← Book details Afnan Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 9 OF 16

Sashe 9

Afnan Part 1 Complete Hausa Novel · about 7 min read

"Dagaske har yanzu baka Yi abin da zaisa *AY* ya taimakeka ba ko yayarda da abin da kazo dashi"
"Me yakamata nayi akai kenan" ?
"Sunansa muddum kanemo asalin sunansa ka turamasa message da wannan sunan wallahi summa tallahi ko minti 5 bazaka karaba alokacin saika ga kiransa"
"Sunansa Kuma to kenan wadannan sunayen ba sunansa bane ,to mené amfanin nemo sunan?"
"Sunansa Yana da amfani kafcikin nahiyarna daidaikun mutanene wadan da suka san asalin sunansa Wanda iyayensa suka rada masa, koni kaina bansan asalin sunanshi ba ,
"Aina zansamu sunan nashi?"
Kaje kaduba duk wata kafa ta sadarwa idan Allah ya taimakeka zakasan me asalin *AY* take nufi idan kayi Haka tabbas zai yarda aykin da gaskene tun da har kanemo asalin sunansa Dan bakowane yasan waye shiba"
"Tom shikkenan madam nagode kwarai da gaske yanzu ki turamin number tashi ta kasar *London* din saina jarraba".
Daga Haka sukayi sallama ya katse wayar.

***
Zama yayi ya kalli bangon dake fece din inda yake kome yake tinani oho ,can Kuma sai Naga ya dauki wayarsa ya rubuta *L.B.M.AY* kurawa sunan idon yayi Yana nazarin abin da sunan yake nufi can Kuma sai Naga ya dauki letter (L) ya saka _Lion a Gaba itama Letter(B) din sai yasaka _boss sannan ya dakko itama (M) yasaka nata _man daga Nan kuma sai ya tsaya domin besan me *AY*ke nufiba, TIKTOK yashiga yiyi search din Lion be fito ba, sai ya sake searching din boss man shima be fito ba, haushine ya kamasa Dan Haka ya koma FECBOOK nanma yayi irin yadda yayi a tiktok Amma shiru kakeji ,kansa ya Dora a tsakanin gywoyinsa yatafi duniyar tunani, Can kuma kamar an tsikareshi ya Mike yace" Kay to ay in hakane naje you tube Mana " cikin sauri ya shiga yin searching din likitocin *dick* na duniya Baki daya ,sai gashi an watsomasa mutane da dama', shigarsu ya dingayi Yana duba video din har yazo kan wani vidéo da baka ganin komai sai duhu tsaki yayi ya kashe wayar ya kwanta agurin Yana tunani, sai Kuma yace" kardai wannan video din shine ,mutumin da be yadda asan sunansa bama shi zai yarda aga fuskarsa"? Tabbas ko shine ,Mike wa zaune yayi har gumi yake faman hadawa wajan kunna data hannunsa kuwa harrawa yake wajen danna video, kunnawa yayi yaji anfara magana Amma Bata ganin komai sai duhu " ASSALAMUALAIKUM" INAYIWA YAN,UWANA MAZA DA MATA BARKANKU DA ZUWA WANNAN TARO ME ALBARKA ,WADA ADUK SHEKARA NASABA HALARTARSA AKASA ME TSARKI WATO SAUDIYA, TO DA FARKO DAI SUNANA *AREEYAAN NOOR MUTALLAF* WANDA AKAFI SANI DA BOSS MAN WASU KUMA DAYAWA SUNA KIRANA DA LION KO AY.... Ay tun da AREEF yaji wannan sunan nasa na asali ya tabbatar da shine wan da yake nema yasa ya katse video din tare da ajiye wayar a gefe ya durkusa yayi sujjada Yana Mai yiwa Allah godiya da ya nunamasa wannan Rana. Mikewa yayi ya dauki number da hajiya Fateema ta turamasa yashiga rubuta message kamar Haka.

"ASSALAMUALAIKUM" inamaka barka da wannan lokacin sannan Ina maka fatan alkairi,nine dai AREEF Wanda akullum yake cikin nemanka Kuma bana gajiya da nemanka harsai ka fuskanceni ,doctor AREEYAAN wow suna me dadi inafatan kamar yadda kake da wannan sunan yasa ganinkama yaxamemin me kyau , ok nafatan kataimakeni kataimaki kanwata domin kayi mata ayki nagode ".
Daga Haka AREEF ya tura message din.
Cikin minti 2 yaji Kira ya shigo wayarsa ,Yana dubawa wazai gani doctor...... Bakinsa da jikinsa har rawa suke wajan daukar wayar yace "alhamdulillah Allah nagode maka Ashe dama' zanga wanan ranar "hello doctor AREEYAAN!!!!.

__ 💋 *AFNAN* 💋______
*Chptar 9*

💃💃*TO!! TO!! TO!! Shhhh*😌 *KUNA INA MASOYA LITTAFIN*💋*AFNAN*💋WANAN LITTAFIN DABAN YAKE DA SAURAN AFNAN FA AKA FADA MUKU KUNSAN YADDA KUKAJI WANNAN LITTAFIN ZA A KWASHI ROMON DADI ACIKINSA AFNAN LITTAFINE MECIKE DA TARIN ABIN BAN AL,AJANI FADAKARWA NISHADAN TARWA DUK ACIKIN WANNAN LITTAFIN ME SUNA 💋 *AFNAN* 💋.
*NICE TAKU HAR KULLUM MARUBUCIYAR *✍️
🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼
_*AFNAN*_
_*BY*_
_*HAFSAT UMAR ƊAN GORO*_
🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼🌼

_*JARUMAI💪🏻WRITER'S ASSOCIATION📚*_

_*Marubuciyar*_
1- Burina Mu'azzam
2- Ba Mahaifiyata bace
3- Babana ne sila
4- Ummu Amani
5- Amatullah
6- Zuciyarta
7- Mace Rayuwa
8- Rayuwar Ƙasƙanci
9- Mar'atussaliha
10-Babbar sakayya
_And now_
💋_*AFNAN*_💋
*BOOK one*

*Chapter 9*

_______ "hello doctor AREEYAAN ,kana jina?" Daga can bangaren wani saurayine kekkewa dauke da tell phone a hannunsa ,ka dakaga wanna saurayin kaga asalin cikkakken balaraben usul ,bakinsa ya fara motawa Yana cewa " ba Yaya AREEYAAN bane AYAAN ne "
"To kenan Ina doctor din?" Yanzu Ina kokarin hadaka dashine abin da yasa nakiraka banason kace an wulakanta ka ko mu barka da jira shiyasa nakiraka don n'a fadamaka yayana Yana amsa wayane ta umarceni da nafada maka kabashi nan da minti 5 zai kiraka da asalin number sa" murmushi AREEF yayi yace" oky Tom Babu damuwa Bari zanjira shi" okay AYAAN ya kashe wayar kitt.

"Nafara yadda da abinda hajiya Fateema ta fadamin akan doctor ,yanzu shi Dan zaiyi wani uzurin sai yasa ankirani an bani hakuri Sabi da Kar ya batamin lokaci " ikon Allah ya saka hannunsa a kumatun da Yana zabga murmushi shikadai, jiyayi kamar muryar AFNAN tana cewa" Yaya murmushi me kake"? Dagowa yayi da sauri Dan ya tabbatar itace tayi maganar ,ayko ita dince Dan Haka ya karasa kusa da ita yace "AFNAN kin tashi ?" Sannu ko yajikin naki meyake damunki, ko kina bukatar wani abune?" Lokaci daya ya gigice Yana jefo Maya tambayoyi, wash Yaya dagani inason na maka magana " tom shikkenan kanwaty" ya karasa maganar tare da dagota zuwa jikinsa, "inajinki AFNAN" aziyar zuciya ta sauke tare da saka idanuwanta anashi Tace" Yaya AREEF kayafemin Dan Allah" nayafe Miki Kuna mekikai min!!? "Yaya nakasa jurewa ne shiyasa har takaini da saka hannu a gabana Dan Allah kada kace zakayi fishi Dani" uhm kanwata kenan ayni bana fishi dake Koda nayi ma bazan iya jurewa ba Dole sai na sakko, yanxu dai ba wanan ba albishirinka"? Goro!! Fari ko jaa?" Fari fat Yaya" to nasamu nasarar samun doctor a waya Kuma ma yamin alkawarin Nan da minti biyar zai kirani" hmm. Yaya Allah natsani doctor dinan "? Meyasa AFNAN shine fa Wanda zai taimakeki kisamu lafiya" Yaya Sabi da Yana wahalar min dakai natsani mutum irinsa Allah Yaya natsanesa" Kuma ay Naga lafiya ubangiji ne ke bayarwa ba shiba allah da ta halicceni da wanan abin shiyasan meyake nufi dani kuma shiyake son ganina a Haka, dan Haka koda ace zai min aykinann Banaso nafison nayi zamana a Haka narayu tare dakai cikin farinciki iya soyayyar dakake nunamin ta isheni yayaemin damuwa ta " ta karasa maganar hawaye na bin kuncinta" a,a AFNAN kada kiyanke hukunci cikin fishi Kuma ba acewa antsani mutum sai dai kice kin tsani halinsa, Kuma mu basanin asalin halinsa mukaiba balls har mumasa kallon mutum me wulakanta Dan Adam, AFNAN indai har kina Sona Kuma kin yarda Ni AREEF na Isa dake ki Bari ayi Miki aykinnan" runtse ido tayi ta bude Sana Tace" Yaya duk abin da kakeso Nima inaso Babu damuwa indai kanaso na amince ayimin aykin indai haka shine yafi alkairi arayuwar mu Baki daya"wow kanwata Daman Haka kika iya magana me dadi " Masha Allah Allah yayi Miki albarka"ameen Yaya na "ta Kara rungumesa tsam a jikinta.

*LONDON*

Babban gidan da yakasance daya daga cikin gidajen doctor na kasashe dadama tsayawa tsara kyau da ado da daula irin nagidan Bata bakine, Kai tsaye wannan saurayin Naga ya nufi wata kofa wadda take daga hannun dama' afalon wadda takasance itace kofa ta goma Sha biyu a gurin, shiga yayi dauke da sallama abakinsa ,saikuma yayi shiru can najiyo wata tausasassiyar murya daga ciki ance" yes" cikin nutsuwa ya tura kofar yashiga ciki, Baki nabude tare da sakin yawu kukukut tsabar haduwar dakin da tsaruwar sa dafarko idan kashiga dakin zaka tarasa yar madaidaiciyar loka a gefe wadda Tasha ado da kayan alatu na duniya, sai Gaba Kuma akwai gado Dan karami Wanda befi kwanciyar mutum daya ba ,Amma saidai kana hawansa saikasan ka hau gado ba muna gadoba ,wannan katifar ta kan gadon Kana hawa zakaji kamar a kan audiga kake tsabar laushi ,gefe guda Kuma covar ce itama karama me dauke da murfi biyu ,gaba kidaya jikinta kelkeline n'a gwaldin color, can gefe Kuma kujerace itace wadda na hango mutumin a zaune akai nai daga bayan sa yadda nagansa Zan iya fasal tamuku yanayinsa ,dogone sosai a Haka sai dai Yana da kauri ta sama ma,ana kirjinsa Yana da Fadi,duk da gashin kansa da na ga ya lullube Gaba daya kafadarsa da fuskarsa bana iya tantance wane irin mutum ne, karasawa AYAAN yayi yace" barka da safiya yaya" Kai kawai ta daga masa batare da ta juyo KO yayi magana ba , magana AYAAN yasake yi yace" yaya Yashirya fa ,yakamata ka taimakesa gaba kidaya angama tantancesa yacancanci a karbi aykinsa" kada kamanta Yana jiran kiranka ayanzu" Kai yakara dagamasa ta cigaba da abin da yake still dai be juyo ba ,Juyawa kaninnasa yayi ya fita tare da danna wani abu sai kofar dakin ta rufe.

Lokacin da yafito falon Ajiyar zuciya yayi yace" hooo yayana kenan "wanan mutumin saï a hankali narasa irinsa" daga Haka ya fice daga falon yashiga daya daga cikin kofofin dake falon.
Chapter 9 · 0% Book details