Sashe 3
Beelal Buk Part 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read
"Kai dalla ka rufewa mutane baki waye sa'anka a cikinmu? Ko dan ka ga ana ɗaga maka ƙafa, to bari ka ji na faɗa maka kai baka isa ka sa mu yi abin da bamu yi niyya ba, sai shegen surutun tsiya, ga wa'azi kamar wani limami, kai ga wanda mahaifiyarka ke koya maka sanin Allah da sanin ya kamata" Idrisu ya katse shi cikin ɗaga murya.
Shiru Beelal ya yi dan yadda Idrisu ya masa magana ya tsorata saboda da ƙarfi ya zafice shi dan haka sai ya ja bakinsa ya yi shiru.
"Baaba na ɗakko keken nan fito ka gani, ko a san a bin yi ka san maganin abu a yi shi" Imran da ke can waje ya faɗa da ɗan ƙarfi.
Haka Idrisu ya fito daga cikin shagon yana washe baki, ya baro Beelal a can ciki.
"Kai gaskiya abokina ka iya bada shawara to ka ga wannan da babu shi ma sai mun nemo amma tun da gurgu ya bar wa ɗan uwansa gurgun mage gado ka ga mun huta da nema" Idrisu ya faɗa yana kallon tsohoh keken guragun da ya ya tsufa jikinsa duk tsatsa.
"Eh mana, ai mu gaba ta kaimu gobarar titi, kai kana ina fito dalla ka zauna a ciki kamar wanda kake ganin dodanni" Imran ya faɗa yana kiran Beelal da bai fito daga shagon ba.
"Ka fito da rarrafe saboda tsaro ba dan tsoro ba, dan yanzu idan ka fito da ƙafarka wani ɗan sa ido ya gani sai a gama gane lagonmu" Idrisu ya faɗa yana kallon shagon nasu yana jiran fitowar Beelal.
A hankali Beelal ya sanya hannu ya share hawayensa, ya yi dibara ya miƙe ya tahowarsa a ƙafarsa ba tare da ya rarrafo ba kamar yadda aka buƙata.
Ganinsa ya fito a tsaye sai Imran ya tafi da sauri ya je bayan Beelal ya sanya hannu ya hankaɗo Beelal, aikuwa Beelal ya tafi tagal -tagal sai kuwa ya faɗa a kan gwiwoyinsa aikuwa ya ji faɗuwar sosai wani zafi ya ziyarci gwiwoyinsa.
"Ka min dai dai ai maganin marar kunya da rashin jin magama kenan" Idrisu ya faɗa yana kallon Imran.
"Hasbunallahu wa ni'imal wakil, ya haka" Cewar Aminullah da ya ƙaraso wajen cikin sauri dan tun lokacin da ya shawo kwana ya hango Imran ya hankaɗa wani yaro da ya fito daga cikin shagonsu hakan ya sanya ya ƙaraso da sauri.
"Kai ba fa da kai ake yi ba mu ba ma son shishigi da shiga shiri ba shanu" Idrisu ya faɗa yana hararar Aminullah. Aminulla kuwa ganin abin da suka yi da gangan ne sai kawai ya nufi wurin Beelal cikin tausayawa musamman ma da ya lura da larurar da ke tattare da yaron sai ya ji wani mugun tausayinsa ya mamaye masa zuciya. Cikin sauri da azama ya sanya hannu ya ɗaga yaron tsaye yana masa sannu tare da dudduba jikin Beelal ɗin dan ganin ko ya ji ciwo. Dan shi Aminullah duk tunaninsa ma yaron bara yake suka masa wannan wulaƙancin.
"Kai fa wannan zaƙiyar da kake yiwa mutane, da shiga shirgin da ba naka ba, ba ka ji ba an ce mutum ya bar abin da babu ruwansa ba, amma kai kullum cikin kutsa kai cikin abin da bai shafe ka ba kake" Imran ya faɗa yana hararar Aminullah da ke riƙe da Beelal.
"Ko ma dai me zaku faɗa ku faɗa amma dai abin da kuka yi baku kyauta ba in sadakar ce ba za ku bashi ba sai ku ce ya tafi amma ba wai ku masa wannan kora da halin ba" Aminullah ya faɗa shi ma yana kafe su da ido.
"To kai an faɗa maka kowa ma irinka ne, ko kuma an ce maka bara yake, to wannan da kake gani tun daga arewa na taho da shi kudu saboda yake bara yana samo mini kuɗi, dan haka babu ruwanka ka sake shi ya zo ya hau kekensa" Idrisu ya faɗa yana kallon Aminullah.
Baki sake Aminulla yake kallonsu yana rayawa a ransa wace uwa ce wanann marar dogon tunani za ta baiwa mutum kamar Idrisu yaro kamar wannan da sunan a zo da shi ya yi bara, Idrisu da ko ciwon kansa bai sani ba ta yaya har haka za ta faru.
"Sake shi to tunda ka ji kanun labaran sai ka kiyaye shiga abin da baka ciki wanda babu ruwanka" Imran ya ce yana wani ɗaga kai sama.
"Amma duk da kun ce ba ruwana ya za a yi ku ɗakko wannan tsohon keken ku ce ya hau bayan kuma keken ya riga da tsufa duk ya yi tsatsa, bayan ma yana da ƙafarsa ya za a yi ya hau keken guragu" Aminullah ya faɗa yana kallon fuskar Beelal cike da tausayawa dan ya san ba da son ran yaron ba.
Da sauri Imran ya sanya hannu ya fisgi Beelal daga hannun Aminullah yana aikawa Aminullah ɗin wata harara tare da Beelal ɗin.
"Ka rainawa mutane hankali har ka tsaya ja in ja damu, shin ma ina ruwanka da mu ne? Menene alaƙarmu da kai, ko muna da wani haɗi ne da kai bayan na addinin muslunci, da kuma haɗin kama hayar shago ɗaya? Dan haka ka fita idanunmu mu rufe in har kana son zama lafiya"
MMN AFRAH 09030283375
❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️
*BEELAL*
💦💦💦💦💦💦
NA
MAMAN AFRAH
Book 2
*FCW*💛
Page 5️⃣➡️6️⃣
Aminullah yana ji yana gani Imran ya kama Beelal ɗin ƙiii ko tsayawa babu, har sai da ya dangana shi da kan ƙarfen keken, dan wurin zaman ko katifa babu ta cire sai ƙarfen kawai, yana zaunar shi tare da yiwa Beelal ɗin mugun kallo.
"Tuƙa mu tafi" Idrisu ya faɗa cikin zafin rai, su duka daga Imran ɗin har Idrisun sai muzurai suke kamar waɗanda suka yiwa sarki ƙarya.
"Ban iya ba wallahi ko taɓa hawa ban yi ba" Beelal ya faɗa kamar zai fashe da kuka.
"Banda rainin wayo ya ma za a yi ka ce wai baka iya tuƙa kekenku na nakasassu ba, ai sabo da ku aka ƙeroshi dan haka yanzu ya zama dole ka tuƙa ko baka so" Cewar Imran yana kallon Beelal.
"Bari dai ka ga ƙarshen rainin wayo dan ya ɓata mana lokaci ne yasa yake ja mana rai" Cewar Idrisu yana fisgar keken da uban ƙarfi suka fara tafiya, Imran na bin bayansu, Aminullah da ke shirin yin magana ganin sun ja keken sai ya saki baki yake bin su da kallo, yana ɗaga hannu kamar mai neman taimako.
"Ku bishi a hankali dan Allah" Cewar Aminullah cikin ɗaga murya amma ko sauraronsa ba su yi ba.
Beelal kuwa hannu biyu ya sanya ya riƙe wajen tuƙin ganin irin gudun gangancin da Idrisu yake yi da keken ƙura sai tashi take. Sai da suka ɗan yi tafiya mai ɗan tazara Idrisu ya saki keken ba tare da ya tsayar da keken ba, da sauri Beelal ya sauke ƙafarsa mai lafiyar ya taka ƙasa hakan sai ya zamana kamar ya taka birki ne, dan yadda Idrisu ya saki keken da ƙarfi kaɗan ya rage Beelal ya hantsila daga shi har keken.
"Kai ka fara tuƙawa da kan ka ka ga mun baro waccan lungun da shagonmu yake mun fito cikin jama'a tun daga nan har zuwa ko ina ma na unguwar nan kasuwa ce dan haka yanzu za ka fara tuƙawa ka yi gaba mu kuma mu biyo ka a baya kuma kar ka nuna ma ka san mu, duk da ba lallai wani ya hango jirginmu ba, kuma ba lallai wani ya lura cewa mun sanka ba saboda babu yadda za a yi wani ya kalleka ya haɗamu da kai" Cewar Idrisu yana hararar Beelal.
"Ka ga duk wannan faɗin wajen duk wurin ma kasuwa ce amma kar ka shiga can ciki ka je ka ɓata kake bararka a iya nan, ungo nan, duk wani abu na ci kake sakawa a nan kafin a samo maka robar da za kake sakawa, kuɗi kuma kake sakawa a acikin aljihunka idan sun taru muna gefe za mu karɓa sai ka cigaba da barato wani" Imran ya faɗa yana miƙa masa wata ledar yaluwa mai sarsar da ya fito da ita a aljihunsa.
"To" Cewar Beelal yana haɗa hannayensa wuri ɗaya ya sanya hannun biyu ya karɓi ledar, dan Mamarsa ta koya masa cewa ba a karɓar abu da hannun hagu ko kuma a karɓa da hannu ɗaya sai dai duk abin da mutum zai karɓa ya sanya hannu biyu tare da ɗan rusunawa saboda hakan shi ne cikar tarbiya.
"Ka taimaki kan ka" Idrisu ya faɗa yana faɗaɗa murmushinsa dan har ya hango sun fara samun kuɗi.
"Me zan ke cewa barar, mai zan ke faɗa idan ina barar" Cewar Beelal cikin sanyin murya.
"Ka ji wani rainin wayo kuma yanzu kai abin da kuke faɗa ne baka sani ba, ai a gani na nakasashshe babu wanda zai koya masa yadda zai yi bara tun da dan ita aka halicceshi a nakashe"
Cewar Imran yana wani yatsina fuska.
"Allah ya haliccemu ne dan mu bauta masa kuma Allah ya hore min rai da lafiya da sassan jiki dai dai gwargwadon yadda zan nemi ilimi in nemi halal ɗin ba wai in yi bara ba, Allah ba ya son roƙo ma"
"Inyeee to wallahi wannan darasin sai dai ko ka bari sai ranar da ka koma gun wacce ta koya maka wato mahaifiyarka ka faɗa mata hakan idan da rabon zaku sake haɗuwa ma kenan, idan kuna da rabon sake sanya juna a idanu dan mu wannan karatun mun daɗe da saninsa" Idrisu ya faɗa yana hankaɗa keken da Beelal ɗin ke ka.
Daddagewa Beelal ya yi ya riƙe kan keken, ya cije leɓensa na ƙasa da haƙorinsa, ya shiga ƙoƙarin tuƙa keken cikin iko da hikimar ubangiji sai gashi ya tuƙa keken.
"Ɗan rainin wayo ashe ma ya iya ya sa kake wahalar turashi" Cewar Imran.
"Rabu da shi mana in ma bai iya ba da ya ji uwar bari ai ya tuƙa dole ne ai ya nemo mana abin da aka kawo shi takanas domin ya yi wato bara" Idrisu ya faɗa yana dariya idanunsa na hango Beelal na jan keken dakyar.
Shiru Beelal ya yi dan yadda Idrisu ya masa magana ya tsorata saboda da ƙarfi ya zafice shi dan haka sai ya ja bakinsa ya yi shiru.
"Baaba na ɗakko keken nan fito ka gani, ko a san a bin yi ka san maganin abu a yi shi" Imran da ke can waje ya faɗa da ɗan ƙarfi.
Haka Idrisu ya fito daga cikin shagon yana washe baki, ya baro Beelal a can ciki.
"Kai gaskiya abokina ka iya bada shawara to ka ga wannan da babu shi ma sai mun nemo amma tun da gurgu ya bar wa ɗan uwansa gurgun mage gado ka ga mun huta da nema" Idrisu ya faɗa yana kallon tsohoh keken guragun da ya ya tsufa jikinsa duk tsatsa.
"Eh mana, ai mu gaba ta kaimu gobarar titi, kai kana ina fito dalla ka zauna a ciki kamar wanda kake ganin dodanni" Imran ya faɗa yana kiran Beelal da bai fito daga shagon ba.
"Ka fito da rarrafe saboda tsaro ba dan tsoro ba, dan yanzu idan ka fito da ƙafarka wani ɗan sa ido ya gani sai a gama gane lagonmu" Idrisu ya faɗa yana kallon shagon nasu yana jiran fitowar Beelal.
A hankali Beelal ya sanya hannu ya share hawayensa, ya yi dibara ya miƙe ya tahowarsa a ƙafarsa ba tare da ya rarrafo ba kamar yadda aka buƙata.
Ganinsa ya fito a tsaye sai Imran ya tafi da sauri ya je bayan Beelal ya sanya hannu ya hankaɗo Beelal, aikuwa Beelal ya tafi tagal -tagal sai kuwa ya faɗa a kan gwiwoyinsa aikuwa ya ji faɗuwar sosai wani zafi ya ziyarci gwiwoyinsa.
"Ka min dai dai ai maganin marar kunya da rashin jin magama kenan" Idrisu ya faɗa yana kallon Imran.
"Hasbunallahu wa ni'imal wakil, ya haka" Cewar Aminullah da ya ƙaraso wajen cikin sauri dan tun lokacin da ya shawo kwana ya hango Imran ya hankaɗa wani yaro da ya fito daga cikin shagonsu hakan ya sanya ya ƙaraso da sauri.
"Kai ba fa da kai ake yi ba mu ba ma son shishigi da shiga shiri ba shanu" Idrisu ya faɗa yana hararar Aminullah. Aminulla kuwa ganin abin da suka yi da gangan ne sai kawai ya nufi wurin Beelal cikin tausayawa musamman ma da ya lura da larurar da ke tattare da yaron sai ya ji wani mugun tausayinsa ya mamaye masa zuciya. Cikin sauri da azama ya sanya hannu ya ɗaga yaron tsaye yana masa sannu tare da dudduba jikin Beelal ɗin dan ganin ko ya ji ciwo. Dan shi Aminullah duk tunaninsa ma yaron bara yake suka masa wannan wulaƙancin.
"Kai fa wannan zaƙiyar da kake yiwa mutane, da shiga shirgin da ba naka ba, ba ka ji ba an ce mutum ya bar abin da babu ruwansa ba, amma kai kullum cikin kutsa kai cikin abin da bai shafe ka ba kake" Imran ya faɗa yana hararar Aminullah da ke riƙe da Beelal.
"Ko ma dai me zaku faɗa ku faɗa amma dai abin da kuka yi baku kyauta ba in sadakar ce ba za ku bashi ba sai ku ce ya tafi amma ba wai ku masa wannan kora da halin ba" Aminullah ya faɗa shi ma yana kafe su da ido.
"To kai an faɗa maka kowa ma irinka ne, ko kuma an ce maka bara yake, to wannan da kake gani tun daga arewa na taho da shi kudu saboda yake bara yana samo mini kuɗi, dan haka babu ruwanka ka sake shi ya zo ya hau kekensa" Idrisu ya faɗa yana kallon Aminullah.
Baki sake Aminulla yake kallonsu yana rayawa a ransa wace uwa ce wanann marar dogon tunani za ta baiwa mutum kamar Idrisu yaro kamar wannan da sunan a zo da shi ya yi bara, Idrisu da ko ciwon kansa bai sani ba ta yaya har haka za ta faru.
"Sake shi to tunda ka ji kanun labaran sai ka kiyaye shiga abin da baka ciki wanda babu ruwanka" Imran ya ce yana wani ɗaga kai sama.
"Amma duk da kun ce ba ruwana ya za a yi ku ɗakko wannan tsohon keken ku ce ya hau bayan kuma keken ya riga da tsufa duk ya yi tsatsa, bayan ma yana da ƙafarsa ya za a yi ya hau keken guragu" Aminullah ya faɗa yana kallon fuskar Beelal cike da tausayawa dan ya san ba da son ran yaron ba.
Da sauri Imran ya sanya hannu ya fisgi Beelal daga hannun Aminullah yana aikawa Aminullah ɗin wata harara tare da Beelal ɗin.
"Ka rainawa mutane hankali har ka tsaya ja in ja damu, shin ma ina ruwanka da mu ne? Menene alaƙarmu da kai, ko muna da wani haɗi ne da kai bayan na addinin muslunci, da kuma haɗin kama hayar shago ɗaya? Dan haka ka fita idanunmu mu rufe in har kana son zama lafiya"
MMN AFRAH 09030283375
❤️❤️❤️❤️❤️❤️❤️
*BEELAL*
💦💦💦💦💦💦
NA
MAMAN AFRAH
Book 2
*FCW*💛
Page 5️⃣➡️6️⃣
Aminullah yana ji yana gani Imran ya kama Beelal ɗin ƙiii ko tsayawa babu, har sai da ya dangana shi da kan ƙarfen keken, dan wurin zaman ko katifa babu ta cire sai ƙarfen kawai, yana zaunar shi tare da yiwa Beelal ɗin mugun kallo.
"Tuƙa mu tafi" Idrisu ya faɗa cikin zafin rai, su duka daga Imran ɗin har Idrisun sai muzurai suke kamar waɗanda suka yiwa sarki ƙarya.
"Ban iya ba wallahi ko taɓa hawa ban yi ba" Beelal ya faɗa kamar zai fashe da kuka.
"Banda rainin wayo ya ma za a yi ka ce wai baka iya tuƙa kekenku na nakasassu ba, ai sabo da ku aka ƙeroshi dan haka yanzu ya zama dole ka tuƙa ko baka so" Cewar Imran yana kallon Beelal.
"Bari dai ka ga ƙarshen rainin wayo dan ya ɓata mana lokaci ne yasa yake ja mana rai" Cewar Idrisu yana fisgar keken da uban ƙarfi suka fara tafiya, Imran na bin bayansu, Aminullah da ke shirin yin magana ganin sun ja keken sai ya saki baki yake bin su da kallo, yana ɗaga hannu kamar mai neman taimako.
"Ku bishi a hankali dan Allah" Cewar Aminullah cikin ɗaga murya amma ko sauraronsa ba su yi ba.
Beelal kuwa hannu biyu ya sanya ya riƙe wajen tuƙin ganin irin gudun gangancin da Idrisu yake yi da keken ƙura sai tashi take. Sai da suka ɗan yi tafiya mai ɗan tazara Idrisu ya saki keken ba tare da ya tsayar da keken ba, da sauri Beelal ya sauke ƙafarsa mai lafiyar ya taka ƙasa hakan sai ya zamana kamar ya taka birki ne, dan yadda Idrisu ya saki keken da ƙarfi kaɗan ya rage Beelal ya hantsila daga shi har keken.
"Kai ka fara tuƙawa da kan ka ka ga mun baro waccan lungun da shagonmu yake mun fito cikin jama'a tun daga nan har zuwa ko ina ma na unguwar nan kasuwa ce dan haka yanzu za ka fara tuƙawa ka yi gaba mu kuma mu biyo ka a baya kuma kar ka nuna ma ka san mu, duk da ba lallai wani ya hango jirginmu ba, kuma ba lallai wani ya lura cewa mun sanka ba saboda babu yadda za a yi wani ya kalleka ya haɗamu da kai" Cewar Idrisu yana hararar Beelal.
"Ka ga duk wannan faɗin wajen duk wurin ma kasuwa ce amma kar ka shiga can ciki ka je ka ɓata kake bararka a iya nan, ungo nan, duk wani abu na ci kake sakawa a nan kafin a samo maka robar da za kake sakawa, kuɗi kuma kake sakawa a acikin aljihunka idan sun taru muna gefe za mu karɓa sai ka cigaba da barato wani" Imran ya faɗa yana miƙa masa wata ledar yaluwa mai sarsar da ya fito da ita a aljihunsa.
"To" Cewar Beelal yana haɗa hannayensa wuri ɗaya ya sanya hannun biyu ya karɓi ledar, dan Mamarsa ta koya masa cewa ba a karɓar abu da hannun hagu ko kuma a karɓa da hannu ɗaya sai dai duk abin da mutum zai karɓa ya sanya hannu biyu tare da ɗan rusunawa saboda hakan shi ne cikar tarbiya.
"Ka taimaki kan ka" Idrisu ya faɗa yana faɗaɗa murmushinsa dan har ya hango sun fara samun kuɗi.
"Me zan ke cewa barar, mai zan ke faɗa idan ina barar" Cewar Beelal cikin sanyin murya.
"Ka ji wani rainin wayo kuma yanzu kai abin da kuke faɗa ne baka sani ba, ai a gani na nakasashshe babu wanda zai koya masa yadda zai yi bara tun da dan ita aka halicceshi a nakashe"
Cewar Imran yana wani yatsina fuska.
"Allah ya haliccemu ne dan mu bauta masa kuma Allah ya hore min rai da lafiya da sassan jiki dai dai gwargwadon yadda zan nemi ilimi in nemi halal ɗin ba wai in yi bara ba, Allah ba ya son roƙo ma"
"Inyeee to wallahi wannan darasin sai dai ko ka bari sai ranar da ka koma gun wacce ta koya maka wato mahaifiyarka ka faɗa mata hakan idan da rabon zaku sake haɗuwa ma kenan, idan kuna da rabon sake sanya juna a idanu dan mu wannan karatun mun daɗe da saninsa" Idrisu ya faɗa yana hankaɗa keken da Beelal ɗin ke ka.
Daddagewa Beelal ya yi ya riƙe kan keken, ya cije leɓensa na ƙasa da haƙorinsa, ya shiga ƙoƙarin tuƙa keken cikin iko da hikimar ubangiji sai gashi ya tuƙa keken.
"Ɗan rainin wayo ashe ma ya iya ya sa kake wahalar turashi" Cewar Imran.
"Rabu da shi mana in ma bai iya ba da ya ji uwar bari ai ya tuƙa dole ne ai ya nemo mana abin da aka kawo shi takanas domin ya yi wato bara" Idrisu ya faɗa yana dariya idanunsa na hango Beelal na jan keken dakyar.