Sashe 32
Budurwar Mijina Part 1 Complete Hausa Novel · about 4 min read
A haka ya samu ya Koreta yana maida numfashi sai yake ganin kamar Lubna zata gane ya had'u da Hadeeza wayarsa ya d'auko ya Kira lubna Koda ta d'auka hira ya ringa janta dashi da alama ta fara saukowa dan ta dan biye Masa har take tambayarsa mai zata dafa mishi daddare sosai yake jinsa cikin farinciki saukowar da tayi hira Suka dan tab'a kafin ya kashe wayarsa ya sake alwala a bandakin office d'insa yayi sallah Koda ya iddar cire rigarsa yayi ya wanke a bandakin ya rage daga shi sai vest da dogon wando dan gani yake Yana zuwa gida lubna zata ji kamshin turaren Hadeeza a jikinsa a yanzu tsoro yake lubna ta gano Yana tare da Hadeeza bai san Mai yasa zuciyarsa taki bashi hadin Kan ya rabu da ita ba tana da tsara shi shikenan.
LUBNA
Tunda mahfuz ya kirani a waya ban Kara komawa bacci ba na tashi na nemawa kaina abinci naci na gyara ko'ina nayi wa mimi wanka na dawo Palo na zauna haka kawai nake Jin wani irin kadaici da ace a wancan unguwar muke da yanzu na Shiga gidan mmn Iman mun Sha hira.
Wayata na dauka dan na kirata Ina kuwa kiranta tace min yanzu takeso ta kirani akan ta shigo layin gidana.
Kasa hakura nayi ta shigo na fita waje na tsaya har ta karaso cikin farinciki na rungume ta mmn Iman nada wani irin matsayi a zuciyata Ina kaunarta sabida tana kaunata duk wani abu da ya shafeni tana daukarsa da mahimmanci damuwata damuwarta ce, duk da ta girmeni ko jinina ce ita sai haka.
Hira muka barke dashi ta hau tsokana ta akan nayi fresh anya daga dawowata mahfuz bai yiwa Mimi kanwa ba,nariga da nasan halinta ban biye mata ba
Na Shiga kitchen na dora Mana abincin muna hira Ina girkin har na sauke na zubo Mana muna cikin ci nake bata labarin duk abinda ya faru daga dawowata gidan har ganin da mukayi wa Hadeeza jiya da wani ban b'oye mata komai ba
Cokalin hannunta ta ajiye tana "Lubna ki ajiye duk wani fushi ki cire komai a ranki a yanzu ya Kamata ki zage wajen kyautatawa mahfuz wlh yarinya nan shaidaniya ce,duk da kince ya mata kashedi a gabanki zata yi duk abinda zatayi dan ta dawo rayuwarsa ke Kuma kisan yanda zakiyi ki hana hakan faruwa,yanzu balain da ake ta fama dashi kenan wlh shekaranjiya Abban Iman ya bani lambar wata da ta sako shi a gaba yace na kirata na nace mata ta daina kiransa a waya bakiga zagin da nayiwa yar iska ba,yau ma Yana Kira a wayarsa ya mikomin yace min itace tanajin muryata ta kashe"
"Toh mmn Iman ke mijinki Yana Sanki baya iya Miki boye boye,mahfuz bazai tab'a bani wayarsa na zagi Hadeeza ba wlh nasani,wane irin kyautata wa ne banyiwa mahfuz ba mmn Iman a karshe dai sai da yaci amanata har gida ya kawomin budurwarsa wlh ko yanzu na tuna sai naji zuciyata namin zafi, fushin mummy ne banaso shiyasa na bar shi ya samu nutsuwa dani,amma wlh na kasa manta abinda yamin"
"Idan har kina tunawa dole kiyita Jin zafi amma Ina shawartarki da ki manta da komai wlh mijinki na kaunarki shuumar yarinya ya hadu da ita"
Shawarari mmn Iman tayi ta bani ta bud'e Jakarta ta fito da lodin magunguna mata akan na ringa amfani dasu,na jawo mijina jikina na yafe Masa abinda yamin tariga da tasan bazan iya mantawa ba amma na daure.
Muna taren mahfuz ya kirani, ita ta ringa min rada har na biyewa mahfuz muka tab'a hira har na tambayeshi abinda zan dafa yace na dafa koma mene zaici.
Ina jin farinciki a muryarsa har ya kashe wayar sai ga text dinsa nan a wayata
Zuwan mmn Iman da shawawarinta ya faranta min sosai hakane yasa na cire komai a raina na Kuma dauki shawararta akan na sake karkato da hankalin mahfuz kaina.
Magungunan da ta kawomin wayanda zan iya sha na Sha na matsewa na matse nayi abincin da yake so karfe shidda ya dawo da kwalliya ta yazo ya Sameni.
Sakin fuskar daya samu da tarbar da na mishi yasa sai da ya samu nutsuwa dani har mamakinsa nake dan kamar karo jarraba yayi.
A ranar guduwa ne banyi ba dan sai daya kusa fanshe watani da baiyi ba.
A wanan gabar na Kara jawo mijina jikina duk wani abu na kyautatawa Ina masa,lokaci zuwa lokaci shaidan kaso bijiromin da cin amanar da yamin sai nayi saurin yakicewa balle idan naga bai dawo da wuri ba.
Wayarsa kuwa Yana ajiyewa zan d'auka na hau Masa bincike duk binciikena dai ba abinda nake gani hakane yasa na saki jikina Ina tunanin dagaske ya rabu da Hadeeza.
Mahfuz......
LUBNA
Tunda mahfuz ya kirani a waya ban Kara komawa bacci ba na tashi na nemawa kaina abinci naci na gyara ko'ina nayi wa mimi wanka na dawo Palo na zauna haka kawai nake Jin wani irin kadaici da ace a wancan unguwar muke da yanzu na Shiga gidan mmn Iman mun Sha hira.
Wayata na dauka dan na kirata Ina kuwa kiranta tace min yanzu takeso ta kirani akan ta shigo layin gidana.
Kasa hakura nayi ta shigo na fita waje na tsaya har ta karaso cikin farinciki na rungume ta mmn Iman nada wani irin matsayi a zuciyata Ina kaunarta sabida tana kaunata duk wani abu da ya shafeni tana daukarsa da mahimmanci damuwata damuwarta ce, duk da ta girmeni ko jinina ce ita sai haka.
Hira muka barke dashi ta hau tsokana ta akan nayi fresh anya daga dawowata mahfuz bai yiwa Mimi kanwa ba,nariga da nasan halinta ban biye mata ba
Na Shiga kitchen na dora Mana abincin muna hira Ina girkin har na sauke na zubo Mana muna cikin ci nake bata labarin duk abinda ya faru daga dawowata gidan har ganin da mukayi wa Hadeeza jiya da wani ban b'oye mata komai ba
Cokalin hannunta ta ajiye tana "Lubna ki ajiye duk wani fushi ki cire komai a ranki a yanzu ya Kamata ki zage wajen kyautatawa mahfuz wlh yarinya nan shaidaniya ce,duk da kince ya mata kashedi a gabanki zata yi duk abinda zatayi dan ta dawo rayuwarsa ke Kuma kisan yanda zakiyi ki hana hakan faruwa,yanzu balain da ake ta fama dashi kenan wlh shekaranjiya Abban Iman ya bani lambar wata da ta sako shi a gaba yace na kirata na nace mata ta daina kiransa a waya bakiga zagin da nayiwa yar iska ba,yau ma Yana Kira a wayarsa ya mikomin yace min itace tanajin muryata ta kashe"
"Toh mmn Iman ke mijinki Yana Sanki baya iya Miki boye boye,mahfuz bazai tab'a bani wayarsa na zagi Hadeeza ba wlh nasani,wane irin kyautata wa ne banyiwa mahfuz ba mmn Iman a karshe dai sai da yaci amanata har gida ya kawomin budurwarsa wlh ko yanzu na tuna sai naji zuciyata namin zafi, fushin mummy ne banaso shiyasa na bar shi ya samu nutsuwa dani,amma wlh na kasa manta abinda yamin"
"Idan har kina tunawa dole kiyita Jin zafi amma Ina shawartarki da ki manta da komai wlh mijinki na kaunarki shuumar yarinya ya hadu da ita"
Shawarari mmn Iman tayi ta bani ta bud'e Jakarta ta fito da lodin magunguna mata akan na ringa amfani dasu,na jawo mijina jikina na yafe Masa abinda yamin tariga da tasan bazan iya mantawa ba amma na daure.
Muna taren mahfuz ya kirani, ita ta ringa min rada har na biyewa mahfuz muka tab'a hira har na tambayeshi abinda zan dafa yace na dafa koma mene zaici.
Ina jin farinciki a muryarsa har ya kashe wayar sai ga text dinsa nan a wayata
Zuwan mmn Iman da shawawarinta ya faranta min sosai hakane yasa na cire komai a raina na Kuma dauki shawararta akan na sake karkato da hankalin mahfuz kaina.
Magungunan da ta kawomin wayanda zan iya sha na Sha na matsewa na matse nayi abincin da yake so karfe shidda ya dawo da kwalliya ta yazo ya Sameni.
Sakin fuskar daya samu da tarbar da na mishi yasa sai da ya samu nutsuwa dani har mamakinsa nake dan kamar karo jarraba yayi.
A ranar guduwa ne banyi ba dan sai daya kusa fanshe watani da baiyi ba.
A wanan gabar na Kara jawo mijina jikina duk wani abu na kyautatawa Ina masa,lokaci zuwa lokaci shaidan kaso bijiromin da cin amanar da yamin sai nayi saurin yakicewa balle idan naga bai dawo da wuri ba.
Wayarsa kuwa Yana ajiyewa zan d'auka na hau Masa bincike duk binciikena dai ba abinda nake gani hakane yasa na saki jikina Ina tunanin dagaske ya rabu da Hadeeza.
Mahfuz......