban tashin hankali ma yana da mata ina jin
ma baturiya ce a london suka hadu sukayi
aure, ita ma yanaji da ita, nasan ta fini kyau
nesa ba kusa ba. Ya zanyi? Ummi ta daki
kafada ta tace ke dalla wawuya daman ke irin
wannan mutumin kika samu amma zaki bari ya
subuce miki? Lallai kin cika wawuya baki da
wayo. Ai kawai kije a zuba miki aiki tuntuni
zaiji ya tsani baturiya ya biyo ki, balle mai kudi
ne, kina shiga zaki fanshe kudafen da kika
kashe a kansa. Na girgiza kai nace babu
ruwana da taba matarsa, suyi zamansu ni dai
yaso ni kawai, tunda ina sonsa. Idan kuma
akwai abin da malamin zai yi min na daina
sonsa ni nafi son haka, saboda nayi iyakacin
adduar da zanyi don na daina jin sonsa na
kasa dainawa kullum karuwa yake ma. Ummi
tace yaya za'ayi kice a cire miki sonsa ai
shirme kenan. Ace yaji abin da kike ji koma
ince fiye da yadda kike ji don an fi son namiji
yafi na mace sai afi zama lafiya. Ke ban da
abinki wata budurwar ba irin wannan take
nema ba ma ta kai shi wajen malami a rike
mata sai ko ta wanne hali, ko ba komai ai ka
tsira da kudi ko babu soyayyar. Na girgiza kai
nace ai ni ba kudinsa nake so ba, shi nake so.
Ni na yadda ya so ni kada ma yabani kudinsa,
na yarda idan na fara aiki in ciyar da kaina ba
sai ya ciyar dani ba. Ummi ta rike baki tace
Aisha farida haka kike sonsa kamar ki cinye
shi? To ko asiri yayi miki irin wannan son dai
bana lafiya bane. Na girgiza kai nace ko kadan,
Allah ne yayi masa baiwar kyau, ilimi, arziki, da
jan aji dole mata suke sonsa. Shi kansa baya
son haka. Bai ma san inayi ba balle ace shi ma
yana sona har yaje yayi min asiri. Jarraba ce
kawai ta afka min, nima ba don ina so ba, haka
Allah ya tsaro min. Sai na fashe da kuka. Ta
rungume ni tace taso muje in kai wajensa
yanzu, nima daman ina shawarar zuwa yau ko
gobe, al'amarina ya cabe ni da yassar. Na mike
tsaye ina goge hawayena yayin da ita kuma ta
canja kayan jikinta ta saka wata jar atamfa
riga da zani ta goya 'yarta da take barci akan
gado, muka fito ta kullo dakin. Ta leka tayi wa
matar kanin mijinta sallama wacce katanga ce
kadai ta rabu tace da ita zamuje bakin asibiti
zata raka ni inyi sare sare. Muka fito muka
kama hanya tun a hanya na sanar mata ko
kudin mota bani dashi, tace babu komai zata
biya min, gakudin cefanenta nan yau ko
cefanen ma bazatayi ba. Ce masa zatayi dan
aiken ya zubar da markade. Ta juyo ta dube ni
tace to ke yanzu da baki da kudi yaya za'ayi
miki aiki? Dole fa sai kin kashe kudi idan kina
son aiki yace. Tafiya mai nisan gaske mukayi a
motar bus mai zuwa kurna, sai da muka hau
acaba muka niki tafiyar kafa saboda babur ma
ba zai iya shiga lokon ba, wahala iri iri muka
sha kafin muka isa gidan. Nace muje dai muji,
na san yadda zanyi. Sai na fashe da kuka. Ta
rungume ni tace taso muje in kai wajensa
yanzu, nima daman ina shawarar zuwa yau ko
gobe, al'amarina ya cabe ni da yassar. Na mike
tsaye ina goge hawayena yayin da ita kuma ta
canja kayan jikinta ta saka wata jar atamfa
riga da zani ta goya 'yarta da take barci akan
gado, muka fito ta kullo dakin. Ta leka tayi wa
matar kanin mijinta sallama wacce katanga ce
kadai ta rabu tace da ita zamuje bakin asibiti
zata raka ni inyi sare sare. Muka fito muka
kama hanya tun a hanya na sanar mata ko
kudin mota bani dashi, tace babu komai zata
biya min, gakudin cefanenta nan yau ko
cefanen ma bazatayi ba. Ce masa zatayi dan
aiken ya zubar da markade. Ta juyo ta dube ni
tace to ke yanzu da baki da kudi yaya za'ayi
miki aiki? Dole fa sai kin kashe kudi idan kina
son aiki yace. Tafiya mai nisan gaske mukayi a
motar bus mai zuwa kurna, sai da muka hau
acaba muka niki tafiyar kafa saboda babur ma
ba zai iya shiga lokon ba, wahala iri iri muka
sha kafin muka isa gidan. Nace muje dai muji,
na san yadda zanyi. Munci sa'a babu layi
sosai, mun tarar da maza uku a kofar gida,
mata biyu a cikin gida. Muka gaishe su muka
bi layi. Gabana sai faduwa yake tamkar
zuciyata zata fito sarari, sai in zunguri ummi
ince na fasa ta tashi mu tafi. Sai ta mintsine ni
tace ba inda zamu je sai mun shiga. Na daure
har layi yazo kanmu, muka shiga ciki. Daga
sanda naga kasar duba da dogon carbi sai na
tabbatar na kauce hanya, domin nasan
makomar masu bin 'yan tsubbu masu duba, in
har kaje wajen mai duba ya fada maka gaibu
ka yarda dashi, to baka da sallah har tsawon
kwanaki arbain. Allah ba zai karba ba. Ya san
ummi sosai, ya san matsalolinta don haka sai
ya hau mata bayani. Tace malam a bincika min
dai. Sai ya jawo farantin kasa yayi zane
zanensa ya hau yi mata bayanai kamar wanda
ke karantawa. Na dubi kasar naga babu rubutu
babu alamarsa na rasa inda yake karanto
wadannan labarai, sannan na dubi sama da
kasa banji motsin wanda yake fada masa ba.
Yace ummi wannan tsohuwar budurwar nan
tasa da yake so itace take raba ku, ta tashi
tsaye tana asiri sai ta fitar dake ta shiga gidan,
sannan faccalatki matan kanin mijinki da kuke
gida daya, itama tana saka miki hannu saboda
mijinki ya fi nata zuciyar nema, kin fi ta
hutawa, don haka take so ta raba ku.
Tags :
Ummi ta fusata ta hau bayani. Lallai biri yayi
kama da mutum, domin tun sanda mijina ya
siyo mana generator sai ta yini a daki baata
fito tsakar gida ba, haka ma zance tsohuwar
budurwarsa ba su rabu ba suna tare har yanzu,
naga sakonta a wayarsa. Yanzu malam yaya
za'ayi? Sai naga ya karkace ya zayyano mata
abubuwa kamar su turarruka na wuridi, kaji,
dan akuya ja, farin kyalle da kudin yaran
dazasu zauna aiki, dubu ashirin da biyar. Ko ta
nuna damuwa ma batayi ba sai kawai ta ce
gobe zan kawo dubu goma sha biyar a fara,
don Allah malam ka ragargaza min su kamar
yadda suke son su raba ni da mijina suma a
rabasu da mazansu, ni kuma mu zauna daram
ina so a kama min shi don wulakanci yake yi
min kwanan nan har da cewa bai san inda yake
kallo ba ya aure ni, don ni ba irin tsarin
rayuwarsa bace. Sakacinki ne inji malam. Ya
juyo ya dube ni sai na takure a lungu kirjina
yana dukan ukuk uku. Yace ke fa meye
matsalarki, ko baki fada ba zan iya ganin
asiran da akayi miki a jikinki, ki tashi tsaye
wajen neman tsari. Ummi ta kwanto da 'yarta
daga bayanta ta gyara zama tace malam, aisha
farida kawata ce, a taimaka mata. Matsalarmu
kusan iri daya ce, ayi mata bincike tukunnan.
Ta bukaci ina saka abin sadaka kafin ya fara,
sai ummi ta zaro dari biyu zata mika masa na
rike hannunta nace ba sai an bincika min ba
malam zan fada da bakina. Na koro masa
bayani tas, sai yayi dariya ya kyakyata yace
wannan karamin aiki ne a wajena, idan har zaki
sayi kayan aiki na baki kwana biyu inda dr
shureim imran ne kim gama samunsa. Ina jin
haka sai naji farin ciki ya lullube ni nayi dariya,
na tambaye shi me dame za a siya? Sai yayi
min zancen abubuwa daban daban, wasu na
sansu wasu ban sansu ba. Aka hada kudin ya
kama naira dubu ashirin da daya. Sai na dafe
kirji nace malam bani da kudi ko zaka yi min
bashi idan komai ya kankama sai in biya? Ya
dubi ummi cike da bacin rai yace ina kika samo
min wannan yarinyar? Baki fada mata dokar
aikina bane? Sabon shiga ce ko? Toh ni bana
fadar farashi a nemi ragi balle ace inyi a bashi,
a cikin kudin nan babu sisi nawa, duk na
rauhanai ne. Ummi tace ayi hakuri malam,
laifina ne ban fada mata dokokinka ba zamu
dawo gobe tare zamu nemo kudin mu kawo.
Mun goda. Banyi godiya ba na kada kai na fito,
hankalina ya gama tashi. Muna fita kofar gida
ummi ta hau yi min fada tana cewa me yasa
ban bari anyi min bincike ba inji bayani dalla
dalla ba, sannan me yasa nace ayi min aiki
bashi alhali tun a kan hanya na baki labarinsa?
Nace to bani da kudi ko naira hamsin ta kaina
bani da ita. Me zance? Tace ki sayar da
kadararki mana. Nace ai bani da ko barimar
gwal balle dan kunne. Ta tabe baki tace ni dai
shawarar da zan baki itace kije kisan abinyi
don nima nan da kika ganni bashi zanje in ciyo
in kai masa idan aiki yaci da kansa zai baki
kudi kije ki biya. Malamin nan fa aikinsa kamar
yankan wuka, sha yanzu magani yanzu. Kije
kiyi tunani zuwa gobe ki samo kudi, kizo mu
kai don ni ma daga nan gari zan shiga neman
bashi. Ta bani kudin mota mukayi sallama na
shiga motar unguwarmu, ita kuma ta shiga
motar dawanau ban san inda ta nufa ba. Ina
zaune a mota tamkar gunki ina tunani, sai da
kondasta yyayi ta magana sannan na gane dani
yake, na mika masa kudin mota. Haka da aka
zo inda zan sauka ma na manta har aka wuce
dani, sannan na ankara nace a sauke ni. Saida
na dawo baya. Na shiga gida a cakude, narasa
inda zan saka raina, tunanina gaba daya ya
koma wajen inda zan samo rancen kudi in
kaiwa malam gobe. Cikin unguwar nan da
batsewarta babu matar da zata iya fitar da
dubu biyar ma kai tsaye saboda talauci. Da
yamma na shirya na fita neman kudi gida gida,
da kyar na hado rancen dubu biyu. Na zarce
kai tsaye shagon da musbahu yake sana'a. Sai
yayi matukar mamakin ganina ya tambayeni
lafiya ya ganni a hargitse haka? Na fada masa
cewar matsalar kudi ce ta taso min, bani da
lafiya. 'Yar karamar tiyata za ayi min gobe a
asibitin ana neman naira dubu ashirin. Sai ya
dafe kirji yace aisha farida babu inda zan sami
dubu ashirin a yau. Ai ko bashi babu in da zan
samu. Ko idan anyi wa likitan bayani zai yarda
yayi miki aiki a bashi karshen wata sai in biya
shi. Na girgiza kai nace babu zance bashi
kuma dole in hada kudin daga yau zuwa dare.
Yace to inje gida zai aiko yaro ya kawo min
abin da ya sauwaka. Zaije ya fita ya nemo
abinda ya samo. Nayi godiya na tafi. Ko awa
guda banyi ba da shiga gida sai ga dan aike da
dubu uku har da doguwar wasika yana mai
bani hakuri abin da ya samo kenan. Amaa zaici
gaba da nemowa zuwa gobe. Ya jero min
kalaman soyayya ko gama karantawa banyi ba
na yayyaga na zubar, burina in hada kudin nan
in kai. Ina zaune a mota tamkar gunki ina
tunani, sai da kondasta yyayi ta magana
sannan na gane dani yake, na mika masa kudin
mota. Haka da aka zo inda zan sauka ma na
manta har aka wuce dani, sannan na ankara
nace a sauke ni. Saida na dawo baya. Na shiga
gida a cakude, narasa inda zan saka raina,
tunanina gaba daya ya koma wajen inda zan
samo rancen kudi in kaiwa malam gobe. Cikin
unguwar nan da batsewarta babu matar da
zata iya fitar da dubu biyar ma kai tsaye
saboda talauci. Da yamma na shirya na fita
neman kudi gida gida, da kyar na hado rancen
dubu biyu. Na zarce kai tsaye shagon da
musbahu yake sana'a. Sai yayi matukar
mamakin ganina ya tambayeni lafiya ya ganni
a hargitse haka? Na fada masa cewar matsalar
kudi ce ta taso min, bani da lafiya. 'Yar
karamar tiyata za ayi min gobe a asibitin ana
neman naira dubu ashirin. Sai ya dafe kirji yace
aisha farida babu inda zan sami dubu ashirin a
yau. Ai ko bashi babu in da zan samu. Ko idan
anyi wa likitan bayani zai yarda yayi miki aiki a
bashi karshen wata sai in biya shi. Na girgiza
kai nace babu zance bashi kuma dole in hada
kudin daga yau zuwa dare. Yace to inje gida
zai aiko yaro ya kawo min abin da ya
sauwaka. Zaije ya fita ya nemo abinda ya
samo. Nayi godiya na tafi. Ko awa guda banyi
ba da shiga gida sai ga dan aike da dubu uku
har da doguwar wasika yana mai bani hakuri
abin da ya samo kenan. Amaa zaici gaba da
nemowa zuwa gobe. Ya jero min kalaman
soyayya ko gama karantawa banyi ba na
yayyaga na zubar, burina in hada kudin nan in
kai. Uwani uwar adashe ita kadai na tabbatr
zan iya samun rancen kudi a wajenta ko nawa
ne saboda itace naga koda yaushe mata suna
aiko mata da zubin kudin adashe, ina hango
shigarsu da fitarsu daga windon dakina domin
dakinta na kusa da dakina. Ina idar da sallar
magriba na tabbatar abida tana daki tana
wuridi ba zata fito tsakar gida ba, sai tayi
sallar ishai kamar yadda ta saba. Sai nayi
sanda na fito dakina na fada dakin uwani, sai
tayi mamakin ganina a wannan lokaci, naci
sa'a maigidanta bai dawo ba. Ta saka fitilar
kwai a gaba tana kirga kudi kashi kashi. Farin
ciki ya rufe ni da naga kudin nan sai na shiga
marairaice mata inayi mata dadin baki cewar
ta ranta min dubu goma sha bakwai zan biya
ta gobe da yamma. Ta tsorata matuka har da
dafe kirji ta tambaye ni, me zakiyi da kudi
haka? Na shaida mata kawata ce zata haihu a
asibitinmu ance ba zata iya haihuwa da kanta
ba sai an yi mata tiyata. Ga mijinta ba ya gari
yana lagos. Amma ya sako kudin ta banki, to
kasancewar asabar ce babu banki, lahadi ma
babu aiki ba za a iya fitar da kudin ba, sai
ranar litinin. Shine tace in ranto mata zuwa
litinin zata biya. Uwani tace a'a aisha farida
kinsan halin mutane kayi musu rana suyi ma
mutum dare. Ki zo ki taimake su suki biya, ko
kuma ni in taimake ki, kiki taimakona. Kinsan
dai kudin nan da kika gani kudin cizo ne, bana
kashewa bane da masu shi. Gobe haj rabi ce
zata dauki adashen nan dubu talatin. Mace
dayace bilki bata saka mata ba, na aika tace
gobe zata aiko yana aikowa sai in hada in
aikawa haj rabi daukarta. Yanzu idan na baki
aka zo aka sami matsala yaya zanyi? Kinsan
bani dashi, lada suke bani duk wata dubu daya
dan tarawar da nakeyi. Niko ikon sgiga
adashen ma bani dashi dan bani dashi. Nace
na sani uwani, idan Allah Ya yarda babu
matsala, ranar litinin da sassafe zanje bankin
da kaina in karbo miki. Tace to shikenan gashi
nan. Ta kirgo dubu goma sha bakwai tabani, na
karba na kirga sun cika cas, nayi godiya.
Sannan na roki arzikin ta rufa min asiri kada ta
fadawa kowa ko abida kada taji, salin alin zan
dawo mata da kudinta. Tayi min alkawari babu
wanda zaiji. Na shiga daki na hada kan kudina
na adana a jaka. Naira dubu ashirin. Farin ciki
fal a zuciyata, har sai da abida ta fuskanci
haka a daren, a da bana iya cin abinci sosai,
amma a daren taga har da kari nayi. Da bana
son magana sai taji na isheta da labari a ranar.
Ta san na daina fara'a amma a ranar na ishe
ta da kyakyata daria har da wake wake.
Saboda na riga na sami kudin da bana tantama
na gama samun dr shureim imran. Gari na
wayewa na shiga tunanin karyar da zan
shiryawa yaya hussaini wacce zai bari in fice,
domin ranar lahadi ce babu aiki, kuma kulle
yake min. Na shirya tsaf na kira abida gefe na
shirga mata karyar cewa zanje asibiti yau ma,
ana yiwa wata nurse bikin gama aiki, tayi retire
ance kowa sai yaje kuma da kayan gida. Na
santa da wayo ta san yadda zata fadawa
maigidanta ya aminta da ita. Ta shiga daki ta
tsaro shi sai ga ta da dari biyu kudin babur.
Naji tausayinsu ya kama ni saboda nafi su kudi
yanzu, da sun san kudin da yake jikina da basu
rabu da dari biyunsu ba. Nayi godiya na karbe
na tafi, abida ta rakani har zaure tana yi min
fatan alkairi. Tana jaddada min in ragowa
'ya'yanta kayan walima. Na amsa mata da zan
rago musu da yawa ma kuwa. Ina fita na hau
acaba sai gidan ummi kawata. Da yake sassafe
ne mijinta ma bai fita ba yana daki, tajani
zuwa falonta muka zauna muna magana cikin
sirri. Ta tambaya yaya ake ciki, na samo kudin
kuwa? Na ciro mata himilin kudin daga jakata
sai ta rike baki tace lallai kinyi kokari, nima na
hada dubu goma sha biyar bari inje inyi masa
karya inzo mu tafi. Yau lahadi ba zai fita da
wuri ba, gara muyi tafiyarmu. Ta shiga daki ba
dadewa ta fito a shirye da goyonta muka nufi
kofar fita, har mun kai zaure faccalarta ta biyo
mu da sauri. Tana cewa ummi unguwa zakije
baki fada min ba mu fita tare? Yau ne sunan
mariya 'yar jummai, ki tsaya in shirya mu fita
gaba daya mana. Ummi ta doka mata harara
tace dani aisha faida da Allah muje, dole ne sai
mun fita tare. Myka kada kai muka fice muka
bar ta a tsaye tana kallonmu har abin tausayi.
Muna fita nace da ita haba ummi ya za ayi kiyi
mata wulakanci? Ai sai ki bata amsa mai dadi
ko ba kya so tabimu. Ummi ta tabe tace ai na
daina raga mata tunda bincike ya nuna bata
kaunata. Ni da mutunci da ita har abada. Nace
to amma ai maganar malamai ce, babu tabbas
zaiyiwu kirkira yayi. Ta harare ni tace lallai kina
wasa da aikin malamin nan. Idan yayi miki
duba tabbas zaki ga komai a hankali daya
bayan daya. In bai gani ba zai fada ne ko da
ya taba ambato sunanta in ba yanzu ba, kuma
nima na lura tun sanda muka sayi generator ta
canja min, taga mun cigaba a rayuwa. DUK
KYAN TAKALMI 11 Bansake magana ba dai har
muka isa gidan malam. Yana ganin mu ya fara
washe baki, fara'ar yau tafi ta jiya. Muka
zazzage masa kudaden jakarmu kakaf domin
bayan dubu ashirin da dayan da ya karba sai
da ya sake kwakwalo min wasu kudaden daban
daban har dubu biyar da dari biyar. Kuma na
harhada na bashi, a takaice dai har cikon dubu
daya da dari biyar nan gaba zan ciko masa. Ita
ma ummi ya kara mata wasu kudin, idan ta
tashi cikowa ba dubu goma zata ciko masa ba,
goma sha uku zata ciko. Yace ya bamu
kwanaki uku mu dawo, ranar laraba kenan kafin
komai zai daidai ta. Muka fito muna murna,
ummi tana tabbatar min komai zai daidaita in
kwantar da hankalina. Na tafi gida ita ma ta
koma gidanta, na sake shirgawa abida wata
karyar tunda ban taho da kayan walima ba,
naso in siyo musu lemo da biskit amma na
juyewa malam kudin dukka, da kyar ma na
karaso gida, sai da kudi ya kare. Ko kusa ban
damu da himilin bashin dake kaina ba, burina
aiki yaci in mallaki dr shureim shine a gabana.
Na yina ina hidindimuna da 'yan gidanmu cikin
walwala da farin ciki. Da dare yayi na shiga
barci sai na tsinci kaina na canza tunanina ba
irin na da bane. Yanzu tunani nake gani a
gidansa har mun zama ma'aurata, gani dare-
dare a cikin hadaddiyar motar nan tasa muna
tafe muna hirar soyayya. Na dade ina
tunaninsa sannan nayi bacci, na dora da
mafarkinsa mai dadin gaske. Na sa wa
zuciyata na sami dr shureim na gama kamar
yadda malam ya bani tabbaci. Naso in makara
saboda dadin mafarki, na tashi a gaggauce na
shirya na karbi kudin babur a wajen abida.
Yayana ya bata ta bani donshi yana riga ni fita
ma. Sai uwani ta biyo ni zaure da sauri ta
tsayar dani tace yanzu zaki karbo kudin daga
banki? Ko sai kin taso zaki taho dashi? Bilki ta
kawo zubinta jiya na wajenki kawai nake jira in
aikawa haj rabi na fada mata yau da rana zan
aiko mata. Sai zuciyata ta hau dukan uku uku
na fara zullumin inda zan nemo wadannan
makudan kudi. Na hau rawar murya ina kame
kame, nace sai an taso zan taho da kudin. Ina
kan babur ina tunanin yadda za'ayi idan na
dawo gida babu kudin? Ina shiga cikin asibiti
naji farin ciki ya lullunbe min zuciyata saboda
ko ba komai an fara aiki, zuciyarsa ta fara
bugowa gare ni. Sai kuwa naci sa'ar a ranar an
tura mu bangarensu dole zan ga ofishinsa ko
ba ma wajensa aka mu tura mu ba. Muna
shiga kuwa dakin darasin muka ci karo dashi
da dr lukman suna fitowa medical students
suna biye dasu zasu je zagayen marasa lafiya
(ward). Na tare su da sauri na gaishe su, sai
naji caraf ya amsa hadda kallon fuskata, ba
murmushi yake ba haka bai bata rai ba. Dr
lukman ne yake dariya, har yake yi min wasa
yace ke 'yar shagamu ina kika shiga kwana
biyu, rannan har yahaya umar yace in baki
waya ku gaisa, nace ba kya kusa. Nayi dariya
nace to yaushe zanzo ka kirawo min shi a
wayar muyi magana? Da yake yana tafiya ne
sanda yake magana, har yakai barandar waje
banji abin da yace ba. Sai wani dalibi ne yake
bayansu ya juyo yace min cewa yayi kizo gobe.
Na yini ina farin ciki saboda naga canji wajen
amsa gaisuwata da kuma kallon mutuncin da
dr shureim ya min. Ban fara fargaba ba sai da
aka tashi daga makaranta na tunkaro hanyar
gida. Na shiga zullumin karyar da zan gina
wacce ba za'a rutsoni ba, dakin uwani na nufa
kai tsaye sai ta fara murna tana gyara hannu
zata karbi kudi ta kidaya. Sai na zube a
gabanta ina marairaice murya ina bayani. Nace
wallahi tun safe ban huta ba muna ta kai kawo
a cikin asibitin saboda matar bata da jini, don
haka ba za'a yankata ba dole sai an kara mata
jini. 'Yan uwanta ne suka zo maza da mata
muna ta auna jinin har a sami wanda ya dace
da nata shi yasa ban samu fita daga asibitin
ba naje banki, amma gobe da sassafe zanje in
karbo. Uwani ta bata rai, yadda ta amsa min a
ciki ciki na san bata so haka ba, ta bini da kallo
har na fice daga dakin. Ina cin abincin rana na
fice wajen musbahu ban same shi ba, na bar
masa doguwar wasika. Nazo giftawa ya
makoftanmu nayi ido hudu dahare ta leko
kenan ta ganni, ita ma dari takwas ta ranta
min kudin dinkinta zata kai domin ta kusa
haihuwa, ita ma ranar litimin din nace zan
kawo mata. Dole na shiga gidan na tsara mata
karya iri iri na ce gobe zan kawo mata. Itama
ta nuna min bataji dadi ba, har mijinta yayi
fada da yaga kayan dinkin a ajiye bata kai ba.
Naji hankalina ya sake tashi na fito a gigice na
shiga gidan mu har sai da abida ta shiga
damuwa ganin yanayin da na shigo. Tayi ta
tambayata ko lafiya? Nace lafiya kalau. Idan
naji damuwa ta gallabeni sai in tuno menayi da
kudin, kuma nan gana me zan samu. Sai inji
sanyi a raina. Washe gari talata na fita zuwa
makaranta, kai tsaye ofishin dr lukman na
wuce. Ina shiga na iske shi zai fita. Yace dani
ke kuwa baiwar Allah ai ba da sassafen nan
zaki zo ba, sai da rana in aiki ya lafa ko? Nayi
turus banji dadin amsar daya bani ba, ya wuce
abinsa ya barni a tsaye. Sai ga gogan nawa
yau kuma shigar hausa yayi, shadda ruwan
bula tazarce ya dora hular da ta dace da kalar
kayansa. Ya ratayo laptop dinsa a kafadarsa
sai naga ya kara yin kyau matuka babu wacce
zata kalle shi bata sake kallonsa ba. Ya tari dr
lukman sukayi magana, sannan kowa ya wuce.
Sai naji zuciyata na tafarfasa saboda shaukin
so, kai kace zakanya ce mai tsananin jin
yunwa ta ga nama haka zuciyata ta dinga zillo
tamkar ta ballo ta fito da taga abincinta. Sai
dai wannan abincin bana lasa bane, yafi
karfinta. Tamkar soyayyen nama ne aka soya
yana kamshi amma aka zazzaga masa guba
kaga duk kwadayin mutum doke ya kalla ya
wuce ko da kuwa marmarin naman zai kashe
shine. Na fara takawa a hankali na matsa daga
bakin kofar kafin ya karaso. Tun daga nesa na
amshi wata galleliyar harara daga gareshi.
Daya karaso bakin kofa kafin ya lalubo mukulli
ya bude kofar sai da ya waiwayo bayansa inda
nake a tsaye ya wurgo min wata hararar wacce
tafi ta dazu wulkilewa. Sai nayi sauri na juya
na fara tafiya ba tare da nasan inda zanje ba,
sai gani a bakin gadon marasa lafiya nayi wuki
wuki suna kallona ina kallonsu. Sannu likita,
zoki duba cikinsa ki gani ya kumbura. Inji wata
tsohuwa mai zaman jinyar danta. Na girgiza
kai nace ki kira likita ni ba likita bace. Nayi
saurin barin wajen na dawo bakin kofar ofis din
na tsaya, nayi kamar in tura kofar in shiga sai
na fasa. Na hakura na tafi ba don zuciyata
tana so ba. Ina zuwa ofishinmu na iske
kawayena suka hau min surutu. Wai aisha
farida ina kike shiga ne aka nemeki aka rasa
kullum har anyi test jiya ba kya nan? Nayi
shiru na koma gefe na zauna na rasa abun da
yake min dadi. Naci sa'a khadija sani tace inzo
in rakata ta siyo ruwa zata sha magani. Ashe
itama ta kunso labarai kala kala take so mu
kebe ta fatsar. Ta dube ni ta tabe baki tace
baki tambayeni dr shureim ba. Sai naji gabana
ya fadi, sai na zargi kaina ina ganin kamar
kowa yasan halin da nake ciki. Na zabura nace
kamar yaya ban tambaye ki dr shureim ba?
Tace kin manta inda muka kwana na nuna miki
sakonsa a wayata? To in fada miki an gasa
minshi da addua, ba adadi har sai da yaji ba
dadi. Ina kiransa ya amsa, yace dani wacece?
Sai na fada masa sunana khadija sani ismail.
Ni daliba ce a schl of nursing tanan aminu
kano, kuma ina attachment a nan cikin asibiti,
sai yace yayi kyau lafiya? Nace lafiya so nake
yayi saving lambata zan dinga kira muna
gaisawa. Na dafe kirji nace yayi saving lambar?
Tace kwarai kuwa, don da na sake kira sai da
ya ambaci sunana. Sai naji kwalla ta cika min
ido, kishi ya kamani, jikina yayi sanyi kalau.
Taci gaba da cewa da na sake kira sai yayi
tsiyar. Na tambaya a sanyaye meye tsiyar?
Tace wulkanci yayi min kamar zai zageni, wai
kada in sake kiransa. Kuka wiwi nayi da
hawaye na hakura dashi ma ni yanzu. Allah Ya
sa bai san fuskata ba, na goge lambarsa na
daina kiransa yanzu. Dadi ya rufeni, amma fa
na kara tausayawa kaina. Na bata shawarar
tayi hakuri taci gaba da addua, Allah Ya
musanya mata da abin da yafi alkhairi. Ta
amsa min da ameen. Da aka tashi daga
makaranta sai na kasa komawa gida, sai
nacewa khadiji sani ismali zanbi ta gidansu
somin 'yan gidanmu ba sa nan sun tafi unguwa
sai dare zasu dawo. Khadija tayi farinciki da jin
haka, sai muka dunguma muka tafi har yanzu
labarin dr takeyi min. Ban cika bata amsa ba,
tamkar tana min famin gyambon da yake
damuna da zugi ne. Kwakwalwata ta cunkushe
na rasa abin da yake min dadi, na kasa
tantance abin da zanyi. Abinci kala kala aka
jera min a gabana, amma na kasa ci da yawa
saboda damuwa. Khadija sani ta dube ni tace
wai don Allah aisha farida me yake damunki ne
kwana biyu kin susuce tamkar bake ba. Ba kya
son magana, ba kya son karatu gashi ba kya
son cin abinci tundazu dan abincin da kika
zuba kin kasa cinyewa, bakiga yadda kika rame
ba, kika kwanjale ba. Kin cika zurfin ciki, ba a
jin sirrinki daman. Wai me yake faruwa ne?
Nayi murmushi nace haka kowa yake ambata,
malaria ce ke cin jikina. Tace toh kisha magani
mana, yaya zaki zauna da ciwo kina malamar
asibiti, ko in saya miki babu kudi hannunki? Ta
soso min inda yake min kaikayi, na gyara zama
nace kamar kinsan satin nan cikin matsalar
kudi muke, kinga yanzu haka yayana ne aka
bashi ajiyar kudi, ya kawo gida aka shiga har
daki aka sace, ya rasa yadda zaiyi. Mai kudin
yana ta damunsa har da zai kai shi police
station yake ambato. Khadija tace a garin yaya
aka shiga har daki aka yi muku sata, babu
mukulli ne? Nace maso abinka ya fika dabara,
kinsan rayuwar cikin gari, gidan yawa aka shiga
aka dauke. Khadija tace babu dadi, Allah Ya
kiyaye gaba. Shi kuwa mai kudin bai san
kaddara bane? Yayi hakuri mana sai ya samu
ya biya shi. WaLlahi nima a cikin matsala nake,
domin na karbi kudi a wajen abba yayi dubu
hamsin kwanan nan haka ma a wajen mama.
Har sun gane ba'a makaranta nake kashewa ko
na tambaya basa bani. Sai tambayata suke me
nayi da kudi a cikin satin nan, naki fada, ai ban
isa ince malamai na kaiwa ba sai a kusa kashe
ni.
Tags :
Bansake magana ba dai har muka isa gidan
malam. Yana ganin mu ya fara washe baki,
fara'ar yau tafi ta jiya. Muka zazzage masa
kudaden jakarmu kakaf domin bayan dubu
ashirin da dayan da ya karba sai da ya sake
kwakwalo min wasu kudaden daban daban har
dubu biyar da dari biyar. Kuma na harhada na
bashi, a takaice dai har cikon dubu daya da
dari biyar nan gaba zan ciko masa. Ita ma
ummi ya kara mata wasu kudin, idan ta tashi
cikowa ba dubu goma zata ciko masa ba,
goma sha uku zata ciko. Yace ya bamu
kwanaki uku mu dawo, ranar laraba kenan kafin
komai zai daidai ta. Muka fito muna murna,
ummi tana tabbatar min komai zai daidaita in
kwantar da hankalina. Na tafi gida ita ma ta
koma gidanta, na sake shirgawa abida wata
karyar tunda ban taho da kayan walima ba,
naso in siyo musu lemo da biskit amma na
juyewa malam kudin dukka, da kyar ma na
karaso gida, sai da kudi ya kare. Ko kusa ban
damu da himilin bashin dake kaina ba, burina
aiki yaci in mallaki dr shureim shine a gabana.
Na yina ina hidindimuna da 'yan gidanmu cikin
walwala da farin ciki. Da dare yayi na shiga
barci sai na tsinci kaina na canza tunanina ba
irin na da bane. Yanzu tunani nake gani a
gidansa har mun zama ma'aurata, gani dare-
dare a cikin hadaddiyar motar nan tasa muna
tafe muna hirar soyayya. Na dade ina
tunaninsa sannan nayi bacci, na dora da
mafarkinsa mai dadin gaske. Na sa wa
zuciyata na sami dr shureim na gama kamar
yadda malam ya bani tabbaci. Naso in makara
saboda dadin mafarki, na tashi a gaggauce na
shirya na karbi kudin babur a wajen abida.
Yayana ya bata ta bani donshi yana riga ni fita
ma. Sai uwani ta biyo ni zaure da sauri ta
tsayar dani tace yanzu zaki karbo kudin daga
banki? Ko sai kin taso zaki taho dashi? Bilki ta
kawo zubinta jiya na wajenki kawai nake jira in
aikawa haj rabi na fada mata yau da rana zan
aiko mata. Sai zuciyata ta hau dukan uku uku
na fara zullumin inda zan nemo wadannan
makudan kudi. Na hau rawar murya ina kame
kame, nace sai an taso zan taho da kudin. Ina
kan babur ina tunanin yadda za'ayi idan na
dawo gida babu kudin? Ina shiga cikin asibiti
naji farin ciki ya lullunbe min zuciyata saboda
ko ba komai an fara aiki, zuciyarsa ta fara
bugowa gare ni. Sai kuwa naci sa'ar a ranar an
tura mu bangarensu dole zan ga ofishinsa ko
ba ma wajensa aka mu tura mu ba. Muna
shiga kuwa dakin darasin muka ci karo dashi
da dr lukman suna fitowa medical students
suna biye dasu zasu je zagayen marasa lafiya
(ward). Na tare su da sauri na gaishe su, sai
naji caraf ya amsa hadda kallon fuskata, ba
murmushi yake ba haka bai bata rai ba. Dr
lukman ne yake dariya, har yake yi min wasa
yace ke 'yar shagamu ina kika shiga kwana
biyu, rannan har yahaya umar yace in baki
waya ku gaisa, nace ba kya kusa. Nayi dariya
nace to yaushe zanzo ka kirawo min shi a
wayar muyi magana? Da yake yana tafiya ne
sanda yake magana, har yakai barandar waje
banji abin da yace ba. Sai wani dalibi ne yake
bayansu ya juyo yace min cewa yayi kizo gobe.
Na yini ina farin ciki saboda naga canji wajen
amsa gaisuwata da kuma kallon mutuncin da
dr shureim ya min. Ban fara fargaba ba sai da
aka tashi daga makaranta na tunkaro hanyar
gida. Na shiga zullumin karyar da zan gina
wacce ba za'a rutsoni ba, dakin uwani na nufa
kai tsaye sai ta fara murna tana gyara hannu
zata karbi kudi ta kidaya. Sai na zube a
gabanta ina marairaice murya ina bayani. Nace
wallahi tun safe ban huta ba muna ta kai kawo
a cikin asibitin saboda matar bata da jini, don
haka ba za'a yankata ba dole sai an kara mata
jini. 'Yan uwanta ne suka zo maza da mata
muna ta auna jinin har a sami wanda ya dace
da nata shi yasa ban samu fita daga asibitin
ba naje banki, amma gobe da sassafe zanje in
karbo. Uwani ta bata rai, yadda ta amsa min a
ciki ciki na san bata so haka ba, ta bini da kallo
har na fice daga dakin. Ina cin abincin rana na
fice wajen musbahu ban same shi ba, na bar
masa doguwar wasika. Nazo giftawa ya
makoftanmu nayi ido hudu dahare ta leko
kenan ta ganni, ita ma dari takwas ta ranta
min kudin dinkinta zata kai domin ta kusa
haihuwa, ita ma ranar litimin din nace zan
kawo mata. Dole na shiga gidan na tsara mata
karya iri iri na ce gobe zan kawo mata. Itama
ta nuna min bataji dadi ba, har mijinta yayi
fada da yaga kayan dinkin a ajiye bata kai ba.
Naji hankalina ya sake tashi na fito a gigice na
shiga gidan mu har sai da abida ta shiga
damuwa ganin yanayin da na shigo. Tayi ta
tambayata ko lafiya? Nace lafiya kalau. Idan
naji damuwa ta gallabeni sai in tuno menayi da
kudin, kuma nan gana me zan samu. Sai inji
sanyi a raina. Washe gari talata na fita zuwa
makaranta, kai tsaye ofishin dr lukman na
wuce. Ina shiga na iske shi zai fita. Yace dani
ke kuwa baiwar Allah ai ba da sassafen nan
zaki zo ba, sai da rana in aiki ya lafa ko? Nayi
turus banji dadin amsar daya bani ba, ya wuce
abinsa ya barni a tsaye. Sai ga gogan nawa
yau kuma shigar hausa yayi, shadda ruwan
bula tazarce ya dora hular da ta dace da kalar
kayansa. Ya ratayo laptop dinsa a kafadarsa
sai naga ya kara yin kyau matuka babu wacce
zata kalle shi bata sake kallonsa ba. Ya tari dr
lukman sukayi magana, sannan kowa ya wuce.
Sai naji zuciyata na tafarfasa saboda shaukin
so, kai kace zakanya ce mai tsananin jin
yunwa ta ga nama haka zuciyata ta dinga zillo
tamkar ta ballo ta fito da taga abincinta. Sai
dai wannan abincin bana lasa bane, yafi
karfinta. Tamkar soyayyen nama ne aka soya
yana kamshi amma aka zazzaga masa guba
kaga duk kwadayin mutum doke ya kalla ya
wuce ko da kuwa marmarin naman zai kashe
shine. Na fara takawa a hankali na matsa daga
bakin kofar kafin ya karaso. Tun daga nesa na
amshi wata galleliyar harara daga gareshi.
Daya karaso bakin kofa kafin ya lalubo mukulli
ya bude kofar sai da ya waiwayo bayansa inda
nake a tsaye ya wurgo min wata hararar wacce
tafi ta dazu wulkilewa. Sai nayi sauri na juya
na fara tafiya ba tare da nasan inda zanje ba,
sai gani a bakin gadon marasa lafiya nayi wuki
wuki suna kallona ina kallonsu. Sannu likita,
zoki duba cikinsa ki gani ya kumbura. Inji wata
tsohuwa mai zaman jinyar danta. Na girgiza
kai nace ki kira likita ni ba likita bace. Nayi
saurin barin wajen na dawo bakin kofar ofis din
na tsaya, nayi kamar in tura kofar in shiga sai
na fasa. Na hakura na tafi ba don zuciyata
tana so ba. Ina zuwa ofishinmu na iske
kawayena suka hau min surutu. Wai aisha
farida ina kike shiga ne aka nemeki aka rasa
kullum har anyi test jiya ba kya nan? Nayi
shiru na koma gefe na zauna na rasa abun da
yake min dadi. Naci sa'a khadija sani tace inzo
in rakata ta siyo ruwa zata sha magani. Ashe
itama ta kunso labarai kala kala take so mu
kebe ta fatsar. Ta dube ni ta tabe baki tace
baki tambayeni dr shureim ba. Sai naji gabana
ya fadi, sai na zargi kaina ina ganin kamar
kowa yasan halin da nake ciki. Na zabura nace
kamar yaya ban tambaye ki dr shureim ba?
Tace kin manta inda muka kwana na nuna miki
sakonsa a wayata? To in fada miki an gasa
minshi da addua, ba adadi har sai da yaji ba
dadi. Ina kiransa ya amsa, yace dani wacece?
Sai na fada masa sunana khadija sani ismail.
Ni daliba ce a schl of nursing tanan aminu
kano, kuma ina attachment a nan cikin asibiti,
sai yace yayi kyau lafiya? Nace lafiya so nake
yayi saving lambata zan dinga kira muna
gaisawa. Na dafe kirji nace yayi saving lambar?
Tace kwarai kuwa, don da na sake kira sai da
ya ambaci sunana. Sai naji kwalla ta cika min
ido, kishi ya kamani, jikina yayi sanyi kalau.
Taci gaba da cewa da na sake kira sai yayi
tsiyar. Na tambaya a sanyaye meye tsiyar?
Tace wulkanci yayi min kamar zai zageni, wai
kada in sake kiransa. Kuka wiwi nayi da
hawaye na hakura dashi ma ni yanzu. Allah Ya
sa bai san fuskata ba, na goge lambarsa na
daina kiransa yanzu. Dadi ya rufeni, amma fa
na kara tausayawa kaina. Na bata shawarar
tayi hakuri taci gaba da addua, Allah Ya
musanya mata da abin da yafi alkhairi. Ta
amsa min da ameen. Da aka tashi daga
makaranta sai na kasa komawa gida, sai
nacewa khadiji sani ismali zanbi ta gidansu
somin 'yan gidanmu ba sa nan sun tafi unguwa
sai dare zasu dawo. Khadija tayi farinciki da jin
haka, sai muka dunguma muka tafi har yanzu
labarin dr takeyi min. Ban cika bata amsa ba,
tamkar tana min famin gyambon da yake
damuna da zugi ne. Kwakwalwata ta cunkushe
na rasa abin da yake min dadi, na kasa
tantance abin da zanyi. Abinci kala kala aka
jera min a gabana, amma na kasa ci da yawa
saboda damuwa. Khadija sani ta dube ni tace
wai don Allah aisha farida me yake damunki ne
kwana biyu kin susuce tamkar bake ba. Ba kya
son magana, ba kya son karatu gashi ba kya
son cin abinci tundazu dan abincin da kika
zuba kin kasa cinyewa, bakiga yadda kika rame
ba, kika kwanjale ba. Kin cika zurfin ciki, ba a
jin sirrinki daman. Wai me yake faruwa ne?
Nayi murmushi nace haka kowa yake ambata,
malaria ce ke cin jikina. Tace toh kisha magani
mana, yaya zaki zauna da ciwo kina malamar
asibiti, ko in saya miki babu kudi hannunki? Ta
soso min inda yake min kaikayi, na gyara zama
nace kamar kinsan satin nan cikin matsalar
kudi muke, kinga yanzu haka yayana ne aka
bashi ajiyar kudi, ya kawo gida aka shiga har
daki aka sace, ya rasa yadda zaiyi. Mai kudin
yana ta damunsa har da zai kai shi police
station yake ambato. Khadija tace a garin yaya
aka shiga har daki aka yi muku sata, babu
mukulli ne? Nace maso abinka ya fika dabara,
kinsan rayuwar cikin gari, gidan yawa aka shiga
aka dauke. Khadija tace babu dadi, Allah Ya
kiyaye gaba. Shi kuwa mai kudin bai san
kaddara bane? Yayi hakuri mana sai ya samu
ya biya shi. WaLlahi nima a cikin matsala nake,
domin na karbi kudi a wajen abba yayi dubu
hamsin kwanan nan haka ma a wajen mama.
Har sun gane ba'a makaranta nake kashewa ko
na tambaya basa bani. Sai tambayata suke me
nayi da kudi a cikin satin nan, naki fada, ai ban
isa ince malamai na kaiwa ba sai a kusa kashe
ni. DUK KYAN TAKALMI 12 Sai naji hankalina
ya tashi, har na fara nadamar katobarar da na
tafka. Ta bude jakarta ta zaro dukka kudin da
yake jakarta, dubu daya da dari biyu ne kacal
sai 'yan canji. Ta miko min naira dubu daya, na
karba nayi ta godiya. Tayi ajiyar zuciya tace
wallahi dr ya cuce ni, na kashe kudina a banza
ko gezau baiyi ba. Na fada cikin marainiyar
murya nace karki damu kaddara ce Allah Ya
aiko mana. Sai nayi sauri na gyara zancen son
naga tayi sauri ta dubeni, sai nace ciwon 'ya
mace na 'ya mace ne, tunda ya shafe ki nima
ya shafe ni. Bakiji yadda zuciyata take tafasa
ba don takaici. To shi dr dame yafi sauran
likitoci su basa wulakanci sai shi? Khadija tace
yafi sauran mana ke kuwa, shifaa a london yayi
karatunsa, ke har pri sa secondary duk a can
yayi rabin rayuwarsa, sai da yazo nigeria fisha
ya tafi. Ance dai yayi aiki a asibitin nan
shekara 2 a lokacin yana karamin likita. Sai ya
koma ya sake shekaru hudu ya zama
consultant sannan ya dawo kwanan nan. A
bangaren ilimi addini kuwa a saudia yayi
karatun kurani, larabawa suka koyar dashi,
ance yafi kowanne likita sanin kurani. Don tun
yana yaro yaje saudia sai da ya sauke ya dawo
london, ya karasa primary kinga kuwa Allah Ya
yi masa baiwar da ba kowa yake da ita ba.
Gashi dan attajiri shima attajiri, ga ilimi dukkan
bangarorin biyu, ga wani kyau tamkar sai da
zaba aka bashi. Kowacce mace dole taso shi,
sai dai idan ta ga ba ta samu bata hakura
irina. Maryam ahmad ma na gano sonsa
takeyi, har wani kishi takeyi dani, nace kije na
bar miki in dai shureim ne zaki gaji ki kyale shi.
Amma ke aisha farida naga bai dadaki da kasa
ba, ko zancensa ma ba kya so. Kowa yana
yabon kyawunsa, ke ko ki kula. Baiyi miki
bane? Sai naji tamkar an saki bom a kahon
zuciyata, saboda faduwar gaba. Nayi firgigit
nace yanzu khadija ina ta kaina ina ni ina cusa
kaina wajen irin wannan halitta? Ai sai ku
kyawawa, masu mota 'ya'yan attajirai. Khadija
tace kin hutawa kanki wallahi kina burge ni
yadda kike tafiyar da rayuwa, ba kya jajubo wa
kanki abun da zai wahalar dake. Nima nayi
nadama ba zan sake shiga irin wannan hatsarin
ba. Yanzu mun bata da malaman nan
makaryata, wai yaga aurenmu har da haihuwar
'yan biyu. Shine ai na saki jiki nayi ta tura
musu kudi suna cemin zai zo da kafarsa
nemana ga mutum kamar zai yayyaga ni cikin
waya don masifa. Bani ba wani malami ai
yanzu na rufawa kaina asiri nace mohd ya aiko
da iyayensa muyi aure. Ina laifinsa yaro
matashi, yana da mota da gidan kansa da aikin
bankinsa, nima da aikina ya ishe mu rayuwar
duniya. Sai naji hankalina ya tashi, dana sani
ta afko min. Na gyara zama nayi tagumi ina
duban khadija na rasa in da zan saka raina, sai
yanzu na fara gane kuskuren da na tafka a
rayuwa. Ummi ta cuce ni. Na fada a cikin
zuciyata yayin da hawaye ya cika min ido.
Nace da khadija kina so kice min gaba daya
asirin da malamanki suka sha zabgawa ko
daya bai taba shi ba, asiri baya cinsa kenan?
Tace baya cinsa tunda bai ci shi ba, babu abin
daya yi masa. Malamina daya ne ya fada min
gaskiya tun da farko naji haushinsa, daga
karshe na gane gaskiya ya fada min. Yace dani
yaron nan da kike so gaskiya ya rike adduar
neman tsari dare da rana, da wuya a jefe shi ya
taba shi, sai dai kawai kije kiyi addua in da
alkhairi Allah Ya hada ku ta wata hanyar, a
dadin rai yazo, kuma ina so ki sani ba'ayiwa
Allah dole. Khadija tace aiki ma daina damuwa,
Allah Ya ganar dani har na dade ina istigfari.
Su maryam anmad ne suka rage suma Allah Ya
ganar dasu. Shiyasa aka ce wani kyau bala'I
ne, sai a dilmiyar da kai in bakayi taka tsan
tsan ba. Yanzu dr shureim in ba don Allah Ya
sa nutsatte bane da mata sai sun halakar
dashi. Haka ma mace mai kyau idan baatayi a
hankali ba maza su halakar da ita, su rude ta
da kudi tabi su koda kuwa tana da aure. Ke dai
Allah Ya sa mu gane gaskiya. Sai naji khadija
ta burge ni, tafi ni gaskiya. Ina ma a llokacin
da naje neman shawara wajen ummi khadija na
samu ta fada min abinda ta fada yanzu, da ba
wa zuciyata hakuri, da ban je na jefe kaina a
rigima ba. Yanzu gashi komawa gida ya
gagareni. Da me zan biya wannan dimbin
bashin na kaina gashi babu alamar nasara a
aikin malamin. Khadija ta katse min tunanina
tace duk inda ya kai da takama da kwalliya, da
yanga karshen alewa dai kasa. Dole mace zai
aura, ba auri kansa da kansa ba. Kuma dole
yayi 'yar murya kafin a bashi ita, dole ya kashe
kudi ya bauta mata saboda Allah Ya wajabta
masa ciyarwarta, sutura, kula da lafiyarta,
muhallinta da duk wata dawainiyarta. Daman
dai ance DUK KYAN TAKALMI dole kafa ce zata
saka sannan a taka kasa. Lallai zanso inga irin
macen da zai aura, karshenta fa ya kare a
mummuna, baka, 'yar talakawa, kinsan karshen
irinsu kenan. Nace yana da mata fa har da 'ya,
kema kinsan dr shuriem ba zai auri kucaka ba.
Khadija tace ke aisha farida wa ya fada miki
wannan? Nayi murmushi nace matarsa ma
baturiya ce a london suka hadu, a london take
zaune. Da bakinsa naji yana fada. Kuma a
gabana sukayi waya da ita cikin harshen
turanci ko hausa bata ji. Khadija ta gyara zama
tace don Allah da gaske kike? Ni da kin fada
min haka tuntuni ai da ban wahalar da kaina ba
wallahi. To wai ina kika ganshi ne har kika ji
yana waya, nifa tun ganin nan nasa da mukayi
yana motarsa ban sake ganinsa ba. Ko dai ba
shi kika gani ba? Nace shine wallahi, abokin dr
lukman ne, likitan kwakwalwa wanda matron
maryam take aikena wajensa. Kinsan tana da
kanwa mai matsalar kwakwalwa, to yana duba
to ko ba ranar clinic ba. Khadija tace lallai ba
zai saurari kujari-kujari irinmu ba, mai mata
baturiya mai zaiyi damu? Naji zuciyata tana
kokarin bugawa, sai na mike na tayar da sallar
la'asar daman da alwalar azahar dina bamu
dade dayi ba. Nayi sallama nayi addua, Allah
Ya biya min bashin da yake kaina. Na yunkura
zan mike in tashi, sai khadija tace dani aisha
farida gaskiya akwai abinda yake damunki,
saboda duk jikinki yayi sanyi, yanzu ko yanayin
sallarki ya canza ba irin na da ba, ba kya
samun nutsuwa wajen yin sallh, kin daina
doguwar addua bayan kin idar da sallah. Nayi
shiru ina tunani nace a raina yanzu son dr
shureim har addinina zai taba, bayan karatuna
da ya tava ga zaman lafiya dana rasa. Sai na
zuba wani zazzafan hawaye nayi sauri na boye
fuskata don kada ta gane. Na dauki jakata na
rataya nace mata zan tafi gida. Ta rako ni har
bakin titi na hau acaba na tafi, ita kuma ta
koma gida. Sai a hanya na fara tunanin halin
da zan fada idan naje gida, don haka nace dan
acaba ya kai ni zango gidan ummi kenan. Ina
isa cikin gidan na tarar da kofarta a kulle
alamar bata nan, sai naji banji dadi ba don
haka na leka bangaren faccalarta na
tambayeta. Tace min bata nan tun jiya ta tafi.
Sai naji zuciyata ta buga na dafe kirji na
tambaya kafiya? Ta tafi unguwa tun jiya bata
dawo ba? Amsar da ta bani itace babu komai.
Na sami kujera na zauna nace da ita ki fada
min gaskiya, ummi kawata ce bata boye min
komai. Sai tace to kiyi mata waya mana sai ta
fada miki da bakinta tunda aminiyarki ce. Na
jikina a sanyaye nace to sai anjima na tafi. Sai
naga ta bini da kallo alamar tausayawa tace
dani gaskiya ummi tana gidansu mijinta ya
sake ta. Kuna fita shekaran jiya ya kai mata
takardar sakinta gidansu, ashe bai bata izinin
fita ba ta biki kuka fita har ina cewa ku jirani in
shirya kuka ki. Na dawo na tsuguna a gabanta
nace innalillahi wainna ilaihir rajiun. Yanzu
yassar saboda dan wannan dalilin ya saki
ummi? Tace a'a ba wannan kadai ba, daman
akwai wata kasa. Ummi bata da kunya, ga ta
da bin bokaye da 'yan tsubbu kowa yasani,
mijinta ya sani saboda yana tono binne binnen
da takeyi, da kuma barbade barbade da takeyi
masa a abinci. Da zarar sun fada mata karya
sai ta zai tana habaici ta bata da kowa, har
uwarsa da ta haife shi bokanta yace uwar
mijinta bata sonta. Yanzu ya dace ace ummi
tazo ta zazzageni? Jiya ita da kannenta da
kyar aka fitar dasu daga gidan nan wai sai sun
dake ni. Har da cewa yadda na raba zamanta
da mijinta nima zamana da mijina sai ya kare,
sai in babu malamai a kano. Kinga kenan
malaminta ne ya fada mata ina yi mata asiri.
Ta tabe baki ta harareni tace to ai fitar da
kukayi gidan boka kuka je, saboda yassar
yabiku a baya har yaga inda kuka nufa, shi
yasa ya kai takardar sakinta gidansu. Ko kin
dauka ban gane ki bane munafuka kin san inda
take. Aiko ki tayi kizo ki barbada min wani abu
ko? Na zabura na mike tsaye na dafe kirjina
nace ni?? Wallahi bansan ummi ba ta nan ba
da bazan zo ba. Ba na irin wadannan halayya
kuma ba da wata manufa nazo ba. Tace dani
fita daga gidan nan kafin in tara miki jama'a.
Kuma duk ranar da kika kuskuara kika hadu da
yassar yace sai ya balla miki kafa, tun a
sakandire kike yi mata hudubar tsiya, yasan kin
tsane shi, shine kika biyo ta har gidan aurensu
kika kai ta gidan boka, wato a kashe shi kuci
gado ko? Tunda nake a duniya ba a taba yimin
cin mutunci, kazafi da wulakanci irin na
wannan ranar ba. Duk irin gulmace gulmacen
nan da ake yi a lungunmu tun ina yarinya ba
ataba cewa ga abin da aisha farida tace ba.
Lalli na jefa rayuwata cikin wani mawuyacin
hali saboda son dr shureim imran. Na gaggauta
ficewa daga gidanta kafin ta tara min jama'a
kamar yadda ta fada, kuka nake wiwi na hau
acaba ba tare da nasan inda na nufa ba. Sai da
dan acaba ya tambaye ni sau uku hajiya ina
zan kaiki? Sannan nace ka kaini gadon kaya.
Gidansu maryam ahmad kenan. Ita ma inje inji
halin da take ciki da dr shureim dinta. Duk da
haka ban daina sonsa ba. Maryam ahmad tayi
mamakin ganina, amma ganin ina fara'a ta san
lafiya kalau kenan. Tace dani shegiya aisha
farida umar daga ina kike, ba ki koma gida ba
ne har yanzu na ganki da uniform a jikinki?
Nace ke dai bari, yau bana jin komawa gida da
wuri, zumunci nake ji, zuwa nayi in gaishe da
su mamarki. Sai taji dadi taja hannuna har
dakin mahaifiyarta muka gaisa, na gaisa da
kannenta da 'ya'yanta biyu wanda Allah Ya
yiwa mijinta rasuwa ya barta dasu amma fa da
dimbin dukiya. Muka koma dakinta muka zauna
akan wani makeken gado, ta kunna mana AC
yayin da ta dinga kwallawa 'yan aikin gidansu
kira suna kawo min abubuwa kala kala kamar
su juice, kayan marmari, cincin da cake. Sai
taga duk na kasa ci sosai, ina yawan yin shiru
idan tana magana kamar hankalina baya tare
da ita. Sai ta zungureni nake dawowa
hankalina, na rasa yadda zan dauko mata
maganar dr shureim domin kada ta zargi wani
abu ta gano saboda zancensa na zo gidansu.
Domin ban taba zuwa ba gidansu haka kawai
ba, sau daya na taba zuwa kuma daga
makaranta muka zo muka yi mata gaisuwar
mijinta, da yake gidanta na kallon gidansu ne.
Muka shigo nan ma muka yi mahaifiyarta, to
anan na san gidansu. Da kanta ta dauko min
hirarsa tace baki tambayeni likitana ba dr
shureim. Sai na zauna dai dai nace yaya akayi?
Ki bani labari, akwai cigaba ko? Tace wanne ci
gaba ni da tun kafin aikin da na rabawa
malami bai je ko ina ba abu ya dagule gaba
daya, nace to su daina adduar yafi karfina. Dr
shureim yafi karfin ya kwanta in taka shi da
takalmin kafata, kinji. Anya mutumin nan
haifarsa akayi ba tikowa yayi daga sama ba?
Ace mutum ya hadu ta ko ina babu aibu a
tattare dashi? Sai naji na kara tsanar kaina, na
fada cikin shamulalliyar murya, me ya faru?
Tace mutuminki na same shi a ofis dinsa
wancan sati, malamina ya bani laya na kunshe
a karkashin harshena wai in dai da layar nan
duk abin da nace masa ya zauna babu musu.
Bayan turarukan da na dume jikina da goshina
dasu, wasu masu wari kamar na 'yan bori, ni
kaina sun isheni da wari balle shi dan gayu. Ina
shiga kaina tsaye ko fargaba banayi saboda an
bani tabbaci, ni kuma na yarda da cewar na
same shi na gama kamar yadda suka bani
tabbaci. Shi da wata likita mace ina jin dai
daliba ce, bata gama ba. Ta cika tayi taf kamar
zata fashe saboda fushi. Ta wani galla min
harara nima na harare ta saboda abin da ya
kawo ta shi ya kawo ni. Da na gaishe su babu
wanda ya amsa sai na sami kujera na zauna a
kusa da ita, shima yana zaune a kujerarsa. Ya
juyo ya dubeni sarai sannan ya dukar da kansa
yaci gaba da rubuce rubucensa. Ya gama ya
mika mata takarda, gami da cewa Allah Ya
sawake jeki. Ta tabe baki ta dubi takardar da
alama magani ya rubuta mata sai tace inje in
sha wannan kenan? Ya ce eh In sha Allah
kurajen zasu warke. Sai tace doctor muje ka
kaini chemist din mana, nina fi so ka tabbatar
masu kyau ne. Sai ya bata rai yace ba aikina
bane in rubuta miki magani, kuma in raka ki
zabar miki wanda zaki saya ba, komai a rubuce
yake zasu karanta su baki. Tace kaki zuwa ka
duba ni a gida, kwanana biyu ban fito ba har
waya nayi na fada maka. Na turo maka sakon
adireshina kaki zuwa. Sai ya harare ta yace
bani da lokacin zuwa duba dalibaina don basu
da lafiya. Ta sake turo baki tace amma ai
daliban daban daban ne, ba daya nake da
sauran ba. Ya daka tsawa ya zazzare mata ido
yace dalibaina dukka daya suke, daidai kike da
wannan. Ya nuna ni, ita kuma ta wurgo min
harara, nayi murmushin jin dadi nima na harare
ta sama da kasa. Yace idan baki da abin da
zaki fada min mai ma'ana game da karatunki ki
tashi ki tafi, kada ki kara shigo min ofis. Ta fice
sai ya juyo wajena ya tambaye ni cikin fushi,
ke kuma fa? Menene? Ina fitowa na kira
malamin da ya bani laya da turaren nan mai
daga hankali don wari kamar na 'yan bori.
Yana daukar wayar sai yace malama an sami
nasara kuwa? Nace nasarar me mutum kamar
zai mare ni? Sai yace to an sami kuskure ne
daga wajenki ina ganin baki yi yadda nace ba.
Nace komai daidai nayi banyi kuskuren komai
ba. Yace yaushe zaki zagayo sai in sake
bincikawa muga ta hanyar da zamu sake
bullowa kuma? Nace Allah Ya sawake in sake
kashe wani kudin bayan wanda na tula maka
na baya har da yankan rago amma a banza.....
Kafin in rufe bakina ya kashe wayarsa, nayi ta
kira har yau a kashe. Ko yau ma na gwada a
kashe, yaga na gane shi dan damfara ne babu
abin da ya iya. Haka nabi duk sauran malaman
naci musu mutuncu sukayi ta kame kame, sai
yanzu na gasgata cewar malaman zamanin nan
sun raina wa mata wayo, sun mayar dasu
jahilan karshen zamani. Idan kura tana
maganin zawayi tayi wa kanta, ke kina ganin
malaman kinga wahalallu masu matsala sun
kasa maganin matsalarsu, wai suce zasuyi wa
wani maganin matsalar su, sai suyi ta canke
canke don basu ma san ya ake duban ba. Ai ni
na dawo daga rakiyarsu na goge lambar
kowannensu, ko sun kira ni tsuye su nakeyi, sai
su waya da sauro. Ko wata na gani zata bata
lokacinta wajen bin malamai zan hanata sai dai
idan taki yadda in kyale ta, idan taje taga uwar
bari zata dawo da kanta tayi min bayani. Duk
wadannan bayanai da maryam keyi tuni sun
ragargaza min zuciya, kwakwalwata ta riga ta
dau gobara, na rike kai kawai tamkar mai
ciwon kai yayin da na sulale na kwanta akan
gadonta tamkar sumammiya. Na yarda da
cewar komai ya sami bawa rubutacce ne, in ba
haka da ya za'ayi tun farko inji wadannan
labarai akan malamai kuma in dauki
zunzurutun kudi in kai wa wani? Nace a raina
me yasa na fara zuwa gidan ummi neman
shawara banzo wajen khadija da maryam sun
fada min halin malaman zamani ba? Tun daga
lokacin na tabbatar kudin sun mula kuma ba
zan sami dr shureim ba. Maryam labari take
bani kala kala, amma bana fahimta ina can ina
tunanin abin da zanje in tarar a gida, haduwata
da uwani mai adashe da sauran makoftan da
na ciyo bashi, sannan bayanan da zanyi wa
yaya hussaini in da naje na kai dare bayan tun
karfe biyu na rana muka tashi.
A gidan su maryam nayi sallar magriba, na yi
ishai muka ci abincin dare. Taga bani da niyyar
tafiya sai ta fara mamaki, tana jero min
tambayoyi iri iri kasancewar ta sanni ba mai
bin gidan kawaye bane kwata kwata balle tace
na saba daman. Sai da na fuskanci har ta fara
gyangayi , tara da kwata na dare sannan na
fara haramar tafiya gida ba don naso ba,
saboda niyyata sai karfe goma sha daya na
dare zan koma gida kafin nan kowa yayi bacci.
dole na fito ta raka ni kofar gidansu na hau
babur na tafi. Ina tafe ina adduoi har na isa
unguwarmu, daga nesa da gidanmu nace mai
acaba ya sauke ni, don bana so 'yan gidanmu
suji karar babu na san idonsu yana kan hanya
suna zuba idon dawowata. Na biya dan acaban
kudinsa yayin da nake tafiya tamkar hawainiya
ina yi ina waige waige tamkar barauniya. Da
sanda na shiga zauren gidanmu naci sa'a babu
'yan matan gidan masu zance a zaure da
samarinsu. Sai na leka tsakar gidan, nan ma
ban ga kowa ba. Sai na cire takalmana na rike
a hannuna ina sanda dana zo giftawa ta
windown dakin uwani sai na tsugunna nayi
duku duku na wuce don kada taga giftawata,
najiyo motsin mutum a daki ina kyautata zaton
ba ta yi bacci ba. Da yake babu wuta sai
hasken fitilar kwai da kyandira zaka dinga
hangowa a dakunan don haka na hango kyallin
kyandir a dakin abida ina hango inuwarta a
tsaye jikin labule, sai dai ba zan tantance abin
da takeyi a tsaye ba. Na duba kofar dakin sai
naga takalman yaya hussaini da alama ya
dawo, nan da nan tsoron da nake ciki ya karu.
Nayi maza na tura kofar dakina na shiga na
iske ta shimfidar da 'ya'yanta ta rage hasken
fitilar kwai a gefe. Shiga ta dakin ke da wuya
ko jakata ban ajiye ba naji motsi a kofar
dakinmu, nan da nan na tsuguna na takure a
lungu. Sai na sankare saboda firgici. Abida ce
ta shigo hankalinta a tashe, tana ambaton
subhanallahi, yaya zanyi yau. Tana rufe bakinta
sai muka hada ido yayin da zaka dinga hango
mamaki a cike da fuskarta gami da firgici. Ni
kuma ina tsugunne ina kokarin daidaita
numfashina domin na shide, don tsoron yaya
hussaini da uwani a tunanina daya daga
cikinsu ne. Aisha farida lafiya? Yaushe kika
dawo? Ina kika shiga yau tun safe? Abida ce ta
jero min wadannan tambayoyi masu wuyar
amsawa. Na mike tsaye a sanyaye ba tare da
na san abinda zance mata ba. Ta sakke kallona
tace da ban ganki ba yanzu da kin jawo min
masifa yau, saboda yanzun nan yayanki ya
shigo ko minti biyar baiyi da shigowa ba, ya
shigo da ciwo a kafarsa sun fadi akan babur
shine yace in taso ki, ki rubuta masa allura ko
maganin da zai sha ko ki dauko akwatin
taimakon gaggawa (first aid box) ki zo kiyi
masa dressing. Na kasa ce masa bakya nan,
shine na shigo nan ina tunanin abin da zance
masa. Ina kika shiga kika sa hankalina ya tashi
ko abincin dare banci ba? Me yake faruwa
tsakaninki da uwani tayi ta zuwa nemanki
ranta a bace tunda rana? Na zazzare ido nace
me tace miki? Abida ta girgiza tace nayi nayi
ta fada min dalilin nemanki din da takeyi, sai
tace inkin dawo in tambayeki ita ba zata fa.
Ranta fa a bace har zage zage nake jiyowa
tanayi daga dakinki. Ke kuwa aisha farida me
ya hadaki dasu uwani ke da ba a zama a yi
gulmar wani dake, me ya kai ki tsoma baki a
maganarsu? Nasan wata gulma suka hado aka
ce dake a ciki, to ni shawarar da zan baki gobe
da sassafe kafin ki fita kije ki samu uwani ku
sulhunta, idan kinsan kin fada ki basu hakuri,
idan baki fada ba ki wanke kanki tun kafin
yayanki yaji abinda yake faruwa yaci miki
mutunci, kinsan halinsa. Duk kin susuce a
kwanakin nan kin canja halinki sai kiya ta nuku
nuku kamar mara gaskiya. Nayi shiru ina
sauraronta yayin da na cire kayan makaranta
na saka doguwar rigar baccina na saka katon
hijabi na dauko 'yar akwati na wuce gaba, tana
tsaye tana kallona cike da mamaki da takaici.
Nayi sallama a kofar dakinsu, yayi min izini na
shiga, na durkusa na gaishe shi yayin da ya
miko min kafarsa naga ciwon nayi masa sannu
da adduar Allah Ya kiyaye gaba. Sannan na
bude akwatin na shiga aikin saka iodine da
auduga. Ita kuwa abida tana can tana kinkimar
'ya'yanta daya bayan tana kai su fitsari. Naga
gama masa yayi min godiya na fito. Har yanzu
abida na dakina tana jirana bata gama jero min
tambayoyin da suka cika zuciyarta dam! Ta
dube ni ta yatsune fuska tace baki fada min ba
fa in da kika je ko daman kinsan da maganar
su uwani shiyasa baki dawo gida da wuri ba?
Na bata rai na turbune fuska nace ni ba
wannan bane ya tsayar dani, bayan mun tashi
daga asibiti aka ce mu dawo za'ayi mana
darasi daga karfe hudu zuwa shida, wani sabin
likta ne zai gabatar da wata sabuwar cuta
shine naga ba zan iya dawowa gida ba in sake
komawa da yamma ba, sai nabi khadija sani
gidansu da yamma muka koma, bamu baro
asibiti ba sai da karfe bakwai ana sallar
magriba, tace inzo gidansu idan nayi sallah sai
in wuce. Shine kuma muka zauna muna hira
bansan dare yayi haka ba. Abida ta tabe baki
da alama ba ta yadda da bayanai na ba. Ta
sake dubana tace aisha farida me ya hadaki da
musbahu kuma shima ya dinga aiko wani yaro
da wasika, zuwansa biyu. Nayi nayi ya bayar a
ajiye mike yace a'a, ance hannu da hannu zai
baki. Sai na sake gigivewa na hau kame kame
nace musbahu kuma? Meye hadina dashi? To
ina jin bani aisha faridar ba. Abida tayi
murmushin takaici tace kila na fara zama
kurma har a ambaci aisha farida inji ba daidai
ba. Babu abinda zance miki tunda boye boye
kike yi min tun yanzu. Sai dai kiyi hankali da
mutane, ki kuskuri bin shawarar batattun
kawaye, ki rike mairaici da talaucinki. Ta juya
ta fice ta rufo mana kofa. Na sulale na kwanta
na dora hannu aka ina juye juye, sai dai ban
fasa karanto innalillahi wainna ilaihir rajiun ba.
Yadda naga rana haka naga dare, barci ya
gagareni. Fargaba da tunanin haduwata dasu
uwani ta gallebe ni. Haka na kwana ban rintsa
ba saboda tashin hankali, don haka da asuba
kiran sallar farko na mike na shiga bandaki
nayi wanka, duk da sanyin ruwan ban damu da
saina dumama ba, na fito nayi sallar asuba na
kakaba kayan makaranta. Na dauki jakata na
dauko biro da takarda na rubutawa abida
wasika na ajiye takardar a bude akan
tabarmata yadda zata gani daga shigowarta.
Na fita daga dakin ina sanda tamkar barauniya
nayi sauri na fice, da yake kofar gidan a bude
take maza masu zuwa masallaci sun bude. Na
rufe fuskata saboda kada inci karo da mazan
gidanmu, duk da banji motsin fitowar yayana
ba, daga dukkan alamu kafar ta matsa masa
da ciwo tunda bai fito sallar asuba ba, dan
baya fashi in dai lafiyarsa kalau. Sai nayi ta
tafiya da kafata sabida rashin babura
kasancewar gari bai waye ba duku duku ne. Na
dade ina takawa da kafata sannan Allah Ya
jeho min mai babur na hau, mun dade da fara
tafiya ba tare da nasan inda zance ya kaini ba.
Ya sake tambayata malama ina zan kai ki? Da
farko nace masa asibitin aminu kano, har
munyi nisa na canza shawara nace ya kaini
jakara, umguwarsu ummi wato gidan iyayenta.
Muka isa kofar gidan na sauka daga kan acaba
sannan na biya shi kudinsa. Abinka da cikin
gari 'yan gargajiya basu san baccin safe ba
kowa ya tashi ya shiga safgoginsa. Mai kosai
ta ta fara suya, masu waina suna danawa.
Haka masu koko da masu shayi da biredi sun
fara tafasawa. Duk inda ka waiga yara ne
dauke da 'yan kwanuka a kansu an aiko su
sayan abin karin kumalllo. Na shiga cikin
gidansu ummi cike da fargabar abinda zanje in
tarar, ummin na iske a tsakar gida ita kadai ta
saka buta a gaba da alama alwalla za tayi,
tunani da damuwa sun hana ta sukuni. Ta
buga tagumi kamar mai tunani yayin da
idanuwanta sukayi luhu luhu. Tayi matukar
firgita data daga ido ta dubeni , ta cika da
mamakin ganina a daidai wannan lokacin. Ta
fada cikin firgici aisha umar lafiya? Sai na fara
zubar da hawaye shar shar shar daga
idanuwana. Ta mike tsaye da sauri taja
hannuna zuwa dakin da take kwana, a cike
yake da yara daga dukkan alamu kannenta ne,
yara 'yan kuci kuci da masu dan wayo.
Kowannensu barci yake da munshari yayi da
zarnin fitsarinsu da warin daudar jikinsu suka
daki hancina. Kamar inyi amai, na dai daure na
zauna akan wata dakwalkwalalliy ar katifa da
ummin take kwana don naga 'yarta a shimfide
a gefe. Anan tace in zauna bari taje tayi alwala
tayi salla sai tazo mu zauna. Kallonta kawai
nakeyi tamkar gunki na kasa magana, na dubi
yaran da suke linkaya a cikin fitsari babu
abinda ya dame su. Naji dama nice su nake
linkaya a cikin fitsarin nan da irin wannan
rayuwa da na jefe kaina. Ba jimawa ummi ta
shigo sanye da hijabi da alama ta idar da
sallah ko addua batayi ba sabida rashin
mutuswar dake tattare da ita. A firgice ta shigo
tana sauri kamar zata ci da kai, ta goya 'yarta
duk da himilin fitsarin da ta ci a napkin, zarni
kwar. Tace in taso mu tafi gidan malam. Na
mike da sauri muka fice ba tare da ta leka
dakin mahaifiyarta tayi mata sallama ba. Tafiya
muke fankam fankam tamkar fatake, muna tafe
muna tayar da kura kamar shanu, mu dukanmu
hankalinmu a tashe. Na juya na dube ta nace
ummi malamin nan kuwa yana da gaskiya?
Nifa har yanzu banga komai ba. Ummi ta tabe
baki tace uhmm ke dai bari. Ai shiyasa nake so
muje mu ritsa shi kafin ya gudu, macucin
banza. Kinsan mijina ya sake ni kuwa? Korar
kare yayi min fa. Na zabura na dafe kirji nace
au daman kinsan macuci ne kika kaini wurinsa.
Tace ke dai muje muji abinda zai ce mana. Na
fada a bayyane innalillahi wainna ilaihir rajiun.
Allah ba Ya dorawa bawanSa abinda ba zai iya
ba sai dai bawa ya dorawa kansa. Ina zan
sami himilin kudin da na ranta in biya masu
shi, ummi yaya zanyi? Ummi ta dubeni a
fusace tace to ni kinsan irin zaryar da ake yi
min a gidanmu saboda bashi? Ke dai kawai
Allah ya rufa mana asiri. Na fusata nace babu
wanda ya taba saka ni a tozarci da tashin
hankali a rayuwata irinki. Ta harare ni tace dan
Allah aisha ki rufe min baki, gara kema baki
aure shi ba balle ya sake ki, nifa har da goyo,
na zama bazawarar karfi da yaji. Haka dai
muka tafi muna ta fada a hanya kamar zamu
cinye kanmu a cikin bus. Tana jin haushina ni
har nafi jin haushinta fiye da malamin ma.
Muka iske shi a zaure yana ganawa da wasu
guda biyu da alama hamshakan masu kudi ne,
daga ganin motar da suka zo da ita da kuma
kayan da yake jikinsu. Malam yana ganinmu
sai ya bata rai, bai amsa gaisuwarmu bai sai
bakinsa ne suka amsa. Muka wuce jikinmu a
sanyaye zuwa cikin gidan, da kyar daya daga
cikin matansa ta bamu tabarma muka zauna
sai wani irin kallon banza suke yi mana dan
suna suyar dakwalen kajin da aka karba daga
wajen mutane na sadaka amma suke juyewa a
cikinsu babu wata sadaka. Shi da iyalansa sun
zama tika tika saboda da cin kaji da raguna da
suke karba da sunan za'a rabawa almajirai. Na
zunguri ummi na nuna mata kajin da ido, ta
gyada kai ta fada a hankali tace eh kudinmu
ne, ai yau sai na masa rashin mutunci. Can
malam ya shigo ko kallonmu baiyi ba ya wuce
dakinsa, yayin da matarsa daya ta dinga
wucewa da abinci kala kala tana kai masa,
kamar shayi, kaji soyayyu, wainar kwai da
biredi. Mu dai muna zaune muna kallon ikon
Allah. Su kayi kasonsu a faranti yara da manya
suka dauka kowa yana ci babu ko sala daya da
suka bamu. Malam yaci ya gyatse, yazo ya
wuce ya shige wanka. Ya fito ya shiga daki ya
fesa kwalliya da farar shadda mai kyau sannan
yazo ya wuce ciki daki in da yake ganawa da
baki. Sannan ya aiko matarsa yace ta kiramu.
Muka shiga muka iske shi a tsaye a tsakiyar
dakin, muka sake gaishe shi ya amsa a
gaggauce. Yace daman yau mu kayi daku zaku
dawo? Haushi ya kama mu, sai ummi ta kalle
ni, nima na kalle ta sai ta murguda baki tace
yau ne laraba ko? Kuma yau kace mu dawo. Ya
kalli agogo yace kuma ce muku nayi kuyi
sammako? Ummi ta fada a fusace, kamawa
tayi ka ganmu yanzu kasan ba lafiya ba. Ni dai
ina zaune a lungu nayi kuri ina kallon irin
wannan damfara kiri kiri, a lokacin da zai karbi
kudinmy yana fara'a yanzun da muka zo karbar
aiki rai ya baci. Ummi tana durkushe tana
kokarin sakko da goyonta. Sai yace ba sai kin
sauke goyonki ba yanzu zan sallame ku akwai
inda zanje don sauri nake yi. Ummi tace ko
yanzu zaka sallame mu ai na sakko da 'yata
tasha nono ko? Tunda ta farka tana kuka. Yace
meye ma yake tafe daku? Ummi ta waigo ta
sake dubana tace kinji ya manta ma. Saina
sankare a zaune na tabbatar mun fada hannun
mayaudati kamar yadda kawayena khadija da
maryam suka fada. Ummi ta sake cewa malam
gaskiya komai ya kwabe tsakanina da mijina,
har ya sake ni. Ga kawata ma taji shiru bai zo
ba. Yace kuje zan bincika naga abinda yake
faruwa, amma aiki dai na gama. Ummi tace
wanne bncike kuma, kai da ka mance abinda
muka fada maka. Ya zazzare mata ido yace ke
ba'ayi mana tsiwa ana kibi a hankali. Ummi ma
ta zare masa ido tace tsiwwa ko zance
gaskiya? Ni dai ba zan gidan nan ba sai an san
abin da za'ayi, kudin da muka biya a banza
kenan, bashi muka ciyo muka kawo maka.
Aisha farida kiyi magana kyayi shiru. Na fada a
sanyaye mai zance ummi? Ya jawo wata jakar
leda a fusace sai ga daurin rubutu kashi kashi,
ya miko min daya ya mikawa ummi daya, ya
sake kwance wata ledar ya miko min laya daya,
ya mika mata daya. Duk iri daya ce. Yace kuje
kusha rubutun nan a tsaye, sannan ku kasance
layan nan a jikinku sai kuyi kokari ku hadu da
mazan da kuke so, ku tambayesu duk abinda
kuke so daga gare su zasu yi muku. Ummi ta
karba ta tabe baki tace mu fa ba wani abu
muke nema a wajen mazan ba illa soyayyarsu.
Yace to ai haka nake nufi ko soyayya ko kudi
duk zasu baku. Na zuba abubuwan daya bani a
cikin jakata na mike tsaye nace da ummi taso
mu tafi. Ta mike a fusace tace zamu tafi
malam, sai dai gaskiya idan bamu ga canji ba
zamu dawo, asan abinyi dan bangane irin
wannan aikin ba. Muka fice yayin da ya bimu
da harara, muka fito tsakar gida dukkanin mu
rai a bace. Matansa sunyi carko carko suna
kallonmu domin suna jiyo duk abubuwan da
ummi take fada. Ta harare su tace Allah Ya isa
kudinmu da ake damfarar mu ana cin kaji, ko
wacce shegiya tayi bul- bul da abincin haram.
Ni dai nayi wuf na fice kada a biyo mu da duka,
har zaure suka rako ummi suna zaginta tana
zaginsu. Naja hannunta muka tafi, a hanya ta
fashe da kuka don takaici, ni kukan ma na kasa
yi sabida tsananin tashin hankali. Tace dani
aisha kinga macutan malamai ko? Wallahi ni
ban taba kula da cutar da wannan dattijon yake
min ba sai yau. Duba kiga yadda komai ya
dagule mana. Nayi ajiyar zuciya nace yanzu
ummi meye abinyi? Tace kije wajensa ki gwada
ki gani bayan kin sha rubutun kin daura layar.
Nima yanzu gidan yassar zanje in gani ko zai
kula ni, idan abinda ya bani bai yi aiki ba
wallahi sai na dawo na tarawa malamin nan
mutane. Nace kina ganin wannan rubutun da
layar daya bamu ta gaskiya ce? Ta wa da naki
fa iri daya ne, babu wani suna daya tambaya
balle ace kowa daban, rubutun ma daga gani
ba namu bane saboda baiyi niyyar bamu komai
ba sai da yaji kince babu inda zakije idan baiyi
wani abu ba sannan ya bamu. Tace ke dai
muje mu gwada mu gani. Mukayi sallama na
hau acaba zuwa asibitin malam ummi kuwa ta
hau bus zuwa unguwar zango gidan yassar. Ina
sauka na bude jakata na zaro kullin runutu na
tashi tsaye kamar yadda ya umurce ni na
shanye, yayin da na ciro layar nan na damke a
hannuna na nufi ofishin sahibina. Ina mai
karanto adduoi don neman dacewa. Zuciyata
cike da fargaba. Na tura kofar ofishin a
sanyaye gami da yin sallama, zazzakar
muryarsa ce ta amsa sannan na tura kai na
shiga. Kallo daya yayi min ya dukar da kansa
kasa bai sake dagowa ba yaci gaba da rubuce
rubucensa. Na gaishe shi ya amsa a shelake
yayin da fuskarsa babu annuri. Na dade a tsaye
bai ce dani komai ba kuma yaki dagowa ma ya
kalle ni. Nayi ajiyar zuciya na tambaye shi a
tsorace dr lukman ya zo kuwa? Da yazo da
baki ganshi ba. Amsar da ya bani kenan. Nace
likita ina da tambaya game da kurajen fuska.
Sai yace dani ke fita ki bani wuri, nan ba
ofishin dr lukman bane, ya koma ofishinsa a
room 8 an gama masa gyaran, kada ki sake
shigowa nan nemansa. Nayi sadan sadan na
fice, na dade a tsaye a bakin kofar daga waje
ina takaici tamkar in rusa ihu. Sai wata zuciyar
ta raya min ko in saka layar a bki in tauna zata
fi aiki. Sai na zura ta a baki ina taunawa na
sake tura kofar na zura kaina ciki. A tsaye a
tsakiyar ofishin na iske shi yana duba wani
littafi a jikin durowar littattafan dake kusa da
bakin kofar. Nace dan Allah likita zan iya bar
ma sako ka bawa dr lukman? Naje ofishinsa
baya nan..... Ban rufe bakina ba naji ya banko
kofar ya rufe booom saura kada ya bame da
fuskata, ba dan na daka tsalle nayi baya ba,
daya illata ni. Tunda na kalli kofar waje
bansake waiwayr ofishinsa ba, na saka a raina
ni dashi har abada koda kuwa zan mutu banyi
aure ba a duniya dan wannan wulakancin ya
isa. Naji na tsane shi na tsani kaina. Na tsani
ummi da ta saka ni a hanyar halaka kuma na
tsani malamin daya cuce ni ya tagayyara ni. Na
toho da layar daga bakina na farke ta saiga
takadda a ciki babu abinda yake ciki sai zanen
wani hatimi mai gida gida an rubuta alifun,
ba'un, ta'un kawai aciki. Na fusata na yayyaga
kuci kuci na watsar yayin da kuka ya turnuke
ni. DUK KYAN TAKALMI 14 Kawata ummi
wacce na taba baki labari tana son wani
malamin mu a sakandirw abdulyasar shi kuma
baya son ta amma daga baya ya fara sonta har
ya aure ta, ita na tuntuba don ta bani shawara.
Sai tace dani malamai ne suka yi mata aiki,
dole akayi masa yazo ya aure ba a hayyacinsa
ba. Don haka sai ta jani wajen malaminta ya ce
in kawo masa naira dubu ashirn da biyar zaiyi
min asirin da dr shureim zai zo har inda nake
da kansa, ya aure ni. Dogon salati abida ta
dauka ta dafe kirji tace farida boka? Me ya
kaiki bin bokaye akan wannan 'yar karamar
matsalar? Sai na daga ido da sauri na dube ta,
ina mamakin yadda ta ambaci matsalata 'yar
karamar matsala. Nace a raina lallai abida bata
san yadda dr shureim take ba da yadda
halayensa suke ba shiyasa take ambaton haka.
Abida ta dora hannu aka tace innalillahi wa
inna ilaihir rajiun. Aisha farida kinyi kuskure.
Wai shin ina wayon nan naki? Ina dubarunki?
Ina iya zama da jama'ar da kika koya daga
wajen magabatanki? Ai wannan matsalar taki
karama ce. Ke kika zamar da ita babba gashi
kin cuci rayuwarki duniya da lahira. A duniya
kin jawowa kanki bashin da zai kaiki zuwa ga
kotu a daure ki, kin dauko hanyar rugurguza
karatunki. Sannan kin taba lahirarki domin
ibadae ki ta ragu saboda damuwa da kika jefa
kanki, kinje wajen boka mai duba wanda Allah
Ya haramta, duk wanda yaje wajen mai duba,
mai zuba wuri ko mai bugun kasa kuma ya
gasgata abin da ya duba ya fada masa tabbas
bashi da sallah har kwana arbain , Allah ba zai
karba ba. Idan kika mutu a tsakanin wadannan
ranakun me zaki cewa Ubangijinki? Kin zama
makaryaciya domin karairayi iri iri kike
shirgawa wanda ada ba halinki bane kuma
kinsa makomar makaryaci wuta ce. Baki kyauta
min ba farida da baki fada min matsalarki ba
har sai da komai ya cabe. Na girgiza kai nace
na hakura da dr shureim yadda iyayena suka
bar duniya na san na rabu dasu har abada
haka na rabu da shi daman bai san abinda
nake yi ba. Wallahi anty abida ba da ganfan na
dorawa kaina sonsa ba haka na tsinci kaina,
nima ba da son raina ba. Abida tace haba haba
kamar yaya zaki hakura dashi bayan wadannan
bala'I da kika fada a dalilin sonsa ai ba zai tafi
a banza ba. Nayi miki alkwarai da izinin Allah
(SWT) sai kin sami soyayyar dr shureim cikin
ruwan sanyi. Na kasa kunne ina sauraron
maganar abida tamkar tatsuniya. Na dauke ta
a matsayin mai iya zance don hankalina ya
kwanta kawai. Duk da nasan babu abin da ya
gagari Allah, amma abin da kamar wuya wai
gurguwa da auren nesa. Abida ta luta da
tunanin da nake yi a zuciyata ta ga alamar ban
yarda da abubuwan da ta fada min ba. Tace
aisha farida kin manta da yadda akayi na auri
yayanki hussaini? Kin manta ra'ayinsa na son
girma ba zai auri kanwarsa ba a lokacin da
iyayenmu suka yi sha'awar hadamu aure yake
kokarin bijirewa? Kin manta yadda muka fara
zama dashi a gidan nan, ni dake muna
tsoronsa ko muryarsa muakji jikinmu sai ya
dau rawa muna guje guje? Yaya kika ga
zamana dashi a yanzu? Bari in fada miki
abinda baki sani ba farida, yayanki hussaini a
tafin hannuna yake yanzu idan naso in daga shi
sama, idan naki sai in kifa shi kasa ya fado.
Yaya hussaini a halin yanzu baya iya bacci
idan ina fushi dashi sai ya bani hakuri na
hakura sannan hankalinsa yake kwanciya.
Hussaini baya boye min komau na game da
samunsa, baya boye min duk halin da yake ciki
na game da abokan sa zuwa danginsa balle
'yan matan waje domub mazan zamaninan
ba'a rasa su da 'yan matan zamani, ko basu ce
suna sonsu ba su 'yan matan zasu kawo
kansu. Ki tambaye ni ya akayi haka ta faru? Ta
ina na samo kansa? Farida wallahi ban taba
zuwa wajen wani boka ko malami ba nace ina
neman a mallake min hussaini. Mutane suna
mamakina yadda nake tankwasa hussaini yake
yin abinda nake so, har wasu kawayena da
'yanuwana suke tsokana ta wai ina hada su da
malamina wanda ya tankwara min hussaini.
Idan na fada musu ban taba zuwa wajen wani
malami ba a rayuwata sai suki yadda. Aisha
farida bana addua har karshen rayuwata in
taka kafata wajen wani malami ko boka don
yayi min adduar mallaka. Ina daga hannayena
sama in roki Allah Ya mallaka min mijina, mu
zauna lafiya, yasoni kamar yadda nake sonsa.
Na girgiza kai nace na fada cikin kuka anty
abida na hakura da dr shureim saboda bai san
halin da nake ciki ba, mutumin da baya kallon
fuskata baya amsa min gaisuwata, ta yaya zai
soni? Kawayena guda biyu har mota gare su
kyawawa ne, ko khadija bata fini kyau ba.
Maryam ta fini kyau suma dole suka gaji da
wulakancinsa suka hakura dashi. Na rasa
yadda zanyi in daina sonsa duk da adduoin da
nake kwana ina yi don Allah Ya yaye min sonsa
amma sai karuwa yake yi na fada tsaka mai
wuya, hatta da karatuna ya tabarbare saboda
sau biyu supervisor dina yana zuwa yana duba
ni daga makarantar mu bana nan. Don haka na
san in banyi da gaske ba dole sai na maimata
attachment dinnan wata shekarar. Ko a littafi
ban taba karanta labarin wacce ta fada irin
wannan matsananciyar soyayyar da na fada ba,
makauniya kuma gurbatacciyar soyayya don
bai san dani ba balle ya san abinda nake yi ba.
Sai na rushe da kuka. Abida tayi murmushi ta
dafa kafada ta sai ta girgiza ni tace haba
farida, ke macece fa, dama akwai wani da
namiji da zai baki tsoro duk haduwarsa? Ina so
ki yadda da kanki, ki dauka duk in da wata
mace ta je zaki iya zuwa, ki dauka duk abinda
tayi zaki iya yi. Ki manta da farar fatar
baturiyar da yake aure, ke bakar fata sai ki fita
a wajensa. Sai naji abida ta fara bani haushi da
wadannan maganganun nata masu kama da
almara. Na rasa yadda zanyi in fahintar da ita
waye dr shureim. Na tambaye ta cike da
damuwa ta yaya zan samu soyayyarsa, har
nafi baturiya farar fata da yake matukar so? Na
fada miki fa bai sanni ba, yana dai ganina daga
dukkan alamu ma ya tsane ni da zara ya ganni
yake hada rai. Abida ta sake yin dariya tace kin
manta kissar matan nan da akayi mana a
makarantar islamiya? Kin manta matar nan da
take wajen malami ta nemi da ya bata abinda
zata mallake mijinta. Kissar ta rabu gida biyu,
an samu sabanin malamai, sabanin malamai
kuwa rahama ce duk dai abu daya suke
nunawa. Na farko aka ce ta da ta fadawa
malamin cewar maganin mallaka take so ya
bata, sai ya umurce ta data je cikin daji ta
nemo masa gashin idon zakanya mai rai da shi
zai hada mata asirin mallaka. Matar nan ta
firgita da jin wannan babban aiki sai tace dashi
malam ina zanje in samo gashin idon zakanya
mai rai ai bazata bari a tsinka ba saboda
fadanta. Cinye mutane take yi. Malam yace shi
dai gaskiya saida wannan gashin zai iya hada
mata wannan magani. Matar nan ta tashi ta
koma gida zuciyarta cike da zullumin tadda
za'a yi ta iya cirar gashin idon dabbar da tafi
kowacce irin dabba a duniyar nan hatsari. Da
farko sai taje kasuwa ta sayi rago aka fede
mata ta dauki himilin nama ta shiga dawa, tana
hango zakanya da 'ya'yanta daga nesa suka
fita neman abinci sai taje bakin ramin ta ajiye
mata naman nan ta gudu ta labe. Da zakanya
ta dawo sai ta iske abinci lafiyayye a kofar
dakinta ita da 'ya'yanta suka taru suka ci.
Washe gari ma haka matar nan ta kawo
gyararren rago ta ajiye mata bayan ta tafi kiwo
ta sake labewa bayan ta ajiye. Zakanya taje
neman abinci ta dawo ta iske abinci har gida
suka ci ita da 'ya'yanta. Haka matar nan ta
dinga yiwa zakanya sai dai su dan matsa daga
bakin ramin don su dawo su tarar da abinci. Da
zarar sun matsa kuwa matar sai tazo ta ajiye
musu sai su dawo su tarar da abinci kamar
kullum. Zakanya ta tabbatar lallai kawai wata
mai kirki da take kyauatta mata dan haka ko
sanda taga matar ta ajiye mata abinci bata
biyo ta nemi ta lahanta ta ba. Ba sai dai tazo
taci kawai. Har suka fara sabawa tana ajiye
mata abinci a gabanta bata guduwa. Har ta kai
ta kawo matar ta fara shafa jikin zakanyar nan
bata motsawa. Tayi ta shafata don sabo har
ranan matar ta samu ta tsigi gashin idon
zakanya ba tare da zakanyar taji zafi ba. Mata
ta kaiwa malam gashin nan ya karba ya duba
ya tabbatar gashin idon zakanya ne mai rai
don yaga jini jini a jikin gashin. Sai ya cika da
mamaki ya tambayeta ta yaya akayi ta samo
gashin? shine ta bashi labarin yadda tayi.
Malam yace to haka zakije ki yiwa mijinki
kamar yadda kika yiwa wannan zakanya babu
wata mallaka da tafi hanyar nan da kika bi kika
saba da zakanyar nan. Na tambaye ta cike da
damuwa ta yaya zan samu soyayyarsa, har
nafi baturiya farar fata da yake matukar so? Na
fada miki fa bai sanni ba, yana dai ganina daga
dukkan alamu ma ya tsane ni da zara ya ganni
yake hada rai. Abida ta sake yin dariya tace kin
manta kissar matan nan da akayi mana a
makarantar islamiya? Kin manta matar nan da
take wajen malami ta nemi da ya bata abinda
zata mallake mijinta. Kissar ta rabu gida biyu,
an samu sabanin malamai, sabanin malamai
kuwa rahama ce duk dai abu daya suke
nunawa. Na farko aka ce ta da ta fadawa
malamin cewar maganin mallaka take so ya
bata, sai ya umurce ta data je cikin daji ta
nemo masa gashin idon zakanya mai rai da shi
zai hada mata asirin mallaka. Matar nan ta
firgita da jin wannan babban aiki sai tace dashi
malam ina zanje in samo gashin idon zakanya
mai rai ai bazata bari a tsinka ba saboda
fadanta. Cinye mutane take yi. Malam yace shi
dai gaskiya saida wannan gashin zai iya hada
mata wannan magani. Matar nan ta tashi ta
koma gida zuciyarta cike da zullumin tadda
za'a yi ta iya cirar gashin idon dabbar da tafi
kowacce irin dabba a duniyar nan hatsari. Da
farko sai taje kasuwa ta sayi rago aka fede
mata ta dauki himilin nama ta shiga dawa, tana
hango zakanya da 'ya'yanta daga nesa suka
fita neman abinci sai taje bakin ramin ta ajiye
mata naman nan ta gudu ta labe. Da zakanya
ta dawo sai ta iske abinci lafiyayye a kofar
dakinta ita da 'ya'yanta suka taru suka ci.
Washe gari ma haka matar nan ta kawo
gyararren rago ta ajiye mata bayan ta tafi kiwo
ta sake labewa bayan ta ajiye. Zakanya taje
neman abinci ta dawo ta iske abinci har gida
suka ci ita da 'ya'yanta. Haka matar nan ta
dinga yiwa zakanya sai dai su dan matsa daga
bakin ramin don su dawo su tarar da abinci. Da
zarar sun matsa kuwa matar sai tazo ta ajiye
musu sai su dawo su tarar da abinci kamar
kullum. Zakanya ta tabbatar lallai kawai wata
mai kirki da take kyauatta mata dan haka ko
sanda taga matar ta ajiye mata abinci bata
biyo ta nemi ta lahanta ta ba. Ba sai dai tazo
taci kawai. Har suka fara sabawa tana ajiye
mata abinci a gabanta bata guduwa. Har ta kai
ta kawo matar ta fara shafa jikin zakanyar nan
bata motsawa. Tayi ta shafata don sabo har
ranan matar ta samu ta tsigi gashin idon
zakanya ba tare da zakanyar taji zafi ba. Mata
ta kaiwa malam gashin nan ya karba ya duba
ya tabbatar gashin idon zakanya ne mai rai
don yaga jini jini a jikin gashin. Sai ya cika da
mamaki ya tambayeta ta yaya akayi ta samo
gashin? shine ta bashi labarin yadda tayi.
Malam yace to haka zakije ki yiwa mijinki
kamar yadda kika yiwa wannan zakanya babu
wata mallaka da tafi hanyar nan da kika bi kika
saba da zakanyar nan. Don haka babu wani
asiri da ci idan babu biyayya, na kaskan da kai,
ba tsabta, ba kalamai mai taushi tsakanin mata
da miji. Nima nan da kika ganni da wannan
kissar nayi amfani har na sami hussaini tamkar
jaririn da sai an dauka, sai an juya, haka zaki bi
ki samu soyayyar dr shureim. Na dube ta a
shelake nace ta yaya? Ta nisa tace zan fada
miki abubuwa guda biyar idan kika kiyaye zaki
sami shureim a garabasa ba tare da kin wahala
ba, kamar kibtawar ido da bismillah. Fardida
duk inda namiji ya kai da ji da kai, da daga kai
karshensa dai mace zai aura kuma dole ta
bautar dashi ko yaki dan kada ya bare sai yayi
dan Allah Ya wajabta akansu dole suyi. Dole ne
miji ya ciyar da matarsa, dole ne tufatar da ita,
dole ya nemo mata muhalli, dole ya kai ta
asibiti idan bata da lafiya. Idan aka sami marar
tsoron Allah wanda ba zaiyi dan Allah ba to
zaiyi ko dan kada duniya ta zageshi. Dan idan
ya bar ta cikin tsumma, ba abinci za'a nuna ta
agari ace matar wane ce baya kula da ita. Dan
haka DUK KYAN TAKALMI, duk tsadar takalmi,
ba za'a daura shi a wuya ba ko a goshi ba,
dole kafa za'a saka kuma a taka a kwata,
shiga daji, a shiga bandaki, a tako kazanta, a
taka bola ko a tako kaya dashi. To haka dr
shureim zai zama a wajenki da izinin Ubangiji,
babu boka babu malam. Naji tamkar tana busa
mi sarewa a kunnuwana saboda dadadan
bayananta, na gyara zama nace meye abu
biyar din da zan kiyaye....? Ban rufe bakina ba
sai muka ji ana buga mana kofa kamar za a
karya, hayaniyar matan da muke jiyowa daga
nesa ya matso bakin kofar dakin mu. Fadi ake
ke aisha farida, ki fito ko a balle kofar nan.
Yaya zakici kudin mutane ki shiga daki ki buya,
ga 'yan sanda nan an kira su, suna kofar gida
za'a tafi dake. Ko ki bude ko a kirawo su, su
shigo ciki su tafi dake. Na dora hannu aka na
fashe da kuka nace anty abida yaya zanyi? Na
shiga uku , yanzu ankwa 'yan sandan nan zasu
saka min su wuce dani ta gaban mutanen
unguwar nan ko kamar wacce nayi sata kowa
yana ganina ko? Hawaye ya zubo daga
idanuwanta itama, sai ta mike tsaye ta tashe ni
tsaye nima, ta dafa kafaduna da hannayenta
biyu. Tace kiyi ta karanta innalillahi wainna
ilaihir rajiun. Ki fita kice da yan sanda su rufa
miki asiri kamar yadda Allah ya rufa musu asiri,
su taimake ki kada su saka ki a gaba, zaki hau
babur kije can sai su same ki acan ba sai sun
saka ki a gaba ba. Nace ai bazasu yadda ba,
sai sun saka ni a gaba kamar wacce tayi sata.
Tace ke dai kici gaba da addua, ki fada musu
hakan zasu yadda. Idan kinje can ki basu
hakuri kice a baki kwanaki biyu zaki nemo
kudin ki biya su, ni kuma anan zan tilastawa
yayanki dole ko rance ne ya fita ya nemo a
biya su kudinsu kaddara ce ta hau kanki kada
ki damu. Kuma koda wasa kada ki sake ki
fadawa wani ko wata abinda kikayi da kudin
nan, dan kada ma labari ya dawo kunnen
yayanki kenje wajen boka, ki barshi a kawarki
kika taimakawa aka yi mata tiyata mijinta
bashi da hali, yafi sauki dan idan muka
kusukura mu ka bari yaji wannan labari sai ya
bata mana rai. Dazu na siyar da samiruna hudu
na biya su maijidda, dahare da dija dillaliya da
kikaje suma kika ranto kudadensu. Wata tace
dari takwas kika karba mata, wata dari bakwai,
wata dubu daya, suma na suka zo suke daga
min hankali suna nemanki danaji kudin ba yawa
sai na aika kasuwa aka karyar min da su nazo
na bibbiya su. Na uwani ne naji kudin da yawa
ba zan iya biya ba. Kiyi hakuri aisha farida, kiyi
ta istigfari game da wajen bokan da kika je,
kinyi wa Allah laifi kuma kiyi ma Sa alkawari
har ki koma gare shi ba zaki sake zuwa ba.
Kiyi ta karanta wannan adduar ta neman biyan
bashi "Allahumma bi jalika an haramika wa
agnani fadhlika amman siwaka". Sannan ta
bude kofa da sauri muka fito saboda bugun da
ake yi ya tsananta. Dandazon matan gidanmu
da matan unguwa da yaransu sun taru suna
kallona. Abida na rike da hannuna muna kuka
muka nufi hanyar waje. Muryar yaya hussaini
mukaji ya daka tsawa mai firgitarwa har sai da
kowa ya firgita. Yace da matarsa ta sake ni in
tafi ni kadai ta dawo daki inje can in karata ni
kadai. Ni da ita muka fashe da kuka. Ta
rungumeni sannan ta lalubo hannuna ta damka
min kudi naira dari biyu. Ta juya ta bar mi, sai
na cigaba da tafiya a sanyaye na fice yayin da
dandazon mata suke biye dani suna ta cece
kuce. Masu bada hakuri nayi, masu neman
ba'asi nayi, haka masu zuga nayi. Uwani kuwa
sai mayar da zancen take yi. In da Allah Ya
taimake ni duk sanda nazo wucewa ta ofishin
'yan sandar unguwarmu sai na duka na gaishe
su kullum, suna ganina suka gane ni nima na
gane su. Kalmar da suka fara ambato itace ah
kece daman? Ke kuwa yarinyar nan mai hankali
meya jawo kika shiga rigima irin wannan? Na
fashe da kuka nace ku taimake ni dan Allah ina
neman wata alfarma guda daya. Sai mai kivar
cike yace yarinya ai babu wata alfarma da
zamu iya yi miki anan, duk wata alfarma sai
dai ayi ta a ofishinmu. Tunda an riga an kira
mu dole mu tafi dake. Nace daman zanbi ku,
bana so ku saka ni a gaba da ankwa ku wuce
dani ta gaban mutanen unguwa yara suna bina
suna kallo kamar wacce tayi sata. Zan hau
babur ya kain ni sai mu hadu a can. Wallahi ba
zan gudu ba. Sai suka yi dariya suka ce idan
kin gudu ma ai zaki dawo, ba gamu a kofar
gidanku ba. Ko zaki shiga duniya ki bar
iyayenki saboda bashin da bai kai dubu ashirin
ba? Suka yi min izini na tari acaba na hau, duk
da babu nisa daga gidanmu. Na dan dade ina
jiransu sannan suka karaso, aka shiga da mu
uku ofishin mataimakin DPO, 'yan kallo aka
barsu a farfajiyar suka ci gaba da gulmace
gulmacensu. Saii a lokacin na gane makiyana
wadanda ada na dauka masu kaunata ne,
wadanda ada bana kulawa ashe sune masu
kaunata, sune masu jimamin abinda ya same
ni, sune masu nemar min afuwa a wajen
wadanda na yiwa laifi, sune masu fada har da
tayar da jijiyoyin wuya idan aka zage ni. Uwani
ta mayar da zance, haj rabi ma haka sai aka
tambayeni shin abinda suka fada gaskiya ne
kuwa? Na amsa nace haka ne, sannan na basu
hakuri gami da yin alkawari zan biya nan da
kwana biyu. Uwani ta zabura tace karya nakeyi
bani da ko kobo, don haka yace a kulle ni babu
ruwansa. Mataimakin DPO ya sake tambayata
haka aka yi? Na amsa masa da haka ne. Don
haka yace aje a kulle ni har sai yayana yazo
yayi belina kuma yayi alkawarin zai biya
sannan a fito dani, idan kuwa yaki zuwa sai a
kaini kotu alkali ya yanke min hukuncin dauri
daidai laifina.
DUK KYAN TAKALMI 2* 1
katsina amma zama ya kai kakannina garin
shagamu. Anan aka haifi mahaifi har yayi
aure aurensa ya hayayyafa don haka babu
garin da muka fi sani wanda ya wuce
shagamu. Mahaifiyata ma 'yar garin
shagamu ce. Yanzu shekaruna ashirin da
uku a duniya, na fito daga dangi wadanda
suke talakawa liki. Ilahirin dangina kakaf na
wajen uwa dana wajen uba basu da hali.
Koda yake akwai daidaiku masu rufin asiri
amma ba za a kira su masu arziki ba amma
dai sunfi wasu. Wannan dalili yasa bamu
cika karatu mai zurfi ba wasu daga primary
suke tsayawa, wasu sun shiga scondary
amma talauci sai yasa a cire su basa
karasawa. Masu dan gara gara ne ma suke
kammala secondary amma fa jami'a ta
gagaresu sai dai kallo. Danginmu suna da
dimbin yawa mata da maza, yara da manya
gamu da tsofaffi tukuf tukuf Allah Ya ara
musu tsawon rai. Mahaifina yana daya daga
cikin dattijan domin ya tsufa jagof, tun tashi
na daman a tsohonsa na ganshi har ya
makance saboda tsufa. Shine babba a cikin
'yan gidansu don haka yafi kannensa tsufa
kuma yafi sauran 'yan uwansa talauci
kasancewar yafi su tara mata har guda hudu
da tulin 'ya'ya har guda arba'in da uku.
Nice 'ya ta arba'in da biyu a wajensa,
kanwata guda daya kacal mai suna
munauwara. Mu biyu ne kadai muke uwa
daya uba daya a gidan domin mahifiyarmu
ce amaryarsa, ya aure ta tana kankanuwa
yayin da yake tsohonsa. Sauran matansa
ma duka sun tsufa wasu daga cikin manyan
'ya'yansa sun girme ta suma har sun aurar
da 'ya'yansu suna da jikoki wadanda suka
fini ma. Don haka ban mori dadin uba ba,
sanda na fara wayo baya ganina kasancewar
ya makance.
Aikina shine kullum inzo dakinsa in riko
hannunsa in fito dashi kofar gida sai in
zaunar dashi akan kujerar katakonsa sannan
ni kuma in zauna a gefensa ina sauraron
hirar da sukeyi shida abokansa,
makwabtansa da 'yanuwansa tsofaffi. Ina
jin dadin sauraron tsofaffi labarai masu
al'ajabi na mutanen da. Ina fahimta sosai
kuma ina rikewa a kwakwalwata tas, babu
abinda nake mantawa harma idan suka fadi
wata kalma da ban sani ba sai in tambayesu
su bani amsa. Idan babana ya aike ni dauko
ruwa, fura ,koko ko kuma kurtun tofin
yawunsa a dakinsa sai inji duk raina ya baci
saboda za'a tsallake wani shashi daga cikin
hirar. Sai in zura da gudu don inyi sauri in
dawo kada a wuceni, idan na dawo kuwa na
sa su dole su dawo da labarin baya. Anan
na koyi iya magana mai ma'ana da jan
hankalin mai saurarona da kuma fitar da
lafazai masu girma da hikima tamkar wata
babba. Daga nan na samo suna "Farida
tsiri" inji kawayena haka suke kira na domin
duk wanda na zauna dashi zaiyi tunanin
wayona yayi yawa zan cuce sho ko zanyi
masa dubara ko in yaudare shi. Duk sanda
zanji labarin anyi gulmata bai wuce ace na
cika iyayi ba da dadin zance rai-rai-rai
kamar aku. Ko kuma ace na cika kissa da
kisisina bana fushi ko ma za'ayi min, ga tsiri
ina magana kamar wata tsohuwa wacce
taga jiya taga yau. Ina jin dadin halayena
kuma dashi nake cin ribar zaman duniya.
Zan iya zama da kowanne irin mutum ne
komai bakin halinsa da muguwar zuciyarsa,
duk sharrinsa ko alkhairinsa haka kuma duk
in da ya kai ga masifa da zafin rai zamu
zauna lafiya. Da kowacce irin kabira zan iya
zama lafiya. Da bakar fata da inyamuri,
hausa, babarbare, bafillatani, bayarabe,
ibira ne, tangale ne, mumuye ne, margi ne,
basayi ne, ba'are ne, dan niger ne ko kuwa
adon dawo ne dan bur sudan duk na san
yadda zan tafiyar dasu.
Mahaifina yana da yawan magana ba zai iya
zama shi kadai ba, ba tare da bakinsa yana
motsi ba, sai na gado sho don haka tamu
tazo daya sai mu hadu muyi tayi. Har baya
so in matsa daga gabansa don haka ban
cika zuwa makaranta ba, ko yayyena zasu
korani sai in ruga da gudu dakinsa in labe a
bayansa. Sai yace musu "inga mara kunyar
da zai shigo ya banbare aisha daga bayan,
baza taje makarantar ba nan dakin ma
makaranta ce". Aji ne mai zaman kansa don
darasi take duka na iya rayuwar zaman
duniya. Ku fada min ko a jami'a wanne
darasi ne za'a zaunar da dalibi a karanto
masa rayuwa karara balle dan primary aji
daya? To ku kyale ta ba in da zata je sai ta
ga dama sannan zata je makarantar. Dalilin
zuwanta makaranta don ta koyi rubutu ne
kawai. Idan sukaji yana fada basa karasowa
cikin dakin, su gama labe-labensu ina hango
inuwarsu ta jikin asabari sai inki fita, sai sun
gaji da jirana sannan su tafi. Idan hantsi
yayi sai inje zaure in kinkimo kujerar katako
in kai masa kofar gida, sannan in share
wajen in shimfida tabarmi a kasa wasu
tabarmin in shimfida akan wasu dakali biyu
da suke kofar gida. Sannan in dawo dakinsa
in mika masa sandarsa na riko hannunsa in
fito dashi kofar gida wajen kujerarsa, sai ya
laluba ya zauna sannan in koma gefensa in
zauna sai ya fara bani labari ko tatsuniyoyi.
Sannu a hankali sai 'yan majalisarsa su fara
bulbulowa daga gabas wasu daga yamma
wasu daga barin kudu, wasu daga arewa.
Yawancinsu kannensa ne uwa daya uba
daya, ko uba daya. Wasu kuma kakanni
suka hada, wasu makwabtaka ce ta hada ko
auratayya, wasu kuwa manyan abokansa ne
da akayi kuruciya tare. Babu wanda yake da
kasa da shekaru sittin a wajen. Anan na
samu tarbiyar girmama babba duk
kankantarsa, domin idan na gaishe su daga
tsaye ko daga zaune ba zaus amsa ba ko
kuma inji duka dal a bayana wai nayi rashin
da'a. Sai kaji sun daka mintsawa suce inzo
in durkusa har kasa sannan in gaishe su.
Tun ina jin haushin inyi kuka har na daina,
tun ina mantawa har na saba. Sannan na
koyi durkusawa har kasa idan zan mikawa
babba abu koda kuwa da kadan ya girme ni
kuma da hannu biyu. Sun hana ni mikawa
sa'ana ko yaron dana girma abu a
wulakance ko da hannun hagu. Sun
gargadeni ni da na guji wulakanta dan adam
ko da kuwa almajiri ne domin babu kyau
wulakanci da girman kai.
Anan nakoyi daubarun cin jarabawa a
makarantar boko ko kuma saurin haddace
kur'ani a makarantar allao. Sunce in zamana
mai yawan kallon bakin malamina ina
sauraro, ina ganin yadda yake fitar da
lafazinsa daga hanka, ganda, tantanin
makwallato da kuma dumbarun bakinsa. Yin
haka zai sa in dinga fitar da kalma yadda
ake bukata a fada. Kada in dinga zama a
bayan aji, ko da yaushe kujerata ta zamana
a gaban malam saboda gudun yin wasa da
yara. In zama mai yawan tambayar duk
abin da ban gane ba anan take ba sai an
wuce wajen ba. Sannan in dinga kwafar
rubutu daidai in da ban gane ba ko ban
gani ba in tambayi malam ko wani na kusa
dani wanda nasan yasan abin da yake yi.
Kada in sake in koma gida in yarda jakata
ko allona ba tare da nayi bita ba. Sunce da
zarar naci abinci na huta in samu lungu in
shiga inyi ta tilawa zanji na fahimci abin da
ban gane ba a a aji watakila saboda yunwa
ko gajiya ta hana in gane a lokacin. Suka
shawarce in yawaita yin aikin gidan
(homework) tare da yayyena wadanda suke
ajin gaba dani, kada in sake in dinga yi ni
kadai ba tare da wani ya duba min ba. Duk
abinn nan dana fada min na haddace sai dai
anan nake zubarwa saboda bana kaunar
zuwa makaranta, har gara ma makarantar
allo dan itama a kofar gidanmu take dole
inje.
Idan rana ta bude sai majalisa ta yoye, ni
kuma sai kama hannun tsohona in shiga
dashi daki sannan inje in karbo masa
abincin rana daga wajen matar da take da
girki. Tuwo ne dai na masara ko na dawa,
miyar kuka ce ko danyen karkashi. Shinkafa
sai jifa jifa ake siyowa a dafa ko kuma idan
an samu wani dan albarka cikin yayyena ko
sirkiai su kawo mana a dafe ko danye. Da
yamma sai in sake zuwa inyi shimfida in fito
dashi, 'yan majalisarmu basa tashi basa
manta lokacin sai kagansu daya bayan daya
suna bulbulowa. Duk wannan zance da
nake yi muku ina da shekara hudu ne zuwa
tara, ban cika shekara goma ba a duniya
Allah Ya karbi ran mahaifina. Mahaifina ya
rasu a ranar wata juma'a da safe. Bazan
taba manta wannan ranar ba saboda itace
ranar dana taba makara ban tashi da karfe
bakwai na safe banje wajensa ba, domin
kullum karfe bakwai a dakinsa take min.
Wannan kuwa ya faru ne a sanadiyar wata
kasala da wani yanayi da jikina yake min ba
dadi. Ni ba mai barci ba, haka ni ba ido
biyu ba. Tamkar wani abu mai nauyi aka
saka aka dirirritseni na kasa juyi. Sai dai
kuma idona a rufe ba kamar mai tunani
kamar mai mafarki domin abinda nake
nanatwa hirar da mukayi da mahaifina ce a
daren jiya kafin inzo in kwanta. Daga ni sai
shi bayan 'yan majalissa sun watse muna
labari kamar yadda muka saba. Ya laluba ya
dafa kaina yace aisha ki zama mai rikon
amana a rayuwarki yin haka zai ja miki farin
jini a wajen al'umma. Ki kiyayi munafunci,
ma'ana gulma shine yi da mutum yin haka
zai zubar miki da kima. Ki guji sata duk
rintsi kada ki taba abin wani yin haka zai
zubar miki da mutunci ke da zuri'arki gaba
daya za'a dinga yi muku gori. Ki guji yin
zina, laifi ne a wajen Allah kuma rashin
mutunci zai dasu a idon jama'a zaki zama
abar zagi, kowa ya fada miki magana, sai ki
zama ballagaza ko yaro karami ba zai
girmamaki ba. Ki kiyayi kwadayin abin wani,
ki nema naki na kanki duk kankantarsa ki
hakura kiyi amfani dashi shine zaman
lafiyarki da farin cikin rayuwarki. Kada ki
raina baiwar da Allah ya baki, kada ki dinga
ganini wadanda suka fiki. Kada zuciyarki ta
mutu kice ba zaki shiga ku fafata ba, ki
zama mai karfin zuciya da kudiri na alkhairi
kada zuciyarki ta dinga karaya. Sannan ki
zama mai godiya ga Allah a duk halin da
kika tsinci kanki na dadi ko wuya. Ki zama
mai yawan kyauta ko abinda kika mallaka
kalilan ne kada ki makale hannu kice baki
dashi, sai ranar da kika samu da yawa zaki
dinga bayarwa. Ki nemi ilimi mai yawa, na
muhammadiyya dana zamani komai wuya
domin kada a barki a baya a rayuwar duniya
da lahira. Allah Yace mu nemi ilimi a duk
inda yake domin sai munsan shi zamu
bauta masa. Allah baya karbar ibadar jahili,
har baccin mai ilimai yafi jahilin da zai
kwana yana sallah.
Sai naji mahaifiyata tana girgiza ni tana ta
ambaton sunana, idan na bude ido na dube
ta sai in koma in kwanta har sai da ta daga
ni zaune. Tace dani wanne irin bacci ne
haka har tara da rabi tayi baki je kin kaiwa
babnki koko ba, bayan kinsan baya jin dadin
jikinsa? Cikin magagin bacci nace mata yau
baba ya fita kofar gida da kansa, yayi shara
yayi shimfida da kansa. Sai ta harareni tace
karyar banza, a mafarki ko a ido biyu?
Yaushe kika ganshi ke da na tashe ki
dakyar? Sai na tuna ashe mafarki ne don
haka na mike a firgice ko sallah banyi ba na
fita kofar gida na hau shara, na fitar da
kujerarsa da tabarmi kamar kullum. Sannan
nazo na dauki koko a kwanon sha da
kudaya na duma na nufi dakin tsohona.
Wata irin al'ada ce matan gidanmu sukeyi
wai mata mai girki bata shiga dakin miji
saboda kada ayi gulmarta ace ta cika jaraba,
tsohon Allah sai anje an nanike maka,
makahon da yake ta kansa yau da lafiya
gobe babu. Kina shiga dakinsa za'a fara
lekowa ta lungu lungu ana kus kus, kina
fitowa kuwa zaki hadu da harara , zumde,
yafice da habaice habaice. Tsakanin shi
dasu gaisuwa daga bakin kofa ya fadi abinda
zai fada ki juya idan kin zuba masa abincin
ki aiki 'ya'yanki ko jikokinki su mika masa.
Daga baya ma da aka ga nice karama mai
shiga wajensa kullum sai aka dora min
alhakin kai masa abinci kullum, duk wacce
ta gama sai ta kwalla min kira inzo in kai
masa abinci.
Na shiga dakinsa sai na iske shi a lullube
kamar mai bacci, sai na zata lambo yayi ko
fushi yake yi dani dan banzo da wuri ba. Nayi
ta sallama shiru, sai nazo dai dai kunnensa na
durkusa na gaishe shi bai amsa ba, sai na
shiga yi masa bayanin abinda ya tsayar dani,
shimfida nayi har su malam shehu sun fara
zuwa. Sai naji yayi shiru bai motsa ba, sai
kawai na bude lullubin sai ga idanuwansa a
kakkafe yana kallon sama kamar mai
murmushi. Nace lallai baba kana jina ashe kayi
kasake kana kallon sama kana murmushi. Sai
bai bani amsa ba! Ni kuma sai naji raina ya
baci, sai nayi fushi na tashi na fita bakin kofar
dakin na zauna ina kumbure kumbure. Matan
gidan suka fara yimin tsiya suna cewa ke kuma
me akayi miki? Ke da baban naki ne kuma yau
ake jin kanku "yar lelensa wacce baya bari a
taba ki. Sai nace dasu yana ji ina tayi masa
magana yaki kulani, idonsa biyu yaki yi min
magana idanuwansa suna kalllon sama kamar
yana murmushi. Sai jikinsu ya fara basu tabbas
akwai wata matsala domin suma sun leka suna
gaishe shi bai amsa ba duk da dai anji motsin
alwalarsa da asuba amma baya baccin safe.
Sai matansa suka kutsa cikin dakin da sauri
kuma a gigice. Kururuwa da lafazansu ne ya
gigita ni, har yau ban kara jin mummunar
kalma a kunnena irin ta ranar ba. Suka ce
wayyo malam babu, malam ya mutu, munga ta
kanmu, ihu mun shiga uku, rumfa ta gaji da
shirgin kaya ta rushe. Ire iren kalaman da suke
fada kenan suna rusa kuka kururuwa. Sai naji
zuciyata ta hau dukan uku, na dafe kirjina na
fada a bayyane nace Innalillahi wainnailaihi
rajiun. Allah Ya jikanka baba, Allah ya sa
aljannah ce makomar ka. Allah da Ya karbi
abunSa dan yafi mu sonsa, daga gareka muka
zo kuma gare Shi zamu koma. Da ka tafi ba
kayi gaggawa ba haka mu da muka rage ba
muyi nawa ba. Sai manyan maza da mata suka
jeru a kaina suna kallona babu wanda ya kara
magana balle ihu. Mamaki marar iyaka zaka
dinga hangowa daga cikin idanuwansu. Ina
salati ina hawaye cikin natsuwa ba tare da
kwarmato ba. Sai yaya hussaini ya fashe da
kuka yace farida lallai baba ya shigar dake
makaranta, ya saka ki a aji ya koyar dake
darussan dako a jami'a ba za koya miki ba.
Baba yayi gaskiya da yake hana ki tafiya daga
wajensa har sai da kika koya ilimi wanda zai
isheki zaman duniya da lahira. Ya juya ya duba
iyayensa da 'yan uwansa yace wannan abinda
farida ta fada ya zama darasi a wajenku,
wa'azi ne, nasiha ce zuwa gare mu. Ihu da
kwarmato da dora hannu aka kuna fadin mun
shiga uku, ina zamu saka kanmu? Gatanmu ya
fadi. Dawa zamu zauna a duniya? Rumfa ta
gaji da shigi ta rushe. Dukka sabo ne, bata ne,
jahilci ne, azaba kuke karawa mamaci. Tabbas
idan ka saba da abu ranar da zaka rabu dashi
akwai ciwo, kuka wajibi idan akayi mutuwa
amma ba'a son ihu da kururuwa. Kamata yayi
ayai ta karanta innalillahi wainna ilaihi rajiun
sannan ayiwa mamaci fatan samun aljannan.
Ku dubi karamar yarinya nan farida itace kusan
wacce tafi kowa kankanta a cikin gidan nan
amma ita kadai ce tayi abinda ya dace , itace
wacce tafi mu shakuwa dashi, tafi mu sonsa,
kuma itace tafi mu nuna masa kaunar da take
yi masa shine data yi masa addua. Muyi koyi
da ita don tafi mu ilimi, tafi mu sanin ya
kamata. Sai suka daina ihu suka koma suna
ambaton sunan Allah. Yaya hussaini ya tashe
ni tsaye yasa gefen rigarsa ya goge min
hawaye. Yace ki daina kuka 'yar karamar
kanwata, kowa yasan ke aka yiwa mutuwar
nan sai kuma kika fi kowa yin tawakkali haka
Allah yake so. Ina mai yi miki albishir Allah ba
zai bari ki wahala ba, da izininsa ba zakiyi
kaskantaccen maraici a rayuwarki ba, duk da
kin rasa mahaifinki a lokacin da kike da
karancin shekaru saboda baki mance da
Ubangijinki ba wanda shine gatan ki. Allah
Yana tare da duk wanda yasan da Shi kuma
wanda yake neman taimakonsa. Farida nayi
miki alkawari zan dauki nauyinki, zan rike ki
amana har izuwa ranar da zan aurar dake
saboda wannan tawakkalin da kika nuna, zan
rike ki tamkar 'yar dana haifa ta cikin. Wacce
hakkin cinta, shanta, suturarta, tarbiyyarta,
iliminta da suka wajaba a kaina har zuwa ranar
da zan aurar da ita sannan nauyinta ta koma
hannun mijinta. Ki shiga ciki wajen baba kiyi
masa sallama, kiyi masa irin adduar da kika yi
masa yanzu ta neman gafara da rahamar
Ubangiji. Mutuwa ce kadai ta raba kaunar dake
tsakaninku. Na juya da sauri na shiga wajen
tsohona, durkusa a gabansa setin kunnensa na
tofa masa kulhuwallahu ahad uku, sannan nayi
masa adduar samun aljanna da neman hasken
kabari. Nayi masa fatan Allah ya sa ya tashi a
cikin gafartattun bayi a cikin alummar manzon
Allah (SAW). Sannan mahifiyata ta jawo
hannuna muka fito waje, cikin kuka mai tsanani
tace dani farida na yafe miki duk abin da kika
yi min. Allah yayi miki albarka a rayuwarki ta
duniya da lahira. Alhamdulillahi nayi dace da
'ya ta gari, mai jin kan iyayenta. Ina fatan nima
zakiyi min irin wannan adduar idan na riga ki
tafiya. Muna zazzaune a tsakar gida maza
suka shiga sukayi masa wanka, suka hada shi
suka fita da shi akayi masa sallah. Aka dauke
shi aka tafi dashi gidansa na karshe, gidan da
ba'a fitowa unguwa, gidan da ba'a leke, gidan
da ba'a jiyo motsinka balle a gaishe ka ka
amsa wato kabarinsa. Bakina bai gushe da
karanta masa kulhuwallahu ba da inna
a'adaina kalkausar har karshe. Shi ya bani
adduar yace ita ake so a dinga karantawa
mamaci. Da akayi sadakar bakwai sannan aka
watse, lokacin mutuwa ta dawo min sabuwa fil,
idan aka tashe mu daga bacci za'a tura mu tafi
makarnatar boko sai in nufi dakinsa zan buya
sai in ga a rufe sannan in tuna ashe ya rasu,
dole a tura keyata zuwa makaranta raina baya
so, da yamma ma sai a tura ni makarantar
allo. Ina tuna nasihohin da tsohona da
abokansa sukayi min na dabarun samun
nasarar karatu, sai nake bin duk yadda suka
umurce ni sai naga ina ganewa kuma ina cin
jarabawa don haka saina fara jin dadin
makarantun da nake zuwa, na dawo ina zuwa
makaranta da kaina ba sai an tura ni dole ba.
Ranar asabar da lahadi muna zuwa makarantar
allo da safe da yamma amma ranar alhamis da
juma"a da yamma ba ma zuwa koina don babu
makarantar allo, sai na fitar da kujeran babana
in shimfida tabarmi kamar yadda na saba. Sai
inga tsofaffin nan suna zuwa daya bayan daya
suna zuwa suka taru kamar yadda suka saba
da, don har sun daina taruwa tun bayan da ya
mutu. Baba ahmadu ne ya maye kujerar
babana shine babba ina gefensa koda yaushe,
duk sanda suka kalle ni sai inga suna hawaye
suna tausayina da alama suna tunawa da
yayansu, abokinsu, amininsu, makwabcinsu,
abin kaunarsu. Zaman majalisar yakoma ranar
alhamis da juma'a ne kawai da yamma. Kuma
munci gaba da hirarrakin mu kamar yadda
muka saba. Bayan rasuwar mahaifinmu da
shekara guda yaya hussaini yayi aure, ya auri
'yar kanin babanmu mai suna abida dai dai
lokacin daya sami dan karamin aiki a union
bank, da certificate dinsa na secondary a
matsayin masinja a branch na kano dan haka
kano ya kauro damu. Da zamu tafi mahifiyata
ta hada min kayana kakaf tana kuka ina kuka,
kanwata munauwara ma tana kuka, 'yan gidan
kacokan suka fito suna mana fatan Allah Ya
kiyaye hanya da fatan Allah Ya bamu zaman
lafiya, Ya hada mu da abokan arziki a can.
Muka tare masu babura biyu muka hau da
jakunkunan kayanmu muka nufi tasha, muka
hau doguwar mota mai zuwa kano. Kano ta
dabo tumbin giwa, mai mata da motoci ko da
me kazo an fika. Rabona da shagamu kenan
har yau ban sake komawa da sunan zama ba
sai dai inje da sunan ziyara. A wata unguwa a
cikin kano mai suna sharifai zauran tudu, yaya
hussaini daman ya kama mana haya tun kafin
muzo, a gida mai dakuna bakwai muka kama
dakuna biyu. Don haka mutane ne da yawa a
cikin gidan, bandakin daya ne kacal, kicin daya
da tsakar gida daya ake amfani dasu mata da
maza, yara da manya. Abunka da gidan yawa,
kazanta ba'a magana. Gashi daman gidan ya
tsufa ya farfashe ba gyara sai warin bola da
kwata kowa kyashi ya hana shi gyarawa. Idan
ka share cikin dakinka da kofar dakinka ka
gama shara babu wanda zai share tsakar gidan
da zaure balle kofar gidan. Ga gida a lungu ko
mota bata shiga lokon, ga wata tafkekikyar
kwalbati da ta cinye fadin lungun, kowa a
tattakure babu sakewa, yara basa iya wasan
guje guje su more sboda matsi. Haka kowacce
mace ta baza kayan san'arta a cikin gida, cikin
zaure ko kofar gida saboda sai an taimakawa
mazan rayuwar zata tafi dai dai. Daman mazan
da yawansu buga buga sukeyi, wani sai ya
dawo gida babu abinda ya samo, da dan kudin
sana'ar natar za'a yi cefane kuma ta bawa
yaranta kudin makaranta. A gidan ma har gara
yaya hussaini tunda yana daukar albashi duk
tsiya dai karshen wata zai samu duk da dai dan
albashin bashi da yawa kuma rabin kudin a
acaba yake tafiya, kafin wata ya kare sai anci
bashi dole kafin a biya an jigata. Duk da haka
dai munfi sauran, muna dan cancanawa dai
muna rayuwa. Ni da abida muka fara sana'a,
muna soya wainar fulawa a kofar dakinmu,
kuma ana saya ba laifi duk da cinikin naira
biyar biyar ne, duk da haka muna samun na
sayan maggi, gishiri, a ciki ake bani kudin
makaranta da kudin dinkin tsummokaran mu
idan sun yayyage. A makarantar bokon cikin
unguwa aka saka ni, kamar sauran yaran
unguwar haka aka saka ni a makarantar allo da
yamma ta islamiya da daddare. Bana fashin
zuwa makarantar kullum saboda ina tsoron
yaya hussaini sosai, baya yi min wasa koda
yake matarsa ma baya sakar mata fuska ,
mutum ne mai zafin zuciya. Lallaba shi muke
kamar kwai. A daki daya nake zaune babu
komai a ciki daga 'yar karamar katifa sai 'yar
jakar kayana ta buhu a gefe ko ledar daki ba'a
shimfida ba sai tsurar ragargajejjen siminti da
wani yagulallan labule. Dakin su abida da
mijinta ne mai labule mai kauri, an shimfida
leda a kasan da katuwar katifa sai akwatin
kayansu a gefe. Kayan kitchen da danyan
abinci suna dakina wasu a dakinsu. Haka muke
rayuwa amma muna farin ciki saboda mun
sami ci gaba fiye da a garinmu tunda daman
can a cikin talauci aka haife mu. Bayan
kaurowar mu da shekara daya mahaifiyata ta
tara kudin motarta da guzurinta tazo ganina
sabida tun kaurowarmu bamu je shagamu ba,
saboda matsalar tattalin arziki sai ita tazo dan
taga yadda muke rayuwa don koda yaushe
magana ta takeyi don tana sona sosai har fiye
da 'yar autarta. Nayi murna matuka da ganinta
har ita ta fini murna, yaya hussaini da matarsa
ma sunyi murna da ganinta kuma sunji dadin
tsarabar da ta kawo mana. Ni da abida atamfa
dai dai ta kawo mana, yaya hussaini ta kawo
masa yadi, sannan ta kawo mana doya,
dankali, ayaba da lemo jifgi guda. Allah cikin
ikonsa cikin daren data zo muna kwance da ita
a dakina ciwon ciki ya turnuke ta kafin in
bugawa yaya kofa ya fito don a kai ta asibiti
rai yayi halinsa. Ummata ta mutu a gabana ina
kallonta ban isa in hana ta tafiya ba, Ubangiji
ya nemi kayanSa. Sai na tuna wasiyyat da ta
bar min cewar idan ta riga ni mutuwa inyi mata
addua kamar yadda na yiwa mahaifina. Nayi
mata addua sosai kuma ban manta ambaton
innalillahi wa'innalialhir rajiun ba har gari ya
waye. Sai dai nayi kuka mai yawa saboda na
kara wayo na san zafin mutuwar sosai ba
kamar da ba, na tausayawa kaina sai nafi
tausayin kanwata munauwara. Gata karama ita
kadai ta rage babu uwa, babu uba, babu ni 'yar
uwarta. Nasan a gidanmu 'yan ubanci akeyi
kowa yana tattalin 'yan dakinsu, nasan sai dai
dangin mahaifiyta ne zasu dauke ta suma
kuma duka kanwar ja ce, talauci ne tsagoronsa.
Rashin kudin motar da za'a kai gawarta
shagamu shi ya hana yaya ya kai ta can a
binne sai kawai ya buga waya ya sanar dasu
wannan mummunan labari. Sun kuwa gigice da
jin haka sai suka yanke shawara gara wasu su
taho kanon ayi jana'iza a binne ta anan. Allah
Ya rubuto anan kasarta take. Da suka iso sai
akayi mata sallah aka binne ta. Kafin kwana
bakwai wasu daga cikin danginmu sai da suka
zo kano sukayi gaisuwa sannan suka koma,
wasu da yawa basu sami damar zuwa ba, da
yake a can ma ana zaman makokin don ba
kowa yake da kudin zuwa ba. Da akayi albashi
ni da yaya hussaini da matarsa mukaje
shagamu don yin gaisuwa da kuma zancen
abinda ta bari. Baiwar Allah bata da komai
daman mijinta bai bar mata komai ba, dan
matan basu samu gida ba! Basu samu gona
ba. Ko mu 'ya'yan kudi kadan aka bamu da
akayiwa gidan da gona kudi wani yayanmu ne
ya saya dan ba zai rabu ba. Daga ragargajejjen
gadonta sai tsumokaren kayanta aka ajiye
mana shine gadonmu. Na kasance marainiya
babu uwa ba uba, sai ni sai halina sai kuma
yayana hussaini da matarsa sai Allah. Kuma
ina godiya ga Allah a kowanne lokaci don ban
mantawa da nasihohin da mahaifina yayi min
ta karshe. Allah yana ganina, kuma Yana
taimakona, Bai bari na tagayyara ba. Babbar
baiwar da Allah ya min itace daya bani jama'a,
masu sona suna da yawa a duniya, mata da
maza. Yara da manya kowa yana yabon
halayyata koda kuwa an kushe ni sai kaji ana
yabona. Na godewa Allah Shine gatana shine
majibancin al'amurana. Aisha farida ta rushe
da kuka hade da hawaye mai radadin fita.
Hawaye ne yake ta kwaranya tamkar an bude
ruwa a famfo. Barrister Mu'azzam ya juya ya
dubi abokinsa barrister nuruddeen shima ya
kalle shi sannan suka juya su dukka suka sake
duban aisha farida, suka cigaba da mamakin
wannan yarinya mai surutu da zazzakar murya,
ga iya magana tana fitar da kalamai dalla dalla
a jejjere tamkar wacce wani ya labe yake rada
mata. Wannan itace fadi ba'a tambaye ki ba,
amma fa sunji dadin sauraron labarinta, yayi
ma'ana kuma sun karu da abubuwa da yawa
na game da zamantakewar rayuwa. Sannan sun
tausaya mata, ta cancanci a tausaya mata
domin rayuwarta tana cike da abubuwan ban
tausayi. Daga ganin ta a kidme take a dimauce
ta fado musu ta gaishe su, kafin su amsa ta
sami kujera ta zauna ta hau basu labari. Yau
ne rana ta farko da suka fara ganinta a
rayuwarsu itama haka, farida batasan wacce
irin damuwa bace ta hana su zama a gidajensu
suka fito a cikin daren nan suka zauna a wajen
shakatawa mai suna "fish park" dake
nassarawa GRA. Barrister muazzam ya zaro
dan karamin handkerchief fari kal daga gaban
aljihun rigarsa (suit) ya mika mata ba tare da
yayi magana ba, ta dago da jajayen idanuwanta
tana gogewa wani sabon hawaye fil yana
bulbulowa daga idanuwanta. Barrister
muazzam ya mika hannu a sanyaye kan teburin
dake gabansu ya dauko wani kwalin lemo ya
tsiyaya a cikin kofuna biyun da suke gabansu
ya mika mata, sai ta karba sannan tayi godiya
ta fara kurba a cikin nutsuwa yayin da shima
ya dauki daya kofin ya kwankwadi lemon a
cikin kofin ya mikawa abokinsa shima ya karba
ya fara sha ba tare da wani daga cikinsu yace
uffan ba. Sai aisha farida ta fara tunanin ko
kurame ne bata sani ba tazo ta hau su da
surutu, saboda tun sanda ta zo ta zauna ana
fiye da mintuna talatin babu wanda yayi ko tari
a cikinsu har yanzu sai kallonta kawai sukeyi
da ido. Ta kurbi lemo ta ajiye kofin akan teburi
ta sharce hawaye da hankicin dake hannunta
tayi murmushi. Tace bayin Allah shin baku
magana ne, ko kurame ne?
Kallonta kawai suke yi har yanzu babu wanda
ya tanka mata, su kalleta su juya su kalli
junansu. Sai taji hankalinta ya tashi, tayi ajiyar
zuciya tace yaya sunanku? Barista nuruddeen
ya dubi barr muazzam ya kifta masa ido
alamar kada yayi magana. Suka ci gaba da
sauraronta tana ta magana ita kadai, sai taji ta
zama tamkar wata mahaukaciya wacce bata
san ma abinda take yi ba, taji duk ta tsani
rayuwarta, sai ta tashi a sanyaye ta juya zata
tafi. Barr muazzam yaji tausayinta sai yace
aisha farida meyasa zaki tafi? Ta juyo da sauri
ta dube shi sai ta girgiza kai tace kuyi hakuri
ban san na takura muku ba, na shiga masifa,
na shiga kunci har na dimauce ban san dalilin
da yasa nazo wajenku na dinga zazzago muku
labari baku tambaye ni ba. Na ganku
kammalallu dan haka na zata zaku karbe ni
hannu bibibuy , kuba bani shawara dan ban san
abinda zanyi ba anan gaba. Barr muazzam
yace dawo ki zauna, shirun da mukayi miki don
bamu sanki ba kuma bamu san manufarki ba
kinsan duniya abar tsoro ce bai kamata nan da
nan ka yarda da mutumin da baka taba gani
ba. Kuncin rayuwar kuwa mun fiki shiga shine
ya fito damu nan ko Allah zaisa muji dan
sanyi. Ta dawo ta zauna a sanyaye ya yin da
take tuhumar kanta da laifin rashin hankali,tana
jin haushin kuskuren data tafka daga ganin
mutane bata san su ba kawai ta zo ta zauna ta
hau basu labari,ta fadi sirrinta bayan ba'a
tambaye ta ba,lallai dole suyi mata kallon wata
sakarya. Ta tambayi zuciyarta shin ko cutar
tabin hankali ce ta kama brain din ta domin
sanda ma ta fara magana bata sani ba.
Mu'azzam ne ya ktse tunanin da take yi ya ce
"ni sunana Barr Mu'azzam,abokina kuma Barr.
Nuruddin. Mecece takamaimiyar matsalarki?
Menene dalilin da ya fito da ke daga gidanku
zuwa nan a cikin daren nan? Naga ba tare da
mijinki ku ka zo sayan kifi ba kamar yadda
nake ganin wasu ma'auratan hausawanmu na
yi? Me kika fito nema? Wanne irin taimako kike
nema daga garemu? Kina so mu saya miki kifi
ne ko kuwa kudin mota ki ke nema? Ta yi
murmushi ta ce "gaskiya ne,na cancanci a
tambaye ni domin ban yi kama da mai kamun
kai ba. A rude na shigo nan dan yau ne rana ta
farko dana taba zuwa nan,ban san inda zan
nufa ba sai na hango ku kawai na ji a raina
tamkar naga yayyena,wadanda zasu iya
taimakona shine na taho wajen ku ko Allah zai
sa ku kwace ni daga mugun dan sandan da
yake shirin cutar da rayuwata. Barr nuruddin ya
dubi abokinsa ya tsuke fuska ya ce "kai kada fa
ka yayumo mana ruwan dafa kanmu,ka bar
yarinyar nan ta kama gabanta. Me yasa ka
dawo da ita har ta yi niyyar tafiya? Ka cika
kwashe- kwashe kamar baka san irin yan
matan nan ba ne yan club? Idan ba yar club ba
wacce budurwar kirki ce zata baro gidan
iyayenta ta shigo wajen nan da dare? Ka duba
ka ga nisan unguwarsu tun daga cikin gari
zuwa nan? Zuwa ta yi ta tsara mu ko daya
daga cikinmu zai dauke ta. Ke yarinya ki kama
gabanki mu ba irinki bane,je ki can ki sami yan
uwanki irin ki. Shawarar da zan baki kuma ita
ce ki koma skul ki taimaki lyf din ki don yawan
duniya ba riba sai asara,akamr yadda kika ce
mahaifinki ya yi maki wasiyya kafin ya rasu"
aisha farida tayi dariya maimakon ta ji haishi
sai ta gyada kai tace "gaskiya ne yayana na ji
dadin shwararka kuma zan dauka insha Allah
zanyi amfani da ita. Sai nauyi da kunya ya
kama barrista mu'azzam ya ji kamar ya nutse
a cikn kasa saboda baranbaramar da abokinsa
yake yi,baya kara,ba kunya balle jin nauyi yake
maganarsa,ya harare shi yace haba nuraddin
kai fa mtsalata da kai kwaba mahgana babu
taunawa. Ka bari ka ji uzurinta idan ka gama
jin inda ta nufa sai ka yanke mata hukunci.
Kamar ba lauya ba ai sai ka gama sauraron
labarinta tun daga farko har karshe sannan ka
gama jero mata tambayoyi ta gama amsawa
ka kula da inda ta nufa sannan ka yi mata
nasiha ba fada ba. Yanzu da a kotu muke sai
ka fadi a sharia dan kawai kana jin haushin ka
sai ka huce akan yar mutane,to ba ita ta kar
zomon ba ko rataya ba'a bata ba.
Posted by Bashir Sani Mahmud on 22 Aug 2017
Aisha farida tayi karfin hali tace ba damuwa, ai
laifina ne dan banyi kama da mai kamun kai
ba, tunda ba'a tambaye ni ba nazo na fara yi
muku surutu, nasan ba'a son mace marar
kamun kai. Barr muazzam ya girgiza kai yace
zuwanki nan ba laifi bane dan kin zo kin zauna
a kusa damu, kujeru ne a jejjere kowa zai iya
zuwa ya zauna. Da kika zo kika same mu kinyi
mana sallama duk da tun kafin mu amsa har
kin zauna. Daman kamata yayi ki gabatar
mana da kanki kuma kinyi hakan sai dai kika
zarce da bamu labari shine abinda ya daure
mana kai kenan. Kallon junan da kikaga muna
yi ina tunanin ya sanki ne, shima yana tunanin
ko na sanki ne. Aisha bani labarin takamaiman
abinda ke damunki, muma nan da kika ganmu
matsala ce take addabarmu, ki saki jiki ki fada
mana mu dake sai mu taimaki juna da
shawarwari. Barr nuruddeen ya fusata ya mike
tsaye ya dubi abokinsa yace malam in ka gama
kazo ka same ni a cikin mota mu tafi, dan ba
zan iya zama ina sauraron wannan shirmen
naku ba. Bansan sanda ka zama marar aji ba,
daga haduwa da 'yar tasha sai ka hau hira da
ita kai ma kana baza sirrinka, idan taji
matsalar ka me wannan zatayi maka? Itama
bata san yadda zatayi da kanta ba balle ta
bawa wani shawara. Kada ka sake ka ambaci
sunana a cikin labarinku kai dai ka fadi taka
matsalar. Ya juya a fusace ya tafi bai daina
fada ba yana tafe yana magana yana wurwurga
hannu har ya fice daga cikin gate din. Aisha
farida da barr muazzam suka bishi da kallo har
sai da suka daina hango shi. Ta sunkuyar da
kanta kasa sai hawaye ya fara zubowa daga
idanuwanta. Kada ki yi kuka aisha, ki mayar da
komai ba komai ba. Kece fa kika gama bani
labarin cewa zaki iya zama da kowanne irin
mutum a duniya. Inji brr muazzam. sai tayi
murmushi ta shiga goge hawayenta tace ko
kusa ban damu ba, banji haushi ba. Kawai dai
abokinka yayi min kallon ballagar mace, 'yar
tasha, 'yar club, karuwa kenan. Shine mutum
na farko a rayuwata daya taba jifata da
wadannan munanan sunaye, saboda bai sanni
ba, sai dai ina fatan ya sanni nan gaba. Barr
muazzam yace yi hakuri kanwata, ki cigaba da
bani labarin rayuwarki, ina jin dadin sauraronki.
Haqiqa Aisha farida,labarinki yakai maqura
gurintausayi,nayi kuka sosai,rabena da
irinkukannan yaukimani wata takwas
kenan.tunrasuwar yayata,ayau nafisa mamawa
kinsani cikintausayin ki,maganardanakeyi
yanzuhaka nakasa tsayarda hawayendake
zuba'a idona. kitaimaka kibani lbrin cigabanki
da daukakardakikasamu kozansamisukuni
yau...wallah nafisa natausayamiki sosai. BABI
NA BIYU Da na karasa makarantar primary sai
yaya hussaini ya kaini wata makaranta a wajen
sabongari na zana jarabawar common entrance
ta shiga makarantar federal. Allah cikin ikonsa
sai naci jarabawa aka turani makarantar da na
zaba wato FGC kano. Yayi min sayayya iya
karfinsa ya kaini, ya bibbiya dukka kudaden
makarantar da aka bukata, ya dawo gida ya
barni a can. Nayi kuka saboda rashin sabo,
gashi bansan kowa ba a makarantar amma
daga baya na saba da dalibai 'yan uwana sai
na fara jin dadin rayuwar makarantar. Jama'a
na sona saboda yadda nake da fara'a, ladabi
da son aiki bana kiwa don haka kowa yana son
ya jani a jiki saboda ina da matukar tsafta. Na
yi suna a makarantar nan da nan malamai ma
suka sanni saboda kwazona da wayo, ga iya
magana. Na gama aji uku hutun da zamu shiga
aji hudu aka cireni, abu ya ci tura hidimomu
sun karu, yayana ba zai iya cigaba da yi min
siyayya ba da biyan kudin makaranta ba
kasancewar shima ya hayyayyafa. A jejjere ba
kakkautawa abida take haihuwa, 'ya'yanta na
farko ma 'yan biyu ne maza abubakar da umar,
sai ta haifi mace mas'uda ga wani cikin a
jikinta ko yaye ta goyen bata yi ba. Ga kudin
haya ya karu, cefane ya karu, farashin abinci
ya karu, gashi an kara kudin makaranta ya
kusa ninka na da ma. Daman duk sanda zan
koma makaranta sai ya ciyo bashi kafin ya
harhada ni in tafi. Ya kira ni daki ya zaunar da
ni yayi min bayanin halinda ake ciki, sai ya bani
hakuri cewar zai mayar dani makarantar
gwamnati ta ;yan mata dake shekara. Dole na
koma makarantar shekara naci gaba da karatu,
daga aji 4 na fara, sai na zama zakaran gwajin
dafi nafi kowa kokari saboda dana sami horo a
FGC a wajen yaran kabilun da basa jin hausa
da yaran hausawan da suka sami horon turanci
tun daga primary. Ajin kimiya na shiga (science
class) har Allah ya kaini aji shida aka bani
shugabar dalibai, duk wata gasa ko muhawara
ta turanci tsakaninmu da wasu makarantun ni
nake tsayawa makarantarmu, idan bana nan
babau abinda yake tafi dai dai. Shugabar
makarantar mu tana alfahari dani, kullum tana
kwatance dani saboda kokarina. Da muka
gama makarantar ita da malamai sai da sukayi
takaicin rashina saboda ba'a sami madadina
ba. Bayan gama makarantata da wata uku
yayana ya harhada 'yan kudadensa ya bani
kudin mota da guzuri na zuwa shagamu,
saboda duksanda yake zuwa shi da matarsa da
'ya'yansa ina makaranta ba'a zuwa dani.
Tsofaffin abokan hirata har sun gaji da
tambayata wasu ma sun mutu, haka wasu
daga cikin yayyena sun murmutu duk banje ba.
Ina samun wasikun kanwata munauwara akai
akai duk sanda ta sanda ta sami mai zuwa sai
ta bayar an kawao min, ta shaida min cewar
an cire ta daga makaranta tana secondary aji 3
anyi mata aure saboda rashin kudi. Ni kadai
yaya hussaini ya saka a mota zuwa shagamu,
dana isa garin shagamu a tasha na hau acaba
zuwa gidanmu, ban manta hanya ba. Da yawan
'yan gidanmu basu shaida ni ba sai daga baya
suka gane ni, sunga na girma nayi kyau. Duk
da rashin wadatar da muke ciki a kano sai
naga na fisu kyawun gani, cikakkiyar lafiya da
gogewa. Na zagaya dangi na kusa dana nesa
har sai da naji kafafuwana zasu gutsire saboda
yawansu. Na ziyarci gidan kanwata dake agege
a lagos anan take aure, rayuwarta abin tausayi,
gida ne irin na haya mai dauke da dakuna fiye
da ashirin, yare kala kala kamar hausawa,
yarbawa, igbo, da wasu yaruka daban daban.
Bandaki daya ne kacal, tunda asubahi ake fara
layin shiga bandaki. Mijinta iliyasu shima dan
shagamu ne amma a lagos yake facin taya, ita
kadai ce sana'arsa. 'Ya'yansu biyu a lokacin.
Saboda tausayin halinda na same ta kusan
dukka kayana na sakawa na bata kyauta,
sannan na hada mata mayafai, sarkokina,
takalmana, guda dai dai na rarrage. Duk
kudaden dana samu na bata dukka kudin mota
na komawa ta kano kadai na ware. Muka sha
kuka tare da nazo tafiya, kukan da muke na
tunawa da iyayenmu ne da kuma kukan
rabuwa, don munsan zamu dade kafin mu sake
haduwa. Na dawo kano jakata kwalam babu
komai duk na rabar da kyana kuma da masu
kyan na tafi dasu. Tsummokaran, tsofaffin,
yagaggun kadai na bari a gida. Haka nazo na
dinga karancin kaya duk sun ragargaje dan
haka na daina zuwa taron biki ko gidan
kawayena. Abida tayi ta min fada tace nayi
garaje ai ba'ayin haka tun da nasan ban ajiye
wasu ba a lufge kuma bani da mai dinka min
wasu ai bai kamata in rabar ba. Idan fita ta
kama ni dole sai dai in ari kayan abida in saka
inje, ina dawowa in cire mata. Abinka da
cakudi, zaman saka ido, kowa yana kula da
shige da ficenka. Gulmammaki iri iri bayan
zumde da yafice zaka ga anayi mana, abin ya
kai har su dinga kiran 'ya 'yan abida suna
bugun cikinsu suna tambayarsu wai ina kayana
suka ga ina arar na abida? Irin wannan gutsiri
da tsomar sai da ta wuce kan matan gida ta
koma wajen mazansu, su kuma suka
tseguntawa yayana hussaini, suka ce masa bai
dace in dinga arar kayan abida ina fita kofar
gida ina tsayawa da samari ba, ina yawo da
kawayena a gari. Idan ba an lura ba in a
duhune sai a zaci abida ta fara bin maza.
Sukayi ta zuba masa bayanan da dole
hankalinsa yayi matukar tashi, ransa yayi
mummunan baci. Ya shigo dakina ransa a bace
ya iske ni a kwance yace min in kira abida
itama ta shigo nan dakin yana da magana da
ita. Mukazo muka durkusa a gabansa muna
karkarwa saboda yadda muka ga ransa a bace
gashi mutum ne mai zafin zuciya. Ya umarci
abida ta fada masa gaskiya kada ta kuskura
tayi masa karya akan abinda zai tambayeta,
haka nima ya gargadeni kafin ya yi mana
tambayoyin. Muka yi masa alkawarin zamu
fada gaskiya, ba zamuti karya ba. Cike da
fargaba mai tsanani muke sauraron abinda zai
fada mana. Ya cewa abida da gaske ne aisha
farida tana aron kayanki ta saka ta fita yawo a
gari? Sai abida ta dafe kirji tace Innalillahi
wainna ilaihir rajiun! Ya daka mata tsawa mai
firgitarwa yace baki bani amsa ba. Nan da nan
ta fara hawaye, jikinta na karkarwa tace eh
haka ne. Sai ya kai mata mari har sai da ta
fadi kasa, ya fada cikin fushi yace to ta hada
kayanta ta tafi gidansu. Na rushe da kuka na
dinga rokarsa ya yafe mata ba laifinta bane
nice na tambaye ta. Nima din ya yafe min na
daina daga yau. Sai ya rufe ni da duka yana
duma, yana tattaka ni da kafa tamkar zai kashe
ni. Munafukan matan gidan ne suka zo suka
kwace ni dakyar, ransa yayi matukar baci sai
fada yake yana zaginmu wai sai mun harhada
kayanmu mun bar masa gidansa. Ana bashi
hakuri tamkar zuga shi akeyi dakyar ya haukra
ya kyale mu amma tun daga lokacin baya raga
mana, komai mukayi sai ya hantare mu, sai
harara koda yaushe. Sai na daina fita koina ,
koda yaushe ina fama da dinkin yaga da zare
da allura. Abida ta iske mijinta a dakinsu ta
ajiye masa abinci sannan ta durkusa ta gaishe
shi. Ya amsa dakyar cikim fushi, bata damu ba
ta zauna a kusa dashi ta dauko muhuci ta fara
yi masa firfita. Sai yayi mata tsawa yace ta
bari baya so, ta tashi ta fita ta bashi waje.
Cikin lallausar murya tana zubar da hawaye
tace ka yafe mana laifukan da muka maka,
munyi kuskure, fushin da kake yi damu ya
hanamu sukuni, bama jin dadin rayuwarmu,
rayuwa tayi mana kunci. Dan ban fada maka
bane halin da ake ciki kada ranka ya baci, ashe
dana fada maka ma zaifi sauki. Aisha farida ce
ta rabar da kayan sakwarta kakaf a shagamu
saboda tausaya musu da tayi, ta gansu cikin
tsumma, shine ta dawo bata da kaya sai
yagaggu. Dan haka bata iya fita wajen
kawayenta shine nake bata aron kayana ta
saka tana dawowa take cirewa, bansan abinda
'yan gulma suka fada maka ba har ya jawo
ranka ya baci ka dauki mataki cikin fushi. Sai
yayi shiru yana sauraronta can yace ai duk
laifinki ne, meyasa ba zaki fada min halin da
ake ciki a cikin gidana ba har sai da wasu suka
fada min a waje? Kinsan irin zaman da mukeyi
da 'yan gidannan, zaman saka ido ne, duk
shige da ficen mu akan idonsu. Ashe gaba daya
lungunnan gulmar ku ake yi shiyasa raina ya
baci. A take ya bata naira dubu biyu yace ta
bani inje in sayo atamfofi guda biyu 'yan naira
dari takwas takwas inyi dinkin dari bibbiyu.
Abida mace mai hakuri da tsananin wayo, ta
iya zama da mijinta duk zafin zuciyarsa, tabbas
macen da bata da hakuri da wayo ba zata iya
zama dashi ba, sai gashi da kansa yayi
nadamar aninda yayi mana, sai yaji kunya yazo
yana lallaba mu. DUK KYAN TAKALMI 5
Saurayina guda daya nake kulawa mai suna
musbahu, lungun mu daya dashi kowa yasan
mu tare, yana sona sosai nima haka saboda
yana kula dani. Tun sanda na gama sakandire
yake so ya aiko gidanmu ayi zancen aure sai
aka sami matsala daga gidansu, mahaifiyarsa
bata sona 'yar kanwarta take so ayi musu
auren gida, shi kuma ni yake so ya
aura.mahaifiyarsa ta tsane ni haka kawai, ko a
hanya na gaishe ta bata amsawa shiyasa na
daina zuwa gidansu don da ina zuwa wajen
kanwarsa jamila kawata ce ajinmu daya a
shekara. Musbahi ma yaji labarin duka dana
sha saboda aron kaya, sai naga ya siyo min
leshi guda daya da atamfa ya hada min da
naira dari biyar kudin dinki, sannan yayi min
fada in daina boye masa sirrina saboda yadda
yake sona a ransa, matsalata ai matsalarsa ce.
Yace duk sanda na shiga matsala in fada masa
ko bashi da kudi zai ciyo bashi yayi min komai
in dai baifi karfinsa ba. Yaci gaba da bani
hakuri akan halinda yake ciki shi da
mahaifiyarsa, ita ta hana shi ya turo gidanmu
zancen aurenmu. Ya umarce ni da mu dage da
addu'a Allah Ya karkato da zuciyar
mahaifiyarsa kaina taji tana sona ayi auren
dani. Sakamakon jarabawar mu na sakandire
ya fito naci credit takwas, geography ne kadai
naci pass shima dan a ranar da muka yi
jarabawar bani da lafiya. Sai misbahu yace idan
ya sami kudi zai saya min form din jamb in
wuce jami'a. Sai nace ba zan iya karatu a
jami'a ba saboda 'ya'yan masu kudi ne sukeyi,
bani da mai bani kudin mota da kudin sayan
handout, gashi dole sai an saka sutura masu
kyau. Sai shima ya gasgata zancena yaga
shima bashi da halin da zai dauki nauyin duk
wadannan sabida dan abinda yake samu ba
mai yawa bane. Duk da wasu lokutan sukan
sami ayyuka da yawa suna samun kudi a
business center yake aiki, suna typing a
computer, suyi kalandu ko meme. Sai yace to
zai samo min management in fara, nan ma
nace bana so nafi son inyi schl of nursing
saboda ba ruwana da neman kayan sakawa,
suna da uniform, sai yace shikenan zai binciko
yaji duk yadda akeyi a shiga amma in fara jin
ra'ayin yayana. Yayana ya amince da
shawararmu kuma yaji dadi musamman da
musbahu yazo har kofar gidanmu ya sa akayi
masa sallama da yayana hussaini ya kara yi
masa bayani. Yace zai taimaka min da wata
dawainiyar kudin makarnatar sai ya amince
yayi masa godiya. Musbahu da yayana ne suka
hada gwiwa suka bani duk kudaden da ake
bukata na shiga makarantar koyar aikin jinya
ta malam aminu kano dake unguwar court
road. Karatun shekara uku ne a shekara ta uku
ne muke zuwa asibiti koyar aiki don haka
karatu na yi tayi haikan, ban taba samun
matsala ba cinye jarabawata nake yi koda
yaushe. A asibitin malam aminu kano ake horar
damu koyar aiki (attachment). Ina zuwa
kkullum daga unguwarmu sharifai zuwa court
rd akan acaba saboda idan nace zan hau bus
zan bata lokacina zanyi in makara. Kudin
acabana kit da kit babu canji wata rana ko
purewater zan sha sai dai kawayena su saya
min. Duk da idan za'a je sayan abinci ko shan
lemo sai in gudu bana binsu saboda kullum sai
dai su saya min, ni kuma na fara jin kunya sun
gane bani dashi. Kawata khadija sani ismail
kadai wacce bata gajiya da taimakona kuma
duk sanda tace muje cin abinci naki zuwa ko
na sulale na gudu sai ranta ya baci, har tayi
fushi dani. Sai inyi tayi mata bayanan karya in
kirkiro uzurin dana je nayi ba guduwa nayi ba
sai ta ki yadda tasan karya nakeyi. Ba ita nake
ji ba, sauran kawayenmu nakeji don suna nuna
min bakin hali daga baya kuma in dinga jin
kananan maganganu cewar na cika san banza
kullum bana fitar da kudina ina sayawa kaina
abu balle in sayawa wani, sai dai ni kullum a
saya min. Rashin sani yafi dare duhu, kallon
kitse sukeyi wa rogo. Hakika ni mai yawan
tsafta ce in kula da fararen kayan makaranta
ta, kullum tsaf dani, ina kalkale jikina tas a
wanke ga karin guga. Gani nafi duk 'yan ajin
mu kokari yawanci ni nake basu amsa. Khadija
bazata iya rabuwa dani ba dan bata da kokari
sai dai gata, tunda iyayenta suna da hali. Duk
wasu manyan littattafai na karatu (text book)
babanta yana saya mata duk tsadarsu, sai nafi
morarsu don ni ce mai hazakar karatun ba ita
ba. Da taimakon Allah da taimakon khadija sani
nake cin jarabawa dan ba zan iya sayan
littattafan nan masu tsada ba. Badan Allah Ya
sa na iya kitos ba ina yiwa makwabta, da wata
rana ma ba zanje makaranta ba saboda duk
ranar da yaya hussaini ya tashi bashi da kudi
sai yace in hakura kada inje makaranatar randa
ya samu naje. Ni kuma bana so inyi fashi, da
kudin kitson nake harhadawa in tafi duk da
kitso a unguwar bashi da tsada, kan manya
naira talatin ko arba'in, na yara kuwa naira
ashirin ko goma ne. Ban taba fadawawa
kawayena sirrina ba, duk da yawan kawayen da
nake dasu a ajinmu mata da maza, sai dai ayi
hayaniya wasa da dariya a watse, ina taka
tsantsan da harshena a koda yaushe. Babu
wanda a cikinus ya san yadda gidanmu yake,
basu taba zaton haka nake rayuwa ba, sai dai
sun fahimci wani abu akwai wasu matsaloli
wanda ba zasu boyu ba. Suyi ta zargi da sake
sakensu a ransu su kadai, ni dai bazasu ji daga
bakina ba kuma ba zasu iya tara ta su
tambaye ni ba. Ni daman bana zuwa gidan
kowa balle azo gidanmu, mu hadu a abkin gate
ne mu rabu idan an tashi. Bana jin dadin
rayuwata a wannan bangaren saboda bani da
wata takamaimiyar kawa ko masoyin da zan
amayar musu da radadin da zugin matsalolin
da suke addabata. Kawata guda daya, itace
aminiyata, yayata, masoyiyata wato matar
yayana abida. Muna zama ni da ita mu raba
dare ko mu yini muna tattauna matsalolinmu,
koda yaushe ina samun nutsuwa da kwarin
gwiwa idan abida ta bani hakuri akan talaucin
da na tsinci kaina da shawarwari, sai inji sanyi
a raina, tawakkali ya kama zuciyata sai inji ta
tuno min da nasihohin da mahaifina yayi min a
baya. Idan nayi haka sai in dawo da walwalata,
ni burina guda daya ne shine in gama karatuna
in fara aiki in taimaki kaina, in taimaki 'yan
gidanmu. Babbar matsalar ma da tafi damuna
shine zaman cakudi a gidanmu, cikin tsagoron
kazata da cinkosa, babban burina ba wuce inga
mun bar gidan nan da umguwar mu canja gida
ko haya ce dai mu kama gidan da muke mu
kadai. Dakina daya da yara, ga dakin dan
karami mun cunkushe gashi su dukka yaran
abida fitsarin kwance sukeyi dan haka sun ruba
katifar sai zarni take dan haka na hakura da
katifar na bar musu. Na koma kwana akan
tabarma, idan na tashi da safe sai inyi salla
akai in nada in jingine a lungu sai zan sake yin
wani sallar sannan in shimfida. Har yanzu
kayana a jakar bagco yake a gefen shimfidata,
rayuwata ba irin na 'yan matan 'yan boko bace,
tamkar a kauye nake ba'a birni ba. Ko inyi
tunanin shiga hanyar banza, ban taba sha'awar
makalewa gidan kawaye ba ko arar kayan
kawa, na rike talaucina na kama kaina bana
sha''awar kayan wani. Daga makaranta sai
gida, a gidan ma nafi zama a daki kullum ina
karatu. Idan kaga na fito aiki nazo taya abida,
wankan 'ya'yanta , tsarkinsu ko aikin girki. Sai
'yan gidanmu da sauran 'yan unguwa suka
shiga yimin shaidar girman kai ne dani dan ni
'yar boko ce, basa ganin fara'ar da nake yi
musu. Kullum ina gaishe su ko basu ganni ba,
tabbas mutum ba'a iya iya masa, saboda dan
Adam ya kasance mai butulci ne. BABI NA UKU
Wata rana ranar litinin da misalin karfe daya na
rana muna cikin a sibiti, a bangaren marasa
lafiya muke wadanda aka kwantar dasu
sakamakon wasu kurajen da suka feso a
jikinsu. Muna biye da ma'aikaciyar jinya matron
maryam tana nunnana mana yadda ake aiki,
domin neman karin bayani sai tace bari ta
hada mu da kwararren likita wanda ya kware a
bangaren fata. Ta tura wani daki ta shiga
muma muka bita a baya da alama dakin
daukan darussa ne sabida naga kujeru ne zalla
da allo makale a jikin bangon. Kamar yadda
naji ta ambaci sunansa, dr shureim imran. Mun
iske shi tsaye a tsakiyar ajin tare da wasu
daliban likitoci guda 3 maza biyu, mace daya
da alama sunzo sunyi masa tambayoyi ne akan
wasu abubuwan da basu gane ba. Bayanai
yake yi musu cikin harshen turanci kai kace
baturen america ne, kalmomin kimiyyar
(botanical names) da yake ta ambato yana
jerowa layi layi da ka ba tare da yana duba
littafi ba, kai kace shine ya lakaba musu sunan
don ya haddace. Muna sake kutsawa cikin
ofishin yayin da zazzakar muryarsa, daddada
take sake shiga kunnuwanmu sai duk muka
kagu mu isa gabansa don mu kalli fuskar mai
muryan nan daddada. Kasancewar kofar ta
cushe muna shiga don muna da yawa, ga
dalibai likitoci nan suna kokarin fitowa sun
gama daukar darasin. Kowa ya kagu yayi ido
hudu da mai daddadar muryar nan, keyarsa
kawai na fara hangowa daga nesa sai na
tabbatar bakar fata ne dan uwana saboda ban
hango jan kunne ba da farin gashi irin na
turawa ba. Bakin gashi ne tattaura irin namu
na hausawa, sai dai gashin a gyare yake yana
shekin mai kuma ya kwanto lambar zuwa
karshen keyarsa. Kansu babu hula, yana sanye
da bakaken kaya riga da wando (suit), farar
riga mai dogon hannu daga ciki, ya daure
wuyansa da jan kyalle wato necktie. Dana
matso ciki sai na fara hango gefen fusakarsa,
wata lafiyayyiyar fata na fara hangowa mai
dauke da launi mai tsananin kyau. Irin kalar da
take tsada a duniya wato hasken duhu
(chocolate color). Ko dana sake samun daman
na matso kuda dashi sai ga gefen fuskarsa tar
ina gani wato idonsa daya da gefen hancinsa,
sai kawai naji wata mummunar fadywar gaba
ta far min ni ma bansan dalili ba har wadanda
ke kusa dani zasu iya jiyo karar ajiyar zuciya
danayi. Tunda nake a rayuwata ban ta ba ganin
irin wadannan dara daran idanuwan ba masu
tsananin haske daga ciki, da bakar kwayar ido
mai tsananin baki, aka zagaye idon da wasu
gashin ido da gashin gira masu yawa da
tsananin baki, ya gyara su sunyi kira mai kyau
suna sheki. A nutse ya waiwayo da kyakkyawar
fuskarsa gaba daya ya dube mu, bani kadai ba
duk wata 'ya mace da take wajen sai dataji a
ranta dama ace wannan kadarar mallakarta ce.
'Yan uwansa maza ma sai da suka raya a
ransu dama ace sune shi, ga kyau ga ilimi.
Ashe a da dana ke hango gefen fuskarshi ban
hango komai ba, kyau mai sunan kyau sai ka
kalle shi gaba dayansa daga kafarsa zuwa
kansa. Dogon mutum ne sosai ma kyawun
sura, bashi da kiba da yawa, haka bashi da
rama. Yayi kama da irin bakaken turawan nan
da ake kira african American, hukuncin da na
yanke masa kenan dan ko kusa baiyi kama da
'yan nigeria ba! Tabbas ruwa biyu ne suka
hadu suka same shi bakar fata da farar fata.
Saurayina guda daya nake kulawa mai suna
musbahu, lungun mu daya dashi kowa yasan
mu tare, yana sona sosai nima haka saboda
yana kula dani. Tun sanda na gama sakandire
yake so ya aiko gidanmu ayi zancen aure sai
aka sami matsala daga gidansu, mahaifiyarsa
bata sona 'yar kanwarta take so ayi musu
auren gida, shi kuma ni yake so ya
aura.mahaifiyarsa ta tsane ni haka kawai, ko a
hanya na gaishe ta bata amsawa shiyasa na
daina zuwa gidansu don da ina zuwa wajen
kanwarsa jamila kawata ce ajinmu daya a
shekara. Musbahu ma yaji labarin duka dana
sha saboda aron kaya, sai naga ya siyo min
leshi guda daya da atamfa ya hada min da
naira dari biyar kudin dinki, sannan yayi min
fada in daina boye masa sirrina saboda yadda
yake sona a ransa, matsalata ai matsalarsa ce.
Yace duk sanda na shiga matsala in fada masa
ko bashi da kudi zai ciyo bashi yayi min komai
in dai baifi karfinsa ba. Yaci gaba da bani
hakuri akan halinda yake ciki shi da
mahaifiyarsa, ita ta hana shi ya turo gidanmu
zancen aurenmu. Ya umarce ni da mu dage da
addu'a Allah Ya karkato da zuciyar
mahaifiyarsa kaina taji tana sona ayi auren
dani. Sakamakon jarabawar mu na sakandire
ya fito naci credit takwas, geography ne kadai
naci pass shima dan a ranar da muka yi
jarabawar bani da lafiya. Sai misbahu yace idan
ya sami kudi zai saya min form din jamb in
wuce jami'a. Sai nace ba zan iya karatu a
jami'a ba saboda 'ya'yan masu kudi ne sukeyi,
bani da mai bani kudin mota da kudin sayan
handout, gashi dole sai an saka sutura masu
kyau. Sai shima ya gasgata zancena yaga
shima bashi da halin da zai dauki nauyin duk
wadannan sabida dan abinda yake samu ba
mai yawa bane. Duk da wasu lokutan sukan
sami ayyuka da yawa suna samun kudi a
business center yake aiki, suna typing a
computer, suyi kalandu ko meme. Sai yace to
zai samo min management in fara, nan ma
nace bana so nafi son inyi schl of nursing
saboda ba ruwana da neman kayan sakawa,
suna da uniform, sai yace shikenan zai binciko
yaji duk yadda akeyi a shiga amma in fara jin
ra'ayin yayana. Yayana ya amince da
shawararmu kuma yaji dadi musamman da
musbahu yazo har kofar gidanmu ya sa akayi
masa sallama da yayana hussaini ya kara yi
masa bayani. Yace zai taimaka min da wata
dawainiyar kudin makarnatar sai ya amince
yayi masa godiya. Musbahu da yayana ne suka
hada gwiwa suka bani duk kudaden da ake
bukata na shiga makarantar koyar aikin jinya
ta malam aminu kano dake unguwar court
road. Karatun shekara uku ne a shekara ta uku
ne muke zuwa asibiti koyar aiki don haka
karatu na yi tayi haikan, ban taba samun
matsala ba cinye jarabawata nake yi koda
yaushe. A asibitin malam aminu kano ake horar
damu koyar aiki (attachment). Ina zuwa
kkullum daga unguwarmu sharifai zuwa court
rd akan acaba saboda idan nace zan hau bus
zan bata lokacina zanyi in makara. Kudin
acabana kit da kit babu canji wata rana ko
purewater zan sha sai dai kawayena su saya
min. Duk da idan za'a je sayan abinci ko shan
lemo sai in gudu bana binsu saboda kullum sai
dai su saya min, ni kuma na fara jin kunya sun
gane bani dashi. Kawata khadija sani ismail
kadai wacce bata gajiya da taimakona kuma
duk sanda tace muje cin abinci naki zuwa ko
na sulale na gudu sai ranta ya baci, har tayi
fushi dani. Sai inyi tayi mata bayanan karya in
kirkiro uzurin dana je nayi ba guduwa nayi ba
sai ta ki yadda tasan karya nakeyi. Ba ita nake
ji ba, sauran kawayenmu nakeji don suna nuna
min bakin hali daga baya kuma in dinga jin
kananan maganganu cewar na cika san banza
kullum bana fitar da kudina ina sayawa kaina
abu balle in sayawa wani, sai dai ni kullum a
saya min. Rashin sani yafi dare duhu, KALLON
KITSE sukeyi wa ROGO. Hakika ni mai yawan
tsafta ce in kula da fararen kayan makaranta
ta, kullum tsaf dani, ina kalkale jikina tas a
wanke ga karin guga. Gani nafi duk 'yan ajin
mu kokari yawanci ni nake basu amsa. Khadija
bazata iya rabuwa dani ba dan bata da kokari
sai dai gata, tunda iyayenta suna da hali. Duk
wasu manyan littattafai na karatu (text book)
babanta yana saya mata duk tsadarsu, sai nafi
morarsu don ni ce mai hazakar karatun ba ita
ba. Da taimakon Allah da taimakon khadija sani
nake cin jarabawa dan ba zan iya sayan
littattafan nan masu tsada ba. Badan Allah Ya
sa na iya kitos ba ina yiwa makwabta, da wata
rana ma ba zanje makaranta ba saboda duk
ranar da yaya hussaini ya tashi bashi da kudi
sai yace in hakura kada inje makaranatar randa
ya samu naje. Ni kuma bana so inyi fashi, da
kudin kitson nake harhadawa in tafi duk da
kitso a unguwar bashi da tsada, kan manya
naira talatin ko arba'in, na yara kuwa naira
ashirin ko goma ne. Ban taba fadawawa
kawayena sirrina ba, duk da yawan kawayen da
nake dasu a ajinmu mata da maza, sai dai ayi
hayaniya wasa da dariya a watse, ina taka
tsantsan da harshena a koda yaushe. Babu
wanda a cikinus ya san yadda gidanmu yake,
basu taba zaton haka nake rayuwa ba, sai dai
sun fahimci wani abu akwai wasu matsaloli
wanda ba zasu boyu ba. Suyi ta zargi da sake
sakensu a ransu su kadai, ni dai bazasu ji daga
bakina ba kuma ba zasu iya tara ta su
tambaye ni ba. Ni daman bana zuwa gidan
kowa balle azo gidanmu, mu hadu a abakin
gate ne mu rabu idan an tashi. Bana jin dadin
rayuwata a wannan bangaren saboda bani da
wata takamaimiyar kawa ko masoyin da zan
amayar musu da radadin da zugin matsalolin
da suke addabata. Kawata guda daya, itace
aminiyata, yayata, masoyiyata wato matar
yayana abida. Muna zama ni da ita mu raba
dare ko mu yini muna tattauna matsalolinmu,
koda yaushe ina samun nutsuwa da kwarin
gwiwa idan abida ta bani hakuri akan talaucin
da na tsinci kaina da shawarwari, sai inji sanyi
a raina, tawakkali ya kama zuciyata sai inji ta
tuno min da nasihohin da mahaifina yayi min a
baya. Idan nayi haka sai in dawo da walwalata,
ni burina guda daya ne shine in gama karatuna
in fara aiki in taimaki kaina, in taimaki 'yan
gidanmu. Babbar matsalar ma da tafi damuna
shine zaman cakudi a gidanmu, cikin tsagoron
kazanta da cinkoso, babban burina ba wuce
inga mun bar gidan nan da umguwar mu canja
gida ko haya ce dai mu kama gidan da muke
mu kadai. Dakina daya da yara, ga dakin dan
karami mun cunkushe gashi su dukka yaran
abida fitsarin kwance sukeyi dan haka sun ruba
katifar sai zarni take dan haka na hakura da
katifar na bar musu. Na koma kwana akan
tabarma, idan na tashi da safe sai inyi salla
akai in nada in jingine a lungu sai zan sake yin
wani sallar sannan in shimfida. Har yanzu
kayana a jakar bagco yake a gefen shimfidata,
rayuwata ba irin na 'yan matan 'yan boko bace,
tamkar a kauye nake ba'a birni ba. Ko inyi
tunanin shiga hanyar banza, ban taba sha'awar
makalewa gidan kawaye ba ko arar kayan
kawa, na rike talaucina na kama kaina bana
sha''awar kayan wani. Daga makaranta sai
gida, a gidan ma nafi zama a daki kullum ina
karatu. Idan kaga na fito aiki nazo taya abida,
wankan 'ya'yanta , tsarkinsu ko aikin girki. Sai
'yan gidanmu da sauran 'yan unguwa suka
shiga yimin shaidar girman kai ne dani dan ni
'yar boko ce, basa ganin fara'ar da nake yi
musu. Kullum ina gaishe su ko basu ganni ba,
tabbas mutum ba'a iya iya masa, saboda dan
Adam ya kasance mai butulci ne. BABI NA UKU
Wata rana ranar litinin da misalin karfe daya na
rana muna cikin a sibiti, a bangaren marasa
lafiya muke wadanda aka kwantar dasu
sakamakon wasu kurajen da suka feso a
jikinsu. Muna biye da ma'aikaciyar jinya matron
maryam tana nunnana mana yadda ake aiki,
domin neman karin bayani sai tace bari ta
hada mu da kwararren likita wanda ya kware a
bangaren fata. Ta tura wani daki ta shiga
muma muka bita a baya da alama dakin
daukan darussa ne sabida naga kujeru ne zalla
da allo makale a jikin bangon. Kamar yadda
naji ta ambaci sunansa, dr shureim imran. Mun
iske shi tsaye a tsakiyar ajin tare da wasu
daliban likitoci guda 3 maza biyu, mace daya
da alama sunzo sunyi masa tambayoyi ne akan
wasu abubuwan da basu gane ba. Bayanai
yake yi musu cikin harshen turanci kai kace
baturen america ne, kalmomin kimiyyar
(botanical names) da yake ta ambato yana
jerowa layi layi da ka ba tare da yana duba
littafi ba, kai kace shine ya lakaba musu sunan
don ya haddace. Muna sake kutsawa cikin
ofishin yayin da zazzakar muryarsa, daddada
take sake shiga kunnuwanmu sai duk muka
kagu mu isa gabansa don mu kalli fuskar mai
muryan nan daddada. Kasancewar kofar ta
cushe muna shiga don muna da yawa, ga
dalibai likitoci nan suna kokarin fitowa sun
gama daukar darasin. Kowa ya kagu yayi ido
hudu da mai daddadar muryar nan, keyarsa
kawai na fara hangowa daga nesa sai na
tabbatar bakar fata ne dan uwana saboda ban
hango jan kunne ba da farin gashi irin na
turawa ba. Bakin gashi ne tattaura irin namu
na hausawa, sai dai gashin a gyare yake yana
shekin mai kuma ya kwanto lambar zuwa
karshen keyarsa. Kansu babu hula, yana sanye
da bakaken kaya riga da wando (suit), farar
riga mai dogon hannu daga ciki, ya daure
wuyansa da jan kyalle wato necktie. Dana
matso ciki sai na fara hango gefen fuskarsa,
wata lafiyayyiyar fata na fara hangowa mai
dauke da launi mai tsananin kyau. Irin kalar da
take tsada a duniya wato hasken duhu
(chocolate color). Ko dana sake samun daman
na matso kusa dashi sai ga gefen fuskarsa tar
ina gani wato idonsa daya da gefen hancinsa,
sai kawai naji wata mummunar fadywar gaba
ta far min ni ma bansan dalili ba har wadanda
ke kusa dani zasu iya jiyo karar ajiyar zuciya
danayi. Tunda nake a rayuwata ban ta ba ganin
irin wadannan dara daran idanuwan ba masu
tsananin haske daga ciki, da bakar kwayar ido
mai tsananin baki, aka zagaye idon da wasu
gashin ido da gashin gira masu yawa da
tsananin baki, ya gyara su sunyi kira mai kyau
suna sheki. A nutse ya waiwayo da kyakkyawar
fuskarsa gaba daya ya dube mu, bani kadai ba
duk wata 'ya mace da take wajen sai dataji a
ranta dama ace wannan kadarar mallakarta ce.
'Yan uwansa maza ma sai da suka raya a
ransu dama ace sune shi, ga kyau ga ilimi.
Ashe a da dana ke hango gefen fuskarshi ban
hango komai ba, kyau mai sunan kyau sai ka
kalle shi gaba dayansa daga kafarsa zuwa
kansa. Dogon mutum ne sosai ma kyawun
sura, bashi da kiba da yawa, haka bashi da
rama. Yayi kama da irin bakaken turawan nan
da ake kira african American, hukuncin da na
yanke masa kenan dan ko kusa baiyi kama da
'yan nigeria ba! Tabbas ruwa biyu ne suka
hadu suka same shi bakar fata da farar fata.
Duk da tashin hankalin da na shiga da naji
bayananta sai nayi murmushin karfin hali nace
subhanallah! Bai kamata kice zaki bi kowacce
hanya ba gara ma kice zaki bishi da addua in
da alkhairi Allah ya yi. Khadija tace bawai ina
nufin zan fita daga musulunci ba akansa ba,
amma fa dole saina saka malamaina sunyi min
addua. Na fahimci maryam ahmed da mansura
mahmud suna sonsa kin san su da bin
malamai, in ban dage ba sai sun janye
hankalinsa. Gaskiya tunda nake a duniya ban
taba ganin Kyakkyawan bakar fata irinsa ba, ko
kin taba gani? Na girgiza kai nace ban taba
gani ba, amma shima yana ji da kansa dan
yasan ya hadu kuma mata suna nuna masa
haka. Ba kya ganin 'yan matan nan medical
student suna ta kawo hare harens garshi?
Khadija tace tabbas na gani, shiyasa nace sai
nayi da gaske fa. Ai mu uku ne kadai muka
amayar da maitarmu a waje, nasan mata da
yawa sun dasa a ajin fada ne kawai basu yi ba.
Kin burge ni aisha umar, sai naga kwata kwata
ba ya gabanki, ko a bayan idonki muna yabonki
don kina kama kanki bakya shiga rigimar da
tafi karfinki. Sai kawai nayi murmushi nace a
raina kallon kitse kike yiwa rogo, aini zuciyata
tuni ta kunsa min abinda zuciyoyinku basu
kunsa muku ba. Tabbas nasan burina da fatana
akan dr shurain yafi nasu. Aisha umar kalli
motar can, inji khadija yayin da ta matse 'yan
yatsunna don gigicewa. Na juya da sauri, sai
naga wata dankareriyar mota baka mai farin
gilashi. A cikin motar kuma zankadeden mutum
ne, sanye da farar riga da bakin gilashi a
fuskarsa. Ya kalle mu, muma kallonsa mukayi
sai ya kawar da kai ya fisgi motarsa da gudu
ya nufi gate din fita. Na dubi motar har da
waiwaye sannan na juyo na dubi khadija nace
motar nan ta hadu, haka mutumin da yake
cikin motar ma ya hadu. Wanene shi? Tace au
baki gane shi bane? Dr shuraim ne likitan da
muke zancensa yanzu. Dan halak yaki ambato.
Sai nace kai bashi bane, ai shi bakar suit ya
saka. Tace bakar ta saman ya cire, ya bar
farar ta ciki. Baki shaida jan neck tie din bane?
Sai nayi shiru saboda haduwarsa tafi karfin
tunanina, sama ta yiwa yaro nusa ba zai iya
tabawa ba sai dai ya daga ido ya hango. Sai
na tuna ai Allah ne ya halicce shi wanda ya
halicce ni, babu wanda yafi wani a wajensa sai
wanda yafi bauta masa don haka na daina
raina kaina. Na kudira a raina zan sake rikar
addinina yadda zan sami babban rabo a lahira,
koda kuwa ban sami wanda nake so a duniya
ba. Zuciya ta fara warwarewa daga kuncin
daya damke ta na son maso wani. Tun ina
sauraron surutun da khadija takeyi har na
daina ganewa, burina kawai in ganni a gida na
shige lungun dakina. Ina hau yamutsattsiyar
tabarmata in kudindina inyi ta aiyano ni tare da
abin kauna ta shuraim. Ina daukar jakata sai
nayi musu sallama na nufi gate din fita a
sanyaye ina tafe ina tunani. Na fita waje na
tsayar da acaba kamar kullum na haye ya kai
ni kofar gidanmu. Tun daga zauren gidanmu
nake cin karo da matan gidan suna ta
hidindimunsu na saye da sayarwa da surutin da
suke yini suna yi, ayi gulmar wannan, a zagi
waccan, yau sai suka ganni ba kamar kullum
ba. Da bayan na gaishe su sai in dan zauna ayi
barkwanci sannan in wuce cikin gida, yau babu
kanta da kyar nake magana, sauri kawai nake
yi in shige ciki. Sunyi zaton yunwa nakeji, har
suke zolayata da cewa abida ba ta nan, ba'ayi
abinci ba. Na wuce abu na, na iske abida tana
dafa a binci a risho. Tana ganina tayi kasake
tana kallona, ta san akwai damuwa tunda bata
jiyo muryata ba, bata gano murmushina ba
saboda ina da yawan dariya. Ta dube ni tace
aisha farida kalau kuwa, ko allura zakiyi wata
mara lafiya ta kwace ta tsira miki? Nayi dariya
nace haba dai ayi haka kuwa? Bana jin dadi
dai. Tace Allah ya sawake, shiga daki kihuta
kafin abinci ya dahu ki ci zaki murmure. Ina
shiga daki na cire uniform dina sai na daura
tawul na dauki kwandon wanka zan je in watsa
ruwa dan inji dan sanyi a jikina saboda na
kwaso rana.sai na ga abida ta shigo tana
dariya tace da ni "af ashe wanka zaki yi da
labari zan baki mai dadi kuma marar dadi." Na
ajiye kwandon wanka na jawo hannunta muka
zauna.Na ce bani in sha ai na fasa wanakan,me
ya faru? Ta yi dariya tace labarin musbahu
tsohon saurayinki da matarsa lubabatu zan
baki daman,aure dai yaki dadi har ya yi mata
saki daya dazun nan aka yi rigimar. Lungun
nan ya cika da mutane mahaifiyarsa dai sai a
taya ta da addua don ta cika naci,ce masa tayi
idan ya sake furta kalmar saki sai ta tsine
masa dole sai ya zauna da lubabatu tasan
akan aisha farida yake yi mata wulaqanci kala-
kala. Tayi rantsuwa tace ko bayan ranta idan
ya saki lubabtu ya aure ki Allah ya isa. Kin ji
wata kiyayya sabuwa ko? Na yi murmushin
karfin hali nace,Allah ya kyauta,ta ma daina
kokarin tsinewa danta a kaina tuntuni na yi
masa sallama nace ya bi mahaifiyarsa don ya
sami rahama. Ya na aiko min da kudi tun ina
karba sai na daina karba daga baya idan ya
aiko sai in mayar da dan aiken in ce bana so
don zaman lafiya. Abida tace haka ya fi,ai gara
da kika yi. Masa haka kin taimake shi. Ni na
dauka ma zancen kika ji tun daga zaure da na
ga kin shigo ranki a bace. Amma fa ki godewa
Allah AF saboda kin samu kyakkyawon yabo a
ung nan. Ba kiji. Yadda kowa yake yabonki
ba,ake ta tsine mata ita kuma. Kowa ya dinga
cewa me ye laifin AF har da bata so danta ya
aura? Yarinya mai nutsuwa da hankali mai ilimi
da fara'a tana gaishe da mutane. Ta zo ta
tauyewa yaro rayuwarsa ta cusa masa
dakalkalalliyar macen da ba ta da tsari. Nace
au daman an sanni da yawa a ung nan haka?
Abida tace "ji ki da Allah da neman magana
waye bai sanki ba,musamman da kika shiga
skul of nursing kina karbar haihuwa kina allura
a cikin ung sai ki ji kowacce mata tana cewa
wajen aisha likita zan je ta rubuta min magani.
A nan dai muka tashi muka rufe hirar nan
zuciyata cike da tausayin musbahu ba don
mahaifiyarsa ba ta sona ba da na aure shi mun
zauna mun rufawa juna asiri,in huta fadawa
cikin hatsarin da nake shirin jefa kaina. Bayan
na yi wanka na ci abinci sai na wartsake na
shiga cikin matan gidan muna ta hira har ma
na ji na fara mantawa da abunda yake damuna
a zuciyata. Sai da kowa ya shiga barci dare ya
fara nisawa sai tunanin Dr shureim imran yace
da wa Allah ya hada ni in ba da ke ba,sai na ji
gaba daya daya zuciyata ta kasa sukuni. Da
zarar na rufe ido sai in ganshi tamkar a zahiri.
Sai na yi ta yaki da zuciyata ina ture shi daga
tunanina.kai in takaice maka a cikin satin nan
ban gane kaina da kaina saboda tsananin
tunaninsa. Idan na je asibiti bana walwala haka
idan na dawo gida ba na jin dadin zuciyata
kada ma dare ya ji labari sai ka ga idona ya
wartsake garau na burma tunanin DR shureim
imran. Da gaske sonsa nake,so ba da wasa
ba.tun ranar kuma ban sake ganinsa ba sai dai
kullum sai khadija ta yi min labarinsa.Albishir
din da ta yi min shi ne ta sami lambar wayarsa
amma tana tsoron kira don tana ganin zai yi
mata wulaqanci. Ta shaida min ta rabawa
malamai kudi ana ta ragargaza mata addu'a ta
koina,a kalla ta raba musu zunzurutun kudi ya
kai N25,000 so take sai an gama addua tas
sannan ta kira shi dolensa ya amince. Sai na
sake jin jikina ya yi sanyi na sake yi wa
zuciyata fada da ta yi ta- ka tsan- tsan ta
daina cusa abunda zai iya kasheta.idan da
khadija. Zata lura duk sanda ta fara yi min
zancen Dr shureim sai jikin yayi sanyi kuma na
kan rasa amsar da zan bata ko shwara.
Kallonta kawai nake tsayawa ina yi yayin da
zata iya ganin hawaye yana cika min ido sai
inyi sauri in mayar da shi ina tauisayinta na fi
tausayin kaina domin na san zuciyata ta fi tata
shiha hatsari kuma ta fini sanin yadda zata yi
da kanta. Ni ko wayar ma bani da ita babu
kudin saka kati balle in saka rai ko zan karbi
lambar in kira inji dadi. Na zama na rasa
walwala ta ko abincin kirki bana iya ci na
dukufa da adduar Allah ya yaye min don sonsa
ya zame min ciwo.naji duk na tsani kaina karfi
da yaji nake fisge tunaninsa daga cikin
zuciyata.amma abu ya ci tura sai ma karuwa
yake yi. Idan naki tunaninsa karfi da yaji a ido
biyu da zarar na kwanta sai nayi mafarkinsa,
sai gani cikin dare ina kuka wiwi ina sallah da
adduar Allah Ya yaye min, Allah Ya kawo abin
da zai sa inji na tsane shi ma. Duk satittikan
nan da nayi ina jinyar sonsa ko a hanya ban
hadu dashi ba balle ma in ji dan sanyi a raina,
ina so ina kara ganin suffarsa don in kawata
tunanina domin kamanninsa suna kokarin
disashe min. Ranar talata da sassafe ina
dirowa daga kan acaba a kofar shiga gate din
asibitin aminu kano sai na yi kicibus dashi a
cikin wannan tsaleliyar motar tasa. Na
waiwaya da sauri na dube shi yayin da shi ma
yake dubana har da rage tafiya amma fa duban
da yake yi min bana kauna bane, hararata yake
yi game da nuna tsana mai yawa a bayyane.
Sai yayi tsaki ya girgiza kai ya kada sitiyarin
motarsa yayi wucewarsa. Sai na dankare a
tsaye ni ban ciro kudin mai acaba na biya shi
ba, ni banyi gaba ba balle ace mantuwa nayi.
Bani kudin mana, inji zalamamman dan acba.
Na ciro kudin na mika masa ya karba yana
shirin ya miko min canjina naira ashirin sai na
girgiza kai nace kayi min sadaka, ku taya ni
addua don bani da lafiya. Sai ya tsaya yana
kallona cike da tausayi yace to ko gida za a
mayar dake idan ba zaki iya aikin ba? Ai komai
sai da lafiya akeyi. Nayi murmushin karfin hali
nace ciwona addua yake bukata ba hutu ba, ko
shan magani. Sannan maganin ciwon yana
cikin asibitin nan, idan na koma gida ai babu
maganin a can. Yace gaskiya ne duk wani
magani yana asibiti. Allah Ya yaye miki
kowanne irin ciwo ne wannan. Na amsa da
amin nagode. Na juya a sanyaye ina tafiya
kamar kwai ya fashe min a ciki. Ina mai
matukar mamaki da takaicin kallon wulakancin
da yayi min. Na kasa tantance ni kuwa laifin
me nayi masa a rayuwata da ya tsane ni,
yaushe ma ya taba ganina banda sau daya
shima a rubibi, yaushe zai ganeni? Aisha farida
umar, karaf naji an kira sunana daga gefena.
Nayi firgigit na juyo da sauri. Khadija sani
ismail na gani ta tsaya da motarta hience 2008
ta sauke gilashin wundonta kasa, na tsallako
inda take na bude gaban motar na shiga. Ina
kokarin gaishe ta sai ta katse ni cikin murna
take magana tace albishirinki? Na kira Dr
shuraim imran jiya ya dauka, sai dai mun fara
magana yace in bashi bane wanda nake newa
wrong number ce, ya katse wayar. Sai na tura
masa sako nace ni dalibarsa ce , na kira in
gaishe shi. Kinga amsar daya bani. Sai ta miko
min wayarta, sai hannuna ya hau kakkarwa,
har sai da ta tsaya tana kallona saboda gaba
daya jikina bari yake yi. Na duba na karanta
sai naga ya runuta "thanks". Sai na lumshe ido
don dadin ganin rubutunsa da lambarsa, naji
dama nice nake yi masa waya da tura sako da
ko amsar da ya bawa khadija na samu ya bani
kadai na gama jin dadin rayuwata, ta isheni
abin farin ciki. Na bude baki nayi magana da
kyar, nace lallai kinji dadi. Tace dadi ka-n jiya
ai jar da barci da munshari don samun
kwanciyar hankalin dana ji. Dole in karawa
malamaina kudi su sake dagewa da addua
sosai. Nayi ajiyar zuciya nace ya san sunanki?
Tace bai tambaye niba, ki kyale shi sai a
hankali, dan wulakanci ne fa wannan da kike
gani. Muka isa bangaren da muke,mun bar
bangaren masu kuraje mun koma bangaren
yara. Muna shiga ciki muka iske 'yan ajinmu a
tsaitsaye kowannensu da dan littafinsa a hannu
da biro, da alama matron ta fara bayani akan
wannan yaro mai ciwon amai da gudawa. A
tsaye nake ina kallon bakin yaron a hannun
mahaifiyarsa yana tsala kuka, amma ban
fahimci bayanan matron ba, ko kadan ban san
me take cewa ba. Tunanina kawai daman ace
dana ne wannan jaririn muka haifa tare da Dr
shureim imran. Sai da ta gama bayani ta juya,
naga an bi ta duuu a baya zuwa gadon wani
yaron marar lafiya, shi kuma mai ciwon
pneumonia ne, sai na ja birki na tsaya cak na
ki bin su saboda kafafuwana da kwakwalwata
sun gaji ba zasu iya daukar abubuwa guda biyu
ba, tunanin dr shuraim imran shi yafi matsa
min, gara in yi shi shi kadai, shi yafi
muhimmanci a gareni don haka na juya na nufi
ofishinmu inda muke zama mu huta da ajiye
jakunkunan mu. Ina shiga sai naga maryam
ahmad tayi kasake a zaune akan kujera tana
matsa wayarta, fuskarta babu walwala. Nayi
mata magana sai naji da kyar take amsa min.
Na tambaya cikin damuwa maryam lafiya? Me
ke damunki? Baki da lafiya ne. Ta girgiza kai
tace lafiya kalau. Ni dai na dame ta da
tambaya lallai sai ta fada min abin dake
damunta. Ko a mafarki ban zata amsar da zata
bani ba kenan. Budar bakin ta ke da wuya tace
waye inba dr shureim ba? Sai naji gabana ya
fadi daf! Na fada a gigice me yayi miki? Sai ta
dube ni kwalla ta cika mata ido tace aisha
farida na yarda dake shi yasa zan fada miki
sirrina, na san kina da rike sirrin jama'a ba
ataba fada miki magana kin yada ba, na san
zaki bani shawarar da ta dace. Ina matukar
son dr shureim imran, har zuciyata sai naga da
in tsaya labe labe shi ma mutum ne kamar ni,
me zai hana in tunkare shi in fada maas tunda
ni bazawara ce, kunyar me zanji? Duk inda
mace ta kai na kai, ina da kyauna da ilimina da
arzikina, gani 'yar asali karewa ma 'yar
sarauta. Dazun nan na tare shi a bakin ofis
dinsa yana ganina ya bata rai na gaishe shi ya
amsa da kyar, ya bude kofar ofis dinsa ya shiga
sai na bi bayansa. Muna shiga sai ya daka min
tsawa yace lafiya? Nace nazo in gaishe shi ne.
Ya fada a fusace yace to naji sai anjima. Nace
kuma ina da magana da nake tafe da ita. Sai
yace fadi maganarki ki fita. Nace so nake mu
saba in karbi lambarka, ka karbi tawa. Ko rufe
bakina banyi ba yace bana bukatar in saba da
ke, haka bana son lambarki, sai anjima. Sai ta
fashe da kuka ta rungumeni. Bansan sanda na
dora hannu aka ba nace mun shiga uku, Allah
Ya jikaina. Maryam ta dago cike da mamaki
tace aisha farida menene? Nayi sauri na gyara
zancen nace ai da kika fada min abin da yayi
miki sai naji kama zan hadiyi zuciya in mutu,
shine nace Allah yaji kaina. Tace meye
shawararki? Shawarar da na ba wa kaina ita
nake kokarin in bata, itace tayi hakuri ta rabu
dashi, taci gaba da addua. Allah ya yaye mata
sonsa ya hadata da mai sonta wanda yafi shi.
Sai tace a'a ai ba isa ba, sai ya san ita yayi
ma wulakanci. Ai ko zata salwantar da
dukiyarta kakaf sai ta rama abinda yayi mata.
Sai tayi masa asirin da sai ya kwanta a kasa
ta murje shi da takalmin kafarta. Ban sake
magana ba na tsaya kawai ina kallonta, yayin
da naji tausayinsa ya kama ni, bana so a
wahalar min da abin kaunata. Daga nan na
kara cire ran mafarkin samun dr shuraim imran
a rayuwata. Naci gaba da jinya ina jiran ranar
ajalina domin mutuwata ce kadai zatayi min
maganin ciwon nan. DUK KYAN TAKALMI 7 Sai
ta fashe da kuka ta rungumeni. Bansan sanda
na dora hannu aka ba nace mun shiga uku,
Allah Ya jikaina. Maryam ta dago cike da
mamaki tace aisha farida menene? Nayi sauri
na gyara zancen nace ai da kika fada min abin
da yayi miki sai naji kama zan hadiyi zuciya in
mutu, shine nace Allah yaji kaina. Tace meye
shawararki? Shawarar da na ba wa kaina ita
nake kokarin in bata, itace tayi hakuri ta rabu
dashi, taci gaba da addua. Allah ya yaye mata
sonsa ya hadata da mai sonta wanda yafi shi.
Sai tace a'a ai ba isa ba, sai ya san ita yayi
ma wulakanci. Ai ko zata salwantar da
dukiyarta kakaf sai ta rama abinda yayi mata.
Sai tayi masa asirin da sai ya kwanta a kasa
ta murje shi da takalmin kafarta. Ban sake
magana ba na tsaya kawai ina kallonta, yayin
da naji tausayinsa ya kama ni, bana so a
wahalar min da abin kaunata. Daga nan na
kara cire ran mafarkin samun dr shuraim imran
a rayuwata. Naci gaba da jinya ina jiran ranar
ajalina domin mutuwata ce kadai zatayi min
maganin ciwon nan. Abida ta lura bana cikin
walwata kullum ina cikin damuwa, ta
tambayeni har ta gaji na kasa fada mata
wannan badakalar cutar da zuciyata ke fama
da ita, babu abinda nake boyewa abida amma
wannan dai ba zai fadu ba. Na gwammace a
dauki gawata a dinga tunanin fuju'an na mutu
babu ciwo ni da Ubangijina munsan abinda ya
kashe ni. Sai na shiga tunanin ko shi yasa ya
dinga hararata saboda masu irin uniform dina
ne suke damunsa ya zata nice? Haka ne ma
babu tantama ya dauka khadija da maryam ce
ni. Bansan takamaiman ofis dinsa ba, don haka
kaina tsaye na tunkari ofishin dr lukman likitan
kwakwalwa dauke da file din matron maryam
ta umurce ni da in kai masa. Ofis na uku tace
min daga hannun dama, don haka kaina tsaye
nan na kwankwasa na shiga tun kafin a bani
izini, saboda saurin da nake yi don inyi in koma
wajen daukan darasi. Abin da nagani a cikin
ofishin shi ya firgita ni har sai da kowa ya gane
na tsorata, dr shureim imran na gani a zaune a
kan kujera da laptop dinsa akan table yana
danne danne, maimakon mai ofis din dr
lukman. Wace wannan? Ya kika koma da sauri?
Wa kike nema? Tambayoyin da na jiyo ana yi
min kenan daga cikin ofishin ni kuwa tuni nayi
waje. Na rufo kofar a hankali na fara sanda zan
juya, jikina yana rawa ina gudun wulakancinsa.
Wata murya naji an kira ni, har na kai kan
barandar waje. Ina juyawa naga mai gadi ce
(security). Tace inje inji doctor. Hankalina ya
tashi kan kace kwabo na fara gumi tamkar ana
gasa ni a garwashi. Ofishin dr lukman kuwa ta
nuna amma ban ga kowa a bakin kofar ba,
kuma har yanzu kofar a rufe. Ni kaina ban san
ayoyin da nake karantawa ba har na isa bakin
kofar, na tura kofar na shiga ina mai jan dan
gajeren hijabina ina rufe rabin fuskata. Ina
sauraron yadda Allahi Zaiyi dani kuma. Nayi
sallama na shiga amma na kasa daga ido in
dube shi. Yaya kika leko kika koma? Wannan
karon kuma wata sabuwar murya naji daban ba
irin ta dazu ba, sai na dago ido da sauro na
dube shi. Dr lukman na gani zaune yana danna
laptop dinsa ba dr shureim imran bane. Sai
mamaki ya rufe ni a zahiti har ya fahimci haka,
na tabbatar son dr shureim yayi min yawa da
har ya fara yi min gizau. Nayi murmushi na
dauka ba ofishin na shigo ba shiyasa na juya.
Na matso na mika masa file din yana dubawa
ya girgiza kai yace me yasa matron zatayi min
haka, ni ba wannan nace ta aiko min ba. To
iyakacin kalmar da na fahinta kenan daga nan
na daina sauraronsa saboda dr shureim imran
na gani ya fito daga bandaki da alama alwala
yayi don jikinsa daruwa. Kallo daya nayi masa
na zazzare ido sai na sunkuyar da kai kasa
yayin da jikina ya hau rawa, zuciyata ta hau
tsalle tana oyoyo ga abincin da na dade ina
yunwarsa. Shine ma dai yayi min kallo sau biyu
ya watsar ya shige lungu ya shimfida abin
sallah. Kafin ya tayar da sallah dr lukman ya
tsokano shi da ci gaba da hirar da suke yi.
Yace wato dr shureim ka tsani ka ga 'yan
acaba kenan? Yayi dariya yace yadda naki
mutuwata haka naki inga mutum ya hau acaba
musamman mace ina takaicin wannan abu, sai
inga ba gara mutum yaje ya kwanta a sibiti ba
yace a zuke jininsa gaba daya a rabawa
marasa lafiya saboda ya mutu, gara yace a
yayyanki duk sassan jikinsa a raba sadakatul
jariya. Dr lukman ya kwashe da dariya har da
buga kafa a kasa. Yace haba dai doctor har
abin ya kai haka? Yace haka ne mana, saboda
yadda zaka ga suna kutsawa a jikin tirela. Na
fada maka fa acaba ne ya kashe san uwa na
uwa daya uba daya, kuma ina tsaye ina kallo
ya kutsa dashi karkashin tirela. Daha cewa dan
acaba kai ni can in siyo batir motarmu ta mutu
a hanya, shikenan ya warce shi sai karkashin
tirela sai gawarsu aka kwakulo. Tun daga
lokacin idan naga mutum akan acaba sai kaga
na bar abun da nakeyi na rike kai, ina taya shi
da addua har sai na daina hangensu.
Musamman mace sai inji kamar in fasa ihu ince
ga motarta nan zo ki hau na tafi da kafa.
Wadanne irin maza ne zasu bar matarsu taje
ta hau acaba, ko bashi da mota ai sai ya bata
kudin drop har inda zata je a mota. Sai a
lokacin na tabbatr da dalilin da yasa yake
hararata rannan ashe, don na sauko daga kan
acaba ne. Ya tayar da sallah, dr lukman ya
miko min file biyu da wanda nazo dashi da
wanda yayi cike cike yace in mayar mata ince
bashi ba, koren file din zata bayar. Na durkusa
na karba na fito da sauri, yayin da zuciyata ta
cika da murna saboda yau taga abinda take
muradi. Sai ya sake burge ni dana ga yana
sallah, naji dadi danaji dalilin hararar da yayi
min rannan ba tsana ta yayi ba. Sai na fara
tunanin hanyar da zanbi in shiga harkarsa ba
tare da yayi min wulkanci ba. Naci sa'a kuwa
ina zuwa nayi mata bayani sai ta miko min
koren file din da yace ta bani in kai masa. Na
taho hanya ina farin ciki hade da fargabar abun
da zanje in tarar. Na isa ofishin sai faduwar
gaban da nake ji ta karu, na fara karanta
ADDUAR WANDA YAJI TSORON MUTANE
"Allahummakfinihim bimaa shi'ita" (Ya Allah Ka
isar mini dasu da abin da kaso). Ina tura kai
sai nayi sallama. Dr lukaman ne ya amsa, har
yanzu gogan nawa yana kan abin sallah ya idar
amma yana jan carbi. Na dago ido na dube shi
a hankali, sai muka hada ido ni dashi, bansan
wanda ya fara kawar da kai gefe ba. Na matsa
lungu ina jiran dr lukman ya gama dubawa sai
da na tabbatar lungun da na shige ko ya daga
ido ba zai ganni ba. Na nutsu kai kace a gaban
sarki nake, yadda nake sanda kai kace da
kayan sata aka kamani, za'a yanke min
hukunci. Wayar dr shuraim imran ce take ruri,
kidan ringing tone din yana tashi a hankali,
wakar soyayya ce ta celen dion mai taken come
bake to me, sai ya danna amsa. Kalmar da ya
fara ambato a cikin harshen turanci ita ta
gigitani, tasa na dimauce sai na tsinci kaina
har da kwalla mai radadin fita saboda kishi.
Daga ji ba sai an fada min ba da matarsa yake
magana, wacce yake tsananin so da kauna fiye
da kowacce 'ya mace a duniya. Tunda nake a
rayuwata ban taba jin namijin bahaushe da ya
fadawa matarsa wannan kalma, ko da yake ni
'yar gargajiyace na tashi cikin 'yan gargajiya
tsakanina da matansu sai ke zo nan, dauko,
dafa, wanke, goge. Kullum sai hantara dube ki
ballagaza, kazama, kwadayayyiya. Haka na
saba ji tun tashina tsakanin miji da matarsa.
Amma dr shuraim imran yace da abar
kaunarsa, salam my dear, my heart, my life
how are you and how is your trip? Hope cool.
Duk da ban jiyo abinda zata fada ba itama da
daddadar kalma ta mayar masa. Ya juye
harshe sai turanci yake zazzagowa ya tambaya
kuna ina yanzu? Sai ta bashi amsa, banji
amsar ba sai yace ok kun bar london yanzu
kuna amsterdam? Awa nawa zaku yi transit
din? Ta fada masa, sai yace karfe goma dai dai
zaku iso kano, ni kuma karfe tara a airport zata
yi min da izinin Ubangiji. Ina kewarki, ina
babyna? Can sai naji ya fara magana cikin
muryar yara yana yiwa yaro wasa, sai na
tabbatar 'yarsa ce itama da turancin yake mata
magana. Kalmar da ya fada ta karshe daga ita
ya kashe waya itace "I love u baby, I miss u
too, I am eager to see ur beautiful face. Take
care bye". Na dinga dauki ba dadi da zuciyata
don so take ta tsinko fado kasa ta ragargaje
don tashin hankalin da ta shiga. Dr lukman ya
dube shi yayi dariya yace madam ce? Ya
lumshe ido tace madam ce ita da baby sun
taho yanzu suna amsterdam sun baro london.
Kaji matar da take makaranta shine ta bar
karatunta ta biyo ni. Dr lukman yace ah da
gaskiyarta, yaushe zata zauna a can mijinta
yana nan? Dr shureim imran yace toh ai
matsalar ba zata iya zaman bane a nan, tana
yin sati biyu a daddafe zata fara magiya inzo
mu koma london, ita ba ta zauna tayi karatunta
ba a can, ita bata bar yarinya tayi karatunta
ba. Dr lukman yace ai da ta dinga barin
yarinyar a gidan iyayenta ba suma a london din
ba gidansu yake? Sai iyayenta su rike muku
'yar kai da ita ku karaci walagiginku tsakanin
london da Nigeria. Dr shureim imran yayi dariya
yace toh ai yarinyar harta fi uwar damuwa ai
ita tace take so uwar tace sai an kawo ta ta
ganni, sai tasa uwar tayi min waya fiye da sau
goma a rana ace min ga baby tana kuka, wai
tana son magana dani. Ina daukar wayar kasan
abinda zata ce min? Daddy I miss you, sai ta
kashe waya shikenan. Su dukka suka kwashe
da dariya, dr lukman yace gaskiya ku canza
tsari, ko kai ka hakura da zaman nigeria ka
koma can ku zauna, daman a can kuka hadu.
Dr shureim imran ya rike baki yace cafdi! Ai ba
zai yiwu ba, ka manta halin babana ai ba zai
bari inyi aiki a can ba, kasan shi da kishin
kasar nan, babu dansa da bai dawo nigeria ba
yanzu. Karatu kadai ya amince muje muyi, aiki
kuwa dole mu dawo mu bautawa kasarmu, mu
taimaki alummar hausa, fulani, musulmai 'yan
uwanmu, bai damu da yawan albashin can ba.
Dr lukman yace haka ka fada min, gaskiya ya
burge ni. Ina ma za'a sami dattijan arewa
irinsa masu kishin YARENSU DA ADDININSU da
kasar nan, da kasar nan ta gyaru. Dr shureinm
yace ai kuwa sanda zanyi aure hana ni yaso yi,
dana dage ina so ni da ita ya shimfida mana
sharudda masu tsauri. Tace taji ta gani zata bi
duk abinda yace. Sharadi na farko da ya
shimfida mana shine dole ta biyo ni nigeria mu
zauna dindindin idan munje london hutu muka
yi da zarar hutu ya kare mu dawo. Sannan dole
ta bar shigar dan siket da wando ta saka
atamfa ko leshi da mayafi don shi ya tsani
english wears. Tace ta yarda yanzu ma zaman
da ya bari tana yi na dan shekaru ne saboda
karatu, ta kusa kare makarantar da zarar ta
kare yace ta hado kayanta kakaf ta kaura kasar
nan, dole anan kasar zatayi aiki ba a can ba.
Tags :
Itama kuma bata iya zaman kasar na, tsoron
sauro takeyi, ko kuda ta gani sai ta hau kuka
ta tashi da gudu. Baby kuwa tana burge ni
babu abinda ba taci, kuma babu in da bata
shiga ta zauna lafiya a kasar nan, bata
damuwa da duk wani canji kuma itama a can
aka haifeta kamar yadda aka haifi uwar a can.
Dr lukman yayi dariya yace ah wannan ita ta
biyo kakanta alhaji, komansu na gargajiya ,
babu zancen cewa ma kai ta biyo, don kai ma
bature ne. Dr shureim imran yace ai kuwa baka
san bature ba, ai ni ko a gidanmu sun san nina
biyo alhaji sak, saboda ko wajen abinci bana
cin su shinkafa, taliya , cake, macaroni da
sauransu. Idan aka ga naci irin wadannan toh
a london nake, ko abj don babu yadda zanyi.
Nifa har kwano nake bawa direbana ya dauka
ya tafi cikin gari unguwar su wani abokina
neman danwake, dambu, ko gurasa mai
kulikuli. Dr lukman ya kwace da dariya yace har
da yawon neman dambu kake sawa ayi? Lallai
dagaske kake. Ni kuma abinda ba'aci kenan a
gidana ko tuwo zasu yi sai dai suyi min
abincina daban, haba ai an wuce wannan
lokacin ina yaro in nadi dambu da tuwo, yanzu
da wayona da 'yan canjina a aljihi inci dambu?
Ko ba haka ba 'yar boko, har yanzu kina cin
dambu? Ya tambayeni, sai nayi sauri na dubi
dodona dr shuriem, domin shi nake tsoro.
Gogan nawa sai yayi dif bai sake magana ba,
yaji an dako dani a zancensu. Jikina ya sake
yin sanyi, nayi murmushi nace bana cin dambu
nima. Dr lukman yace yawwa ashe bani kadai
ne na gaji da cin tuwo ba, muna da yawa.
Daga lokacin hirar ya koma ni da dr lukman
kadai, dr shureim yaki tsoma baki. Dr lukman
yace dani ke 'yar gidan matron maryam ce,
naga kuna kama? Wannan karon ne ma naga
dr shureim ya dubeni kasa kasa, sai yayi wuf
ya mike tsaye yana nade abin sallah, ya linke
ya ajiye sannan ya shiga daura neck tie a
wuya, ya saka bakar suit dinsa. Cikin sanyi jiki
nace a'a ni ba 'yarta bace, malamata ce kawai,
muna shiri sosai. Dr lukman yaci gaba da
rubutu yana magana yace ke ba 'yar gezawa
bace kenan. Tunda matron maryam 'yar
gezawa ce. Nayi dariya nace a'a ni ba 'yar
kano nace ba ma, ni 'yar shagamu ce. Sai ya
tsaya da rubutun ya dube ni ta cikin gilashinsa
yace da gaske kike, ko kanwar yahaya umar
ce? Babban abokina ne, ajinmu daya a
sakandiren da muka yi a yobe. Sai nayi caraf
nace yayana ne, babanmu daya. Sai ya fasa
rubutun ya ajiye biro yace yanzu dan Allah
yahaya umar yayanki ne? Na gyada kai nace
yayana ne. Yace llallai kuwa naga kama, kina
cewa ke 'yar shagamu ce sai naga fuskarku iri
daya daman tun sanda na fara ganinki na rasa
wanda kika min kama. Yana ina yanzu? Yana
nan lagos yana aiki a tasha dan union ne. Yace
subhanallah! Yanzu duk kokarin nan na yahaya
umar bai cigaba da karatu ba a aikin tasha ya
kare? Kinsan fa ni dashi muka kudiri niyyar sai
munyi karatun likita. Tunda muka gama
makaranta a. Yobe na dai ganinsa, naje
gidansu a nan yobe nemansa ban same shi ba
aka ce ya koma garin babansu shagamu, ashe
dangin mahaifiyarsa ne a yobe ko? Shikenan
rabuwarmu dashi, sai dai duk sanda aka
ambaci shagamu sai na tuno shi, saboda dan
shagamu muke ce masa. Mun shaku sosai
dakinmu daya, ajinmu daya. Nayi murmushi
nace eh dangin mahaifiyarsa ne suka rike shi a
yobe, tun yana yaro, daya gama sakandire sai
ya koma gida shagamu, bai cigaba da karatu
ba kuma. Ina rufe bakin dr shureim ya shirya
tsafa, ya dauki jakar laptop dinsa ya dubi
abokinsa dr lukman. Yace ni na tafi sai kuma
gobe. Dr lukman yace aini ma na tashi, ka jira
ni yarinyar nan zan sallama kawai, ka ga ashe
ma ni kanwata ce, haba tun sanda nake
ganinta nake ganin kamar na san fuskar, ashe
kanwar abokina ne childhood frnd yahaya umar.
Ya tabe baki yace a'a ni dai nayi gaba, sai ka
taho kawai. Ya fice ya bar mu. Bai ma bada
amsar labarin da ya bashi ba saboda a kaina
ne ba zai tsoma baki ba, sai na fara dankarawa
zuciyata zagi akan ko taki ko taso sai ta rabu
da son wannan marar mutuncin. Me yayi zafi?
Dan kawai Allah yayi masa baiwa kala kala,
yayi masa farin jini, ana sonsa sai ya dinga
wulakanci, shi waye? Namiji ne fa kamar
kowanne namiji, gasu nan birjik a titi suna bin
mace tana musu yanga kafin ma ta kula su.
Suna 'yar murya suna yi mata wahala, don ta
saurare su. Haka na dinga kushe shi a zuciyata
don in samu sukuni, duk yadda zanbi in raba
zuciyata da sonsa bi nake yi don shine samun
saukina. Dr lukman ya rufe file ya bani,
tambayi lambar wayar abokinsa yayana yahaya.
Nace bani da waya, amma zan karbo masa
lambar a wajen yayana hussaini gobe zan kawo
masa. Sai yayi mamaki don nace bani da waya,
sai ya tambaye ni, yace faduwa wayar taki tayi
ne? Kuma baki hadda ce lambarsa ba? Na
amsa da eh faduwa tayi. Saboda sauri nake in
fice daga ofishin saboda abin kaunata baya
nan, daman saboda shi naji tsayuwar da nake
yi bata isheni ba tun dazu, yana barin ofishin
sai naji duk ofis din ya gindure ni. So nake in
fito inga in daya nufa, kuma da wacce irin mota
yazo yau. Nayi wa dr lukman sallama na fito
bakin barandar da sauri, na waiga kowacce
kusurwa sai ban ganshi ba, ko alamunsa babu,
sai naji haushin dr lukman ya rufe ni, da bai
bari na fito da wuri ba, gashi nan har ya tafi.
Sai zuciyata tace ke da kike yi min fada in rabu
dashi, ina ke ina takaicin don baki gan shi ba?
Nayi ajiyar zuciya mai karfi naci gaba da tafiya
maimakon inbi doguwar baranda sai na sauko
na dinga kutsawa ta kasa cikin motoci. Ban sa
ran ganinsa ba ko kadan amma dai nasan dole
ta nan ya bi, idan zai dauki motarsa ko sawun
takalmansa na taka ai naji sa'ida a raina.
Kamar daga sama naji wata murya mai shige
da tasa daga gefena, abin da yake fada kuwa
shine "wait, wait dr hidaya, na fada miki na
sake fada miki don Allah ki daina damuna da
waya cikin dare, yau matata zata zo kasar na,
bana so ki jawo mana matsala. Aiki ne ya hada
mu anan idan an tashi daga aiki to ban sanki
ba kowa ya kama gabansa. Wanne irin abu ne
haka, ina zan saka raina? A asibiti a dame ni
har gida ma kun fara bina? Yaya akayi kika
nemo gidanmu har kika ba mai gadinmu sako
ya bani? A wanne dalile zakiyi min sayayya ki
kai min gida? Zaki jefa rayuwata cikin damuwa
tsakanina da matata, da kuma iyayena. Na
dinga tafiya a hankali ina kallonsu, a tsaye suke
a jikin motarsa har ya bude mota zai shiga sai
ta tsayar dashi. Ransa a bace yake magana
cikin matsanancin fushi, sai ita ma ta fusata ta
magana cikin kuka da fada. Dr shureim in har
ni 'yar halak ce a cikin uwata da ubana na
kyale ka, har abada ba zan sake nemanka ba.
Ya fada cike da gadara yace shi yafi sauki, naji
dadi sosai kuwa. Ta juya a fusace tana sharce
hawaye, yayin da farin gilashin idonta ya fado
kasa, ido daya ya fita. Na karaso da sauri na
dauko mata na mika mata, sai ta dube ni
jajayen idanuwanta ta karba gami da ce min
thank u very much. Ta wuce da sauri. Dr
shureim ya dube ni, ya sake bude ido ya kalle
ni sosai, na tsaya cak kamar yadda yake tsaye
kyam yana dubana. Na harare shi sama da
kasa naja dogon tsaki na kada kai na wuce na
bar shi nan a tsaye bai daina kallona ba, ni dai
ban waiwaya ba. Na san ya cika da mamakina,
ni dai burina ya cika tunda na fara ramawa
kaina wulakacin da yayi min da sauran
wahallalun mata da 'yan uwana masu sonsa.
Na kudiri aniyar kallon arziki ya daina hada mu
sabida na san ba zan same shi ba kamar
sauran da suka fini haduwa, ga kyau basu
same shi ba. Kamar daga sama naji wata
murya mai shige da tasa daga gefena, abin da
yake fada kuwa shine "wait, wait dr hidaya, na
fada miki na sake fada miki don Allah ki daina
damuna da waya cikin dare, yau matata zata
zo kasar na, bana so ki jawo mana matsala.
Aiki ne ya hada mu anan idan an tashi daga
aiki to ban sanki ba kowa ya kama gabansa.
Wanne irin abu ne haka, ina zan saka raina? A
asibiti a dame ni har gida ma kun fara bina?
Yaya akayi kika nemo gidanmu har kika ba mai
gadinmu sako ya bani? A wanne dalile zakiyi
min sayayya ki kai min gida? Zaki jefa
rayuwata cikin damuwa tsakanina da matata,
da kuma iyayena. Na dinga tafiya a hankali ina
kallonsu, a tsaye suke a jikin motarsa har ya
bude mota zai shiga sai ta tsayar dashi. Ransa
a bace yake magana cikin matsanancin fushi,
sai ita ma ta fusata ta magana cikin kuka da
fada. Dr shureim in har ni 'yar halak ce a cikin
uwata da ubana na kyale ka, har abada ba zan
sake nemanka ba. Ya fada cike da gadara yace
shi yafi sauki, naji dadi sosai kuwa. Ta juya a
fusace tana sharce hawaye, yayin da farin
gilashin idonta ya fado kasa, ido daya ya fita.
Na karaso da sauri na dauko mata na mika
mata, sai ta dube ni jajayen idanuwanta ta
karba gami da ce min thank u very much. Ta
wuce da sauri. Dr shureim ya dube ni, ya sake
bude ido ya kalle ni sosai, na tsaya cak kamar
yadda yake tsaye kyam yana dubana. Na
harare shi sama da kasa naja dogon tsaki na
kada kai na wuce na bar shi nan a tsaye bai
daina kallona ba, ni dai ban waiwaya ba. Na
san ya cika da mamakina, ni dai burina ya cika
tunda na fara ramawa kaina wulakacin da yayi
min da sauran wahallalun mata da 'yan uwana
masu sonsa. Na kudiri aniyar kallon arziki ya
daina hada mu sabida na san ba zan same shi
ba kamar sauran da suka fini haduwa, ga kyau
basu same shi ba. Da na koma gida, dare yayi
sai bacci ya gagare ni, na shifa zulumi da
fargabar kallon da nyi masa. Naji kwata kwata
ban kyauta ba, tausayinsa ya rufe ni, yayin da
sabon sonsa ya tsatsafo daga cikin zuciyata.
Na dora hannu aka ina fadinn na kashe kaina
da kaina, me ya kaini yi masa wulakanci ni da
nake addua, ina saka ran zan same shi
watarana? Na shiga adduar Allah Ya sa baiji
haushina ba. Gari na wayewa na shiga
shiryawa, na tsaya na tsarawa fusakata
kwalliya yadda zanyi kyau sosai. Nayi sauri na
tare yaya hussaini zai fita aiki, nace ya bani
lambar yaya yahaya wani abokinsa likita ne ta
ke nema. Naci sa'a ya rubuta min akan wata
'yar takarda anan take ya miko min, ko karya
kumallo ban tsaya na yi ba, na fice. Allah cikin
ikonSa ina sauke kafata daya daga kan acaba
ko dayar ban sauke ba a bakin gate din asibiti,
sai ga dr shurim ya karyo zai shiga gate. Ya
galla min harara sannan ya figi motarsa ya
wuce, sai naji dariya ta subuce min, nasan
dalilin hararar da yake min bai wuce don na
hau acaba ba, ni kuwa ko a jikina. Acaba kuwa
yanzu na fara hawa tunda ya tsani yaga mace
akan acaba. Idan baya so mu hau sai ya saya
mana motar hawa ni da 'yanuwana mata masu
hawa acaba. Sai na tsinci kaina ina tafe ina
farin ciki, ko babu komai dai yanzu ya fara
sanina, hararar dana samu ma naji dadi, nafi
wadanda bai san suna raye ba. Kai tsaye
ofishinsu na bishi, kafin in isa har ya kai cikin
ofis. Ina murda kofa sai ta wangale sai gani
kicibus gabansa, bai amsa sallamata ba sosai a
ciki ciki ya amsa kamar baya so, kallo daya
yayi min ya dauke kai yaci gaba da dube duben
littafin da yake kan teburinsa , yana tsaye. Na
gaishe shi yayi kamar baiji ba, na fada cike da
gatsali dr lukman nake nema. Ya fada cike da
takaici, kuma aka ce miki nan ne ofishinsa ko?
Na fada cikin tsiwa eh a nan na ganshi jiya shi
yasa yau nazo nan nemansa. Sai ya dago da
sauri ya dubeni cike da mamaki. Can ya dukar
da idonsa kasa, yaci gaba da dube dubensa, bai
bani amsa ba. Na rike kugu nace ga sakonsa
dan Allah ko zaka ajiye masa? Ya sake dagowa
a fusace ya fada cikin fushi, ke an fada miki
nan ba ofishinsa bane, kije ki tambayi inda ofis
dinsa yake. Ko nayi miki kama da wanda zaki
bawa sako? Na murguda baki nace saboda nan
matron maryam tace min inzo in same shi jiya
shiyasa yau ma nazo. Na juya a fusace na fice
na ki rufo masa kofar sosai. Sai naga ya biyo
bayana, ya dade a tsaye yana kallona ina tafiya
har na fice daga harabar, na barshi zuciyarsa
cike da takaici. Na fara samun sa'ida a
zuciyata tunda na fara samun damar yin
magana dashi, duk da ba maganar arziki bace.
Dana dawo ofishin da rana, sai na sami dr
lukman a ofishin dr shureim baya nan. Mun
dade muna hira da abokin yayana, naki tafiya
da wuri ina saka ran ko zai dawo sai bai dawo
ba, takaici ya isheni. Na koma gida cike da
tunaninsa da sonsa zokar a cikin zuciyata, ko
rufe idona nayi suffarsa ce ke fado min. Ina
matukar son abinda ba zan samu ba, sai inyi
kuka inyi dariya ni kadai bana mantawa da
addua, ina neman agaji daga wurin Ubangijina.
Nafi adduar Allah Ya yaye min sonsa akan
adduar Allah Ya karkato da tunaninsa kaina,
saboda a ganina shi zaifi yi min sauki duk da
babu abinda ya gagari Allah. Sai inyi ta
shawagina cikin asibiti a satin nan ko Allah zai
sake hada ni da dr shureim, ban ganshi ba ko a
hanya, ni kuma bana so inje ofishinsu saboda
zai gane akwai wani abu a zuciyata. DUK KYAN
TAKALMI 9 Sai dai kash! Na rabu da karatuna
har 'yan ajinmu sun gane hankalina baya kan
abinda ake koya mana, ban ma cika tsayawa a
wajensu ba, bini bini a neme ni a rasa. Nima na
rasa kaina, duk likitan da naga ya wuce da
bakar suit sai na bishi da kallo in zata abin
kaunata ne, sai inga ashe bashi bane, raina
yayi ta baci. Matron maryam ta lura da haka
sai tayi ta tambayata, amsar dai ita ce babu
komai, idan aka dame ni ince bana jin dadin
jikina. Haka ma dai a gida amsar iri daya ce,
data makaranta ga duk wanda ya dame ni da
tambaya. Na zama tababbiya a cikin satin nan
da ban ganshi ba. Addua nake Allah Ya yaye
min amma tamkar sonsa karuwa yake a
zauciya, ban taba sanin haka dacin soyayya
yake ba a rayuwata ko a film da littafi ban taba
ganin irin abin da ya faru dani ba. Haka kawai
na fara son mutumin da bai san inayi ba.
Shiyasa a rayuwa ba a so ka cika baki akan
abu, muddin ka cika baki akan wani abu
tabbas abun nan sai kaga ya same ka. Bazan
manta ba shekaru hudu da suka wuce akwai
wata kawata ummi, ajinmu daya a shekara.
Allah Ya jarrabe ta da son wani malamin mu
mai suna abdul yasar, shima danji da kaine
kamar dr shureim. Duk sanda taje wajensa sai
yayi mata wulakanci ita kuma tazo tana kuka
tana fada min, takaici ya kama ni maimakon in
bata hakuri sai inyi ta zaginta, ina Allah wadari
da halinta. Kullum sai ince mata me akayi aka
yi da namiji? Har zata je yana wulakanta ta,
duk a cikin samarinta ma babu kassararre,
talaka, bakauye ma irinsa, duk sunfi shi
haduwa ta rabu dashi mana. Sai tace min ita
dai shi take so bata son sauran. Kuma taci
gaba da nace masa tanayi masa wahala bayan
mun gama makaranta daga karshe ya aureta.
Ranan wata asabar da hantsi na shirya naci
ado da wata atamfata shudiya, tunda ranar
babu makaranta saina zankadawa yayana da
matarsa karya nace a asibiti ake nemanmu
zamu yiwa yara allurar rigakafi, yayana ya zaro
kudin acaba naira dari biyu kamar yadda ya
saba bani kullum. Na nufi gidan ummi domin
inji hanyar da ta bi ta samu mai gidanta abar
kaunarta abdul yasar. A kofar nasarawa
gidanta yake duk da na dade banje gidan ba,
amma naci sa'a na gane, rabona da gidan tun
ranar da muka kai ta, haka da ta haihu ma a
gidansu muka same ta muka yi mata barka,
'yar unguwar zango ce. Cike da fargaba na
shiga gidan don kada ace min bata nan inyia
asarar kudin babur din da na kashe nazo, ga na
komawa gida. Sai naci karo da maigidanta a
zauren gidan. Nayi sauri na duka na gaishe da
malamina, ya amsa a gaggauce ko kallon kirki
baiyi min ba, da alama dama ya tsane ni.
Nasan dadin soyayya yasa ummi ta zazzage
masa shawarwarin da na sha bata cewar ta
rabu dashi bakauye ne, bai hadu ba. Babu
wanda ya fada min haka, na lura tun a lokacin
bikin yana kula sauran kawayenmu nice kada
baya son yiwa magana. Na wuce cikin gidan
sadan sadan don banga fuskar da zan tambaye
shi tana nan ko bata nan ba. A tsakar gida na
ganta ta buga tagumi da alama akwai damuwa
a tattare da ita. Tana ganina sai ta mike da
sauri ta rungume ni, na dauka dariya takeyi, sai
naga hawaye. Na cika taf! Na tumbatsa da
mamaki na rike ta ina tambayarta ko lafiya?
Taja ni zuwa cikin dakinta muka zauna a gfen
gado tana magana cikin kuka. Tace aisha farida
wulakancin da yassar yake min ya isheni, don
kawai yaga bazan iya rabuwa dashi bane. Nayo
shiru na kasa magana, yayin da na shiga
hankalina na fasa tambayar abin da nazo
tambaya. Ashe har yanzu da sauran rina a
kaba, ko a yanzu na auri dr shureim ashe idan
naje gidan ma wulakanci yana nan zokar.
Zuciyata ta fara yimin fada tana cewa farida ki
yi ta kanki, ki cire son dr shureim imran idan ba
kin zabi ciwon zuciya ya zama ajalinki ba. Na
tambaya cikin sanyin jiki wai ke ummi yaya aka
yi ma tun farko ya amince ya aureki bayan
baya sonki? Tace ashe ba dake muka je ba, da
maijidda lawan mukaje wajen wani malami a
kurna. Sai na dafe kirji na fada a gigice, na
shiga uku ummi! Malami kuma? Ta gyada kai
tace shine yayi min aiki yace dole sai yasar ya
zo ya aure ni ko ba a hayyacinsa ba. Kuma
yazo din ya aure ni, har nake juya shi yadda
nake so, sai bayan da na haihu ban koma ba.
Kinsan ance idan mace ta haihu duk wani sihiri
da tsarin da yake jikinta karyewa yake yi, sai
tayi sabon shiri. Kuma kin san halin malaman
zamanin nan sunfi so ka dauwama kana zuwa
wajensu kana kai musu abin da ka kwakwala
daga wajen mazan, idan ka dauke kafa bayan
bukata ta biya sai su karya maka aikin, komai
sai ya cakude dole sai ka dawo. Sannan yanzu
bani da waya, bama magana dashi ta waya,
daya fada min irin sadakar da zanyi dan duk
ranar laraba yanayi min waya yace nayi
sadakar sukari ko nono na aljanar da take kula
da soyayyar da yasar yake min, kinga na dade
banyi sadakar ba. Hankalina ya tashi, abin da
nake gani a film yazo har gida. Nace ummi
tsafi kenan fa? Tace haba dai tsafi, babban
malami ne fa ya iya jan aya, baki ga matan
manya da masu kudin garin da suke layi a
gidansa ba, talakawa irina kadan ne. Ya iya
aiki fa. Zuciyata ta fara rabuwa gida biyu, inje
ko kar inje? Amma fa jikina bari yake yi, naji
tana ambaton aljana a cikin al'amuran. Daga
karshe zuciyata ta yanke min, kawai inje ni ma
ayi min asirin da dole zaizo ya so ni ko da
daga baya asirin ya karye ai dai naci riba tunda
bani da buri a rayuwata irin in ga na same shi
yayi min magana ma kawai, balle ace yazi
gidanmu har anyi maganar aure dashi, ya aure
ni na tare gidansa, ai ba karamar riba bace a
rayuwata. Kuma idan haka ne in anyi auren ai
sai in ringa komawa wajen malamin ina kara
masa kudi yana cigaba da sona, yana fada min
abinda zan bayar sadaka ina yin sadakar yadda
son ba zai tafi daga zuciyarsa ba. Tunda kafin
lokacin bikin na gama makaranta na fara aiki,
ko da albashina na dinga biyan malam ko bai
bani kudinsa ba. Sai na gyara zama nace ummi
nima fa matsalar da take tafe dani kenan, nima
irin naki ne ta same ni. Allah ya jarrabe ni da
son wani likita a asibitin da nake attachment,
amma fa likitan yafi ni haduwa nesa ba kusa
ba, gashi daji da kai da wulakanci, har yafi
malam yasar dinki. Na rasa yadda za'ayi ya
saurareni ma balle ayi zancen soyayya. Baki ga
yadda hadaddun likitoci mata suke binsa ba
yaki sauraronsu. Kawayena biyu suke yi masa
asiri dan ya sosu amma bai kama shi ba, ina
jin ya shirya kansa asiri baya cinsa. Wani
babban tashin hankali ma yana da mata ina jin
ma baturiya ce a london suka hadu sukayi
aure, ita ma yanaji da ita, nasan ta fini kyau
nesa ba kusa ba. Ya zanyi? Ummi ta daki
kafada ta tace ke dalla wawuya daman ke irin
wannan mutumin kika samu amma zaki bari ya
subuce miki? Lallai kin cika wawuya baki da
wayo. Ai kawai kije a zuba miki aiki tuntuni
zaiji ya tsani baturiya ya biyo ki, balle mai kudi
ne, kina shiga zaki fanshe kudafen da kika
kashe a kansa. Na girgiza kai nace babu
ruwana da taba matarsa, suyi zamansu ni dai
yaso ni kawai, tunda ina sonsa. Idan kuma
akwai abin da malamin zai yi min na daina
sonsa ni nafi son haka, saboda nayi iyakacin
adduar da zanyi don na daina jin sonsa na
kasa dainawa kullum karuwa yake ma. Ummi
tace yaya za'ayi kice a cire miki sonsa ai
shirme kenan. Ace yaji abin da kike ji koma
ince fiye da yadda kike ji don an fi son namiji
yafi na mace sai afi zama lafiya. Ke ban da
abinki wata budurwar ba irin wannan take
nema ba ma ta kai shi wajen malami a rike
mata sai ko ta wanne hali, ko ba komai ai ka
tsira da kudi ko babu soyayyar. Na girgiza kai
nace ai ni ba kudinsa nake so ba, shi nake so.
Ni na yadda ya so ni kada ma yabani kudinsa,
na yarda idan na fara aiki in ciyar da kaina ba
sai ya ciyar dani ba. Ummi ta rike baki tace
Aisha farida haka kike sonsa kamar ki cinye
shi? To ko asiri yayi miki irin wannan son dai
bana lafiya bane. Na girgiza kai nace ko kadan,
Allah ne yayi masa baiwar kyau, ilimi, arziki, da
jan aji dole mata suke sonsa. Shi kansa baya
son haka. Bai ma san inayi ba balle ace shi ma
yana sona har yaje yayi min asiri. Jarraba ce
kawai ta afka min, nima ba don ina so ba, haka
Allah ya tsaro min. Sai na fashe da kuka. Ta
rungume ni tace taso muje in kai wajensa
yanzu, nima daman ina shawarar zuwa yau ko
gobe, al'amarina ya cabe ni da yassar. Na mike
tsaye ina goge hawayena yayin da ita kuma ta
canja kayan jikinta ta saka wata jar atamfa
riga da zani ta goya 'yarta da take barci akan
gado, muka fito ta kullo dakin. Ta leka tayi wa
matar kanin mijinta sallama wacce katanga ce
kadai ta rabu tace da ita zamuje bakin asibiti
zata raka ni inyi sare sare. Muka fito muka
kama hanya tun a hanya na sanar mata ko
kudin mota bani dashi, tace babu komai zata
biya min, gakudin cefanenta nan yau ko
cefanen ma bazatayi ba. Ce masa zatayi dan
aiken ya zubar da markade. Ta juyo ta dube ni
tace to ke yanzu da baki da kudi yaya za'ayi
miki aiki? Dole fa sai kin kashe kudi idan kina
son aiki yace. Tafiya mai nisan gaske mukayi a
motar bus mai zuwa kurna, sai da muka hau
acaba muka niki tafiyar kafa saboda babur ma
ba zai iya shiga lokon ba, wahala iri iri muka
sha kafin muka isa gidan. Nace muje dai muji,
na san yadda zanyi. Sai na fashe da kuka. Ta
rungume ni tace taso muje in kai wajensa
yanzu, nima daman ina shawarar zuwa yau ko
gobe, al'amarina ya cabe ni da yassar. Na mike
tsaye ina goge hawayena yayin da ita kuma ta
canja kayan jikinta ta saka wata jar atamfa
riga da zani ta goya 'yarta da take barci akan
gado, muka fito ta kullo dakin. Ta leka tayi wa
matar kanin mijinta sallama wacce katanga ce
kadai ta rabu tace da ita zamuje bakin asibiti
zata raka ni inyi sare sare. Muka fito muka
kama hanya tun a hanya na sanar mata ko
kudin mota bani dashi, tace babu komai zata
biya min, gakudin cefanenta nan yau ko
cefanen ma bazatayi ba. Ce masa zatayi dan
aiken ya zubar da markade. Ta juyo ta dube ni
tace to ke yanzu da baki da kudi yaya za'ayi
miki aiki? Dole fa sai kin kashe kudi idan kina
son aiki yace. Tafiya mai nisan gaske mukayi a
motar bus mai zuwa kurna, sai da muka hau
acaba muka niki tafiyar kafa saboda babur ma
ba zai iya shiga lokon ba, wahala iri iri muka
sha kafin muka isa gidan. Nace muje dai muji,
na san yadda zanyi. Munci sa'a babu layi
sosai, mun tarar da maza uku a kofar gida,
mata biyu a cikin gida. Muka gaishe su muka
bi layi. Gabana sai faduwa yake tamkar
zuciyata zata fito sarari, sai in zunguri ummi
ince na fasa ta tashi mu tafi. Sai ta mintsine ni
tace ba inda zamu je sai mun shiga. Na daure
har layi yazo kanmu, muka shiga ciki. Daga
sanda naga kasar duba da dogon carbi sai na
tabbatar na kauce hanya, domin nasan
makomar masu bin 'yan tsubbu masu duba, in
har kaje wajen mai duba ya fada maka gaibu
ka yarda dashi, to baka da sallah har tsawon
kwanaki arbain. Allah ba zai karba ba. Ya san
ummi sosai, ya san matsalolinta don haka sai
ya hau mata bayani. Tace malam a bincika min
dai. Sai ya jawo farantin kasa yayi zane
zanensa ya hau yi mata bayanai kamar wanda
ke karantawa. Na dubi kasar naga babu rubutu
babu alamarsa na rasa inda yake karanto
wadannan labarai, sannan na dubi sama da
kasa banji motsin wanda yake fada masa ba.
Yace ummi wannan tsohuwar budurwar nan
tasa da yake so itace take raba ku, ta tashi
tsaye tana asiri sai ta fitar dake ta shiga gidan,
sannan faccalatki matan kanin mijinki da kuke
gida daya, itama tana saka miki hannu saboda
mijinki ya fi nata zuciyar nema, kin fi ta
hutawa, don haka take so ta raba ku.
Tags :
Ummi ta fusata ta hau bayani. Lallai biri yayi
kama da mutum, domin tun sanda mijina ya
siyo mana generator sai ta yini a daki baata
fito tsakar gida ba, haka ma zance tsohuwar
budurwarsa ba su rabu ba suna tare har yanzu,
naga sakonta a wayarsa. Yanzu malam yaya
za'ayi? Sai naga ya karkace ya zayyano mata
abubuwa kamar su turarruka na wuridi, kaji,
dan akuya ja, farin kyalle da kudin yaran
dazasu zauna aiki, dubu ashirin da biyar. Ko ta
nuna damuwa ma batayi ba sai kawai ta ce
gobe zan kawo dubu goma sha biyar a fara,
don Allah malam ka ragargaza min su kamar
yadda suke son su raba ni da mijina suma a
rabasu da mazansu, ni kuma mu zauna daram
ina so a kama min shi don wulakanci yake yi
min kwanan nan har da cewa bai san inda yake
kallo ba ya aure ni, don ni ba irin tsarin
rayuwarsa bace. Sakacinki ne inji malam. Ya
juyo ya dube ni sai na takure a lungu kirjina
yana dukan ukuk uku. Yace ke fa meye
matsalarki, ko baki fada ba zan iya ganin
asiran da akayi miki a jikinki, ki tashi tsaye
wajen neman tsari. Ummi ta kwanto da 'yarta
daga bayanta ta gyara zama tace malam, aisha
farida kawata ce, a taimaka mata. Matsalarmu
kusan iri daya ce, ayi mata bincike tukunnan.
Ta bukaci ina saka abin sadaka kafin ya fara,
sai ummi ta zaro dari biyu zata mika masa na
rike hannunta nace ba sai an bincika min ba
malam zan fada da bakina. Na koro masa
bayani tas, sai yayi dariya ya kyakyata yace
wannan karamin aiki ne a wajena, idan har zaki
sayi kayan aiki na baki kwana biyu inda dr
shureim imran ne kim gama samunsa. Ina jin
haka sai naji farin ciki ya lullube ni nayi dariya,
na tambaye shi me dame za a siya? Sai yayi
min zancen abubuwa daban daban, wasu na
sansu wasu ban sansu ba. Aka hada kudin ya
kama naira dubu ashirin da daya. Sai na dafe
kirji nace malam bani da kudi ko zaka yi min
bashi idan komai ya kankama sai in biya? Ya
dubi ummi cike da bacin rai yace ina kika samo
min wannan yarinyar? Baki fada mata dokar
aikina bane? Sabon shiga ce ko? Toh ni bana
fadar farashi a nemi ragi balle ace inyi a bashi,
a cikin kudin nan babu sisi nawa, duk na
rauhanai ne. Ummi tace ayi hakuri malam,
laifina ne ban fada mata dokokinka ba zamu
dawo gobe tare zamu nemo kudin mu kawo.
Mun goda. Banyi godiya ba na kada kai na fito,
hankalina ya gama tashi. Muna fita kofar gida
ummi ta hau yi min fada tana cewa me yasa
ban bari anyi min bincike ba inji bayani dalla
dalla ba, sannan me yasa nace ayi min aiki
bashi alhali tun a kan hanya na baki labarinsa?
Nace to bani da kudi ko naira hamsin ta kaina
bani da ita. Me zance? Tace ki sayar da
kadararki mana. Nace ai bani da ko barimar
gwal balle dan kunne. Ta tabe baki tace ni dai
shawarar da zan baki itace kije kisan abinyi
don nima nan da kika ganni bashi zanje in ciyo
in kai masa idan aiki yaci da kansa zai baki
kudi kije ki biya. Malamin nan fa aikinsa kamar
yankan wuka, sha yanzu magani yanzu. Kije
kiyi tunani zuwa gobe ki samo kudi, kizo mu
kai don ni ma daga nan gari zan shiga neman
bashi. Ta bani kudin mota mukayi sallama na
shiga motar unguwarmu, ita kuma ta shiga
motar dawanau ban san inda ta nufa ba. Ina
zaune a mota tamkar gunki ina tunani, sai da
kondasta yyayi ta magana sannan na gane dani
yake, na mika masa kudin mota. Haka da aka
zo inda zan sauka ma na manta har aka wuce
dani, sannan na ankara nace a sauke ni. Saida
na dawo baya. Na shiga gida a cakude, narasa
inda zan saka raina, tunanina gaba daya ya
koma wajen inda zan samo rancen kudi in
kaiwa malam gobe. Cikin unguwar nan da
batsewarta babu matar da zata iya fitar da
dubu biyar ma kai tsaye saboda talauci. Da
yamma na shirya na fita neman kudi gida gida,
da kyar na hado rancen dubu biyu. Na zarce
kai tsaye shagon da musbahu yake sana'a. Sai
yayi matukar mamakin ganina ya tambayeni
lafiya ya ganni a hargitse haka? Na fada masa
cewar matsalar kudi ce ta taso min, bani da
lafiya. 'Yar karamar tiyata za ayi min gobe a
asibitin ana neman naira dubu ashirin. Sai ya
dafe kirji yace aisha farida babu inda zan sami
dubu ashirin a yau. Ai ko bashi babu in da zan
samu. Ko idan anyi wa likitan bayani zai yarda
yayi miki aiki a bashi karshen wata sai in biya
shi. Na girgiza kai nace babu zance bashi
kuma dole in hada kudin daga yau zuwa dare.
Yace to inje gida zai aiko yaro ya kawo min
abin da ya sauwaka. Zaije ya fita ya nemo
abinda ya samo. Nayi godiya na tafi. Ko awa
guda banyi ba da shiga gida sai ga dan aike da
dubu uku har da doguwar wasika yana mai
bani hakuri abin da ya samo kenan. Amaa zaici
gaba da nemowa zuwa gobe. Ya jero min
kalaman soyayya ko gama karantawa banyi ba
na yayyaga na zubar, burina in hada kudin nan
in kai. Ina zaune a mota tamkar gunki ina
tunani, sai da kondasta yyayi ta magana
sannan na gane dani yake, na mika masa kudin
mota. Haka da aka zo inda zan sauka ma na
manta har aka wuce dani, sannan na ankara
nace a sauke ni. Saida na dawo baya. Na shiga
gida a cakude, narasa inda zan saka raina,
tunanina gaba daya ya koma wajen inda zan
samo rancen kudi in kaiwa malam gobe. Cikin
unguwar nan da batsewarta babu matar da
zata iya fitar da dubu biyar ma kai tsaye
saboda talauci. Da yamma na shirya na fita
neman kudi gida gida, da kyar na hado rancen
dubu biyu. Na zarce kai tsaye shagon da
musbahu yake sana'a. Sai yayi matukar
mamakin ganina ya tambayeni lafiya ya ganni
a hargitse haka? Na fada masa cewar matsalar
kudi ce ta taso min, bani da lafiya. 'Yar
karamar tiyata za ayi min gobe a asibitin ana
neman naira dubu ashirin. Sai ya dafe kirji yace
aisha farida babu inda zan sami dubu ashirin a
yau. Ai ko bashi babu in da zan samu. Ko idan
anyi wa likitan bayani zai yarda yayi miki aiki a
bashi karshen wata sai in biya shi. Na girgiza
kai nace babu zance bashi kuma dole in hada
kudin daga yau zuwa dare. Yace to inje gida
zai aiko yaro ya kawo min abin da ya
sauwaka. Zaije ya fita ya nemo abinda ya
samo. Nayi godiya na tafi. Ko awa guda banyi
ba da shiga gida sai ga dan aike da dubu uku
har da doguwar wasika yana mai bani hakuri
abin da ya samo kenan. Amaa zaici gaba da
nemowa zuwa gobe. Ya jero min kalaman
soyayya ko gama karantawa banyi ba na
yayyaga na zubar, burina in hada kudin nan in
kai. Uwani uwar adashe ita kadai na tabbatr
zan iya samun rancen kudi a wajenta ko nawa
ne saboda itace naga koda yaushe mata suna
aiko mata da zubin kudin adashe, ina hango
shigarsu da fitarsu daga windon dakina domin
dakinta na kusa da dakina. Ina idar da sallar
magriba na tabbatar abida tana daki tana
wuridi ba zata fito tsakar gida ba, sai tayi
sallar ishai kamar yadda ta saba. Sai nayi
sanda na fito dakina na fada dakin uwani, sai
tayi mamakin ganina a wannan lokaci, naci
sa'a maigidanta bai dawo ba. Ta saka fitilar
kwai a gaba tana kirga kudi kashi kashi. Farin
ciki ya rufe ni da naga kudin nan sai na shiga
marairaice mata inayi mata dadin baki cewar
ta ranta min dubu goma sha bakwai zan biya
ta gobe da yamma. Ta tsorata matuka har da
dafe kirji ta tambaye ni, me zakiyi da kudi
haka? Na shaida mata kawata ce zata haihu a
asibitinmu ance ba zata iya haihuwa da kanta
ba sai an yi mata tiyata. Ga mijinta ba ya gari
yana lagos. Amma ya sako kudin ta banki, to
kasancewar asabar ce babu banki, lahadi ma
babu aiki ba za a iya fitar da kudin ba, sai
ranar litinin. Shine tace in ranto mata zuwa
litinin zata biya. Uwani tace a'a aisha farida
kinsan halin mutane kayi musu rana suyi ma
mutum dare. Ki zo ki taimake su suki biya, ko
kuma ni in taimake ki, kiki taimakona. Kinsan
dai kudin nan da kika gani kudin cizo ne, bana
kashewa bane da masu shi. Gobe haj rabi ce
zata dauki adashen nan dubu talatin. Mace
dayace bilki bata saka mata ba, na aika tace
gobe zata aiko yana aikowa sai in hada in
aikawa haj rabi daukarta. Yanzu idan na baki
aka zo aka sami matsala yaya zanyi? Kinsan
bani dashi, lada suke bani duk wata dubu daya
dan tarawar da nakeyi. Niko ikon sgiga
adashen ma bani dashi dan bani dashi. Nace
na sani uwani, idan Allah Ya yarda babu
matsala, ranar litinin da sassafe zanje bankin
da kaina in karbo miki. Tace to shikenan gashi
nan. Ta kirgo dubu goma sha bakwai tabani, na
karba na kirga sun cika cas, nayi godiya.
Sannan na roki arzikin ta rufa min asiri kada ta
fadawa kowa ko abida kada taji, salin alin zan
dawo mata da kudinta. Tayi min alkawari babu
wanda zaiji. Na shiga daki na hada kan kudina
na adana a jaka. Naira dubu ashirin. Farin ciki
fal a zuciyata, har sai da abida ta fuskanci
haka a daren, a da bana iya cin abinci sosai,
amma a daren taga har da kari nayi. Da bana
son magana sai taji na isheta da labari a ranar.
Ta san na daina fara'a amma a ranar na ishe
ta da kyakyata daria har da wake wake.
Saboda na riga na sami kudin da bana tantama
na gama samun dr shureim imran. Gari na
wayewa na shiga tunanin karyar da zan
shiryawa yaya hussaini wacce zai bari in fice,
domin ranar lahadi ce babu aiki, kuma kulle
yake min. Na shirya tsaf na kira abida gefe na
shirga mata karyar cewa zanje asibiti yau ma,
ana yiwa wata nurse bikin gama aiki, tayi retire
ance kowa sai yaje kuma da kayan gida. Na
santa da wayo ta san yadda zata fadawa
maigidanta ya aminta da ita. Ta shiga daki ta
tsaro shi sai ga ta da dari biyu kudin babur.
Naji tausayinsu ya kama ni saboda nafi su kudi
yanzu, da sun san kudin da yake jikina da basu
rabu da dari biyunsu ba. Nayi godiya na karbe
na tafi, abida ta rakani har zaure tana yi min
fatan alkairi. Tana jaddada min in ragowa
'ya'yanta kayan walima. Na amsa mata da zan
rago musu da yawa ma kuwa. Ina fita na hau
acaba sai gidan ummi kawata. Da yake sassafe
ne mijinta ma bai fita ba yana daki, tajani
zuwa falonta muka zauna muna magana cikin
sirri. Ta tambaya yaya ake ciki, na samo kudin
kuwa? Na ciro mata himilin kudin daga jakata
sai ta rike baki tace lallai kinyi kokari, nima na
hada dubu goma sha biyar bari inje inyi masa
karya inzo mu tafi. Yau lahadi ba zai fita da
wuri ba, gara muyi tafiyarmu. Ta shiga daki ba
dadewa ta fito a shirye da goyonta muka nufi
kofar fita, har mun kai zaure faccalarta ta biyo
mu da sauri. Tana cewa ummi unguwa zakije
baki fada min ba mu fita tare? Yau ne sunan
mariya 'yar jummai, ki tsaya in shirya mu fita
gaba daya mana. Ummi ta doka mata harara
tace dani aisha faida da Allah muje, dole ne sai
mun fita tare. Myka kada kai muka fice muka
bar ta a tsaye tana kallonmu har abin tausayi.
Muna fita nace da ita haba ummi ya za ayi kiyi
mata wulakanci? Ai sai ki bata amsa mai dadi
ko ba kya so tabimu. Ummi ta tabe tace ai na
daina raga mata tunda bincike ya nuna bata
kaunata. Ni da mutunci da ita har abada. Nace
to amma ai maganar malamai ce, babu tabbas
zaiyiwu kirkira yayi. Ta harare ni tace lallai kina
wasa da aikin malamin nan. Idan yayi miki
duba tabbas zaki ga komai a hankali daya
bayan daya. In bai gani ba zai fada ne ko da
ya taba ambato sunanta in ba yanzu ba, kuma
nima na lura tun sanda muka sayi generator ta
canja min, taga mun cigaba a rayuwa. DUK
KYAN TAKALMI 11 Bansake magana ba dai har
muka isa gidan malam. Yana ganin mu ya fara
washe baki, fara'ar yau tafi ta jiya. Muka
zazzage masa kudaden jakarmu kakaf domin
bayan dubu ashirin da dayan da ya karba sai
da ya sake kwakwalo min wasu kudaden daban
daban har dubu biyar da dari biyar. Kuma na
harhada na bashi, a takaice dai har cikon dubu
daya da dari biyar nan gaba zan ciko masa. Ita
ma ummi ya kara mata wasu kudin, idan ta
tashi cikowa ba dubu goma zata ciko masa ba,
goma sha uku zata ciko. Yace ya bamu
kwanaki uku mu dawo, ranar laraba kenan kafin
komai zai daidai ta. Muka fito muna murna,
ummi tana tabbatar min komai zai daidaita in
kwantar da hankalina. Na tafi gida ita ma ta
koma gidanta, na sake shirgawa abida wata
karyar tunda ban taho da kayan walima ba,
naso in siyo musu lemo da biskit amma na
juyewa malam kudin dukka, da kyar ma na
karaso gida, sai da kudi ya kare. Ko kusa ban
damu da himilin bashin dake kaina ba, burina
aiki yaci in mallaki dr shureim shine a gabana.
Na yina ina hidindimuna da 'yan gidanmu cikin
walwala da farin ciki. Da dare yayi na shiga
barci sai na tsinci kaina na canza tunanina ba
irin na da bane. Yanzu tunani nake gani a
gidansa har mun zama ma'aurata, gani dare-
dare a cikin hadaddiyar motar nan tasa muna
tafe muna hirar soyayya. Na dade ina
tunaninsa sannan nayi bacci, na dora da
mafarkinsa mai dadin gaske. Na sa wa
zuciyata na sami dr shureim na gama kamar
yadda malam ya bani tabbaci. Naso in makara
saboda dadin mafarki, na tashi a gaggauce na
shirya na karbi kudin babur a wajen abida.
Yayana ya bata ta bani donshi yana riga ni fita
ma. Sai uwani ta biyo ni zaure da sauri ta
tsayar dani tace yanzu zaki karbo kudin daga
banki? Ko sai kin taso zaki taho dashi? Bilki ta
kawo zubinta jiya na wajenki kawai nake jira in
aikawa haj rabi na fada mata yau da rana zan
aiko mata. Sai zuciyata ta hau dukan uku uku
na fara zullumin inda zan nemo wadannan
makudan kudi. Na hau rawar murya ina kame
kame, nace sai an taso zan taho da kudin. Ina
kan babur ina tunanin yadda za'ayi idan na
dawo gida babu kudin? Ina shiga cikin asibiti
naji farin ciki ya lullunbe min zuciyata saboda
ko ba komai an fara aiki, zuciyarsa ta fara
bugowa gare ni. Sai kuwa naci sa'ar a ranar an
tura mu bangarensu dole zan ga ofishinsa ko
ba ma wajensa aka mu tura mu ba. Muna
shiga kuwa dakin darasin muka ci karo dashi
da dr lukman suna fitowa medical students
suna biye dasu zasu je zagayen marasa lafiya
(ward). Na tare su da sauri na gaishe su, sai
naji caraf ya amsa hadda kallon fuskata, ba
murmushi yake ba haka bai bata rai ba. Dr
lukman ne yake dariya, har yake yi min wasa
yace ke 'yar shagamu ina kika shiga kwana
biyu, rannan har yahaya umar yace in baki
waya ku gaisa, nace ba kya kusa. Nayi dariya
nace to yaushe zanzo ka kirawo min shi a
wayar muyi magana? Da yake yana tafiya ne
sanda yake magana, har yakai barandar waje
banji abin da yace ba. Sai wani dalibi ne yake
bayansu ya juyo yace min cewa yayi kizo gobe.
Na yini ina farin ciki saboda naga canji wajen
amsa gaisuwata da kuma kallon mutuncin da
dr shureim ya min. Ban fara fargaba ba sai da
aka tashi daga makaranta na tunkaro hanyar
gida. Na shiga zullumin karyar da zan gina
wacce ba za'a rutsoni ba, dakin uwani na nufa
kai tsaye sai ta fara murna tana gyara hannu
zata karbi kudi ta kidaya. Sai na zube a
gabanta ina marairaice murya ina bayani. Nace
wallahi tun safe ban huta ba muna ta kai kawo
a cikin asibitin saboda matar bata da jini, don
haka ba za'a yankata ba dole sai an kara mata
jini. 'Yan uwanta ne suka zo maza da mata
muna ta auna jinin har a sami wanda ya dace
da nata shi yasa ban samu fita daga asibitin
ba naje banki, amma gobe da sassafe zanje in
karbo. Uwani ta bata rai, yadda ta amsa min a
ciki ciki na san bata so haka ba, ta bini da kallo
har na fice daga dakin. Ina cin abincin rana na
fice wajen musbahu ban same shi ba, na bar
masa doguwar wasika. Nazo giftawa ya
makoftanmu nayi ido hudu dahare ta leko
kenan ta ganni, ita ma dari takwas ta ranta
min kudin dinkinta zata kai domin ta kusa
haihuwa, ita ma ranar litimin din nace zan
kawo mata. Dole na shiga gidan na tsara mata
karya iri iri na ce gobe zan kawo mata. Itama
ta nuna min bataji dadi ba, har mijinta yayi
fada da yaga kayan dinkin a ajiye bata kai ba.
Naji hankalina ya sake tashi na fito a gigice na
shiga gidan mu har sai da abida ta shiga
damuwa ganin yanayin da na shigo. Tayi ta
tambayata ko lafiya? Nace lafiya kalau. Idan
naji damuwa ta gallabeni sai in tuno menayi da
kudin, kuma nan gana me zan samu. Sai inji
sanyi a raina. Washe gari talata na fita zuwa
makaranta, kai tsaye ofishin dr lukman na
wuce. Ina shiga na iske shi zai fita. Yace dani
ke kuwa baiwar Allah ai ba da sassafen nan
zaki zo ba, sai da rana in aiki ya lafa ko? Nayi
turus banji dadin amsar daya bani ba, ya wuce
abinsa ya barni a tsaye. Sai ga gogan nawa
yau kuma shigar hausa yayi, shadda ruwan
bula tazarce ya dora hular da ta dace da kalar
kayansa. Ya ratayo laptop dinsa a kafadarsa
sai naga ya kara yin kyau matuka babu wacce
zata kalle shi bata sake kallonsa ba. Ya tari dr
lukman sukayi magana, sannan kowa ya wuce.
Sai naji zuciyata na tafarfasa saboda shaukin
so, kai kace zakanya ce mai tsananin jin
yunwa ta ga nama haka zuciyata ta dinga zillo
tamkar ta ballo ta fito da taga abincinta. Sai
dai wannan abincin bana lasa bane, yafi
karfinta. Tamkar soyayyen nama ne aka soya
yana kamshi amma aka zazzaga masa guba
kaga duk kwadayin mutum doke ya kalla ya
wuce ko da kuwa marmarin naman zai kashe
shine. Na fara takawa a hankali na matsa daga
bakin kofar kafin ya karaso. Tun daga nesa na
amshi wata galleliyar harara daga gareshi.
Daya karaso bakin kofa kafin ya lalubo mukulli
ya bude kofar sai da ya waiwayo bayansa inda
nake a tsaye ya wurgo min wata hararar wacce
tafi ta dazu wulkilewa. Sai nayi sauri na juya
na fara tafiya ba tare da nasan inda zanje ba,
sai gani a bakin gadon marasa lafiya nayi wuki
wuki suna kallona ina kallonsu. Sannu likita,
zoki duba cikinsa ki gani ya kumbura. Inji wata
tsohuwa mai zaman jinyar danta. Na girgiza
kai nace ki kira likita ni ba likita bace. Nayi
saurin barin wajen na dawo bakin kofar ofis din
na tsaya, nayi kamar in tura kofar in shiga sai
na fasa. Na hakura na tafi ba don zuciyata
tana so ba. Ina zuwa ofishinmu na iske
kawayena suka hau min surutu. Wai aisha
farida ina kike shiga ne aka nemeki aka rasa
kullum har anyi test jiya ba kya nan? Nayi
shiru na koma gefe na zauna na rasa abun da
yake min dadi. Naci sa'a khadija sani tace inzo
in rakata ta siyo ruwa zata sha magani. Ashe
itama ta kunso labarai kala kala take so mu
kebe ta fatsar. Ta dube ni ta tabe baki tace
baki tambayeni dr shureim ba. Sai naji gabana
ya fadi, sai na zargi kaina ina ganin kamar
kowa yasan halin da nake ciki. Na zabura nace
kamar yaya ban tambaye ki dr shureim ba?
Tace kin manta inda muka kwana na nuna miki
sakonsa a wayata? To in fada miki an gasa
minshi da addua, ba adadi har sai da yaji ba
dadi. Ina kiransa ya amsa, yace dani wacece?
Sai na fada masa sunana khadija sani ismail.
Ni daliba ce a schl of nursing tanan aminu
kano, kuma ina attachment a nan cikin asibiti,
sai yace yayi kyau lafiya? Nace lafiya so nake
yayi saving lambata zan dinga kira muna
gaisawa. Na dafe kirji nace yayi saving lambar?
Tace kwarai kuwa, don da na sake kira sai da
ya ambaci sunana. Sai naji kwalla ta cika min
ido, kishi ya kamani, jikina yayi sanyi kalau.
Taci gaba da cewa da na sake kira sai yayi
tsiyar. Na tambaya a sanyaye meye tsiyar?
Tace wulkanci yayi min kamar zai zageni, wai
kada in sake kiransa. Kuka wiwi nayi da
hawaye na hakura dashi ma ni yanzu. Allah Ya
sa bai san fuskata ba, na goge lambarsa na
daina kiransa yanzu. Dadi ya rufeni, amma fa
na kara tausayawa kaina. Na bata shawarar
tayi hakuri taci gaba da addua, Allah Ya
musanya mata da abin da yafi alkhairi. Ta
amsa min da ameen. Da aka tashi daga
makaranta sai na kasa komawa gida, sai
nacewa khadiji sani ismali zanbi ta gidansu
somin 'yan gidanmu ba sa nan sun tafi unguwa
sai dare zasu dawo. Khadija tayi farinciki da jin
haka, sai muka dunguma muka tafi har yanzu
labarin dr takeyi min. Ban cika bata amsa ba,
tamkar tana min famin gyambon da yake
damuna da zugi ne. Kwakwalwata ta cunkushe
na rasa abin da yake min dadi, na kasa
tantance abin da zanyi. Abinci kala kala aka
jera min a gabana, amma na kasa ci da yawa
saboda damuwa. Khadija sani ta dube ni tace
wai don Allah aisha farida me yake damunki ne
kwana biyu kin susuce tamkar bake ba. Ba kya
son magana, ba kya son karatu gashi ba kya
son cin abinci tundazu dan abincin da kika
zuba kin kasa cinyewa, bakiga yadda kika rame
ba, kika kwanjale ba. Kin cika zurfin ciki, ba a
jin sirrinki daman. Wai me yake faruwa ne?
Nayi murmushi nace haka kowa yake ambata,
malaria ce ke cin jikina. Tace toh kisha magani
mana, yaya zaki zauna da ciwo kina malamar
asibiti, ko in saya miki babu kudi hannunki? Ta
soso min inda yake min kaikayi, na gyara zama
nace kamar kinsan satin nan cikin matsalar
kudi muke, kinga yanzu haka yayana ne aka
bashi ajiyar kudi, ya kawo gida aka shiga har
daki aka sace, ya rasa yadda zaiyi. Mai kudin
yana ta damunsa har da zai kai shi police
station yake ambato. Khadija tace a garin yaya
aka shiga har daki aka yi muku sata, babu
mukulli ne? Nace maso abinka ya fika dabara,
kinsan rayuwar cikin gari, gidan yawa aka shiga
aka dauke. Khadija tace babu dadi, Allah Ya
kiyaye gaba. Shi kuwa mai kudin bai san
kaddara bane? Yayi hakuri mana sai ya samu
ya biya shi. WaLlahi nima a cikin matsala nake,
domin na karbi kudi a wajen abba yayi dubu
hamsin kwanan nan haka ma a wajen mama.
Har sun gane ba'a makaranta nake kashewa ko
na tambaya basa bani. Sai tambayata suke me
nayi da kudi a cikin satin nan, naki fada, ai ban
isa ince malamai na kaiwa ba sai a kusa kashe
ni.
Tags :
Bansake magana ba dai har muka isa gidan
malam. Yana ganin mu ya fara washe baki,
fara'ar yau tafi ta jiya. Muka zazzage masa
kudaden jakarmu kakaf domin bayan dubu
ashirin da dayan da ya karba sai da ya sake
kwakwalo min wasu kudaden daban daban har
dubu biyar da dari biyar. Kuma na harhada na
bashi, a takaice dai har cikon dubu daya da
dari biyar nan gaba zan ciko masa. Ita ma
ummi ya kara mata wasu kudin, idan ta tashi
cikowa ba dubu goma zata ciko masa ba,
goma sha uku zata ciko. Yace ya bamu
kwanaki uku mu dawo, ranar laraba kenan kafin
komai zai daidai ta. Muka fito muna murna,
ummi tana tabbatar min komai zai daidaita in
kwantar da hankalina. Na tafi gida ita ma ta
koma gidanta, na sake shirgawa abida wata
karyar tunda ban taho da kayan walima ba,
naso in siyo musu lemo da biskit amma na
juyewa malam kudin dukka, da kyar ma na
karaso gida, sai da kudi ya kare. Ko kusa ban
damu da himilin bashin dake kaina ba, burina
aiki yaci in mallaki dr shureim shine a gabana.
Na yina ina hidindimuna da 'yan gidanmu cikin
walwala da farin ciki. Da dare yayi na shiga
barci sai na tsinci kaina na canza tunanina ba
irin na da bane. Yanzu tunani nake gani a
gidansa har mun zama ma'aurata, gani dare-
dare a cikin hadaddiyar motar nan tasa muna
tafe muna hirar soyayya. Na dade ina
tunaninsa sannan nayi bacci, na dora da
mafarkinsa mai dadin gaske. Na sa wa
zuciyata na sami dr shureim na gama kamar
yadda malam ya bani tabbaci. Naso in makara
saboda dadin mafarki, na tashi a gaggauce na
shirya na karbi kudin babur a wajen abida.
Yayana ya bata ta bani donshi yana riga ni fita
ma. Sai uwani ta biyo ni zaure da sauri ta
tsayar dani tace yanzu zaki karbo kudin daga
banki? Ko sai kin taso zaki taho dashi? Bilki ta
kawo zubinta jiya na wajenki kawai nake jira in
aikawa haj rabi na fada mata yau da rana zan
aiko mata. Sai zuciyata ta hau dukan uku uku
na fara zullumin inda zan nemo wadannan
makudan kudi. Na hau rawar murya ina kame
kame, nace sai an taso zan taho da kudin. Ina
kan babur ina tunanin yadda za'ayi idan na
dawo gida babu kudin? Ina shiga cikin asibiti
naji farin ciki ya lullunbe min zuciyata saboda
ko ba komai an fara aiki, zuciyarsa ta fara
bugowa gare ni. Sai kuwa naci sa'ar a ranar an
tura mu bangarensu dole zan ga ofishinsa ko
ba ma wajensa aka mu tura mu ba. Muna
shiga kuwa dakin darasin muka ci karo dashi
da dr lukman suna fitowa medical students
suna biye dasu zasu je zagayen marasa lafiya
(ward). Na tare su da sauri na gaishe su, sai
naji caraf ya amsa hadda kallon fuskata, ba
murmushi yake ba haka bai bata rai ba. Dr
lukman ne yake dariya, har yake yi min wasa
yace ke 'yar shagamu ina kika shiga kwana
biyu, rannan har yahaya umar yace in baki
waya ku gaisa, nace ba kya kusa. Nayi dariya
nace to yaushe zanzo ka kirawo min shi a
wayar muyi magana? Da yake yana tafiya ne
sanda yake magana, har yakai barandar waje
banji abin da yace ba. Sai wani dalibi ne yake
bayansu ya juyo yace min cewa yayi kizo gobe.
Na yini ina farin ciki saboda naga canji wajen
amsa gaisuwata da kuma kallon mutuncin da
dr shureim ya min. Ban fara fargaba ba sai da
aka tashi daga makaranta na tunkaro hanyar
gida. Na shiga zullumin karyar da zan gina
wacce ba za'a rutsoni ba, dakin uwani na nufa
kai tsaye sai ta fara murna tana gyara hannu
zata karbi kudi ta kidaya. Sai na zube a
gabanta ina marairaice murya ina bayani. Nace
wallahi tun safe ban huta ba muna ta kai kawo
a cikin asibitin saboda matar bata da jini, don
haka ba za'a yankata ba dole sai an kara mata
jini. 'Yan uwanta ne suka zo maza da mata
muna ta auna jinin har a sami wanda ya dace
da nata shi yasa ban samu fita daga asibitin
ba naje banki, amma gobe da sassafe zanje in
karbo. Uwani ta bata rai, yadda ta amsa min a
ciki ciki na san bata so haka ba, ta bini da kallo
har na fice daga dakin. Ina cin abincin rana na
fice wajen musbahu ban same shi ba, na bar
masa doguwar wasika. Nazo giftawa ya
makoftanmu nayi ido hudu dahare ta leko
kenan ta ganni, ita ma dari takwas ta ranta
min kudin dinkinta zata kai domin ta kusa
haihuwa, ita ma ranar litimin din nace zan
kawo mata. Dole na shiga gidan na tsara mata
karya iri iri na ce gobe zan kawo mata. Itama
ta nuna min bataji dadi ba, har mijinta yayi
fada da yaga kayan dinkin a ajiye bata kai ba.
Naji hankalina ya sake tashi na fito a gigice na
shiga gidan mu har sai da abida ta shiga
damuwa ganin yanayin da na shigo. Tayi ta
tambayata ko lafiya? Nace lafiya kalau. Idan
naji damuwa ta gallabeni sai in tuno menayi da
kudin, kuma nan gana me zan samu. Sai inji
sanyi a raina. Washe gari talata na fita zuwa
makaranta, kai tsaye ofishin dr lukman na
wuce. Ina shiga na iske shi zai fita. Yace dani
ke kuwa baiwar Allah ai ba da sassafen nan
zaki zo ba, sai da rana in aiki ya lafa ko? Nayi
turus banji dadin amsar daya bani ba, ya wuce
abinsa ya barni a tsaye. Sai ga gogan nawa
yau kuma shigar hausa yayi, shadda ruwan
bula tazarce ya dora hular da ta dace da kalar
kayansa. Ya ratayo laptop dinsa a kafadarsa
sai naga ya kara yin kyau matuka babu wacce
zata kalle shi bata sake kallonsa ba. Ya tari dr
lukman sukayi magana, sannan kowa ya wuce.
Sai naji zuciyata na tafarfasa saboda shaukin
so, kai kace zakanya ce mai tsananin jin
yunwa ta ga nama haka zuciyata ta dinga zillo
tamkar ta ballo ta fito da taga abincinta. Sai
dai wannan abincin bana lasa bane, yafi
karfinta. Tamkar soyayyen nama ne aka soya
yana kamshi amma aka zazzaga masa guba
kaga duk kwadayin mutum doke ya kalla ya
wuce ko da kuwa marmarin naman zai kashe
shine. Na fara takawa a hankali na matsa daga
bakin kofar kafin ya karaso. Tun daga nesa na
amshi wata galleliyar harara daga gareshi.
Daya karaso bakin kofa kafin ya lalubo mukulli
ya bude kofar sai da ya waiwayo bayansa inda
nake a tsaye ya wurgo min wata hararar wacce
tafi ta dazu wulkilewa. Sai nayi sauri na juya
na fara tafiya ba tare da nasan inda zanje ba,
sai gani a bakin gadon marasa lafiya nayi wuki
wuki suna kallona ina kallonsu. Sannu likita,
zoki duba cikinsa ki gani ya kumbura. Inji wata
tsohuwa mai zaman jinyar danta. Na girgiza
kai nace ki kira likita ni ba likita bace. Nayi
saurin barin wajen na dawo bakin kofar ofis din
na tsaya, nayi kamar in tura kofar in shiga sai
na fasa. Na hakura na tafi ba don zuciyata
tana so ba. Ina zuwa ofishinmu na iske
kawayena suka hau min surutu. Wai aisha
farida ina kike shiga ne aka nemeki aka rasa
kullum har anyi test jiya ba kya nan? Nayi
shiru na koma gefe na zauna na rasa abun da
yake min dadi. Naci sa'a khadija sani tace inzo
in rakata ta siyo ruwa zata sha magani. Ashe
itama ta kunso labarai kala kala take so mu
kebe ta fatsar. Ta dube ni ta tabe baki tace
baki tambayeni dr shureim ba. Sai naji gabana
ya fadi, sai na zargi kaina ina ganin kamar
kowa yasan halin da nake ciki. Na zabura nace
kamar yaya ban tambaye ki dr shureim ba?
Tace kin manta inda muka kwana na nuna miki
sakonsa a wayata? To in fada miki an gasa
minshi da addua, ba adadi har sai da yaji ba
dadi. Ina kiransa ya amsa, yace dani wacece?
Sai na fada masa sunana khadija sani ismail.
Ni daliba ce a schl of nursing tanan aminu
kano, kuma ina attachment a nan cikin asibiti,
sai yace yayi kyau lafiya? Nace lafiya so nake
yayi saving lambata zan dinga kira muna
gaisawa. Na dafe kirji nace yayi saving lambar?
Tace kwarai kuwa, don da na sake kira sai da
ya ambaci sunana. Sai naji kwalla ta cika min
ido, kishi ya kamani, jikina yayi sanyi kalau.
Taci gaba da cewa da na sake kira sai yayi
tsiyar. Na tambaya a sanyaye meye tsiyar?
Tace wulkanci yayi min kamar zai zageni, wai
kada in sake kiransa. Kuka wiwi nayi da
hawaye na hakura dashi ma ni yanzu. Allah Ya
sa bai san fuskata ba, na goge lambarsa na
daina kiransa yanzu. Dadi ya rufeni, amma fa
na kara tausayawa kaina. Na bata shawarar
tayi hakuri taci gaba da addua, Allah Ya
musanya mata da abin da yafi alkhairi. Ta
amsa min da ameen. Da aka tashi daga
makaranta sai na kasa komawa gida, sai
nacewa khadiji sani ismali zanbi ta gidansu
somin 'yan gidanmu ba sa nan sun tafi unguwa
sai dare zasu dawo. Khadija tayi farinciki da jin
haka, sai muka dunguma muka tafi har yanzu
labarin dr takeyi min. Ban cika bata amsa ba,
tamkar tana min famin gyambon da yake
damuna da zugi ne. Kwakwalwata ta cunkushe
na rasa abin da yake min dadi, na kasa
tantance abin da zanyi. Abinci kala kala aka
jera min a gabana, amma na kasa ci da yawa
saboda damuwa. Khadija sani ta dube ni tace
wai don Allah aisha farida me yake damunki ne
kwana biyu kin susuce tamkar bake ba. Ba kya
son magana, ba kya son karatu gashi ba kya
son cin abinci tundazu dan abincin da kika
zuba kin kasa cinyewa, bakiga yadda kika rame
ba, kika kwanjale ba. Kin cika zurfin ciki, ba a
jin sirrinki daman. Wai me yake faruwa ne?
Nayi murmushi nace haka kowa yake ambata,
malaria ce ke cin jikina. Tace toh kisha magani
mana, yaya zaki zauna da ciwo kina malamar
asibiti, ko in saya miki babu kudi hannunki? Ta
soso min inda yake min kaikayi, na gyara zama
nace kamar kinsan satin nan cikin matsalar
kudi muke, kinga yanzu haka yayana ne aka
bashi ajiyar kudi, ya kawo gida aka shiga har
daki aka sace, ya rasa yadda zaiyi. Mai kudin
yana ta damunsa har da zai kai shi police
station yake ambato. Khadija tace a garin yaya
aka shiga har daki aka yi muku sata, babu
mukulli ne? Nace maso abinka ya fika dabara,
kinsan rayuwar cikin gari, gidan yawa aka shiga
aka dauke. Khadija tace babu dadi, Allah Ya
kiyaye gaba. Shi kuwa mai kudin bai san
kaddara bane? Yayi hakuri mana sai ya samu
ya biya shi. WaLlahi nima a cikin matsala nake,
domin na karbi kudi a wajen abba yayi dubu
hamsin kwanan nan haka ma a wajen mama.
Har sun gane ba'a makaranta nake kashewa ko
na tambaya basa bani. Sai tambayata suke me
nayi da kudi a cikin satin nan, naki fada, ai ban
isa ince malamai na kaiwa ba sai a kusa kashe
ni. DUK KYAN TAKALMI 12 Sai naji hankalina
ya tashi, har na fara nadamar katobarar da na
tafka. Ta bude jakarta ta zaro dukka kudin da
yake jakarta, dubu daya da dari biyu ne kacal
sai 'yan canji. Ta miko min naira dubu daya, na
karba nayi ta godiya. Tayi ajiyar zuciya tace
wallahi dr ya cuce ni, na kashe kudina a banza
ko gezau baiyi ba. Na fada cikin marainiyar
murya nace karki damu kaddara ce Allah Ya
aiko mana. Sai nayi sauri na gyara zancen son
naga tayi sauri ta dubeni, sai nace ciwon 'ya
mace na 'ya mace ne, tunda ya shafe ki nima
ya shafe ni. Bakiji yadda zuciyata take tafasa
ba don takaici. To shi dr dame yafi sauran
likitoci su basa wulakanci sai shi? Khadija tace
yafi sauran mana ke kuwa, shifaa a london yayi
karatunsa, ke har pri sa secondary duk a can
yayi rabin rayuwarsa, sai da yazo nigeria fisha
ya tafi. Ance dai yayi aiki a asibitin nan
shekara 2 a lokacin yana karamin likita. Sai ya
koma ya sake shekaru hudu ya zama
consultant sannan ya dawo kwanan nan. A
bangaren ilimi addini kuwa a saudia yayi
karatun kurani, larabawa suka koyar dashi,
ance yafi kowanne likita sanin kurani. Don tun
yana yaro yaje saudia sai da ya sauke ya dawo
london, ya karasa primary kinga kuwa Allah Ya
yi masa baiwar da ba kowa yake da ita ba.
Gashi dan attajiri shima attajiri, ga ilimi dukkan
bangarorin biyu, ga wani kyau tamkar sai da
zaba aka bashi. Kowacce mace dole taso shi,
sai dai idan ta ga ba ta samu bata hakura
irina. Maryam ahmad ma na gano sonsa
takeyi, har wani kishi takeyi dani, nace kije na
bar miki in dai shureim ne zaki gaji ki kyale shi.
Amma ke aisha farida naga bai dadaki da kasa
ba, ko zancensa ma ba kya so. Kowa yana
yabon kyawunsa, ke ko ki kula. Baiyi miki
bane? Sai naji tamkar an saki bom a kahon
zuciyata, saboda faduwar gaba. Nayi firgigit
nace yanzu khadija ina ta kaina ina ni ina cusa
kaina wajen irin wannan halitta? Ai sai ku
kyawawa, masu mota 'ya'yan attajirai. Khadija
tace kin hutawa kanki wallahi kina burge ni
yadda kike tafiyar da rayuwa, ba kya jajubo wa
kanki abun da zai wahalar dake. Nima nayi
nadama ba zan sake shiga irin wannan hatsarin
ba. Yanzu mun bata da malaman nan
makaryata, wai yaga aurenmu har da haihuwar
'yan biyu. Shine ai na saki jiki nayi ta tura
musu kudi suna cemin zai zo da kafarsa
nemana ga mutum kamar zai yayyaga ni cikin
waya don masifa. Bani ba wani malami ai
yanzu na rufawa kaina asiri nace mohd ya aiko
da iyayensa muyi aure. Ina laifinsa yaro
matashi, yana da mota da gidan kansa da aikin
bankinsa, nima da aikina ya ishe mu rayuwar
duniya. Sai naji hankalina ya tashi, dana sani
ta afko min. Na gyara zama nayi tagumi ina
duban khadija na rasa in da zan saka raina, sai
yanzu na fara gane kuskuren da na tafka a
rayuwa. Ummi ta cuce ni. Na fada a cikin
zuciyata yayin da hawaye ya cika min ido.
Nace da khadija kina so kice min gaba daya
asirin da malamanki suka sha zabgawa ko
daya bai taba shi ba, asiri baya cinsa kenan?
Tace baya cinsa tunda bai ci shi ba, babu abin
daya yi masa. Malamina daya ne ya fada min
gaskiya tun da farko naji haushinsa, daga
karshe na gane gaskiya ya fada min. Yace dani
yaron nan da kike so gaskiya ya rike adduar
neman tsari dare da rana, da wuya a jefe shi ya
taba shi, sai dai kawai kije kiyi addua in da
alkhairi Allah Ya hada ku ta wata hanyar, a
dadin rai yazo, kuma ina so ki sani ba'ayiwa
Allah dole. Khadija tace aiki ma daina damuwa,
Allah Ya ganar dani har na dade ina istigfari.
Su maryam anmad ne suka rage suma Allah Ya
ganar dasu. Shiyasa aka ce wani kyau bala'I
ne, sai a dilmiyar da kai in bakayi taka tsan
tsan ba. Yanzu dr shureim in ba don Allah Ya
sa nutsatte bane da mata sai sun halakar
dashi. Haka ma mace mai kyau idan baatayi a
hankali ba maza su halakar da ita, su rude ta
da kudi tabi su koda kuwa tana da aure. Ke dai
Allah Ya sa mu gane gaskiya. Sai naji khadija
ta burge ni, tafi ni gaskiya. Ina ma a llokacin
da naje neman shawara wajen ummi khadija na
samu ta fada min abinda ta fada yanzu, da ba
wa zuciyata hakuri, da ban je na jefe kaina a
rigima ba. Yanzu gashi komawa gida ya
gagareni. Da me zan biya wannan dimbin
bashin na kaina gashi babu alamar nasara a
aikin malamin. Khadija ta katse min tunanina
tace duk inda ya kai da takama da kwalliya, da
yanga karshen alewa dai kasa. Dole mace zai
aura, ba auri kansa da kansa ba. Kuma dole
yayi 'yar murya kafin a bashi ita, dole ya kashe
kudi ya bauta mata saboda Allah Ya wajabta
masa ciyarwarta, sutura, kula da lafiyarta,
muhallinta da duk wata dawainiyarta. Daman
dai ance DUK KYAN TAKALMI dole kafa ce zata
saka sannan a taka kasa. Lallai zanso inga irin
macen da zai aura, karshenta fa ya kare a
mummuna, baka, 'yar talakawa, kinsan karshen
irinsu kenan. Nace yana da mata fa har da 'ya,
kema kinsan dr shuriem ba zai auri kucaka ba.
Khadija tace ke aisha farida wa ya fada miki
wannan? Nayi murmushi nace matarsa ma
baturiya ce a london suka hadu, a london take
zaune. Da bakinsa naji yana fada. Kuma a
gabana sukayi waya da ita cikin harshen
turanci ko hausa bata ji. Khadija ta gyara zama
tace don Allah da gaske kike? Ni da kin fada
min haka tuntuni ai da ban wahalar da kaina ba
wallahi. To wai ina kika ganshi ne har kika ji
yana waya, nifa tun ganin nan nasa da mukayi
yana motarsa ban sake ganinsa ba. Ko dai ba
shi kika gani ba? Nace shine wallahi, abokin dr
lukman ne, likitan kwakwalwa wanda matron
maryam take aikena wajensa. Kinsan tana da
kanwa mai matsalar kwakwalwa, to yana duba
to ko ba ranar clinic ba. Khadija tace lallai ba
zai saurari kujari-kujari irinmu ba, mai mata
baturiya mai zaiyi damu? Naji zuciyata tana
kokarin bugawa, sai na mike na tayar da sallar
la'asar daman da alwalar azahar dina bamu
dade dayi ba. Nayi sallama nayi addua, Allah
Ya biya min bashin da yake kaina. Na yunkura
zan mike in tashi, sai khadija tace dani aisha
farida gaskiya akwai abinda yake damunki,
saboda duk jikinki yayi sanyi, yanzu ko yanayin
sallarki ya canza ba irin na da ba, ba kya
samun nutsuwa wajen yin sallh, kin daina
doguwar addua bayan kin idar da sallah. Nayi
shiru ina tunani nace a raina yanzu son dr
shureim har addinina zai taba, bayan karatuna
da ya tava ga zaman lafiya dana rasa. Sai na
zuba wani zazzafan hawaye nayi sauri na boye
fuskata don kada ta gane. Na dauki jakata na
rataya nace mata zan tafi gida. Ta rako ni har
bakin titi na hau acaba na tafi, ita kuma ta
koma gida. Sai a hanya na fara tunanin halin
da zan fada idan naje gida, don haka nace dan
acaba ya kai ni zango gidan ummi kenan. Ina
isa cikin gidan na tarar da kofarta a kulle
alamar bata nan, sai naji banji dadi ba don
haka na leka bangaren faccalarta na
tambayeta. Tace min bata nan tun jiya ta tafi.
Sai naji zuciyata ta buga na dafe kirji na
tambaya kafiya? Ta tafi unguwa tun jiya bata
dawo ba? Amsar da ta bani itace babu komai.
Na sami kujera na zauna nace da ita ki fada
min gaskiya, ummi kawata ce bata boye min
komai. Sai tace to kiyi mata waya mana sai ta
fada miki da bakinta tunda aminiyarki ce. Na
jikina a sanyaye nace to sai anjima na tafi. Sai
naga ta bini da kallo alamar tausayawa tace
dani gaskiya ummi tana gidansu mijinta ya
sake ta. Kuna fita shekaran jiya ya kai mata
takardar sakinta gidansu, ashe bai bata izinin
fita ba ta biki kuka fita har ina cewa ku jirani in
shirya kuka ki. Na dawo na tsuguna a gabanta
nace innalillahi wainna ilaihir rajiun. Yanzu
yassar saboda dan wannan dalilin ya saki
ummi? Tace a'a ba wannan kadai ba, daman
akwai wata kasa. Ummi bata da kunya, ga ta
da bin bokaye da 'yan tsubbu kowa yasani,
mijinta ya sani saboda yana tono binne binnen
da takeyi, da kuma barbade barbade da takeyi
masa a abinci. Da zarar sun fada mata karya
sai ta zai tana habaici ta bata da kowa, har
uwarsa da ta haife shi bokanta yace uwar
mijinta bata sonta. Yanzu ya dace ace ummi
tazo ta zazzageni? Jiya ita da kannenta da
kyar aka fitar dasu daga gidan nan wai sai sun
dake ni. Har da cewa yadda na raba zamanta
da mijinta nima zamana da mijina sai ya kare,
sai in babu malamai a kano. Kinga kenan
malaminta ne ya fada mata ina yi mata asiri.
Ta tabe baki ta harareni tace to ai fitar da
kukayi gidan boka kuka je, saboda yassar
yabiku a baya har yaga inda kuka nufa, shi
yasa ya kai takardar sakinta gidansu. Ko kin
dauka ban gane ki bane munafuka kin san inda
take. Aiko ki tayi kizo ki barbada min wani abu
ko? Na zabura na mike tsaye na dafe kirjina
nace ni?? Wallahi bansan ummi ba ta nan ba
da bazan zo ba. Ba na irin wadannan halayya
kuma ba da wata manufa nazo ba. Tace dani
fita daga gidan nan kafin in tara miki jama'a.
Kuma duk ranar da kika kuskuara kika hadu da
yassar yace sai ya balla miki kafa, tun a
sakandire kike yi mata hudubar tsiya, yasan kin
tsane shi, shine kika biyo ta har gidan aurensu
kika kai ta gidan boka, wato a kashe shi kuci
gado ko? Tunda nake a duniya ba a taba yimin
cin mutunci, kazafi da wulakanci irin na
wannan ranar ba. Duk irin gulmace gulmacen
nan da ake yi a lungunmu tun ina yarinya ba
ataba cewa ga abin da aisha farida tace ba.
Lalli na jefa rayuwata cikin wani mawuyacin
hali saboda son dr shureim imran. Na gaggauta
ficewa daga gidanta kafin ta tara min jama'a
kamar yadda ta fada, kuka nake wiwi na hau
acaba ba tare da nasan inda na nufa ba. Sai da
dan acaba ya tambaye ni sau uku hajiya ina
zan kaiki? Sannan nace ka kaini gadon kaya.
Gidansu maryam ahmad kenan. Ita ma inje inji
halin da take ciki da dr shureim dinta. Duk da
haka ban daina sonsa ba. Maryam ahmad tayi
mamakin ganina, amma ganin ina fara'a ta san
lafiya kalau kenan. Tace dani shegiya aisha
farida umar daga ina kike, ba ki koma gida ba
ne har yanzu na ganki da uniform a jikinki?
Nace ke dai bari, yau bana jin komawa gida da
wuri, zumunci nake ji, zuwa nayi in gaishe da
su mamarki. Sai taji dadi taja hannuna har
dakin mahaifiyarta muka gaisa, na gaisa da
kannenta da 'ya'yanta biyu wanda Allah Ya
yiwa mijinta rasuwa ya barta dasu amma fa da
dimbin dukiya. Muka koma dakinta muka zauna
akan wani makeken gado, ta kunna mana AC
yayin da ta dinga kwallawa 'yan aikin gidansu
kira suna kawo min abubuwa kala kala kamar
su juice, kayan marmari, cincin da cake. Sai
taga duk na kasa ci sosai, ina yawan yin shiru
idan tana magana kamar hankalina baya tare
da ita. Sai ta zungureni nake dawowa
hankalina, na rasa yadda zan dauko mata
maganar dr shureim domin kada ta zargi wani
abu ta gano saboda zancensa na zo gidansu.
Domin ban taba zuwa ba gidansu haka kawai
ba, sau daya na taba zuwa kuma daga
makaranta muka zo muka yi mata gaisuwar
mijinta, da yake gidanta na kallon gidansu ne.
Muka shigo nan ma muka yi mahaifiyarta, to
anan na san gidansu. Da kanta ta dauko min
hirarsa tace baki tambayeni likitana ba dr
shureim. Sai na zauna dai dai nace yaya akayi?
Ki bani labari, akwai cigaba ko? Tace wanne ci
gaba ni da tun kafin aikin da na rabawa
malami bai je ko ina ba abu ya dagule gaba
daya, nace to su daina adduar yafi karfina. Dr
shureim yafi karfin ya kwanta in taka shi da
takalmin kafata, kinji. Anya mutumin nan
haifarsa akayi ba tikowa yayi daga sama ba?
Ace mutum ya hadu ta ko ina babu aibu a
tattare dashi? Sai naji na kara tsanar kaina, na
fada cikin shamulalliyar murya, me ya faru?
Tace mutuminki na same shi a ofis dinsa
wancan sati, malamina ya bani laya na kunshe
a karkashin harshena wai in dai da layar nan
duk abin da nace masa ya zauna babu musu.
Bayan turarukan da na dume jikina da goshina
dasu, wasu masu wari kamar na 'yan bori, ni
kaina sun isheni da wari balle shi dan gayu. Ina
shiga kaina tsaye ko fargaba banayi saboda an
bani tabbaci, ni kuma na yarda da cewar na
same shi na gama kamar yadda suka bani
tabbaci. Shi da wata likita mace ina jin dai
daliba ce, bata gama ba. Ta cika tayi taf kamar
zata fashe saboda fushi. Ta wani galla min
harara nima na harare ta saboda abin da ya
kawo ta shi ya kawo ni. Da na gaishe su babu
wanda ya amsa sai na sami kujera na zauna a
kusa da ita, shima yana zaune a kujerarsa. Ya
juyo ya dubeni sarai sannan ya dukar da kansa
yaci gaba da rubuce rubucensa. Ya gama ya
mika mata takarda, gami da cewa Allah Ya
sawake jeki. Ta tabe baki ta dubi takardar da
alama magani ya rubuta mata sai tace inje in
sha wannan kenan? Ya ce eh In sha Allah
kurajen zasu warke. Sai tace doctor muje ka
kaini chemist din mana, nina fi so ka tabbatar
masu kyau ne. Sai ya bata rai yace ba aikina
bane in rubuta miki magani, kuma in raka ki
zabar miki wanda zaki saya ba, komai a rubuce
yake zasu karanta su baki. Tace kaki zuwa ka
duba ni a gida, kwanana biyu ban fito ba har
waya nayi na fada maka. Na turo maka sakon
adireshina kaki zuwa. Sai ya harare ta yace
bani da lokacin zuwa duba dalibaina don basu
da lafiya. Ta sake turo baki tace amma ai
daliban daban daban ne, ba daya nake da
sauran ba. Ya daka tsawa ya zazzare mata ido
yace dalibaina dukka daya suke, daidai kike da
wannan. Ya nuna ni, ita kuma ta wurgo min
harara, nayi murmushin jin dadi nima na harare
ta sama da kasa. Yace idan baki da abin da
zaki fada min mai ma'ana game da karatunki ki
tashi ki tafi, kada ki kara shigo min ofis. Ta fice
sai ya juyo wajena ya tambaye ni cikin fushi,
ke kuma fa? Menene? Ina fitowa na kira
malamin da ya bani laya da turaren nan mai
daga hankali don wari kamar na 'yan bori.
Yana daukar wayar sai yace malama an sami
nasara kuwa? Nace nasarar me mutum kamar
zai mare ni? Sai yace to an sami kuskure ne
daga wajenki ina ganin baki yi yadda nace ba.
Nace komai daidai nayi banyi kuskuren komai
ba. Yace yaushe zaki zagayo sai in sake
bincikawa muga ta hanyar da zamu sake
bullowa kuma? Nace Allah Ya sawake in sake
kashe wani kudin bayan wanda na tula maka
na baya har da yankan rago amma a banza.....
Kafin in rufe bakina ya kashe wayarsa, nayi ta
kira har yau a kashe. Ko yau ma na gwada a
kashe, yaga na gane shi dan damfara ne babu
abin da ya iya. Haka nabi duk sauran malaman
naci musu mutuncu sukayi ta kame kame, sai
yanzu na gasgata cewar malaman zamanin nan
sun raina wa mata wayo, sun mayar dasu
jahilan karshen zamani. Idan kura tana
maganin zawayi tayi wa kanta, ke kina ganin
malaman kinga wahalallu masu matsala sun
kasa maganin matsalarsu, wai suce zasuyi wa
wani maganin matsalar su, sai suyi ta canke
canke don basu ma san ya ake duban ba. Ai ni
na dawo daga rakiyarsu na goge lambar
kowannensu, ko sun kira ni tsuye su nakeyi, sai
su waya da sauro. Ko wata na gani zata bata
lokacinta wajen bin malamai zan hanata sai dai
idan taki yadda in kyale ta, idan taje taga uwar
bari zata dawo da kanta tayi min bayani. Duk
wadannan bayanai da maryam keyi tuni sun
ragargaza min zuciya, kwakwalwata ta riga ta
dau gobara, na rike kai kawai tamkar mai
ciwon kai yayin da na sulale na kwanta akan
gadonta tamkar sumammiya. Na yarda da
cewar komai ya sami bawa rubutacce ne, in ba
haka da ya za'ayi tun farko inji wadannan
labarai akan malamai kuma in dauki
zunzurutun kudi in kai wa wani? Nace a raina
me yasa na fara zuwa gidan ummi neman
shawara banzo wajen khadija da maryam sun
fada min halin malaman zamani ba? Tun daga
lokacin na tabbatar kudin sun mula kuma ba
zan sami dr shureim ba. Maryam labari take
bani kala kala, amma bana fahimta ina can ina
tunanin abin da zanje in tarar a gida, haduwata
da uwani mai adashe da sauran makoftan da
na ciyo bashi, sannan bayanan da zanyi wa
yaya hussaini in da naje na kai dare bayan tun
karfe biyu na rana muka tashi.
A gidan su maryam nayi sallar magriba, na yi
ishai muka ci abincin dare. Taga bani da niyyar
tafiya sai ta fara mamaki, tana jero min
tambayoyi iri iri kasancewar ta sanni ba mai
bin gidan kawaye bane kwata kwata balle tace
na saba daman. Sai da na fuskanci har ta fara
gyangayi , tara da kwata na dare sannan na
fara haramar tafiya gida ba don naso ba,
saboda niyyata sai karfe goma sha daya na
dare zan koma gida kafin nan kowa yayi bacci.
dole na fito ta raka ni kofar gidansu na hau
babur na tafi. Ina tafe ina adduoi har na isa
unguwarmu, daga nesa da gidanmu nace mai
acaba ya sauke ni, don bana so 'yan gidanmu
suji karar babu na san idonsu yana kan hanya
suna zuba idon dawowata. Na biya dan acaban
kudinsa yayin da nake tafiya tamkar hawainiya
ina yi ina waige waige tamkar barauniya. Da
sanda na shiga zauren gidanmu naci sa'a babu
'yan matan gidan masu zance a zaure da
samarinsu. Sai na leka tsakar gidan, nan ma
ban ga kowa ba. Sai na cire takalmana na rike
a hannuna ina sanda dana zo giftawa ta
windown dakin uwani sai na tsugunna nayi
duku duku na wuce don kada taga giftawata,
najiyo motsin mutum a daki ina kyautata zaton
ba ta yi bacci ba. Da yake babu wuta sai
hasken fitilar kwai da kyandira zaka dinga
hangowa a dakunan don haka na hango kyallin
kyandir a dakin abida ina hango inuwarta a
tsaye jikin labule, sai dai ba zan tantance abin
da takeyi a tsaye ba. Na duba kofar dakin sai
naga takalman yaya hussaini da alama ya
dawo, nan da nan tsoron da nake ciki ya karu.
Nayi maza na tura kofar dakina na shiga na
iske ta shimfidar da 'ya'yanta ta rage hasken
fitilar kwai a gefe. Shiga ta dakin ke da wuya
ko jakata ban ajiye ba naji motsi a kofar
dakinmu, nan da nan na tsuguna na takure a
lungu. Sai na sankare saboda firgici. Abida ce
ta shigo hankalinta a tashe, tana ambaton
subhanallahi, yaya zanyi yau. Tana rufe bakinta
sai muka hada ido yayin da zaka dinga hango
mamaki a cike da fuskarta gami da firgici. Ni
kuma ina tsugunne ina kokarin daidaita
numfashina domin na shide, don tsoron yaya
hussaini da uwani a tunanina daya daga
cikinsu ne. Aisha farida lafiya? Yaushe kika
dawo? Ina kika shiga yau tun safe? Abida ce ta
jero min wadannan tambayoyi masu wuyar
amsawa. Na mike tsaye a sanyaye ba tare da
na san abinda zance mata ba. Ta sakke kallona
tace da ban ganki ba yanzu da kin jawo min
masifa yau, saboda yanzun nan yayanki ya
shigo ko minti biyar baiyi da shigowa ba, ya
shigo da ciwo a kafarsa sun fadi akan babur
shine yace in taso ki, ki rubuta masa allura ko
maganin da zai sha ko ki dauko akwatin
taimakon gaggawa (first aid box) ki zo kiyi
masa dressing. Na kasa ce masa bakya nan,
shine na shigo nan ina tunanin abin da zance
masa. Ina kika shiga kika sa hankalina ya tashi
ko abincin dare banci ba? Me yake faruwa
tsakaninki da uwani tayi ta zuwa nemanki
ranta a bace tunda rana? Na zazzare ido nace
me tace miki? Abida ta girgiza tace nayi nayi
ta fada min dalilin nemanki din da takeyi, sai
tace inkin dawo in tambayeki ita ba zata fa.
Ranta fa a bace har zage zage nake jiyowa
tanayi daga dakinki. Ke kuwa aisha farida me
ya hadaki dasu uwani ke da ba a zama a yi
gulmar wani dake, me ya kai ki tsoma baki a
maganarsu? Nasan wata gulma suka hado aka
ce dake a ciki, to ni shawarar da zan baki gobe
da sassafe kafin ki fita kije ki samu uwani ku
sulhunta, idan kinsan kin fada ki basu hakuri,
idan baki fada ba ki wanke kanki tun kafin
yayanki yaji abinda yake faruwa yaci miki
mutunci, kinsan halinsa. Duk kin susuce a
kwanakin nan kin canja halinki sai kiya ta nuku
nuku kamar mara gaskiya. Nayi shiru ina
sauraronta yayin da na cire kayan makaranta
na saka doguwar rigar baccina na saka katon
hijabi na dauko 'yar akwati na wuce gaba, tana
tsaye tana kallona cike da mamaki da takaici.
Nayi sallama a kofar dakinsu, yayi min izini na
shiga, na durkusa na gaishe shi yayin da ya
miko min kafarsa naga ciwon nayi masa sannu
da adduar Allah Ya kiyaye gaba. Sannan na
bude akwatin na shiga aikin saka iodine da
auduga. Ita kuwa abida tana can tana kinkimar
'ya'yanta daya bayan tana kai su fitsari. Naga
gama masa yayi min godiya na fito. Har yanzu
abida na dakina tana jirana bata gama jero min
tambayoyin da suka cika zuciyarta dam! Ta
dube ni ta yatsune fuska tace baki fada min ba
fa in da kika je ko daman kinsan da maganar
su uwani shiyasa baki dawo gida da wuri ba?
Na bata rai na turbune fuska nace ni ba
wannan bane ya tsayar dani, bayan mun tashi
daga asibiti aka ce mu dawo za'ayi mana
darasi daga karfe hudu zuwa shida, wani sabin
likta ne zai gabatar da wata sabuwar cuta
shine naga ba zan iya dawowa gida ba in sake
komawa da yamma ba, sai nabi khadija sani
gidansu da yamma muka koma, bamu baro
asibiti ba sai da karfe bakwai ana sallar
magriba, tace inzo gidansu idan nayi sallah sai
in wuce. Shine kuma muka zauna muna hira
bansan dare yayi haka ba. Abida ta tabe baki
da alama ba ta yadda da bayanai na ba. Ta
sake dubana tace aisha farida me ya hadaki da
musbahu kuma shima ya dinga aiko wani yaro
da wasika, zuwansa biyu. Nayi nayi ya bayar a
ajiye mike yace a'a, ance hannu da hannu zai
baki. Sai na sake gigivewa na hau kame kame
nace musbahu kuma? Meye hadina dashi? To
ina jin bani aisha faridar ba. Abida tayi
murmushin takaici tace kila na fara zama
kurma har a ambaci aisha farida inji ba daidai
ba. Babu abinda zance miki tunda boye boye
kike yi min tun yanzu. Sai dai kiyi hankali da
mutane, ki kuskuri bin shawarar batattun
kawaye, ki rike mairaici da talaucinki. Ta juya
ta fice ta rufo mana kofa. Na sulale na kwanta
na dora hannu aka ina juye juye, sai dai ban
fasa karanto innalillahi wainna ilaihir rajiun ba.
Yadda naga rana haka naga dare, barci ya
gagareni. Fargaba da tunanin haduwata dasu
uwani ta gallebe ni. Haka na kwana ban rintsa
ba saboda tashin hankali, don haka da asuba
kiran sallar farko na mike na shiga bandaki
nayi wanka, duk da sanyin ruwan ban damu da
saina dumama ba, na fito nayi sallar asuba na
kakaba kayan makaranta. Na dauki jakata na
dauko biro da takarda na rubutawa abida
wasika na ajiye takardar a bude akan
tabarmata yadda zata gani daga shigowarta.
Na fita daga dakin ina sanda tamkar barauniya
nayi sauri na fice, da yake kofar gidan a bude
take maza masu zuwa masallaci sun bude. Na
rufe fuskata saboda kada inci karo da mazan
gidanmu, duk da banji motsin fitowar yayana
ba, daga dukkan alamu kafar ta matsa masa
da ciwo tunda bai fito sallar asuba ba, dan
baya fashi in dai lafiyarsa kalau. Sai nayi ta
tafiya da kafata sabida rashin babura
kasancewar gari bai waye ba duku duku ne. Na
dade ina takawa da kafata sannan Allah Ya
jeho min mai babur na hau, mun dade da fara
tafiya ba tare da nasan inda zance ya kaini ba.
Ya sake tambayata malama ina zan kai ki? Da
farko nace masa asibitin aminu kano, har
munyi nisa na canza shawara nace ya kaini
jakara, umguwarsu ummi wato gidan iyayenta.
Muka isa kofar gidan na sauka daga kan acaba
sannan na biya shi kudinsa. Abinka da cikin
gari 'yan gargajiya basu san baccin safe ba
kowa ya tashi ya shiga safgoginsa. Mai kosai
ta ta fara suya, masu waina suna danawa.
Haka masu koko da masu shayi da biredi sun
fara tafasawa. Duk inda ka waiga yara ne
dauke da 'yan kwanuka a kansu an aiko su
sayan abin karin kumalllo. Na shiga cikin
gidansu ummi cike da fargabar abinda zanje in
tarar, ummin na iske a tsakar gida ita kadai ta
saka buta a gaba da alama alwalla za tayi,
tunani da damuwa sun hana ta sukuni. Ta
buga tagumi kamar mai tunani yayin da
idanuwanta sukayi luhu luhu. Tayi matukar
firgita data daga ido ta dubeni , ta cika da
mamakin ganina a daidai wannan lokacin. Ta
fada cikin firgici aisha umar lafiya? Sai na fara
zubar da hawaye shar shar shar daga
idanuwana. Ta mike tsaye da sauri taja
hannuna zuwa dakin da take kwana, a cike
yake da yara daga dukkan alamu kannenta ne,
yara 'yan kuci kuci da masu dan wayo.
Kowannensu barci yake da munshari yayi da
zarnin fitsarinsu da warin daudar jikinsu suka
daki hancina. Kamar inyi amai, na dai daure na
zauna akan wata dakwalkwalalliy ar katifa da
ummin take kwana don naga 'yarta a shimfide
a gefe. Anan tace in zauna bari taje tayi alwala
tayi salla sai tazo mu zauna. Kallonta kawai
nakeyi tamkar gunki na kasa magana, na dubi
yaran da suke linkaya a cikin fitsari babu
abinda ya dame su. Naji dama nice su nake
linkaya a cikin fitsarin nan da irin wannan
rayuwa da na jefe kaina. Ba jimawa ummi ta
shigo sanye da hijabi da alama ta idar da
sallah ko addua batayi ba sabida rashin
mutuswar dake tattare da ita. A firgice ta shigo
tana sauri kamar zata ci da kai, ta goya 'yarta
duk da himilin fitsarin da ta ci a napkin, zarni
kwar. Tace in taso mu tafi gidan malam. Na
mike da sauri muka fice ba tare da ta leka
dakin mahaifiyarta tayi mata sallama ba. Tafiya
muke fankam fankam tamkar fatake, muna tafe
muna tayar da kura kamar shanu, mu dukanmu
hankalinmu a tashe. Na juya na dube ta nace
ummi malamin nan kuwa yana da gaskiya?
Nifa har yanzu banga komai ba. Ummi ta tabe
baki tace uhmm ke dai bari. Ai shiyasa nake so
muje mu ritsa shi kafin ya gudu, macucin
banza. Kinsan mijina ya sake ni kuwa? Korar
kare yayi min fa. Na zabura na dafe kirji nace
au daman kinsan macuci ne kika kaini wurinsa.
Tace ke dai muje muji abinda zai ce mana. Na
fada a bayyane innalillahi wainna ilaihir rajiun.
Allah ba Ya dorawa bawanSa abinda ba zai iya
ba sai dai bawa ya dorawa kansa. Ina zan
sami himilin kudin da na ranta in biya masu
shi, ummi yaya zanyi? Ummi ta dubeni a
fusace tace to ni kinsan irin zaryar da ake yi
min a gidanmu saboda bashi? Ke dai kawai
Allah ya rufa mana asiri. Na fusata nace babu
wanda ya taba saka ni a tozarci da tashin
hankali a rayuwata irinki. Ta harare ni tace dan
Allah aisha ki rufe min baki, gara kema baki
aure shi ba balle ya sake ki, nifa har da goyo,
na zama bazawarar karfi da yaji. Haka dai
muka tafi muna ta fada a hanya kamar zamu
cinye kanmu a cikin bus. Tana jin haushina ni
har nafi jin haushinta fiye da malamin ma.
Muka iske shi a zaure yana ganawa da wasu
guda biyu da alama hamshakan masu kudi ne,
daga ganin motar da suka zo da ita da kuma
kayan da yake jikinsu. Malam yana ganinmu
sai ya bata rai, bai amsa gaisuwarmu bai sai
bakinsa ne suka amsa. Muka wuce jikinmu a
sanyaye zuwa cikin gidan, da kyar daya daga
cikin matansa ta bamu tabarma muka zauna
sai wani irin kallon banza suke yi mana dan
suna suyar dakwalen kajin da aka karba daga
wajen mutane na sadaka amma suke juyewa a
cikinsu babu wata sadaka. Shi da iyalansa sun
zama tika tika saboda da cin kaji da raguna da
suke karba da sunan za'a rabawa almajirai. Na
zunguri ummi na nuna mata kajin da ido, ta
gyada kai ta fada a hankali tace eh kudinmu
ne, ai yau sai na masa rashin mutunci. Can
malam ya shigo ko kallonmu baiyi ba ya wuce
dakinsa, yayin da matarsa daya ta dinga
wucewa da abinci kala kala tana kai masa,
kamar shayi, kaji soyayyu, wainar kwai da
biredi. Mu dai muna zaune muna kallon ikon
Allah. Su kayi kasonsu a faranti yara da manya
suka dauka kowa yana ci babu ko sala daya da
suka bamu. Malam yaci ya gyatse, yazo ya
wuce ya shige wanka. Ya fito ya shiga daki ya
fesa kwalliya da farar shadda mai kyau sannan
yazo ya wuce ciki daki in da yake ganawa da
baki. Sannan ya aiko matarsa yace ta kiramu.
Muka shiga muka iske shi a tsaye a tsakiyar
dakin, muka sake gaishe shi ya amsa a
gaggauce. Yace daman yau mu kayi daku zaku
dawo? Haushi ya kama mu, sai ummi ta kalle
ni, nima na kalle ta sai ta murguda baki tace
yau ne laraba ko? Kuma yau kace mu dawo. Ya
kalli agogo yace kuma ce muku nayi kuyi
sammako? Ummi ta fada a fusace, kamawa
tayi ka ganmu yanzu kasan ba lafiya ba. Ni dai
ina zaune a lungu nayi kuri ina kallon irin
wannan damfara kiri kiri, a lokacin da zai karbi
kudinmy yana fara'a yanzun da muka zo karbar
aiki rai ya baci. Ummi tana durkushe tana
kokarin sakko da goyonta. Sai yace ba sai kin
sauke goyonki ba yanzu zan sallame ku akwai
inda zanje don sauri nake yi. Ummi tace ko
yanzu zaka sallame mu ai na sakko da 'yata
tasha nono ko? Tunda ta farka tana kuka. Yace
meye ma yake tafe daku? Ummi ta waigo ta
sake dubana tace kinji ya manta ma. Saina
sankare a zaune na tabbatar mun fada hannun
mayaudati kamar yadda kawayena khadija da
maryam suka fada. Ummi ta sake cewa malam
gaskiya komai ya kwabe tsakanina da mijina,
har ya sake ni. Ga kawata ma taji shiru bai zo
ba. Yace kuje zan bincika naga abinda yake
faruwa, amma aiki dai na gama. Ummi tace
wanne bncike kuma, kai da ka mance abinda
muka fada maka. Ya zazzare mata ido yace ke
ba'ayi mana tsiwa ana kibi a hankali. Ummi ma
ta zare masa ido tace tsiwwa ko zance
gaskiya? Ni dai ba zan gidan nan ba sai an san
abin da za'ayi, kudin da muka biya a banza
kenan, bashi muka ciyo muka kawo maka.
Aisha farida kiyi magana kyayi shiru. Na fada a
sanyaye mai zance ummi? Ya jawo wata jakar
leda a fusace sai ga daurin rubutu kashi kashi,
ya miko min daya ya mikawa ummi daya, ya
sake kwance wata ledar ya miko min laya daya,
ya mika mata daya. Duk iri daya ce. Yace kuje
kusha rubutun nan a tsaye, sannan ku kasance
layan nan a jikinku sai kuyi kokari ku hadu da
mazan da kuke so, ku tambayesu duk abinda
kuke so daga gare su zasu yi muku. Ummi ta
karba ta tabe baki tace mu fa ba wani abu
muke nema a wajen mazan ba illa soyayyarsu.
Yace to ai haka nake nufi ko soyayya ko kudi
duk zasu baku. Na zuba abubuwan daya bani a
cikin jakata na mike tsaye nace da ummi taso
mu tafi. Ta mike a fusace tace zamu tafi
malam, sai dai gaskiya idan bamu ga canji ba
zamu dawo, asan abinyi dan bangane irin
wannan aikin ba. Muka fice yayin da ya bimu
da harara, muka fito tsakar gida dukkanin mu
rai a bace. Matansa sunyi carko carko suna
kallonmu domin suna jiyo duk abubuwan da
ummi take fada. Ta harare su tace Allah Ya isa
kudinmu da ake damfarar mu ana cin kaji, ko
wacce shegiya tayi bul- bul da abincin haram.
Ni dai nayi wuf na fice kada a biyo mu da duka,
har zaure suka rako ummi suna zaginta tana
zaginsu. Naja hannunta muka tafi, a hanya ta
fashe da kuka don takaici, ni kukan ma na kasa
yi sabida tsananin tashin hankali. Tace dani
aisha kinga macutan malamai ko? Wallahi ni
ban taba kula da cutar da wannan dattijon yake
min ba sai yau. Duba kiga yadda komai ya
dagule mana. Nayi ajiyar zuciya nace yanzu
ummi meye abinyi? Tace kije wajensa ki gwada
ki gani bayan kin sha rubutun kin daura layar.
Nima yanzu gidan yassar zanje in gani ko zai
kula ni, idan abinda ya bani bai yi aiki ba
wallahi sai na dawo na tarawa malamin nan
mutane. Nace kina ganin wannan rubutun da
layar daya bamu ta gaskiya ce? Ta wa da naki
fa iri daya ne, babu wani suna daya tambaya
balle ace kowa daban, rubutun ma daga gani
ba namu bane saboda baiyi niyyar bamu komai
ba sai da yaji kince babu inda zakije idan baiyi
wani abu ba sannan ya bamu. Tace ke dai
muje mu gwada mu gani. Mukayi sallama na
hau acaba zuwa asibitin malam ummi kuwa ta
hau bus zuwa unguwar zango gidan yassar. Ina
sauka na bude jakata na zaro kullin runutu na
tashi tsaye kamar yadda ya umurce ni na
shanye, yayin da na ciro layar nan na damke a
hannuna na nufi ofishin sahibina. Ina mai
karanto adduoi don neman dacewa. Zuciyata
cike da fargaba. Na tura kofar ofishin a
sanyaye gami da yin sallama, zazzakar
muryarsa ce ta amsa sannan na tura kai na
shiga. Kallo daya yayi min ya dukar da kansa
kasa bai sake dagowa ba yaci gaba da rubuce
rubucensa. Na gaishe shi ya amsa a shelake
yayin da fuskarsa babu annuri. Na dade a tsaye
bai ce dani komai ba kuma yaki dagowa ma ya
kalle ni. Nayi ajiyar zuciya na tambaye shi a
tsorace dr lukman ya zo kuwa? Da yazo da
baki ganshi ba. Amsar da ya bani kenan. Nace
likita ina da tambaya game da kurajen fuska.
Sai yace dani ke fita ki bani wuri, nan ba
ofishin dr lukman bane, ya koma ofishinsa a
room 8 an gama masa gyaran, kada ki sake
shigowa nan nemansa. Nayi sadan sadan na
fice, na dade a tsaye a bakin kofar daga waje
ina takaici tamkar in rusa ihu. Sai wata zuciyar
ta raya min ko in saka layar a bki in tauna zata
fi aiki. Sai na zura ta a baki ina taunawa na
sake tura kofar na zura kaina ciki. A tsaye a
tsakiyar ofishin na iske shi yana duba wani
littafi a jikin durowar littattafan dake kusa da
bakin kofar. Nace dan Allah likita zan iya bar
ma sako ka bawa dr lukman? Naje ofishinsa
baya nan..... Ban rufe bakina ba naji ya banko
kofar ya rufe booom saura kada ya bame da
fuskata, ba dan na daka tsalle nayi baya ba,
daya illata ni. Tunda na kalli kofar waje
bansake waiwayr ofishinsa ba, na saka a raina
ni dashi har abada koda kuwa zan mutu banyi
aure ba a duniya dan wannan wulakancin ya
isa. Naji na tsane shi na tsani kaina. Na tsani
ummi da ta saka ni a hanyar halaka kuma na
tsani malamin daya cuce ni ya tagayyara ni. Na
toho da layar daga bakina na farke ta saiga
takadda a ciki babu abinda yake ciki sai zanen
wani hatimi mai gida gida an rubuta alifun,
ba'un, ta'un kawai aciki. Na fusata na yayyaga
kuci kuci na watsar yayin da kuka ya turnuke
ni. DUK KYAN TAKALMI 14 Kawata ummi
wacce na taba baki labari tana son wani
malamin mu a sakandirw abdulyasar shi kuma
baya son ta amma daga baya ya fara sonta har
ya aure ta, ita na tuntuba don ta bani shawara.
Sai tace dani malamai ne suka yi mata aiki,
dole akayi masa yazo ya aure ba a hayyacinsa
ba. Don haka sai ta jani wajen malaminta ya ce
in kawo masa naira dubu ashirn da biyar zaiyi
min asirin da dr shureim zai zo har inda nake
da kansa, ya aure ni. Dogon salati abida ta
dauka ta dafe kirji tace farida boka? Me ya
kaiki bin bokaye akan wannan 'yar karamar
matsalar? Sai na daga ido da sauri na dube ta,
ina mamakin yadda ta ambaci matsalata 'yar
karamar matsala. Nace a raina lallai abida bata
san yadda dr shureim take ba da yadda
halayensa suke ba shiyasa take ambaton haka.
Abida ta dora hannu aka tace innalillahi wa
inna ilaihir rajiun. Aisha farida kinyi kuskure.
Wai shin ina wayon nan naki? Ina dubarunki?
Ina iya zama da jama'ar da kika koya daga
wajen magabatanki? Ai wannan matsalar taki
karama ce. Ke kika zamar da ita babba gashi
kin cuci rayuwarki duniya da lahira. A duniya
kin jawowa kanki bashin da zai kaiki zuwa ga
kotu a daure ki, kin dauko hanyar rugurguza
karatunki. Sannan kin taba lahirarki domin
ibadae ki ta ragu saboda damuwa da kika jefa
kanki, kinje wajen boka mai duba wanda Allah
Ya haramta, duk wanda yaje wajen mai duba,
mai zuba wuri ko mai bugun kasa kuma ya
gasgata abin da ya duba ya fada masa tabbas
bashi da sallah har kwana arbain , Allah ba zai
karba ba. Idan kika mutu a tsakanin wadannan
ranakun me zaki cewa Ubangijinki? Kin zama
makaryaciya domin karairayi iri iri kike
shirgawa wanda ada ba halinki bane kuma
kinsa makomar makaryaci wuta ce. Baki kyauta
min ba farida da baki fada min matsalarki ba
har sai da komai ya cabe. Na girgiza kai nace
na hakura da dr shureim yadda iyayena suka
bar duniya na san na rabu dasu har abada
haka na rabu da shi daman bai san abinda
nake yi ba. Wallahi anty abida ba da ganfan na
dorawa kaina sonsa ba haka na tsinci kaina,
nima ba da son raina ba. Abida tace haba haba
kamar yaya zaki hakura dashi bayan wadannan
bala'I da kika fada a dalilin sonsa ai ba zai tafi
a banza ba. Nayi miki alkwarai da izinin Allah
(SWT) sai kin sami soyayyar dr shureim cikin
ruwan sanyi. Na kasa kunne ina sauraron
maganar abida tamkar tatsuniya. Na dauke ta
a matsayin mai iya zance don hankalina ya
kwanta kawai. Duk da nasan babu abin da ya
gagari Allah, amma abin da kamar wuya wai
gurguwa da auren nesa. Abida ta luta da
tunanin da nake yi a zuciyata ta ga alamar ban
yarda da abubuwan da ta fada min ba. Tace
aisha farida kin manta da yadda akayi na auri
yayanki hussaini? Kin manta ra'ayinsa na son
girma ba zai auri kanwarsa ba a lokacin da
iyayenmu suka yi sha'awar hadamu aure yake
kokarin bijirewa? Kin manta yadda muka fara
zama dashi a gidan nan, ni dake muna
tsoronsa ko muryarsa muakji jikinmu sai ya
dau rawa muna guje guje? Yaya kika ga
zamana dashi a yanzu? Bari in fada miki
abinda baki sani ba farida, yayanki hussaini a
tafin hannuna yake yanzu idan naso in daga shi
sama, idan naki sai in kifa shi kasa ya fado.
Yaya hussaini a halin yanzu baya iya bacci
idan ina fushi dashi sai ya bani hakuri na
hakura sannan hankalinsa yake kwanciya.
Hussaini baya boye min komau na game da
samunsa, baya boye min duk halin da yake ciki
na game da abokan sa zuwa danginsa balle
'yan matan waje domub mazan zamaninan
ba'a rasa su da 'yan matan zamani, ko basu ce
suna sonsu ba su 'yan matan zasu kawo
kansu. Ki tambaye ni ya akayi haka ta faru? Ta
ina na samo kansa? Farida wallahi ban taba
zuwa wajen wani boka ko malami ba nace ina
neman a mallake min hussaini. Mutane suna
mamakina yadda nake tankwasa hussaini yake
yin abinda nake so, har wasu kawayena da
'yanuwana suke tsokana ta wai ina hada su da
malamina wanda ya tankwara min hussaini.
Idan na fada musu ban taba zuwa wajen wani
malami ba a rayuwata sai suki yadda. Aisha
farida bana addua har karshen rayuwata in
taka kafata wajen wani malami ko boka don
yayi min adduar mallaka. Ina daga hannayena
sama in roki Allah Ya mallaka min mijina, mu
zauna lafiya, yasoni kamar yadda nake sonsa.
Na girgiza kai nace na fada cikin kuka anty
abida na hakura da dr shureim saboda bai san
halin da nake ciki ba, mutumin da baya kallon
fuskata baya amsa min gaisuwata, ta yaya zai
soni? Kawayena guda biyu har mota gare su
kyawawa ne, ko khadija bata fini kyau ba.
Maryam ta fini kyau suma dole suka gaji da
wulakancinsa suka hakura dashi. Na rasa
yadda zanyi in daina sonsa duk da adduoin da
nake kwana ina yi don Allah Ya yaye min sonsa
amma sai karuwa yake yi na fada tsaka mai
wuya, hatta da karatuna ya tabarbare saboda
sau biyu supervisor dina yana zuwa yana duba
ni daga makarantar mu bana nan. Don haka na
san in banyi da gaske ba dole sai na maimata
attachment dinnan wata shekarar. Ko a littafi
ban taba karanta labarin wacce ta fada irin
wannan matsananciyar soyayyar da na fada ba,
makauniya kuma gurbatacciyar soyayya don
bai san dani ba balle ya san abinda nake yi ba.
Sai na rushe da kuka. Abida tayi murmushi ta
dafa kafada ta sai ta girgiza ni tace haba
farida, ke macece fa, dama akwai wani da
namiji da zai baki tsoro duk haduwarsa? Ina so
ki yadda da kanki, ki dauka duk in da wata
mace ta je zaki iya zuwa, ki dauka duk abinda
tayi zaki iya yi. Ki manta da farar fatar
baturiyar da yake aure, ke bakar fata sai ki fita
a wajensa. Sai naji abida ta fara bani haushi da
wadannan maganganun nata masu kama da
almara. Na rasa yadda zanyi in fahintar da ita
waye dr shureim. Na tambaye ta cike da
damuwa ta yaya zan samu soyayyarsa, har
nafi baturiya farar fata da yake matukar so? Na
fada miki fa bai sanni ba, yana dai ganina daga
dukkan alamu ma ya tsane ni da zara ya ganni
yake hada rai. Abida ta sake yin dariya tace kin
manta kissar matan nan da akayi mana a
makarantar islamiya? Kin manta matar nan da
take wajen malami ta nemi da ya bata abinda
zata mallake mijinta. Kissar ta rabu gida biyu,
an samu sabanin malamai, sabanin malamai
kuwa rahama ce duk dai abu daya suke
nunawa. Na farko aka ce ta da ta fadawa
malamin cewar maganin mallaka take so ya
bata, sai ya umurce ta data je cikin daji ta
nemo masa gashin idon zakanya mai rai da shi
zai hada mata asirin mallaka. Matar nan ta
firgita da jin wannan babban aiki sai tace dashi
malam ina zanje in samo gashin idon zakanya
mai rai ai bazata bari a tsinka ba saboda
fadanta. Cinye mutane take yi. Malam yace shi
dai gaskiya saida wannan gashin zai iya hada
mata wannan magani. Matar nan ta tashi ta
koma gida zuciyarta cike da zullumin tadda
za'a yi ta iya cirar gashin idon dabbar da tafi
kowacce irin dabba a duniyar nan hatsari. Da
farko sai taje kasuwa ta sayi rago aka fede
mata ta dauki himilin nama ta shiga dawa, tana
hango zakanya da 'ya'yanta daga nesa suka
fita neman abinci sai taje bakin ramin ta ajiye
mata naman nan ta gudu ta labe. Da zakanya
ta dawo sai ta iske abinci lafiyayye a kofar
dakinta ita da 'ya'yanta suka taru suka ci.
Washe gari ma haka matar nan ta kawo
gyararren rago ta ajiye mata bayan ta tafi kiwo
ta sake labewa bayan ta ajiye. Zakanya taje
neman abinci ta dawo ta iske abinci har gida
suka ci ita da 'ya'yanta. Haka matar nan ta
dinga yiwa zakanya sai dai su dan matsa daga
bakin ramin don su dawo su tarar da abinci. Da
zarar sun matsa kuwa matar sai tazo ta ajiye
musu sai su dawo su tarar da abinci kamar
kullum. Zakanya ta tabbatar lallai kawai wata
mai kirki da take kyauatta mata dan haka ko
sanda taga matar ta ajiye mata abinci bata
biyo ta nemi ta lahanta ta ba. Ba sai dai tazo
taci kawai. Har suka fara sabawa tana ajiye
mata abinci a gabanta bata guduwa. Har ta kai
ta kawo matar ta fara shafa jikin zakanyar nan
bata motsawa. Tayi ta shafata don sabo har
ranan matar ta samu ta tsigi gashin idon
zakanya ba tare da zakanyar taji zafi ba. Mata
ta kaiwa malam gashin nan ya karba ya duba
ya tabbatar gashin idon zakanya ne mai rai
don yaga jini jini a jikin gashin. Sai ya cika da
mamaki ya tambayeta ta yaya akayi ta samo
gashin? shine ta bashi labarin yadda tayi.
Malam yace to haka zakije ki yiwa mijinki
kamar yadda kika yiwa wannan zakanya babu
wata mallaka da tafi hanyar nan da kika bi kika
saba da zakanyar nan. Na tambaye ta cike da
damuwa ta yaya zan samu soyayyarsa, har
nafi baturiya farar fata da yake matukar so? Na
fada miki fa bai sanni ba, yana dai ganina daga
dukkan alamu ma ya tsane ni da zara ya ganni
yake hada rai. Abida ta sake yin dariya tace kin
manta kissar matan nan da akayi mana a
makarantar islamiya? Kin manta matar nan da
take wajen malami ta nemi da ya bata abinda
zata mallake mijinta. Kissar ta rabu gida biyu,
an samu sabanin malamai, sabanin malamai
kuwa rahama ce duk dai abu daya suke
nunawa. Na farko aka ce ta da ta fadawa
malamin cewar maganin mallaka take so ya
bata, sai ya umurce ta data je cikin daji ta
nemo masa gashin idon zakanya mai rai da shi
zai hada mata asirin mallaka. Matar nan ta
firgita da jin wannan babban aiki sai tace dashi
malam ina zanje in samo gashin idon zakanya
mai rai ai bazata bari a tsinka ba saboda
fadanta. Cinye mutane take yi. Malam yace shi
dai gaskiya saida wannan gashin zai iya hada
mata wannan magani. Matar nan ta tashi ta
koma gida zuciyarta cike da zullumin tadda
za'a yi ta iya cirar gashin idon dabbar da tafi
kowacce irin dabba a duniyar nan hatsari. Da
farko sai taje kasuwa ta sayi rago aka fede
mata ta dauki himilin nama ta shiga dawa, tana
hango zakanya da 'ya'yanta daga nesa suka
fita neman abinci sai taje bakin ramin ta ajiye
mata naman nan ta gudu ta labe. Da zakanya
ta dawo sai ta iske abinci lafiyayye a kofar
dakinta ita da 'ya'yanta suka taru suka ci.
Washe gari ma haka matar nan ta kawo
gyararren rago ta ajiye mata bayan ta tafi kiwo
ta sake labewa bayan ta ajiye. Zakanya taje
neman abinci ta dawo ta iske abinci har gida
suka ci ita da 'ya'yanta. Haka matar nan ta
dinga yiwa zakanya sai dai su dan matsa daga
bakin ramin don su dawo su tarar da abinci. Da
zarar sun matsa kuwa matar sai tazo ta ajiye
musu sai su dawo su tarar da abinci kamar
kullum. Zakanya ta tabbatar lallai kawai wata
mai kirki da take kyauatta mata dan haka ko
sanda taga matar ta ajiye mata abinci bata
biyo ta nemi ta lahanta ta ba. Ba sai dai tazo
taci kawai. Har suka fara sabawa tana ajiye
mata abinci a gabanta bata guduwa. Har ta kai
ta kawo matar ta fara shafa jikin zakanyar nan
bata motsawa. Tayi ta shafata don sabo har
ranan matar ta samu ta tsigi gashin idon
zakanya ba tare da zakanyar taji zafi ba. Mata
ta kaiwa malam gashin nan ya karba ya duba
ya tabbatar gashin idon zakanya ne mai rai
don yaga jini jini a jikin gashin. Sai ya cika da
mamaki ya tambayeta ta yaya akayi ta samo
gashin? shine ta bashi labarin yadda tayi.
Malam yace to haka zakije ki yiwa mijinki
kamar yadda kika yiwa wannan zakanya babu
wata mallaka da tafi hanyar nan da kika bi kika
saba da zakanyar nan. Don haka babu wani
asiri da ci idan babu biyayya, na kaskan da kai,
ba tsabta, ba kalamai mai taushi tsakanin mata
da miji. Nima nan da kika ganni da wannan
kissar nayi amfani har na sami hussaini tamkar
jaririn da sai an dauka, sai an juya, haka zaki bi
ki samu soyayyar dr shureim. Na dube ta a
shelake nace ta yaya? Ta nisa tace zan fada
miki abubuwa guda biyar idan kika kiyaye zaki
sami shureim a garabasa ba tare da kin wahala
ba, kamar kibtawar ido da bismillah. Fardida
duk inda namiji ya kai da ji da kai, da daga kai
karshensa dai mace zai aura kuma dole ta
bautar dashi ko yaki dan kada ya bare sai yayi
dan Allah Ya wajabta akansu dole suyi. Dole ne
miji ya ciyar da matarsa, dole ne tufatar da ita,
dole ya nemo mata muhalli, dole ya kai ta
asibiti idan bata da lafiya. Idan aka sami marar
tsoron Allah wanda ba zaiyi dan Allah ba to
zaiyi ko dan kada duniya ta zageshi. Dan idan
ya bar ta cikin tsumma, ba abinci za'a nuna ta
agari ace matar wane ce baya kula da ita. Dan
haka DUK KYAN TAKALMI, duk tsadar takalmi,
ba za'a daura shi a wuya ba ko a goshi ba,
dole kafa za'a saka kuma a taka a kwata,
shiga daji, a shiga bandaki, a tako kazanta, a
taka bola ko a tako kaya dashi. To haka dr
shureim zai zama a wajenki da izinin Ubangiji,
babu boka babu malam. Naji tamkar tana busa
mi sarewa a kunnuwana saboda dadadan
bayananta, na gyara zama nace meye abu
biyar din da zan kiyaye....? Ban rufe bakina ba
sai muka ji ana buga mana kofa kamar za a
karya, hayaniyar matan da muke jiyowa daga
nesa ya matso bakin kofar dakin mu. Fadi ake
ke aisha farida, ki fito ko a balle kofar nan.
Yaya zakici kudin mutane ki shiga daki ki buya,
ga 'yan sanda nan an kira su, suna kofar gida
za'a tafi dake. Ko ki bude ko a kirawo su, su
shigo ciki su tafi dake. Na dora hannu aka na
fashe da kuka nace anty abida yaya zanyi? Na
shiga uku , yanzu ankwa 'yan sandan nan zasu
saka min su wuce dani ta gaban mutanen
unguwar nan ko kamar wacce nayi sata kowa
yana ganina ko? Hawaye ya zubo daga
idanuwanta itama, sai ta mike tsaye ta tashe ni
tsaye nima, ta dafa kafaduna da hannayenta
biyu. Tace kiyi ta karanta innalillahi wainna
ilaihir rajiun. Ki fita kice da yan sanda su rufa
miki asiri kamar yadda Allah ya rufa musu asiri,
su taimake ki kada su saka ki a gaba, zaki hau
babur kije can sai su same ki acan ba sai sun
saka ki a gaba ba. Nace ai bazasu yadda ba,
sai sun saka ni a gaba kamar wacce tayi sata.
Tace ke dai kici gaba da addua, ki fada musu
hakan zasu yadda. Idan kinje can ki basu
hakuri kice a baki kwanaki biyu zaki nemo
kudin ki biya su, ni kuma anan zan tilastawa
yayanki dole ko rance ne ya fita ya nemo a
biya su kudinsu kaddara ce ta hau kanki kada
ki damu. Kuma koda wasa kada ki sake ki
fadawa wani ko wata abinda kikayi da kudin
nan, dan kada ma labari ya dawo kunnen
yayanki kenje wajen boka, ki barshi a kawarki
kika taimakawa aka yi mata tiyata mijinta
bashi da hali, yafi sauki dan idan muka
kusukura mu ka bari yaji wannan labari sai ya
bata mana rai. Dazu na siyar da samiruna hudu
na biya su maijidda, dahare da dija dillaliya da
kikaje suma kika ranto kudadensu. Wata tace
dari takwas kika karba mata, wata dari bakwai,
wata dubu daya, suma na suka zo suke daga
min hankali suna nemanki danaji kudin ba yawa
sai na aika kasuwa aka karyar min da su nazo
na bibbiya su. Na uwani ne naji kudin da yawa
ba zan iya biya ba. Kiyi hakuri aisha farida, kiyi
ta istigfari game da wajen bokan da kika je,
kinyi wa Allah laifi kuma kiyi ma Sa alkawari
har ki koma gare shi ba zaki sake zuwa ba.
Kiyi ta karanta wannan adduar ta neman biyan
bashi "Allahumma bi jalika an haramika wa
agnani fadhlika amman siwaka". Sannan ta
bude kofa da sauri muka fito saboda bugun da
ake yi ya tsananta. Dandazon matan gidanmu
da matan unguwa da yaransu sun taru suna
kallona. Abida na rike da hannuna muna kuka
muka nufi hanyar waje. Muryar yaya hussaini
mukaji ya daka tsawa mai firgitarwa har sai da
kowa ya firgita. Yace da matarsa ta sake ni in
tafi ni kadai ta dawo daki inje can in karata ni
kadai. Ni da ita muka fashe da kuka. Ta
rungumeni sannan ta lalubo hannuna ta damka
min kudi naira dari biyu. Ta juya ta bar mi, sai
na cigaba da tafiya a sanyaye na fice yayin da
dandazon mata suke biye dani suna ta cece
kuce. Masu bada hakuri nayi, masu neman
ba'asi nayi, haka masu zuga nayi. Uwani kuwa
sai mayar da zancen take yi. In da Allah Ya
taimake ni duk sanda nazo wucewa ta ofishin
'yan sandar unguwarmu sai na duka na gaishe
su kullum, suna ganina suka gane ni nima na
gane su. Kalmar da suka fara ambato itace ah
kece daman? Ke kuwa yarinyar nan mai hankali
meya jawo kika shiga rigima irin wannan? Na
fashe da kuka nace ku taimake ni dan Allah ina
neman wata alfarma guda daya. Sai mai kivar
cike yace yarinya ai babu wata alfarma da
zamu iya yi miki anan, duk wata alfarma sai
dai ayi ta a ofishinmu. Tunda an riga an kira
mu dole mu tafi dake. Nace daman zanbi ku,
bana so ku saka ni a gaba da ankwa ku wuce
dani ta gaban mutanen unguwa yara suna bina
suna kallo kamar wacce tayi sata. Zan hau
babur ya kain ni sai mu hadu a can. Wallahi ba
zan gudu ba. Sai suka yi dariya suka ce idan
kin gudu ma ai zaki dawo, ba gamu a kofar
gidanku ba. Ko zaki shiga duniya ki bar
iyayenki saboda bashin da bai kai dubu ashirin
ba? Suka yi min izini na tari acaba na hau, duk
da babu nisa daga gidanmu. Na dan dade ina
jiransu sannan suka karaso, aka shiga da mu
uku ofishin mataimakin DPO, 'yan kallo aka
barsu a farfajiyar suka ci gaba da gulmace
gulmacensu. Saii a lokacin na gane makiyana
wadanda ada na dauka masu kaunata ne,
wadanda ada bana kulawa ashe sune masu
kaunata, sune masu jimamin abinda ya same
ni, sune masu nemar min afuwa a wajen
wadanda na yiwa laifi, sune masu fada har da
tayar da jijiyoyin wuya idan aka zage ni. Uwani
ta mayar da zance, haj rabi ma haka sai aka
tambayeni shin abinda suka fada gaskiya ne
kuwa? Na amsa nace haka ne, sannan na basu
hakuri gami da yin alkawari zan biya nan da
kwana biyu. Uwani ta zabura tace karya nakeyi
bani da ko kobo, don haka yace a kulle ni babu
ruwansa. Mataimakin DPO ya sake tambayata
haka aka yi? Na amsa masa da haka ne. Don
haka yace aje a kulle ni har sai yayana yazo
yayi belina kuma yayi alkawarin zai biya
sannan a fito dani, idan kuwa yaki zuwa sai a
kaini kotu alkali ya yanke min hukuncin dauri
daidai laifina.
DUK KYAN TAKALMI 2* 1