← Book details Budurwar Mijina Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 16 OF 32

Sashe 16

Budurwar Mijina Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Sai da na gama jerawa na dauki balangun na juye a plate na dibar wa ummi na saka mata tuwo mulmule biyu da Miya na dauki karamin exotic na hada a faranti gabad'aya na Kai Mata har daki a kwance na tarar da ita da alama daga wanka ta fito dan jikinta da lema ta saka karamin t shirt da bakin dogon skirt,sai da gabana ya Fadi dana ga surarta take na karbi shawarar mahfuz na in maidata d'akin tsakar gida tab.

Tana ganina ta rarumo hijabi tasa ta tareni tare da karbar farantin hannuna tana "Sannu Aunty"

"Yauwa nace Mata cikin murmushi Ina ga abincin ki nan idan kin gama ci zanzo na Kai ki d'akin can Kamar sai kinfi sakewa acan"

"Toh Aunty ngd da dawainiya"

"Lah ba komai na sakar mata murmushi na fito daga d'akin.

Na Shiga nawa mimi ce kawai a kwance da alama mahfuz ya fita massallaci.

Wanka na Shiga dan tuni na watsar da wankan jego na koma normal wanka.

Ina fitowa daga bandaki yayi daidai da shigowar mahfuz bai d'auke idonsa akaina ba ya zuba min Ido

Nida kayana nasan hali, ya matsu yaga Ina sallah

"Mallama Wai har yanzu shiru nafara gajiya fa"

"Tab kwana ashirin kawai da haihuwa sai nayi arbain fa"

"Wlh baki isa ba tab so kike na mutu kenan ya zauna a gefen gado,na gama shafe shafena na saka kayan shan iska.

Ina sai kayi sallah zamuci abinci ko na zubo yanzu"?

Bari ayi sallah Isha Kar nazo na kasa tafiya massallaci.

"Tom mu tafi Palo mu zauna"

Na dauki Mimi nayi gaba ya biyoni a baya.

A Palo muka zauna Muna kallo muna tab'a hira Yana latsa wayarsa hankalinsa dai Yana Kan wayar gabad'aya.

Sai ni kedai ke zuba surutuna har aka Kira sallah Isha ya fita massallaci bai dawo gidan ba sai wajen tara daga zuwa massallaci abincin ma da na jera Mana ya hucce tuni na cika nayi fam zuciyata ta fara rayamin kodai zance yaje take naji hankalina ya tashi,Ina tsoron tsinaniyar yarinya nan Mai nacin tsiya ce ta dawo rayuwar mijina wayata na d'auko dan na kirashi sai gashi ya shigo,da carbinsa a hannu da jalabiyar sa.

"Daga zuwa massallaci abban Mimi"?

Ina k'ofar gida wlh da Hamisu muke ta hira da kin leko zaki ganmu ai

Sai a lokacin hankalina ya kwanta

Muna cikin cin abincin Muka ji motsin bud'e k'ofar d'akin sai ga ummi ta fito da dogon hijabinta har kasa mahfuz ko kad'an bai dago ba Ina k'ok'arin Magana tace "Aunty dama bacci nakeji shine nace ko Zaki nunamin d'akin"?

Mik'ewa nayi Ina sude hannuna nace "eee zomuje nama dauka kinyi baccin ne wlh'

Nayi gaba tana bina a baya har muka fice daga palon,dama d'akin duk da baa kwana a ciki Ina yawan gyarawa Ina Kuma turarawa sai dai ba bandaki a ciki, bandakin a tsakar gida yake idan nayi baki da bandakin tsakar gidan suke amfani ,Yan uwa ke Shiga bandakin cikin daki.

Muna Shiga d'akin nace "dafatan d'akin ya Miki"?

Kai sosai ma wlh yayi aunty ngd Allah yasaka da alheri"

"Lah ba komai ai an Zama daya sai dai nace sai dasafe kenan"

"Toh aunty sai da safe a shafa min Kan Mimi"

Da murmushi na amsa Mata na fito daga d'akin.

Sai da muka gama cin abincin na kwashe komai na Kai kitchen na dawo na tarar da mahfuz na latse latse a wayarsa.

Nima wayata na d'auko na hau latsawa Ina chatting Ina kallo kafin goma naji bacci ya fara k'ok'arin daukana.
Hakane yasa na kashe data na kalli mahfuz daya danke wayar sa da hannu biyu nace "Tom nidai bacci nakeji zanje na kwanta"

"Kije kiyi kwanciyar ki dan ni ba bacci nake ji ba ko na biki daki ciwon maran zaki sani a banza nidai na fara gajiya fa tam"

"Kazo muje mu kwanta na maka tausa wlh Zan maka dabaru"

"Naki fa kibar ni na cigaba da hira da abokina"

Ya hasko min fuskar wayarsa Inda naga sunan Abdul din da Abokina

"Ai shikenan sai ka shigo"

Bai bani amsa ba Ina shiga ciki na canza kayan jikina zuwa na bacci Ina kwanciya bacci yayi awon gaba dani bansan lokacin da ya shigo ba.

Washegari da wuri na tashi dan na hada breakfast dan mahfuz da wuri yake fita.

Ina cikin soya dankali naji sallamar ummi.

Na amsa Mata daga kitchen ina mamakin me ya sa ta tashi da wuri haka.

Har kitchen tazo ta sameni muka gaisa da ita Ina satar kallonta Ina San yanda take shigar hijabi har kasa da alama tana da kamun Kai

"Aunty Ina tsintsiya nayi shara"?

"Ummi dan Allah koma kiyi kwanciyarki dan kawai ki tayani aiki Kika taso"

"Dan Allah karki hanani tun jiya nakeso na tayaki kina hanani" karfe Tara zanje wajen da zamuyi program din shiyasa na tashi da wuri"

Duk yanda naso hanata ki tayi akan dole na nuna Mata wajen da tsintsiya yake ta d'auko ta fara share palon.

Har tsakar gidan naji tana sharewa.

Sai da ta gama ta Kara shigowa da bokitin mopping da abin mopping din tana cikin mopping mahfuz ya fito daga d'aki cikin shigar suit sai kamshin turare yake.

Adaidai lokacin da Nima na fito da farantin abincin karyawarsa.

Gaisuwar ummi ya amsa ba yabo ba fallasa ya tambayeta ya bakunta ta sunkuyar da Kai tana murmushi nidai idona nakanta atoh karta sake ta kallarmin miji ganin na ajiye farantin a gabansa yasa ta ajiye abin mopping din tana "idan ya gama na dawo na karasa"

Hankalinta na Kara gani,dan naga tana nesa nesa da mijina haka nakeso shima mijina ya iya tsare gida.

"Mai kike murmushi ke kadai"?

Tambayar da mahfuz ya jefomun kenan

"Wlh yarinya nan nada hankali mahfuz da gani ta samu tarbiyya sosai duk da a Lagos take zaune"

Tab'e baki yayi bai ce min komai ba Nima ban Kara magana ba har ya gama cin abincinsa
Ya Mike zai tafi na tafi dan na raka shi munje bakin k'ofa ya juyo Yana "Na manta ban fada Miki ba Abdul jiya yace na fada Miki wanan yarinyar ba komai ta iya ci ba ya roki arzikin a ringa tambayarta abinda zata ci ko a barta ta dafa abinda takeso dakanta wlh badan kin dage ba da sai na Masa rashin mutunci nida gidana azo ana min iko"

"Allah sarki wlh ba damuwa ai kana ganinta kasan Yar hutu ce ba irinmu da duk abinda muka samu ci zamuyi ba Tom ba damuwa ai tunda ba laifi muna da Abubuwan Yan gayu yanzu a gidan idan ma cornflask take so ta ringa Sha gashi nan"

"Ku kuka sani"

Yace a daidai lokacin da ya ida fitar da machine dinsa ya tayar ya tafi Ina daga masa hannu.

Ina komawa ciki na karasa mopping din na turara koina kafin na koma d'akin Ummi dan na tambayeta mai zata ci.

Kwalliya na tarar tanayi a lokacin da na Shiga tana ganina ta saki murmushi tana "so nake na shirya kar nayi latti"

"Kina nufin bazaki karya ba Zaki tafi nidai na soya dankali da kwai sai kayan shayi bansani ba kinaci ko bakya ci idan bakya ci sai a sama Miki wani abu dan Abdul yace Wai ba komai kike ci ba"

"Eee wlh aunty duk wani abu Mai maiko ban fiye ci ba da safe nafiso nasha corn flask haka ko bakin tea"

"Toh shikenan ki gama shiryawan akwai cornflask sai ki hada ki Sha"

Godiya tamin na sakar mata murmushi na fito.

Ban Dade da fitowa ba sai gata ta shigo da dogon hijabinta har kasa da farin glass.

Tana Zama na dauko mata kofi da cokali da tuni na ajiye Mata Madara da cornflask din

Cikin nutsuwa ta hada ta Sha sai satar kallona take narasa Mai yasa take San satar kallona.

Tana gama Sha ta mik'e da Yar Jakarta tana "Bari naje kar makara sai na dawo"

A dawo lafiya" ta fice daga gidan ni Kuma na koma daki.

Ina kwanciya mamn Iman ta hau bugun kofa tana kwallamin Kira

Ko mai take nema a wajena da sassafe haka oho na mike nayi hanyar waje........

Karku manta a gobe zamu gama free pages insha Allahu ku biya 500 ta 2029764071 first bank nafisa Nuhu ko ta Nan 0000551222 taj bank nafisa Nuhu ko katin mtn a turo da shaidar biya ta layin nan 08033719070 yanzu zamu shiga cikin labarin budurwar mijina karki sake a barki a baya

KAYAN MATA

Assalamualaikum kina mace hadaddiya komi kincika ama kinada nakasu tawurin dadadawa miji?

Shin kinkai kin isa kina gogayya d sauran mata Amma tafannin ozaroom mishkila tasamu?

Shin sanyi y addabeki tayanda Baki iya gamsarda miji kullum kina makalemai yana kauda Ido?

Shin minene matsalar?
Kinshiga ko Ina kinnemi magani bawani chanji?

Tosaurara yar uwata aminiyar arziki, ubangiji yakawo mikini har inda kike,kizo kiji qawata,

Inada maganin sanyi me fatattakar kowani irin sanyi duk fitinarshi d izinin ubangiji seyabarki,

Munada magungunan mata masu matuqar kyau,hadaddu gangariya kizama t gaban goshi,komi kikace oga yace don, 🥰 kikerewa sa'o'i, kizama abun riritawa abun tarairaya a kudi qalilan,karki cuci kanki kizauna kina cewa ayni nasan kaina,a inadin? Wallahi ko kanada kyau qara d wanka Kisha kiyi qattt kigigita oga,

Munada tsumi nau'i nau'i
Gumba ta madara,ridi,gyada,dabino,kwakwa,dasauransu
Akway ruwan jaraba
Ruwan Dadi
Hadin minannas
Hadin dafa kaza(manta uwa)
Hadin yar gaban goshi,
Turarukan mallaka.

Duk a farashi mesauqi.

Serious buyers call, WhatsApp 07046881166

Senajiku kusiya kuyi godiya Kuma kumin addua❤️nagode
*BUDURWAR MIJINA*

*NA SADNAF*

*E.W.F.*

*PAID BOOK*

*LAST FREE PAGE*

*PAGE 10*

Ina bud'e kofa na yamutsa fuska Ina "Shi bawa bazaa barsa ya huta ba"

"Eee baza'a barki ki huta ba wuce muje"

Dariya nasa dan muna Yar Wasa da mmn Iman sosai muna Shiga ciki ta zauna a dogon kujera tana kalle kalle nima na zauna a kujera mai kallonta Ina "kefa wani zubin kanki ba dadi Mai kike dubawa ne"

"Mai nake dubawa kuwa so nake na tabbatar da ba kowa a gidan kafin nayi magana duk da Naga fitar mahfuz da bakuwarki"

" Ba kowa dagani sai Mimi kin samo mai zafi kenan"?

Nace Ina maida hankalina gabadaya kanta dan Naga alamar da magana tazo Mai mahimmanci
Chapter 16 · 0% Book details