PART 2
Abdul Jalal Part 2 Complete Hausa Novel · about 17 min read
_PAGE 5️⃣9️⃣112
Bismillahirrahmanirrahim, da sunan Allah me rahama me jinkai, Allah yakara tsira da aminci ga shugabanmu Annabi muhammadu salallahu alaihi wassalam.
Bayan haka bazan gajiba da mika gaisuwata da godiya ga yan uwa da abokan arziki ba, bayan haka
Banyarda a juyamin littafi ba ko amfani da wani bangare ba tareda izinina ba.
Domin gyara, shawara ko sharhi, za a iya tuntubata akan what's app number dina
07063065680
Or email address @ [email protected]
Watpad @Ayshercool7724
_MY FIRST NOVEL _
Shiri sukayi sosai don tafiya garinsu Ummi, da farko akace baza'aje da su Nana ba saboda larurar ciki, amma sukace baza'ayi babu su ba suma suna son zuwa garinsu Ummi.
Shiri sukayi sosai, suka dau motoci suka nufi kwara state.
Tunda suka shiga garin Jalila ta kara tabattar da lallai Akwai banbancin Addini da al'ada.
Jalila tayi mamakin irin kyau da tsaruwar masarautar su Ummin ta, lallai Ummi ta cancanci yabo da jinjina, da ta iya tsallake wannan daular ta zabi Addinin musulunci da kuma soyayya.
Su nasu masarautun basa amfani da doki, se manyan motoci, ga barori nan nata kaiwa suna komowa, gasu da matukar biyayya, duk inda suka ratsa zubewa ake ana girmama su, musamman Ummi.
Seda suka shiga cikin gidan ta kara tabattar da lallai Ummi ba karamar 'yar gata bace ba, Tangamemen hoton Mahaifiyar Ummi ne sakale a wani katon guri kamarta daya sak da Ummi, duk da ta manyan ta seka dauka ya da kanwa ne.
An karbesu cikin girmamawa da mutuntawa, Seda suka huta, Aka dinga gabatar musu da kayan Abinci,
Seda aka jima suka huta sannan Mahaifiyar Ummi ta fito, Mahaifiyar Ummi na ganin Jalila ta rungumeta cikin harshen turanci tace
"ko ba' a gayamin ba nasan wannan itace jikata"
Ummi tayi murmushi tace "Eh itace"
Mahaifiyar Ummi ta kalli su Hanan ta kalli Jalila tace
"wannan 'yan uwanta ne?"
Jawwad yace "Eh duk' yan uwanta ne"
"to wace matar Jalal kenan?"
Nana tace "Jalila ce matarsa"
Mahifiyar Ummi ta jinjina kai tace
"Sunan ta da mijin ta suna kama, mijinki yana da kirki sosai lokacin da mamanki ta dawo gida yana zuwa nan"
Maman Ummi tana da kirki sosai, nan aka dinga gabatar da su gurin mutanen gidan, 'yan gidan sunyi murnar ganin yarinyar' yar uwasu, bayan tsawon shekaru 'yar uwatasu bata tareda su.
Sarkin da yake mulki a wannan lokacin wanda yakasance Yaya ga Ummi shima ya nuna farincikin sa da jin dadi, na ganin su Jalila.
Daddare suna hira, mahaifiyar Ummi take cewa su Jalila,
"nayi dana sanin hana marry ta auri wanda take so a wancan lokacin, dukda ba laifina bane, laifin kakanta ne, yana ganin na auri bahaushe musulmi zaman beyi dadi ba, nayi kewar ta sosai tsawon wannan lokaci, bana iya bacci, sannan mahaifina yace be yadda in tura kasar hausawa a nemo ta ba, duk abunda yafaru da ita babu ruwan wani. Ban taba zaton marry zata iya jure zama tsawon wannan lokacin ba ba tare da mu ba, bayan rasuwar mahaifina shekaru biyar baya, Yayanta ya karbi mulki, shi da kansa yasa a bincika koza'a gano ta amma abun be yuwu ba, na koma Addinin musulinci, Yayana yaba wa kowa damar yayi Addinin da yake so, abun mamaki akan marry na yadda musulmi kuma hausawa mutanen kirki ne, lokacin da ta dawo gidan nan nayi mamaki, labarin da ta bani akan yadda rayuwar hausawa musulmi yake, da kuma karamcin da suka nuna mata, musamman wannan dan kyakywan yaron me dogon hanci, yana burgeni matuka yana girmama ta kaman ta haifeshi, kuma da ta gayamin alakar dake tsakaninsu naga babu wani babbar alaka da suka hada amma yake ta dawainiya da ita shida iyalansa"
Jalila ta kunshe kai tana dariya taji ance Dan kyakywan yaro me dogon hanci
Hanan tace "Dallacan se wani murmushi take dan ance mijinta kyakywa, nima mijina kyakywa ne, dan mijina farine tas"
Nana tai caraf tace "nima mijina yana da kyan ai, tunda kanin mijin Jalila ne"
Sukaita hira suna dariya, mahaifiyar Ummi tana da kirki da sanyin hali kamar Ummi gata da faran faran babu ruwanta.
Amma duk abun nan Jalila hankalin ta yana kan Jalal, ta damu sosai rashin ganin sa, ba karamin missing dinsa take ba.
Kwanan su hudu a garin, sun sha yawo, garin yana da kyau, sun sha hotuna, gasu da yalwar dazuka, Akwai fulani a garin, da babur amma yawancin su yarabawa ne, suma mutane masu kirki da kyakywar mu'amala.
A kwana na biyar suka fara shiri domin tafiya su bar garin.
Mahaifiyar Ummi taji babu dadi, seda tayi mita
"marry meyasa bazaki barmin yaran nan ba su dan kara kwanaki, wallahi sun shiga raina sosai naji dadin zama da su"
Ummi tace
"kiyi hakuri zasu dinga kawomiki ziyara, matan aure ne yaran nan, yakamata su koma gidajen Auren su, sannan Zamuje maiduguri gidan Su Danki Jalal, Abban Jawwad zasu jira mu a can"
"Shikenan amma ba haka naso ba, naso kara zama damu, yanzu na kara tabattar da abunda ake fada akan hausawa musulmai ba haka bane, kuna da kyakywar mu'amala da kuma girmama mutane, Jawwad amma kaima zaka dan dinga zuwa ko?"
Jawwad yai murmushi yace "karki damu, dukkan mu ma zamu dinga kawo miki ziyara, amma kema muna fatan zakizo mana"
"zanzo mana, tunda ina daku, Insha Allah nima zanzo muku"
A kwana na biyar suka karasa shiri zasu tafi, An musu alkhairi me tarin yawa. Suka yi harama Jawwad ya dauke su suka baro garin suka nufi borno state.
A motar ma se hira suke, suna kara yaba kirkin mahaifiyar Ummi da kuma barkwancin ta.
Suka karasa maiduguri a gajiye, bayan la'asar sosai suka karasa, Antyn Jalal tayi murnar ganin su kwarai, musamman da ta gansu tareda Ummi cikin fara'a tace
"kai masha Allah, bakin ba zata, Ummi Kice keda iyalan naki gaba daya kike tafe"
Ummi tace "Aikam dai gasu nan"
"sannunku da zuwa Jawwad, dazu Jalal ya bar garin nan, nasan be san zaku zo ba"
Jalila a ranta taji dama tun dazun sukazo,
"meyasa Jalal yakemin hakane? Duk na damu yaki bari mu hadu sam, why?"
Anty tace
"Jalilan Ummi, gaki ga Ummi, dazu Jalal yabar garin nan, albarkacin ki yasa ya kan leko mu ya kawo mana ziyara, bashi da aiki se yabon matarsa ko kunya ta bayaji" dan murmushi Jalila tayi ta sunkuyar da kai.
Jawwad yayi alwala ya tafi masallaci,
Suma sallolin su suka gabatar, Anty se lallaba su Hanan take saboda ciki da suke dauke da shi.
Jalila tace "Anty ina Husnah ne da Amal?"
"Husnah ta koma gidan ta, Amal kuma tana gidan kanin Babanta"
Daddare mijin Anty ya dawo, yanayin yadda suka gaisa da Ummi ze tabattar maka da sun san juna, nan Ummi take gaya masa daga kwara State suke, ya nuna farincikin sa da jin dadin sa akan hakan, gefe guda kuma ya dinga tsokanar Jalila
"matar so inji mijin ta, ya akayi kukayi sabani da mijin naki ne? Shi ya tafi dazu kekuma kinzo yanzu, ya akayi hakan ta kasance? Gayamin sirrin mana daughter, banda zancenki ba abunda Jalal yake in ya zauna"
Jalila dai kasa magana tayi, kowa tsokanar ta yake saboda Jalal.
Itakam Hanan ana wannan hirar ta silale ta tafi masaukin Jawwad daga ta kai masa Abinci bata dawo ba se bayan karfe daya, Jalila ta dinga ce mata mara kunya.
Washegari wajen Azahar Abban Jawwad da Daddyn Hanan, se Maama da Mummy Hanan suka iso, gida ya dau harami ya cika da baki.
Suna zuwa da suka huta ba tare da bata lokaci ba Daddy ya gabatar da abunda ya kawo su na zuwa su jadadda godoyar su akan karamci da dawainiyar da sukayiwa Ummi.
Abee yace
"babu bukatar ku cigaba dayi mana godiya, duk abunda Jalal yayi wa Wannan baiwar Allah be fadi ba, musamman shima dawainiyar da soyayyar data nuna masa a lokacin da shi da mara uwa kusan daya, mun riga mun zama daya da mu da ku, dan Allah batun godiyar nan a barshi, Allah yakara hada kanmu ya kara mana kaunar juna, Allah ya Albarkaci rayuwar yaran mu, Amma babu godiya a tsakaninmu"
Suka Amsa da Ameen gaba daya.
Kwana daya su Abba sukayi, suka kama hanya zuwa bauchi, kafafuwan Hanan duk sun dan kumbura saboda zaman mota, hakan yasa Jawwad ya damu yace a bauchi ze barta ta huta, in yaso ya biya kudin jirgi su koma Abuja. Tun suna hanya Mahmoud ya kira Nana a waya yace mata yana bauchi, Nana se murna take yi, yau zata ga mijin ta, Jalila ta danyi shiru tana tunanin nata mijin.
A gajiye suka koma garin bauchi, a yan kwanakin nan sun sha yawo, da suka isa bauchi Jalila wanka tayi ta nemi guri ta kwanta tana baccin gajiya.
Jalila bata tashi ba seda Ummi tazo ta tasheta
"ki tashi haka kiyi salla kici Abinci mana, baccin ya isa haka uwar bacci ashe har yanzu baki dena wannan baccin ba"
A shagwabe tace
"Ummi wallahi a gajiye nake shiyasa"
"ki tashi haka dai baccin ya isa"
Jalila ta tashi tai salla ta zubo Abinci ta zauna kenan ta fara ci Nana ta shigo, ta kalli Jalila tace
"se yanzu kika tashi kenan? In kin gama akwai surprise"
"Suprise kuma? Suprise din me?"
"sekin gama tukuna"
Jalila tace "shikenan"
Jalila ta cinye Abincin ta, tanemi guri ta kashingida tana danna waya.
Nana ta dawo dakin ta tarar Jalila tana danna waya, ta dan hade rai tace
"wato baki damu da Suprise din ba ko?"
Jalila tace
"ai naga baki da niyyar gayamin ne"
Nana ta dakko powder da janbaki tazo gaban Jalila ta zauna.
Jalila ta kalleta
"wannan na menene kuma?"
"fita zamuyi, yaya Jawwad yace mu shirya"
Jalila ta dan bata fuska tace
"haba dai muje ina? Banda wannan gajiyar"
"ni dai ba ruwa na, shi yace mu shirya zamu dan fita"
ta shashsha fawa Jalila powder da jan baki sunayi suna fada Jalila tana mitar ita gaskiya bata son kuma fita a gajiye take
Hanan ta shigo tace
"Jalila har yanzu baki je ba?"
Cikin rashin fahimta Jalila tace
"nifa ban gane muku ba, inje ina kuma?"
Nana tace "kije BQ ki duba Suprise din yana can"
"nifa Nana nakasa gane miki, kince Yaya Jawwad yace zamu fita kuma kince zakiyi surprising dina"
Hanan tace
"dan Allah kije ki gani mana, ke ba kyacin ribar abu, ga mitar tsiya"
Jalila tace "saura inje inga shirme, sena muku rashin mutunci"
Hanan tace "in kuma akasin shirmen kika gani fa?"
Jalila tace "Bari dai inje in gani tukuna" ta dauki gyale ta yafa akan riga da skirt din jikinta ta fita
Da taje inda Nana tace taje bata ga kowa ba se Yaya Jawwad a parlor
Jawwad ya kalle ta yace
"Baby ya akayi ne?" ba tace masa komai ba se dai dan shiru da tayi tana nazarin dakin, tana kokarin gano wani abu, kaman kamshin turaren Jalal take ji, Jawwad yayi murmushi yace
"duba wancan bedroom din yana ciki, nasan shi kika biyo"
Ba tareda tace komai ba ta nufi dakin da Jawwad ya nuna mata da sauri, ga mamaki kuwa tana zuwa tatarar Jalal yabawa kofa baya, sanye da dogon wandon jeans da vest a jikin sa yana waya, da gudu ta tafi ta rungume shi ta baya, dan murmushi yayi yai sallama da wanda yake wayar da shi, ya aje wayar ya juyo da ita suna fuskantar juna, har hawaye ya wanke fuskarta.
"Ohhh am sorry dear, waye ya gayamiki ina nan ma tukuna?"
Shigewa jikinsa ta kumayi ta kankameshi kamar wani ze kwace mata shi ta sake fashewa da kuka.
Jalal yace "Subhanallah Kin san bana son kukanki, gayamin me yasa min ke kuka?"
A hankali ta fara magana cikin kuka "Am sorry Jalal, Am sorry"
"Aini bakimin komai ba, kidena kukan nan please"
Kasa denawa tayi, Hawaye ne wani na bin wani keta zuba daga idon ta.
Jalal yace
"Am sorry My love, ni nayi miki laifi, tsawon wannan lokaci dana boye miki nasan inda Ummi take, am very sorry ba laifina bane"
Tasa hannu ta toshe masa baki tareda girgiza masa kai.
"Nina yi maka laifi zaujee"
A hankali ta durkusa akan gwiwowin ta, ta rike kafafuwan sa tareda fadin
"Jalal nagode, bani da kalaman dan zasu nuna maka godiya ta, Allah ya biyaka da gidan Aljanna, sannan Kayi hakuri Jalal abunda na dinga yi maka a baya please forgive me"
Ba karamin mamaki abunda Jalila tayi ya bashi ba, da hanzari ya dagota ya zauna ya rungumeta a jikinsa, cikin sigar rarrashi ya fara magana
"Jalila laifin me kikayi min dana cancanci haka? Nima Ummi uwata ce"
Cikin tsokana yace "yarinya seda Ummi ta sameni sannan ta haifeki fa, kidena min wata godiya abunda nayi kaina nayiwa, sannan ni ba abunda kika yimin dana cancanci ki durkusa kina bani hakuri haka, ni yakamata in durkusa in miki godiya, Bayan Jawwad ban taba tunanin akwai wanda ze damu da al'amurana kamar ke ba, kalli rayuwar da nayi a baya, kalli wadda nake a yanzu, kinsaka rayuwar ki a cikin hatsari saboda ni, wani nasani wani ban saniba, abubuwam da kikayi min a baya kuruciya ce, kuma kinyi ne saboda kina kyamar mummunar Rayuwar da nakeyi, Thank you very much for all what you did for me, kin kawo canji mafi girma a rayuwar ABDUL JALAL, I love you so much my wife "
Ta kara kankame shi tareda fadin
"I love you too, Zaujee"
Yadda tayi maganar yaji wani abu ya tsirga tundaga kansa har tafin kafarsa.
"Jalila Do you really mean what you say?"
Jinjina masa kai tayi
"I mean it zaujee, I love you"
Jalal yaja numfashi yace
"Kalamai masu girma dana dade ina expecting a gayamin, gayamin yaushe kika fara sona ne?"
Murmushi tayi tace
"hmm wani dogon zamani da ya wuce, da farko dai na dauka kishi ne da tausayi daga baya kawai aka shammaceni aka jani fagen soyayya"
Dariya Jalal yayi yace "waye ya jaki fagen soyayyar?"
"Mijina mana daya tamkar da dubu"
"dan Allah ki dan kara cewa kina sona mana"
"I love you Zaujee"
Ya dan kashe mata ido yace "dan kara fada mana"
"Anki din bazan sake fadan ba cikani in tafi"
Kara riketa yayi yana dariya, abu kaman wasa Jalila taji Jalal yana neman wuce gona da iri dan haka ta rike hannunsa, tareda kiran sunansa da dan karfi
"Jalal"
Ya bude idonsa yana kallon ta
"Dan Allah ka kyaleni ba fa a gida muke ba"
"Au a daji muke?"
Kaman zatayi kuka tace
"Ina nufin ba'a gidanmu muke ba, Yanzu Ummi zata iya nemana fa"
"Shikenan karkimin kuka Sarkin kuka, Amma Jalila yakamata mu koma gida fa, yaushe zamu koma?"
"duk lokacin da kake so"
Ya dan lumshe ido yace "ko yanzu?"
Jinjina masa kai tayi alamar eh
"Shikenan ki koma ciki, da safe Insha Allah zan shigo in gaida Ummi, ki shirya gobe zamu fita yawo"
"ina zamuje?"
"Allah ya kaimu gobe zaki gani, in kinyi Salla ki hau online"
Hararsa tayi
"bazan hau ba din, kuma ba yawon dazan bika, kusan sati biyu nayi a cikin damuwa da kewar ka, nima sena rama"
"Haba matar kiyi hakuri, banyi hakan da gangan ba, nasan dana bar wayata a kunne, kirana zakiyi tayi kina koke2, nikuma bana son inji kina kukan nan shiyasa, Allah yabaki hakuri"
Mikewa tayi ta dau mayafinta tace
"kaga na tafi seda safe" kafin yayi wata magana tai waje abunta.
Tana zuwa ta tarar Ummi tana sama ita da Maama a dakin Inna, dan haka kai tsaye dakin da sukw ta wuce taje ta tarar da su Hanan sunyi kwadan garri suna ci.
Tana shiga Hanan kalleta tace "lallai matar so, se yanzu?"
Jalila ta harareta tace "ban sani ba"
Nana tai dariya tace "Jalila ina Jan bakin?"
Cikin ko in kula tace "mun shanye abinmu"
Hanan tace "wallahi Jalila baki da kunya"
Jalila tace "har na kaiki rashin kunya, kudena gulmar nan ku maida kai kuci garrin kwakinku"
Nana tace "zakiga mu maida kai muci garri, kema zezo kanki ne"
Jalila tana idar da sallar isha'i tai Azkar, suka fara waya da Jalal.
Duk soyayyar da Jalila tayi Abaya yanzu take tabattar da shirme ce yanzi ta gane menene hakikanin soyayya, yanzu ta gane se yanzu ta shigo fagen soyayya, Jalal yana tarairayar ta da nuna mata tsantsar kulawa.
Da suka gama wayar ma da Jalal chatting suka koma yi, da kyar sukayi wa juna sallama suka kwanta.
Kusan kullum idan yamma tayi, su Jalal se sun dau matansa sunfita yawo.
Jalal seda ya kyale Jalila takara kwana goma da Ummi sannan yace yana son sukoma Gida, Nana da Hanan duk sun riga sun tafi.
Jalila tunda taji yace su tafi tasan ya mata kara, amma seda tayi kuka, ana gobe zasu tafi Ummi ta kirasu ta zauna da su taita musu nasiha a karshe tace
"Jalila ga amanar dana nan, ki kulamin dashi, kiyaye hakkokinsa ki guji abunda ze bata masa rai koya sa shi yin fushi"
Jalila ta dan tura baki tace
"to shi bazaki ce masa ga amana ta ba"?
Ummi tai murmushi "Jalila ai bazaki taba canza hali ba, ni Jalal ne dana dole in jadadda miki ki kulamin da shi"
Jalal ya dinga yi mata dariya, Jalila tace "Ummi wai bazaki bimu mu koma kano ba?"
Ummi tace
"in biku in muku me? Gidan mu zan koma nima, se an kwana biyu zanzo in ga dakinki, nidai fatana Allah ya zaunar mana daku lafiya a daku nan ku"
Sam ba haka Jalila ta so ba, nan da nan ta fara kuka, Gaba daya yanayin Jalal ya sauya ganin yadda Jalila ta fara kuka Ummi tace
"Jalal tashi ka tafi kyleta, gobe insha Allah zaku tafi"
Haka Jalal ya tashi ya tafi.
Washegari gurin karfe sha daya na safe suka baro Bauchi zuwa kano ba dan Jalila taso ba dan sam bata gaji da ganin Ummin nata ba, ta sha kuka sosai kafin su taho.
Bayan Azahar suka isa gida, Jalal ya tafi masallaci Dan la'asar ta gabato, ita kuma Jalila ta shiga gida da kayan su.
Ta bude Dakin ta ta shiga ta tarar da Akwatina a ciki, set uku blue, silver, da purple kowacce uku da kit.
Mamaki ne yakamata tareda tunanin waye ya kawo wannan kayan? Kuma na menene.
Bata taba su ba, ta ajiye kayan da suka dawo dasu, tai salla ta shiga gyaran gida, saboda duk yayi kura kusan wata guda kenan bakowa a ciki, ta share ko ina tai mopping ta wanke toilet da glasses na window harta gama tana tunanin kayan nan.
Seda akayi sallar magariba Jalal ya dawo hannunsa da ledoji, a parlor ya tarar da ita tana kallon zee world
"Waike ba kya gajiya ne, daga dawowarki kin tsiri aiki"
Batace komai ba se murmushi da tayi ta karbi kayan hannunsa
"ina ka tafine haka?"
"na tsaya nayi salla ne, sannan naje nayi mana siyayya abunda zamuci base kinyi girki ba"
Jalila ta dan numfasa tace "Akwatinan me ka ajiye a dakina?"
"Nakine na lefe ko ba suyi miki bane?"
"Amma Jalal....
Yatsan sa ya dora akan lips dinta yace
"Shhhh bana bukatar sharhi, tuhuma, ko godiya, a cigaba da yimin kwalliya kawai, babu bukatar kimin wata godiya dakko plate da cup muci Abinci"
Jiki a sanyaye ta dakko plate tazo ta ajiye ya zazzage ledar kaza ce da dogayen kwalayen madara, ya zuba a plate ya mika mata yace
"feed me"
Gaba daya ya lura a tsorace take da shi yau, da dane da yanzu watakila ta haye cinyarsa tana tsokanar sa, Amma yau ko kusa dashi taki zuwa karshe dai shi ya dinga bata amma taki ci se kyaleta yayi.
Bayan ta idar da sallar isha'i tai wanka ta haye gadon ta tai kwanciyar ta dan tana jin bacci sosai harta fara bacci taji an kunna wutar lantarkin dake Dakin ta, dan rintse ido tayi, sannan ta bude a hankali ta sauke akan Jalal
Murmushi yayi yace "shine yau ko azo muyi azkar din ko? To ni nazo muyi"
Janyo bargo tayi ta shige ta rufe har kanta ta dunkunkune, ba karamin dariya ta bashi ba, ya kashe fitilar ya hau kan gadon yace
"ni kike gudu haka ko Baby?, fitowa zakiyi"
Ya fara kokarin janye bargon nata,
"nifa bacci nake ji ka kyaleni"
Banza yayi mata seda ya cirota daga bargon, gaba daya Jikin ta yayi sanyi,
"Jalila ni kike gudu haka ko? Hada shigewa bargo, ance ana sona amma ana guduna haka akeyi, burina ya cika ummi na ta warke, Baby na ta hadu da Ummin ta, yakamata a tausayamin haka Baby na azabtu fa"
Haka yai ta mata surutai, Bata gama firgita ba seda taji abunda Jalal din ke kokarin yi ya shallake tunanin ta,
Yau dai Jalila baki ya mutu, ko kwakwaran motsi takasa se kuka da kiran Ummi, duk yadda take tunanin abun ya wuce tunanin ta, seda Jalal fanshe soyayyar sa ta tsawon shekaru.
Kaman ba Jalal din nan me mugun jin kai da hade rai ba.
Bayan komai ya lafa Jalal ya rungume Jalila tsam a kirjinsa yana so yayi magana amma sam yakasa, a hankali taji jikinsa na daukar zafi fiye da kima, ganin yakasa magana yasa shi sakinta ya juya mata baya,
Ji tayi kamar ana girgiza gadon da suke kai, juyawa tayi taga jikin Jalal ne yake karkarwa, ta kai hannunta jikin sa taji kamar wanda aka hurawa wuta bata taba jin jikin dan adam yayi zafin haka ba.
Vote, Comment and
Share please
I want comments not stickers or just thanks
Daga alkalamin Aysher cool
🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️
What's app only 07063065680.
Follow me onWatpad @Ayshercool7724
🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹 🌹
*ABDUL JALAL*
_Story, writing and edited _
By
AISHA HUMAIRA
( _Daddy's girl_)
*PERFECT WRITER'S*
*ASSOCIATION*🌞
(𝕎𝔼 𝔸𝕀ℕ'𝕋 ℙ𝔼ℝ𝔽𝔼ℂ𝕋 𝔹𝕌𝕋 𝕎𝔼'ℝ𝔼 𝔸𝕃𝕎𝔸𝕐𝕊, 𝕋ℝ𝕐𝕀ℕ𝔾 𝕆𝕌ℝ 𝔹𝔼𝕊𝕋 𝕋𝕆 𝕄𝕆𝕋𝕀𝕍𝔸𝕋𝔼 𝔸ℕ𝔻 𝔼ℕ𝕋𝔼ℝ𝕋𝔸𝕀ℕ 𝕆𝕌ℝ ℝ𝔼𝔸𝔻𝔼ℝ𝕊💪)
/https://www.facebook.com/Perfect-writers-association-100452275039839/
*P.W.A*✍️
Bismillahirrahmanirrahim, da sunan Allah me rahama me jinkai, Allah yakara tsira da aminci ga shugabanmu Annabi muhammadu salallahu alaihi wassalam.
Bayan haka bazan gajiba da mika gaisuwata da godiya ga yan uwa da abokan arziki ba, bayan haka
Banyarda a juyamin littafi ba ko amfani da wani bangare ba tareda izinina ba.
Domin gyara, shawara ko sharhi, za a iya tuntubata akan what's app number dina
07063065680
Or email address @ [email protected]
Watpad @Ayshercool7724
_MY FIRST NOVEL _
Shiri sukayi sosai don tafiya garinsu Ummi, da farko akace baza'aje da su Nana ba saboda larurar ciki, amma sukace baza'ayi babu su ba suma suna son zuwa garinsu Ummi.
Shiri sukayi sosai, suka dau motoci suka nufi kwara state.
Tunda suka shiga garin Jalila ta kara tabattar da lallai Akwai banbancin Addini da al'ada.
Jalila tayi mamakin irin kyau da tsaruwar masarautar su Ummin ta, lallai Ummi ta cancanci yabo da jinjina, da ta iya tsallake wannan daular ta zabi Addinin musulunci da kuma soyayya.
Su nasu masarautun basa amfani da doki, se manyan motoci, ga barori nan nata kaiwa suna komowa, gasu da matukar biyayya, duk inda suka ratsa zubewa ake ana girmama su, musamman Ummi.
Seda suka shiga cikin gidan ta kara tabattar da lallai Ummi ba karamar 'yar gata bace ba, Tangamemen hoton Mahaifiyar Ummi ne sakale a wani katon guri kamarta daya sak da Ummi, duk da ta manyan ta seka dauka ya da kanwa ne.
An karbesu cikin girmamawa da mutuntawa, Seda suka huta, Aka dinga gabatar musu da kayan Abinci,
Seda aka jima suka huta sannan Mahaifiyar Ummi ta fito, Mahaifiyar Ummi na ganin Jalila ta rungumeta cikin harshen turanci tace
"ko ba' a gayamin ba nasan wannan itace jikata"
Ummi tayi murmushi tace "Eh itace"
Mahaifiyar Ummi ta kalli su Hanan ta kalli Jalila tace
"wannan 'yan uwanta ne?"
Jawwad yace "Eh duk' yan uwanta ne"
"to wace matar Jalal kenan?"
Nana tace "Jalila ce matarsa"
Mahifiyar Ummi ta jinjina kai tace
"Sunan ta da mijin ta suna kama, mijinki yana da kirki sosai lokacin da mamanki ta dawo gida yana zuwa nan"
Maman Ummi tana da kirki sosai, nan aka dinga gabatar da su gurin mutanen gidan, 'yan gidan sunyi murnar ganin yarinyar' yar uwasu, bayan tsawon shekaru 'yar uwatasu bata tareda su.
Sarkin da yake mulki a wannan lokacin wanda yakasance Yaya ga Ummi shima ya nuna farincikin sa da jin dadi, na ganin su Jalila.
Daddare suna hira, mahaifiyar Ummi take cewa su Jalila,
"nayi dana sanin hana marry ta auri wanda take so a wancan lokacin, dukda ba laifina bane, laifin kakanta ne, yana ganin na auri bahaushe musulmi zaman beyi dadi ba, nayi kewar ta sosai tsawon wannan lokaci, bana iya bacci, sannan mahaifina yace be yadda in tura kasar hausawa a nemo ta ba, duk abunda yafaru da ita babu ruwan wani. Ban taba zaton marry zata iya jure zama tsawon wannan lokacin ba ba tare da mu ba, bayan rasuwar mahaifina shekaru biyar baya, Yayanta ya karbi mulki, shi da kansa yasa a bincika koza'a gano ta amma abun be yuwu ba, na koma Addinin musulinci, Yayana yaba wa kowa damar yayi Addinin da yake so, abun mamaki akan marry na yadda musulmi kuma hausawa mutanen kirki ne, lokacin da ta dawo gidan nan nayi mamaki, labarin da ta bani akan yadda rayuwar hausawa musulmi yake, da kuma karamcin da suka nuna mata, musamman wannan dan kyakywan yaron me dogon hanci, yana burgeni matuka yana girmama ta kaman ta haifeshi, kuma da ta gayamin alakar dake tsakaninsu naga babu wani babbar alaka da suka hada amma yake ta dawainiya da ita shida iyalansa"
Jalila ta kunshe kai tana dariya taji ance Dan kyakywan yaro me dogon hanci
Hanan tace "Dallacan se wani murmushi take dan ance mijinta kyakywa, nima mijina kyakywa ne, dan mijina farine tas"
Nana tai caraf tace "nima mijina yana da kyan ai, tunda kanin mijin Jalila ne"
Sukaita hira suna dariya, mahaifiyar Ummi tana da kirki da sanyin hali kamar Ummi gata da faran faran babu ruwanta.
Amma duk abun nan Jalila hankalin ta yana kan Jalal, ta damu sosai rashin ganin sa, ba karamin missing dinsa take ba.
Kwanan su hudu a garin, sun sha yawo, garin yana da kyau, sun sha hotuna, gasu da yalwar dazuka, Akwai fulani a garin, da babur amma yawancin su yarabawa ne, suma mutane masu kirki da kyakywar mu'amala.
A kwana na biyar suka fara shiri domin tafiya su bar garin.
Mahaifiyar Ummi taji babu dadi, seda tayi mita
"marry meyasa bazaki barmin yaran nan ba su dan kara kwanaki, wallahi sun shiga raina sosai naji dadin zama da su"
Ummi tace
"kiyi hakuri zasu dinga kawomiki ziyara, matan aure ne yaran nan, yakamata su koma gidajen Auren su, sannan Zamuje maiduguri gidan Su Danki Jalal, Abban Jawwad zasu jira mu a can"
"Shikenan amma ba haka naso ba, naso kara zama damu, yanzu na kara tabattar da abunda ake fada akan hausawa musulmai ba haka bane, kuna da kyakywar mu'amala da kuma girmama mutane, Jawwad amma kaima zaka dan dinga zuwa ko?"
Jawwad yai murmushi yace "karki damu, dukkan mu ma zamu dinga kawo miki ziyara, amma kema muna fatan zakizo mana"
"zanzo mana, tunda ina daku, Insha Allah nima zanzo muku"
A kwana na biyar suka karasa shiri zasu tafi, An musu alkhairi me tarin yawa. Suka yi harama Jawwad ya dauke su suka baro garin suka nufi borno state.
A motar ma se hira suke, suna kara yaba kirkin mahaifiyar Ummi da kuma barkwancin ta.
Suka karasa maiduguri a gajiye, bayan la'asar sosai suka karasa, Antyn Jalal tayi murnar ganin su kwarai, musamman da ta gansu tareda Ummi cikin fara'a tace
"kai masha Allah, bakin ba zata, Ummi Kice keda iyalan naki gaba daya kike tafe"
Ummi tace "Aikam dai gasu nan"
"sannunku da zuwa Jawwad, dazu Jalal ya bar garin nan, nasan be san zaku zo ba"
Jalila a ranta taji dama tun dazun sukazo,
"meyasa Jalal yakemin hakane? Duk na damu yaki bari mu hadu sam, why?"
Anty tace
"Jalilan Ummi, gaki ga Ummi, dazu Jalal yabar garin nan, albarkacin ki yasa ya kan leko mu ya kawo mana ziyara, bashi da aiki se yabon matarsa ko kunya ta bayaji" dan murmushi Jalila tayi ta sunkuyar da kai.
Jawwad yayi alwala ya tafi masallaci,
Suma sallolin su suka gabatar, Anty se lallaba su Hanan take saboda ciki da suke dauke da shi.
Jalila tace "Anty ina Husnah ne da Amal?"
"Husnah ta koma gidan ta, Amal kuma tana gidan kanin Babanta"
Daddare mijin Anty ya dawo, yanayin yadda suka gaisa da Ummi ze tabattar maka da sun san juna, nan Ummi take gaya masa daga kwara State suke, ya nuna farincikin sa da jin dadin sa akan hakan, gefe guda kuma ya dinga tsokanar Jalila
"matar so inji mijin ta, ya akayi kukayi sabani da mijin naki ne? Shi ya tafi dazu kekuma kinzo yanzu, ya akayi hakan ta kasance? Gayamin sirrin mana daughter, banda zancenki ba abunda Jalal yake in ya zauna"
Jalila dai kasa magana tayi, kowa tsokanar ta yake saboda Jalal.
Itakam Hanan ana wannan hirar ta silale ta tafi masaukin Jawwad daga ta kai masa Abinci bata dawo ba se bayan karfe daya, Jalila ta dinga ce mata mara kunya.
Washegari wajen Azahar Abban Jawwad da Daddyn Hanan, se Maama da Mummy Hanan suka iso, gida ya dau harami ya cika da baki.
Suna zuwa da suka huta ba tare da bata lokaci ba Daddy ya gabatar da abunda ya kawo su na zuwa su jadadda godoyar su akan karamci da dawainiyar da sukayiwa Ummi.
Abee yace
"babu bukatar ku cigaba dayi mana godiya, duk abunda Jalal yayi wa Wannan baiwar Allah be fadi ba, musamman shima dawainiyar da soyayyar data nuna masa a lokacin da shi da mara uwa kusan daya, mun riga mun zama daya da mu da ku, dan Allah batun godiyar nan a barshi, Allah yakara hada kanmu ya kara mana kaunar juna, Allah ya Albarkaci rayuwar yaran mu, Amma babu godiya a tsakaninmu"
Suka Amsa da Ameen gaba daya.
Kwana daya su Abba sukayi, suka kama hanya zuwa bauchi, kafafuwan Hanan duk sun dan kumbura saboda zaman mota, hakan yasa Jawwad ya damu yace a bauchi ze barta ta huta, in yaso ya biya kudin jirgi su koma Abuja. Tun suna hanya Mahmoud ya kira Nana a waya yace mata yana bauchi, Nana se murna take yi, yau zata ga mijin ta, Jalila ta danyi shiru tana tunanin nata mijin.
A gajiye suka koma garin bauchi, a yan kwanakin nan sun sha yawo, da suka isa bauchi Jalila wanka tayi ta nemi guri ta kwanta tana baccin gajiya.
Jalila bata tashi ba seda Ummi tazo ta tasheta
"ki tashi haka kiyi salla kici Abinci mana, baccin ya isa haka uwar bacci ashe har yanzu baki dena wannan baccin ba"
A shagwabe tace
"Ummi wallahi a gajiye nake shiyasa"
"ki tashi haka dai baccin ya isa"
Jalila ta tashi tai salla ta zubo Abinci ta zauna kenan ta fara ci Nana ta shigo, ta kalli Jalila tace
"se yanzu kika tashi kenan? In kin gama akwai surprise"
"Suprise kuma? Suprise din me?"
"sekin gama tukuna"
Jalila tace "shikenan"
Jalila ta cinye Abincin ta, tanemi guri ta kashingida tana danna waya.
Nana ta dawo dakin ta tarar Jalila tana danna waya, ta dan hade rai tace
"wato baki damu da Suprise din ba ko?"
Jalila tace
"ai naga baki da niyyar gayamin ne"
Nana ta dakko powder da janbaki tazo gaban Jalila ta zauna.
Jalila ta kalleta
"wannan na menene kuma?"
"fita zamuyi, yaya Jawwad yace mu shirya"
Jalila ta dan bata fuska tace
"haba dai muje ina? Banda wannan gajiyar"
"ni dai ba ruwa na, shi yace mu shirya zamu dan fita"
ta shashsha fawa Jalila powder da jan baki sunayi suna fada Jalila tana mitar ita gaskiya bata son kuma fita a gajiye take
Hanan ta shigo tace
"Jalila har yanzu baki je ba?"
Cikin rashin fahimta Jalila tace
"nifa ban gane muku ba, inje ina kuma?"
Nana tace "kije BQ ki duba Suprise din yana can"
"nifa Nana nakasa gane miki, kince Yaya Jawwad yace zamu fita kuma kince zakiyi surprising dina"
Hanan tace
"dan Allah kije ki gani mana, ke ba kyacin ribar abu, ga mitar tsiya"
Jalila tace "saura inje inga shirme, sena muku rashin mutunci"
Hanan tace "in kuma akasin shirmen kika gani fa?"
Jalila tace "Bari dai inje in gani tukuna" ta dauki gyale ta yafa akan riga da skirt din jikinta ta fita
Da taje inda Nana tace taje bata ga kowa ba se Yaya Jawwad a parlor
Jawwad ya kalle ta yace
"Baby ya akayi ne?" ba tace masa komai ba se dai dan shiru da tayi tana nazarin dakin, tana kokarin gano wani abu, kaman kamshin turaren Jalal take ji, Jawwad yayi murmushi yace
"duba wancan bedroom din yana ciki, nasan shi kika biyo"
Ba tareda tace komai ba ta nufi dakin da Jawwad ya nuna mata da sauri, ga mamaki kuwa tana zuwa tatarar Jalal yabawa kofa baya, sanye da dogon wandon jeans da vest a jikin sa yana waya, da gudu ta tafi ta rungume shi ta baya, dan murmushi yayi yai sallama da wanda yake wayar da shi, ya aje wayar ya juyo da ita suna fuskantar juna, har hawaye ya wanke fuskarta.
"Ohhh am sorry dear, waye ya gayamiki ina nan ma tukuna?"
Shigewa jikinsa ta kumayi ta kankameshi kamar wani ze kwace mata shi ta sake fashewa da kuka.
Jalal yace "Subhanallah Kin san bana son kukanki, gayamin me yasa min ke kuka?"
A hankali ta fara magana cikin kuka "Am sorry Jalal, Am sorry"
"Aini bakimin komai ba, kidena kukan nan please"
Kasa denawa tayi, Hawaye ne wani na bin wani keta zuba daga idon ta.
Jalal yace
"Am sorry My love, ni nayi miki laifi, tsawon wannan lokaci dana boye miki nasan inda Ummi take, am very sorry ba laifina bane"
Tasa hannu ta toshe masa baki tareda girgiza masa kai.
"Nina yi maka laifi zaujee"
A hankali ta durkusa akan gwiwowin ta, ta rike kafafuwan sa tareda fadin
"Jalal nagode, bani da kalaman dan zasu nuna maka godiya ta, Allah ya biyaka da gidan Aljanna, sannan Kayi hakuri Jalal abunda na dinga yi maka a baya please forgive me"
Ba karamin mamaki abunda Jalila tayi ya bashi ba, da hanzari ya dagota ya zauna ya rungumeta a jikinsa, cikin sigar rarrashi ya fara magana
"Jalila laifin me kikayi min dana cancanci haka? Nima Ummi uwata ce"
Cikin tsokana yace "yarinya seda Ummi ta sameni sannan ta haifeki fa, kidena min wata godiya abunda nayi kaina nayiwa, sannan ni ba abunda kika yimin dana cancanci ki durkusa kina bani hakuri haka, ni yakamata in durkusa in miki godiya, Bayan Jawwad ban taba tunanin akwai wanda ze damu da al'amurana kamar ke ba, kalli rayuwar da nayi a baya, kalli wadda nake a yanzu, kinsaka rayuwar ki a cikin hatsari saboda ni, wani nasani wani ban saniba, abubuwam da kikayi min a baya kuruciya ce, kuma kinyi ne saboda kina kyamar mummunar Rayuwar da nakeyi, Thank you very much for all what you did for me, kin kawo canji mafi girma a rayuwar ABDUL JALAL, I love you so much my wife "
Ta kara kankame shi tareda fadin
"I love you too, Zaujee"
Yadda tayi maganar yaji wani abu ya tsirga tundaga kansa har tafin kafarsa.
"Jalila Do you really mean what you say?"
Jinjina masa kai tayi
"I mean it zaujee, I love you"
Jalal yaja numfashi yace
"Kalamai masu girma dana dade ina expecting a gayamin, gayamin yaushe kika fara sona ne?"
Murmushi tayi tace
"hmm wani dogon zamani da ya wuce, da farko dai na dauka kishi ne da tausayi daga baya kawai aka shammaceni aka jani fagen soyayya"
Dariya Jalal yayi yace "waye ya jaki fagen soyayyar?"
"Mijina mana daya tamkar da dubu"
"dan Allah ki dan kara cewa kina sona mana"
"I love you Zaujee"
Ya dan kashe mata ido yace "dan kara fada mana"
"Anki din bazan sake fadan ba cikani in tafi"
Kara riketa yayi yana dariya, abu kaman wasa Jalila taji Jalal yana neman wuce gona da iri dan haka ta rike hannunsa, tareda kiran sunansa da dan karfi
"Jalal"
Ya bude idonsa yana kallon ta
"Dan Allah ka kyaleni ba fa a gida muke ba"
"Au a daji muke?"
Kaman zatayi kuka tace
"Ina nufin ba'a gidanmu muke ba, Yanzu Ummi zata iya nemana fa"
"Shikenan karkimin kuka Sarkin kuka, Amma Jalila yakamata mu koma gida fa, yaushe zamu koma?"
"duk lokacin da kake so"
Ya dan lumshe ido yace "ko yanzu?"
Jinjina masa kai tayi alamar eh
"Shikenan ki koma ciki, da safe Insha Allah zan shigo in gaida Ummi, ki shirya gobe zamu fita yawo"
"ina zamuje?"
"Allah ya kaimu gobe zaki gani, in kinyi Salla ki hau online"
Hararsa tayi
"bazan hau ba din, kuma ba yawon dazan bika, kusan sati biyu nayi a cikin damuwa da kewar ka, nima sena rama"
"Haba matar kiyi hakuri, banyi hakan da gangan ba, nasan dana bar wayata a kunne, kirana zakiyi tayi kina koke2, nikuma bana son inji kina kukan nan shiyasa, Allah yabaki hakuri"
Mikewa tayi ta dau mayafinta tace
"kaga na tafi seda safe" kafin yayi wata magana tai waje abunta.
Tana zuwa ta tarar Ummi tana sama ita da Maama a dakin Inna, dan haka kai tsaye dakin da sukw ta wuce taje ta tarar da su Hanan sunyi kwadan garri suna ci.
Tana shiga Hanan kalleta tace "lallai matar so, se yanzu?"
Jalila ta harareta tace "ban sani ba"
Nana tai dariya tace "Jalila ina Jan bakin?"
Cikin ko in kula tace "mun shanye abinmu"
Hanan tace "wallahi Jalila baki da kunya"
Jalila tace "har na kaiki rashin kunya, kudena gulmar nan ku maida kai kuci garrin kwakinku"
Nana tace "zakiga mu maida kai muci garri, kema zezo kanki ne"
Jalila tana idar da sallar isha'i tai Azkar, suka fara waya da Jalal.
Duk soyayyar da Jalila tayi Abaya yanzu take tabattar da shirme ce yanzi ta gane menene hakikanin soyayya, yanzu ta gane se yanzu ta shigo fagen soyayya, Jalal yana tarairayar ta da nuna mata tsantsar kulawa.
Da suka gama wayar ma da Jalal chatting suka koma yi, da kyar sukayi wa juna sallama suka kwanta.
Kusan kullum idan yamma tayi, su Jalal se sun dau matansa sunfita yawo.
Jalal seda ya kyale Jalila takara kwana goma da Ummi sannan yace yana son sukoma Gida, Nana da Hanan duk sun riga sun tafi.
Jalila tunda taji yace su tafi tasan ya mata kara, amma seda tayi kuka, ana gobe zasu tafi Ummi ta kirasu ta zauna da su taita musu nasiha a karshe tace
"Jalila ga amanar dana nan, ki kulamin dashi, kiyaye hakkokinsa ki guji abunda ze bata masa rai koya sa shi yin fushi"
Jalila ta dan tura baki tace
"to shi bazaki ce masa ga amana ta ba"?
Ummi tai murmushi "Jalila ai bazaki taba canza hali ba, ni Jalal ne dana dole in jadadda miki ki kulamin da shi"
Jalal ya dinga yi mata dariya, Jalila tace "Ummi wai bazaki bimu mu koma kano ba?"
Ummi tace
"in biku in muku me? Gidan mu zan koma nima, se an kwana biyu zanzo in ga dakinki, nidai fatana Allah ya zaunar mana daku lafiya a daku nan ku"
Sam ba haka Jalila ta so ba, nan da nan ta fara kuka, Gaba daya yanayin Jalal ya sauya ganin yadda Jalila ta fara kuka Ummi tace
"Jalal tashi ka tafi kyleta, gobe insha Allah zaku tafi"
Haka Jalal ya tashi ya tafi.
Washegari gurin karfe sha daya na safe suka baro Bauchi zuwa kano ba dan Jalila taso ba dan sam bata gaji da ganin Ummin nata ba, ta sha kuka sosai kafin su taho.
Bayan Azahar suka isa gida, Jalal ya tafi masallaci Dan la'asar ta gabato, ita kuma Jalila ta shiga gida da kayan su.
Ta bude Dakin ta ta shiga ta tarar da Akwatina a ciki, set uku blue, silver, da purple kowacce uku da kit.
Mamaki ne yakamata tareda tunanin waye ya kawo wannan kayan? Kuma na menene.
Bata taba su ba, ta ajiye kayan da suka dawo dasu, tai salla ta shiga gyaran gida, saboda duk yayi kura kusan wata guda kenan bakowa a ciki, ta share ko ina tai mopping ta wanke toilet da glasses na window harta gama tana tunanin kayan nan.
Seda akayi sallar magariba Jalal ya dawo hannunsa da ledoji, a parlor ya tarar da ita tana kallon zee world
"Waike ba kya gajiya ne, daga dawowarki kin tsiri aiki"
Batace komai ba se murmushi da tayi ta karbi kayan hannunsa
"ina ka tafine haka?"
"na tsaya nayi salla ne, sannan naje nayi mana siyayya abunda zamuci base kinyi girki ba"
Jalila ta dan numfasa tace "Akwatinan me ka ajiye a dakina?"
"Nakine na lefe ko ba suyi miki bane?"
"Amma Jalal....
Yatsan sa ya dora akan lips dinta yace
"Shhhh bana bukatar sharhi, tuhuma, ko godiya, a cigaba da yimin kwalliya kawai, babu bukatar kimin wata godiya dakko plate da cup muci Abinci"
Jiki a sanyaye ta dakko plate tazo ta ajiye ya zazzage ledar kaza ce da dogayen kwalayen madara, ya zuba a plate ya mika mata yace
"feed me"
Gaba daya ya lura a tsorace take da shi yau, da dane da yanzu watakila ta haye cinyarsa tana tsokanar sa, Amma yau ko kusa dashi taki zuwa karshe dai shi ya dinga bata amma taki ci se kyaleta yayi.
Bayan ta idar da sallar isha'i tai wanka ta haye gadon ta tai kwanciyar ta dan tana jin bacci sosai harta fara bacci taji an kunna wutar lantarkin dake Dakin ta, dan rintse ido tayi, sannan ta bude a hankali ta sauke akan Jalal
Murmushi yayi yace "shine yau ko azo muyi azkar din ko? To ni nazo muyi"
Janyo bargo tayi ta shige ta rufe har kanta ta dunkunkune, ba karamin dariya ta bashi ba, ya kashe fitilar ya hau kan gadon yace
"ni kike gudu haka ko Baby?, fitowa zakiyi"
Ya fara kokarin janye bargon nata,
"nifa bacci nake ji ka kyaleni"
Banza yayi mata seda ya cirota daga bargon, gaba daya Jikin ta yayi sanyi,
"Jalila ni kike gudu haka ko? Hada shigewa bargo, ance ana sona amma ana guduna haka akeyi, burina ya cika ummi na ta warke, Baby na ta hadu da Ummin ta, yakamata a tausayamin haka Baby na azabtu fa"
Haka yai ta mata surutai, Bata gama firgita ba seda taji abunda Jalal din ke kokarin yi ya shallake tunanin ta,
Yau dai Jalila baki ya mutu, ko kwakwaran motsi takasa se kuka da kiran Ummi, duk yadda take tunanin abun ya wuce tunanin ta, seda Jalal fanshe soyayyar sa ta tsawon shekaru.
Kaman ba Jalal din nan me mugun jin kai da hade rai ba.
Bayan komai ya lafa Jalal ya rungume Jalila tsam a kirjinsa yana so yayi magana amma sam yakasa, a hankali taji jikinsa na daukar zafi fiye da kima, ganin yakasa magana yasa shi sakinta ya juya mata baya,
Ji tayi kamar ana girgiza gadon da suke kai, juyawa tayi taga jikin Jalal ne yake karkarwa, ta kai hannunta jikin sa taji kamar wanda aka hurawa wuta bata taba jin jikin dan adam yayi zafin haka ba.
Vote, Comment and
Share please
I want comments not stickers or just thanks
Daga alkalamin Aysher cool
🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️
What's app only 07063065680.
Follow me onWatpad @Ayshercool7724
🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹 🌹
*ABDUL JALAL*
_Story, writing and edited _
By
AISHA HUMAIRA
( _Daddy's girl_)
*PERFECT WRITER'S*
*ASSOCIATION*🌞
(𝕎𝔼 𝔸𝕀ℕ'𝕋 ℙ𝔼ℝ𝔽𝔼ℂ𝕋 𝔹𝕌𝕋 𝕎𝔼'ℝ𝔼 𝔸𝕃𝕎𝔸𝕐𝕊, 𝕋ℝ𝕐𝕀ℕ𝔾 𝕆𝕌ℝ 𝔹𝔼𝕊𝕋 𝕋𝕆 𝕄𝕆𝕋𝕀𝕍𝔸𝕋𝔼 𝔸ℕ𝔻 𝔼ℕ𝕋𝔼ℝ𝕋𝔸𝕀ℕ 𝕆𝕌ℝ ℝ𝔼𝔸𝔻𝔼ℝ𝕊💪)
/https://www.facebook.com/Perfect-writers-association-100452275039839/
*P.W.A*✍️