Sashe 13
Beelal Buk Part 2 Complete Hausa Novel · about 3 min read
"Allah sarki rayuwa kenan wato shi bawa babu abin da ya sani wanda zai faru a yau ko gabe Allah shi ne masanin haka, da a ce na san Idrisu zai ɗauke Beelal da a ranar ko runtsawa ba zan yi ba bare har ya samu damar hakan. Amma kaddara ta riga fata, bawa bai san mai zai faru ba hakan ya sanya ma ubangiji ya ɓoye wa bawa ranar da ajalinsa zai sauka, dan da a ce mutum ya san ranar mutuwarsa da zai rayu ne cikin tashin hankali amma cikin hikima ta ubangiji sai ya ɓoye hakan, ko da a ce saura minti ɗaya ne tak a ɗauki ran mutum amma sai ka ga bai sani ba. Wannan kaɗai ya isa ya sanya bawa yin abubuwan masu kyau domin samun yardar ubangiji"
Ƙaran buɗe get ɗin gidan da Fatimar ke zaune a ƙofar shi ya dawo da ita daga tunanin da zancen zucin da take, mota ce ta fito daga ciki, sannan wani mutumi ya ja get ɗin ya rufe da alama dai mai gadin gidan ne. Da ido Fatima ta bi motar da ta zo ta wuce ta gabanta wacce ke ɗauke da gilashi baƙi wanda hakan ba ya barin na waje ya hangi wanda ke cikin motar.
Har motar ta ɓacewa ganin Fatima sannan ta koma ta ɗan kishingiɗa a kan bencin. Jin ta take garau babu alamar bacci a tare da ita bare kuma yunwa, tabbas ashe dai lafiya da kuma kwanciyar hankali ke sanya mutum jin yunwa har ya ci abinci sau uku a rana ko ma fiye da hakan, amma ita yau da take cikin wani hali sai ta ji yunwar ma bata ji
Kimanin awa guda kenan sai ga motar ta dawo, har motar ta gifta Fatima sai kuma cikin sauri motar ta dawo da baya, sai da ta zo dai dai inda Fatimar ke zaune ta tsaya cak, hakan ya sanya Fatima saurin tashi zaune daga kishingiɗen da take ta shiga wurwurga ido gabanta na faɗuwa, dan bata san su waye a cikin motar ba sannan mai ya tsayar da su a wajenta, alkairi ko akasin haka? Shin korarta za su yi daga ƙofar gidansu ko kuwa taimakonta za su yi, ko kuma wani abu ne yake tafe sa su saɓanin abubuwan da zuciyarta ta ƙiyasta mata...
Shin ya rayuwar Beelal za ta cigaba da kasancewa a garin Lagos? Rayuwarsa a hannun mahaifinsa da abokin mahaifinsa da basu da tausayi bare imani sai tarin son zuciya.
Menene dalilin tsayuwar motar wannan a gaban Fatima shin su waye a ciki? Ya Fatima za ta kasance a cikin Lagos yaushe ne za ta haɗu da Beelal a kwana kusa ne ko sai an ɗauki dogon lokaci.
Ina labarin Hajiya Laɗifa wane hali za ta tsinci kanta idan ta samu labarin barin Fatima da Beelal arewa? Shin wace waina za a cigaba da toyawa a wannan gidan da basu da alƙibla masu bahagon aƙida wanda basu san komai ba sai ƙyamar nakasassu, shin waye ɗan da Hajiya Nuratu ta haifa mai zai zame musu a cikin gidan?
Akwai tarin tambayoyi wanda ake buƙatar amsar su, da kuma wasu abubuwan da sai dai wanda ya karanta labarin Beelal har ƙarshe zai sani, dk amsoshin suna tattare da 300 da zaki biya kuɗin karatu ki karanta har ƙarshe ba tare da kn jira wani ya samo miki ba wataran ma ki rasa wani page ɗin.
Ko daga yau zaki iya biyan kuɗin karatunki, alƙalamin maman afrah ba ya rubuta shirme😍
Mai buƙatar buk 1 ya min magana kyauta ne, mai son buk 2 ya biya 300 idan complt ne 500
09030283375
Ƙaran buɗe get ɗin gidan da Fatimar ke zaune a ƙofar shi ya dawo da ita daga tunanin da zancen zucin da take, mota ce ta fito daga ciki, sannan wani mutumi ya ja get ɗin ya rufe da alama dai mai gadin gidan ne. Da ido Fatima ta bi motar da ta zo ta wuce ta gabanta wacce ke ɗauke da gilashi baƙi wanda hakan ba ya barin na waje ya hangi wanda ke cikin motar.
Har motar ta ɓacewa ganin Fatima sannan ta koma ta ɗan kishingiɗa a kan bencin. Jin ta take garau babu alamar bacci a tare da ita bare kuma yunwa, tabbas ashe dai lafiya da kuma kwanciyar hankali ke sanya mutum jin yunwa har ya ci abinci sau uku a rana ko ma fiye da hakan, amma ita yau da take cikin wani hali sai ta ji yunwar ma bata ji
Kimanin awa guda kenan sai ga motar ta dawo, har motar ta gifta Fatima sai kuma cikin sauri motar ta dawo da baya, sai da ta zo dai dai inda Fatimar ke zaune ta tsaya cak, hakan ya sanya Fatima saurin tashi zaune daga kishingiɗen da take ta shiga wurwurga ido gabanta na faɗuwa, dan bata san su waye a cikin motar ba sannan mai ya tsayar da su a wajenta, alkairi ko akasin haka? Shin korarta za su yi daga ƙofar gidansu ko kuwa taimakonta za su yi, ko kuma wani abu ne yake tafe sa su saɓanin abubuwan da zuciyarta ta ƙiyasta mata...
Shin ya rayuwar Beelal za ta cigaba da kasancewa a garin Lagos? Rayuwarsa a hannun mahaifinsa da abokin mahaifinsa da basu da tausayi bare imani sai tarin son zuciya.
Menene dalilin tsayuwar motar wannan a gaban Fatima shin su waye a ciki? Ya Fatima za ta kasance a cikin Lagos yaushe ne za ta haɗu da Beelal a kwana kusa ne ko sai an ɗauki dogon lokaci.
Ina labarin Hajiya Laɗifa wane hali za ta tsinci kanta idan ta samu labarin barin Fatima da Beelal arewa? Shin wace waina za a cigaba da toyawa a wannan gidan da basu da alƙibla masu bahagon aƙida wanda basu san komai ba sai ƙyamar nakasassu, shin waye ɗan da Hajiya Nuratu ta haifa mai zai zame musu a cikin gidan?
Akwai tarin tambayoyi wanda ake buƙatar amsar su, da kuma wasu abubuwan da sai dai wanda ya karanta labarin Beelal har ƙarshe zai sani, dk amsoshin suna tattare da 300 da zaki biya kuɗin karatu ki karanta har ƙarshe ba tare da kn jira wani ya samo miki ba wataran ma ki rasa wani page ɗin.
Ko daga yau zaki iya biyan kuɗin karatunki, alƙalamin maman afrah ba ya rubuta shirme😍
Mai buƙatar buk 1 ya min magana kyauta ne, mai son buk 2 ya biya 300 idan complt ne 500
09030283375