PART 2
Abdul Jalal Part 2 Complete Hausa Novel · about 16 min read
_PAGE 5️⃣0️⃣ 103
Bismillahirrahmanirrahim, da sunan Allah me rahama me jinkai, Allah yakara tsira da aminci ga shugabanmu Annabi muhammadu salallahu alaihi wassalam.
Bayan haka bazan gajiba da mika gaisuwata da godiya ga yan uwa da abokan arziki ba, bayan haka
Banyarda a juyamin littafi ba ko amfani da wani bangare ba tareda izinina ba.
Domin gyara, shawara ko sharhi, za a iya tuntubata akan what's app number dina
07063065680
Or email address @ [email protected]
Watpad @Ayshercool7724
_MY FIRST NOVEL _
Da Sauri Mummy ta sha gaban Daddy tace
"Wallahi Habib seka gayamin dan me zaka yiwa Jalal Aure ba tareda nasani ba? Sannan kuma 'yar ubanwa aka Aura masa? Wato kaje kun haďa kai da wannan munafukan' yan uwan naka aka Aurawa ďana yarinya ban sani ba, to wallahi baze yuwu ba, ďa dai nawane nina haifi abuna, dan haka ba'a isa a yanke masa hukunci game da rayuwarsa ba tareda sani na ba"
"sekuma kiyi, naga yadda zaki raba Auren ai, indai Jalal ne gaki nan gashi, dai dai yake dake, Akan kira bashi da yarinyar nan zaki kuma lalata alakarki da shine kawai, dan nagaya miki yana sonta"
"karyane Wallahi, Jalal bashi da wata yarinya da yake so, Yarinyar dana zaba masa ita ze Aura"
Dama daddy yasan ze fuskanci wannan kalubalen daga matar tasa, dan haka ya ture ta daga gabansa yabar mata palourn.
Se magariba Su Jalila suka isa garin maiduguri, koda sukaje sun gaji sosai, musamman su Jalila, su da suka sha hidimar biki, basu huta ba akayo wannaan uwar tafiyar.
Gaba daya Jalila ji take jikinta kaman ba nata ba saboda gajiya, har suka je maiduguri kanta a kasa yake, se dai ta jimgina da jikin Nana, ko mota tayi bacci, in aka jima ta shige cikin mayafinta tayi kuka, har sukaje Jalila bata kula kowa ba seda taji an tsaya ance sufito.
Gidan da akayi parking din motar ne yayi awon gaba da tunanin ta, sekace ba a duniya ba, kallo daya zakayiwa gidan kasan mamallaka gidan sunyi hannun riga da talauci, ko da suka fito daga motar Se guďa akeyi, Jalal idonsa gaba daya yana kan Jalila da take a takure, Suka nufi cikin gidan, tun daga harabar gidan wani irin sassanyan kamshi ke tashi, har zuwa cikin gidan, cikin gidan da'a akwai mutane a gidan da sukazo domin karbar Amaren.
Cikin gidan ma kamshin da yake na musamman ne, fiye da na harabar gidan.
Aka basu ďaki, suka gabatar da sallolin da suke kansu, Sannan aka kawo musu Abinci, Jalila da Nana ne kawai a dakin dan haka Nana tace
"Jalila ki daure kici Abincin mana"
Girgiza kai Jalila tayi tace
"Na koshi, ke dai kici kawai, ni kaina kemin ciwo"
"to ko inyi musu magana a nemo miki magani?"
"A'a base kinyi hakan ba, A yanzu dai babu wani magani daze warkar min da wannan ciwon kan"
Suna cikin wannan mujadalar ne Anty ta shigo da tray din fruit a hannunta tace
"Jalila kuci Abincin mana, ga dangin baban Jalal can suna son ganinku kafin su tafi"
Nana tace
"Anty Jalila taki cin Abincin, wai kanta ke ciwo"
"Subhanallah har yanzu kan ke miki ciwo? To daure kici Abincin se a kira likita ya dubaki"
Da kyar Jalila ta cakali Abincin nan ta barshi.
Suka fito parlour inda dangin Daddy keson ganin Amare, se hausa suke suna hadawa da yarensu, sunga fuskar Nana yayinda Jalila ta dukunkune a mayafi taki bari su ganta, dare ya farayi sukayi musu nasiha da Addu'oi, tareda jadadda godiyarsu ga Jalila sannan suka watse a hankali.
Dakin da'aka bawa Su Jalila yana da kyau da matukar girma, suka koma suka canza kaya, Hajiya Salma da kanta ta kawowa Jalila magani ta sha, tana shan maganin ta nemi guri ta kwanta tayi lamoo akan gado, tana missing din wayarta, tun randa Jalal ya kwace be kuma bata ba, tana son tayi amfani da wayarta amma ya rike a gurinsa sekace shi ya saimata.
Nana na kwanciya Mahmud ya kirata a waya, Suka dinga hira suna soyewa, kaman ba gobe zasu tafi ba, suna ta soyayya gwanin sha'awa, Jalila ta tuna kowacce ta samu zabinta, ta auri wanda take so suna cikin farinciki amma banda ita, an haďa ta da wanda be damu da kansa ba ma balle wani, take taji wasu hawayen na zubo mata, ta tabatta Auren Jalal wani sabon shafi ne na kaddarar Rayuwarta.
Hanan kam gidanta yana da girma amma ba can ba, Amma ya tsaru anyi masa gini na zamani, dauke da wadataccen gini, an kashewa gidan kudi sosai, Sannan daddy ya zuba mata kaya yadda yakamata. Wanda sukayi wa Hanan rakiya suna zuwa a ranar suka juyo gida, suka barota tanata rikici, Seda kowa ya watse bayan sallar magariba sannan Jawwad ya shigo gidan, ya sameta tayi zaman dirshan a kasa ta jingina da gado, ta takure kanta sosai, tayi kuka harta gaji, dan girgiza kai yayi ya karaso gabanta ya tsuguna se kamshin turare yake, A hankali yace
"Haba Hanan, kukan ya isa haka, i know you miss home, Amma ba gani ba, sekace wadda akayiwa auren dole, ko kin dena sona ne?"
Girgiza masa kai tayi alamar A'a
"Yawwa my love 😍, kukan ya isa haka, yau ranar daza muyi farinciki ne, kar kanki yayi ciwo, ko nima kina so ki sani kukan ne?" ya fada yana goge mata hawayen fuskarta.
A hankali tace "A'a ni karkayi kuma nadena kukan" tai maganar cikin shagwaba
Murmushi yayi mata yace "Yawwa ai nasan baza kiso ki ganni ina kuka ba, shiyasa nima bana son ganin kukanki"
Haka ya cigaba da rarrashin ta har ta dan saki jiki tana hira, Jawwad da kansa yaje kitchen ya dakko plate da cups, ya bude musu kazar da ya shigo da ita, ya cika mata kofi da youghut me sanyi, yace "Bismillah"
Ta kalli kazar ta kalleshi tace "Ni na koshi"
"me kika ci da kika koshi?"
"bakomai" ta bashi amsa, ya lura gaba daya a firgice take, har hakan yaso ya bashi dariya amma ya maze ya ďan bata fuska yace
"in baki ci ba, zan kwana da yunwa ne, kuma ni inajin yunwa sosai, tunda aka fara biki bana samun cin Abinci fa, se Ulcer ta kamani ko?"
Yai maganar a ďan shagwabe, dariya ya bata tace
"in Ulcer ta kamaka ba rabin zamce ai, Dama haka ka iya shagwaba, wallahi tayi maka kyau"
tai maganar tana dariya, cikin hikima yanayi ya namata hira ya dinga bata kazar tana ci, seda suka kammala, Jawwad ya jagorance su sukayi Sallar nafila, domin nuna godiyarsu ga Allah da kuma fatan zaman lafiya me dorewa a cikin Rayuwar Aurensu.
Se Hamma take tana lumshe ido, da alamun gajiya da kuma bacci a tareda ita, Jawwad ya kalleta yace
"Wannan hammar da kike karki hadiyeni mana"
Tayi dariya ta Mike, tana cewa "gara in hadiyaka in huta ai"
fita Jawwad yayi domin rufe kofofin gidan, da kuma tabattar da komai lafiya.
Hanan ta canza kaya, ta nemi guri ta kwanta, wani nannauyan bacci yayi awon gaba da ita.
Cikin baccin nata ne tana kokarin yin juyi ta jita a jikin mutum, a hankali ta bude ido tace "Haidar"
"My love" ya amsa mata
"bakayi bacci ba?"
"Banyi ba"
"meyasa?"
"ina tunani ne"
"Nasan me kake tunani, be wuce su Jalila ba, ni na gaya maka komai ze wuce, zasu koma normal, Jalila tana son Jalal, kawai dai kasan ta da taurin kai"
A jiyar zuciya yayi, ya kuma kwantar da kansa a jikin ta yace "Naikaina na san Jalal yana sonta sosai, daga baya na yadda da maganar ki soyayyar 'yan uwatanka ne tsakanina da ita, hankalinta akan rayuwar Jalal take, a tunanin ta tausayinsa take ji, amma da haka sonshi yayi mata illa bata sani ba, kaman yadda ban fargaba naki son yakusa karasani"
Ya kai bakinsa kunnenta ya rada mata
"I Love you my Hanan"
Makalkale shi tayi tace "I love you too Haidar"
Daga nan hirar kuma ta canza salo zuwa wani abu na daban, tun Hanan tana daurewa tana biye masa, taji abun ya wuce tunanin ta, ta fara neman taimako, 'yan gidan su ba wanda be sha kira ba dama an hadu da uwar shagwaba, A wanna daren Jawwad ya saukewa Hanan wannan rawan kan nata.
(nima me rahoto naga abun yafi karfina dan haka na dawo da baya, na fito 😜😜😂😂😂)
Gaba daya Nana ta takurawa Jalila da waya, har sha biyun dare tana manne a waya seka ce wata mara aikinyi, haushi duk ya ishi Jalila tana ganin ta fiye zakewa, ji ta ke kaman suna karama ta takaicin da take ciki, ta ja bargo ta rufe har kanta dan ta dena jin abunda Nana take fada.
Washegari tunda safe Su Nana suka fara haramar tafiya.
Wayar Nana Jalila ta karba sukayi waya da Maama, har daki aka kawowa su Jalila breakfast, Nana kanta ba ta sake taci ba, saboda gaba daya ji take ba dadi, zata daga tabar kasarta ta haihuwa Aure kenan.
Karfe sha dayan safe su Nana suka gama shirinsu, suka shirya domin tafiya airport, nan ma seda aka sha daru Da Jalila saboda kuka, haka sukayi Sallama Nana da Mahmud suka tafi.
Hajiya Salma bata bisu ba ita seda ga baya zata koma.
Bayan tafiyar Nana Jalila dakin ta koma ta kwanta gaba daya ji take duniyar tayi mata fadi, ba abokin hira an kawota inda ba wanda ta sani. Ta lura nan gidan Antyn Jalal ne, tana da yara 'yan mata guda biyu, daya zata girmi Jalila, Husnah da Amal, Amma sam basa san mutane basa shiga harkar mutane, dan haka ko sannu bata hadasu da Jalila, sedai sukan gaishe ta.
Hajiya Salma ta shigo ta samu Jalila a kwance tace "Jalila har yanzu jikin ne?"
Jalila tace "A' a naji sauki kaina ne kawai be dena ciwon ba"
"ko dai likita za'a kira"
"A'a Anty naji sauki"
"to shikenan, Amma Jalila ki kwantar da hankalinki, ki cire duk wata damuwa a ranki, Kicigaba da raguwarki kaman yadda kike yi a da kinji"
Jinjina mata kai kawai Jalila tayi.
Koda Hajiya Salma ta fita dakin da Jalal yake taje, yana zaune yana kallon labarai a tashar CNN.
"Sannu Jalal kana nan kana kallo, kai ko tambaya matarka bakayi, ka sameta a sauki, dan haka baka damu da ita ba ko?"
"to me zance? Kokuma me zanyi? Nima ai bata nemana"
"Au hakama zakace ai shikenan, yaushe zaka koma?"
"gobe insha Allah"
"zakaje kano ne kokuwa?"
Jalal ya dan yamutsa fuska yace "daga nan gurin aiki zan koma, bazanje Mummy ta hargitsa min kai ba, lagos zan wuce"
"Shikenan Allah ya kaimu goben" Jalal yace "Ameen Amma, se yaushe Zaku bani ita mu koma kano"?
Hajiya Salma tace
"ita wa kenan?"
"Matata mana" ya bata amsa
Hajiya Salma tace "au ashe matarka ce, baka da kunya Jalal, se lokacin dana shirya yayi tukuna, ashe dai ka damu da ita"
Dan dage kafada yayi irin i don't care din nan.
Jalal idan ya tuna yadda Jalila ta ce bata sonsa a gaban kowa da kowa, yana tunanin wani irin zaman Aure zasuyi? Tsawon lokacin nan dama bata taba sonsa ba kenan? To meze sa ya cigaba da bibiyar ta tunda tace bata sonsa.
Bayan Hanan tayi sallar Asuba komawa tayi kan gado, wani wahalallen bacci ya kuma dauketa. Koda Jawwad ya dawo ya tarar ta koma bacci, ya hau kan gadon ya ďan tsira mata ido, baccin ta take hankali kwance, tuno darun da tayi jiya yayi, ya danyi murmushi ya janyo ta jikinsa ya kwanta shima baccin ya dauke shi.
Wajen karfe tara Jawwad ya tashi, Amma Hanan bata farka ba, ya je ya dafa musu tea ya fita, ya fita ba dadewa Hanan ta tashi daga baccin, taje tai brush tai wanka ta saka wata doguwar riga mara nauyi, ta fito parlour amma bata ga Jawwad ba, ta nemi guri ta zauna a kan kujera, befi mintuna goma da fitowarta ba se gashi ya dawo hannunsa dauke da kaya, yayi sallama ta juyo ta amsa suna hada ido ya kashe mata ido, hakan yasata sunkuyar da kai tana murmushi, ya karaso ya ajiye kayan yace
"good morning dear, kin tashi lafiya?"
"lafiya kalau, kaima ka tashi lafiya?" tai maganar tana kokarin kaucewa hada ido da shi
"lafiya kalau na tashi lafiya, How was your night?" ya kuma jefo mata tambayar.
Pillow ta dauka ta rufe fuska tana murmushi haka Jawwad ya cigaba tsokanarta yana bata kunya.
Ya dakko cups yana kokarin hada musu tea tace "Haidar waye ya dafa tea din nan?"
"ni na dafa" ya bata amsa
"Allah yasa dai baka bari yayi kanzo ba, dan na san baka iya girki ba"
Dariya ta bashi sosai
"Ai nafi ki iya girki in gaya miki, zaki kuma gani"
"to ai shikenan hada min yunwa nakeji"
"Ai wannan tea din nawane ni kadai, bazaki sha ba ke kazarki zaki warming a oven ki cinye"
Zare ido tayi tace
"gaskiya bazan ciba na koshi"
Jawwad yayi dariya yace
"se kin cinye ta kuwa"
"aikuwa bazan ci ba, tsaya in baka a baki" ta dinga bawa Jawwad Abinci a baka, yana bata haka sukayi breakfast cike da kulawa da kaunar juna.
Wunin ranar yau Jalila ji tayi duniyar ta kara mata fadi, ga har yanzu Bata kuma sa Jalal a idonta ba balle ta sa ran karbar wayarta.
Bangaren Jalila ma tunanin ta yaza'ayi tayi zaman Aure da Jalal be damu da kansa ba balle ita, tana ganin shima an cusa masa ita ne kawai baya sonta, banda haka kwanan su nawa da zuwa be nemeta ba ga rashin lafiya tanayi amma ko keyarsa bata gani ba balle tasa ran ze mata sannu.
Ko parlour bata fita tana ďaki, Hajiya Salma da Antyn Jalal suna monitoring din Jalal da Jalila domin ganin actions dinsu, Amma abun mamaki kowannensu yana nuna be damu da ďan uwansa ba, tunda sukazo kwana uku ba wanda ya nemi wani a cikinsu.
Antyn Jalal tana zaune suna hira a parlour su Husnah suna cin Abinci Jalal ya shigo, su Amal suka gaisheshi a ciki ya amsa, dan sun fidda ran ze amsa musu, suka cigaba da cin Abincin su.
Anty tace "Jalal ina zuwa haka?"
"Zan koma lagos ne"
Anty sukayi ido hudu da Hajiya Salma.
Hajiya Salma tace "to wannaan tafiya haka kaman wanda ake kora? Ka gayawa matarka yau zaka koma?"
Cikin ko in kula yace "in kun ganta ku gaya mata"
Anty tace "dan kaniyarka mu zamu gaya mata ka tafi, Anya Jalal ka shirya rike yarinyar nan?"
A ransa yace "ita zaku tambaya in ta shirya zaman Aure dani?"
Hajiya Salma tace "nima dai haka nagani, tunda muka taho bata da lafiya, Amma yaron na ko ta kanta bebi ba, balle in sa ran ya duba ta, ya mata sannu" da sauri yace "bata da lafiya kuma? Me yasa me ta?"
Hajiya Salma tace "ban sani ba" mikewa yayi ya kalli Husna yace
"ina ne dakinta"?
"tana upstairs kusa da ďakina" ta bashi amsa, be kuma bi takansu Anty ba ya haura saman.
Kai tsaye ya bude dakin ya shiga, ya sameta ta dukunkune a cikin bargo, a hankali ya karasa gaban gadon nata ya kai hannu ya janye bargon.
Wata sleeping dress a jikinta blue me matukar kyau, kanta babu dan kwali, dukda tayi parking din gashin nata amma gashin ya hargitse, bacci takeyi sosai, Amma tayi rama a baccin ma se ajiyar zuciya take.
Ya kura mata ido fatarta se sheki take, a hankali ta motsa ta mike hannyen ta wajen kirjinsa, hannayenta sun sha ado da jan lalle, hannunsa yasa a nataa ya rike yana kuma kallon fuskarta, bacci take amma tayi kyau sosai. Ya bata lokaci sosai yana kallon ta. A hankali ya saki hannunta
Ya dakko wata 'yar takarda a Aljihinsa da biro yayi rubutu ya ajiye mata akar kashin pillow dinta, ya mayar mata da hannun ta kan gado ya lullube ta ya fice.
Koda ya sakko bekuma ce musu uffan ba yayi waje abunsa.
Anty tace "kinga danki ko?"
Hajiya Salma tace "ai bari kawai, Jalal Akwai taurin kai, suna son juna amma taurin kai neke damun su, se nunawa suke kaman basu damu da juna ba, Allah shi yabarwa kansa sanin dalilin dayasa ya hadasu, Amma wannan zaman Auren nasu da kallo"
"hakane amma zamu cigaba da yi musu Addu'a, zasu dai daita, bari kiga sukoma gidansu da zama, bazaki sake jin kansu ba"
"hakane Allah ya tabattar da alkhairi, Amma bazata koma kano yanzu ba, sonake hankalin ta ya kwanta ta sake nustuwa, daga nan ma waccan jarababbiyar watakila ta sakko"
Anty tace "tab haba sister Salma, kin manta wacece khadija kenan, ai babu batun ta sakko yanzu, kawai dai mu tayasu da Addu'a" haka suka cigaba da hirarakin su.
Koda Jalila ta tashi ji tayi gaba daya dakin ya gauraye da kamshin Jalal, dan tabe baki tayi ta shiga toilet tayi wanka ta sa kaya, tazo tana kokarin gyara gadon tana cire bedsheet din taga takadda ta fado, ta dauka ta bude, wani tsararren handwriting tagani a jiki.
Am going back to lagos, get well soon
ABDUL JALAL se signing dinsa da date
Juya takaddar tayi ta jefar da ita a gurin tayi tsaki, "kwana nawa bani da lafiya, tunda aka daura auren ko ta kaina bebi ba, se yanzu ze wani rubuta min wata banzar takadda, ya tafi abunda yafi lagos ma ni be shafe ni ba, kuma maimakon ya ajiyemin wayata amma yakuma tafiya da ita sekace tasa.
Haka Jalila ta cigaba da mita, har ta gama gyaran gadon.
Parlour ta fito dan ta gaji da zaman dakin ga shi ba waya a hannunta balle ta debe mata kewa.
Anty na ganin Jalila tayi murmushi tace "Jalila kin fito? Ya jikin naki kuwa?"
"naji sauki Anty"
"to Allah yakara sauki, dazu Mijinki ya shiga dubaki ai"
Dan tabe baki Jalila tayi tai shiru.
Tundaga Ranar kullum cikin turara Jalila suke da samfurin turaruka daban2, a rana se ayiwa kayan sawa turare kusan sau hudu, banda wanda ake tuarar mata jikinta, hatta ruwan wankan Jalila akwai turaren da'ake zubawa, sabulun wankan ta ma na musamman ne aka hada mata, ga mayukan shafawa dana kai, nan da nan Jalila jikin Jalila yara canzawa, duk inda ta gifta kamshi take, duk rashin son kitson Jalila wani na tsufa me kitso take zuwa tayi mata wani, hakama lalle, gaba ďaya wannan gidan sun maida Amfani da turaruka kamar ibada, babu wani aiki da takeyi sedai taci ta kwanta, ko ta yunkura zatayi aiki se a hanata, ga kyan gyra da'ake bata dan haka har wani kiba tayi abunta tai kalau da ita. Jalila idan tana son yin waya sedai ta ari ta Anty tayi, ta mata magana akan wayarta tace tabari Jalal yazo.
Tunda Jalal yazo ko a waya be kuma neman inda Jalila take ba itama ba ta nemi jin inda yake ba.
Mummy ta cigaba da tayarwa da Daddy hankali akan maganar Auren Jalal, amma sam yaki saurararta, ya tattara ya koma Dubai, duk abun nan da ake Ilham bata sani ba.
Daddare Ilham na kwance tana chatting, ta shiga Twitter kamar wadda aka saka ta shiga profile din Jalal Alhamdilillah got married to Jalila Aliyu Imam shine abunda Ilham ta gani zumbur ta tashi Zaune tana kuma mutsukke ido, Amma still taga ba mafarki take ba.
Da sauri ta kira layin Nana, Amma bata shiga, se lokacin ta tuna ai Nana Mahmud ta aura, a England zasu zauna.
Fitowa tayi da sauri ta tafi ďakin Mummy tana kwala mata kira
"ke lafiya kuwa kike min wannan kiram, meya faru ne?"
Nunawa Mummy wayar tayi, mummy tace "me zan gani?"
"Mummy wai dagaske ne Jalal yayi Aure"
Ajiyar zuciya Mummy tayi tace "tun satin da Daddy yaje daurin auren Jawwad, ya hada baki da 'yan uwansa suka masa Aure, nayi2 ya gayamin wacece yaki"
Innalillahi wa inna ilaihi raji un, Mummy kin san wacece kuwa? Jalila ce fa, kalli Abunda ya rubuta ita ya aura Mummy, na shiga uku, Mummy ki kashe Auren nan kafin sun tare, Wallahi idan suka tare na kade, zan rasa komai, komai nawa ya rushe"
Gaba ďaya Mummy tsayawa tayi tana kallon Ilham
"dolene in kashe Auren nan, baze yuwu ba, wallahi ko yana so koba ya so sena kashe auren nan, ni Hajiya zainab zata munafunta, a hada kai da ita a Aurawa ďana wannan makirar yarinyar, in abun gaskiyane ta aurawa nata ďan mana, indai nina haifi Jalal seya saketa, a ďaura masa Aure ko ya nemi inda nake, rabona da shi wata biyar kenan, baze yuwu ba wallahi"
Share please
I want comments not stickers or just thanks
Daga alkalamin Aysher cool
🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️
What's app only 07063065680.
Follow me onWatpad @Ayshercool7724
🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹 🌹
*ABDUL JALAL*
_Story, writing and edited _
By
AISHA HUMAIRA
( _Daddy's girl_)
*PERFECT WRITER'S*
*ASSOCIATION*🌞
(𝕎𝔼 𝔸𝕀ℕ'𝕋 ℙ𝔼ℝ𝔽𝔼ℂ𝕋 𝔹𝕌𝕋 𝕎𝔼'ℝ𝔼 𝔸𝕃𝕎𝔸𝕐𝕊, 𝕋ℝ𝕐𝕀ℕ𝔾 𝕆𝕌ℝ 𝔹𝔼𝕊𝕋 𝕋𝕆 𝕄𝕆𝕋𝕀𝕍𝔸𝕋𝔼 𝔸ℕ𝔻 𝔼ℕ𝕋𝔼ℝ𝕋𝔸𝕀ℕ 𝕆𝕌ℝ ℝ𝔼𝔸𝔻𝔼ℝ𝕊💪)
/https://www.facebook.com/Perfect-writers-association-100452275039839/
*P.W.A*✍️
Bismillahirrahmanirrahim, da sunan Allah me rahama me jinkai, Allah yakara tsira da aminci ga shugabanmu Annabi muhammadu salallahu alaihi wassalam.
Bayan haka bazan gajiba da mika gaisuwata da godiya ga yan uwa da abokan arziki ba, bayan haka
Banyarda a juyamin littafi ba ko amfani da wani bangare ba tareda izinina ba.
Domin gyara, shawara ko sharhi, za a iya tuntubata akan what's app number dina
07063065680
Or email address @ [email protected]
Watpad @Ayshercool7724
_MY FIRST NOVEL _
Da Sauri Mummy ta sha gaban Daddy tace
"Wallahi Habib seka gayamin dan me zaka yiwa Jalal Aure ba tareda nasani ba? Sannan kuma 'yar ubanwa aka Aura masa? Wato kaje kun haďa kai da wannan munafukan' yan uwan naka aka Aurawa ďana yarinya ban sani ba, to wallahi baze yuwu ba, ďa dai nawane nina haifi abuna, dan haka ba'a isa a yanke masa hukunci game da rayuwarsa ba tareda sani na ba"
"sekuma kiyi, naga yadda zaki raba Auren ai, indai Jalal ne gaki nan gashi, dai dai yake dake, Akan kira bashi da yarinyar nan zaki kuma lalata alakarki da shine kawai, dan nagaya miki yana sonta"
"karyane Wallahi, Jalal bashi da wata yarinya da yake so, Yarinyar dana zaba masa ita ze Aura"
Dama daddy yasan ze fuskanci wannan kalubalen daga matar tasa, dan haka ya ture ta daga gabansa yabar mata palourn.
Se magariba Su Jalila suka isa garin maiduguri, koda sukaje sun gaji sosai, musamman su Jalila, su da suka sha hidimar biki, basu huta ba akayo wannaan uwar tafiyar.
Gaba daya Jalila ji take jikinta kaman ba nata ba saboda gajiya, har suka je maiduguri kanta a kasa yake, se dai ta jimgina da jikin Nana, ko mota tayi bacci, in aka jima ta shige cikin mayafinta tayi kuka, har sukaje Jalila bata kula kowa ba seda taji an tsaya ance sufito.
Gidan da akayi parking din motar ne yayi awon gaba da tunanin ta, sekace ba a duniya ba, kallo daya zakayiwa gidan kasan mamallaka gidan sunyi hannun riga da talauci, ko da suka fito daga motar Se guďa akeyi, Jalal idonsa gaba daya yana kan Jalila da take a takure, Suka nufi cikin gidan, tun daga harabar gidan wani irin sassanyan kamshi ke tashi, har zuwa cikin gidan, cikin gidan da'a akwai mutane a gidan da sukazo domin karbar Amaren.
Cikin gidan ma kamshin da yake na musamman ne, fiye da na harabar gidan.
Aka basu ďaki, suka gabatar da sallolin da suke kansu, Sannan aka kawo musu Abinci, Jalila da Nana ne kawai a dakin dan haka Nana tace
"Jalila ki daure kici Abincin mana"
Girgiza kai Jalila tayi tace
"Na koshi, ke dai kici kawai, ni kaina kemin ciwo"
"to ko inyi musu magana a nemo miki magani?"
"A'a base kinyi hakan ba, A yanzu dai babu wani magani daze warkar min da wannan ciwon kan"
Suna cikin wannan mujadalar ne Anty ta shigo da tray din fruit a hannunta tace
"Jalila kuci Abincin mana, ga dangin baban Jalal can suna son ganinku kafin su tafi"
Nana tace
"Anty Jalila taki cin Abincin, wai kanta ke ciwo"
"Subhanallah har yanzu kan ke miki ciwo? To daure kici Abincin se a kira likita ya dubaki"
Da kyar Jalila ta cakali Abincin nan ta barshi.
Suka fito parlour inda dangin Daddy keson ganin Amare, se hausa suke suna hadawa da yarensu, sunga fuskar Nana yayinda Jalila ta dukunkune a mayafi taki bari su ganta, dare ya farayi sukayi musu nasiha da Addu'oi, tareda jadadda godiyarsu ga Jalila sannan suka watse a hankali.
Dakin da'aka bawa Su Jalila yana da kyau da matukar girma, suka koma suka canza kaya, Hajiya Salma da kanta ta kawowa Jalila magani ta sha, tana shan maganin ta nemi guri ta kwanta tayi lamoo akan gado, tana missing din wayarta, tun randa Jalal ya kwace be kuma bata ba, tana son tayi amfani da wayarta amma ya rike a gurinsa sekace shi ya saimata.
Nana na kwanciya Mahmud ya kirata a waya, Suka dinga hira suna soyewa, kaman ba gobe zasu tafi ba, suna ta soyayya gwanin sha'awa, Jalila ta tuna kowacce ta samu zabinta, ta auri wanda take so suna cikin farinciki amma banda ita, an haďa ta da wanda be damu da kansa ba ma balle wani, take taji wasu hawayen na zubo mata, ta tabatta Auren Jalal wani sabon shafi ne na kaddarar Rayuwarta.
Hanan kam gidanta yana da girma amma ba can ba, Amma ya tsaru anyi masa gini na zamani, dauke da wadataccen gini, an kashewa gidan kudi sosai, Sannan daddy ya zuba mata kaya yadda yakamata. Wanda sukayi wa Hanan rakiya suna zuwa a ranar suka juyo gida, suka barota tanata rikici, Seda kowa ya watse bayan sallar magariba sannan Jawwad ya shigo gidan, ya sameta tayi zaman dirshan a kasa ta jingina da gado, ta takure kanta sosai, tayi kuka harta gaji, dan girgiza kai yayi ya karaso gabanta ya tsuguna se kamshin turare yake, A hankali yace
"Haba Hanan, kukan ya isa haka, i know you miss home, Amma ba gani ba, sekace wadda akayiwa auren dole, ko kin dena sona ne?"
Girgiza masa kai tayi alamar A'a
"Yawwa my love 😍, kukan ya isa haka, yau ranar daza muyi farinciki ne, kar kanki yayi ciwo, ko nima kina so ki sani kukan ne?" ya fada yana goge mata hawayen fuskarta.
A hankali tace "A'a ni karkayi kuma nadena kukan" tai maganar cikin shagwaba
Murmushi yayi mata yace "Yawwa ai nasan baza kiso ki ganni ina kuka ba, shiyasa nima bana son ganin kukanki"
Haka ya cigaba da rarrashin ta har ta dan saki jiki tana hira, Jawwad da kansa yaje kitchen ya dakko plate da cups, ya bude musu kazar da ya shigo da ita, ya cika mata kofi da youghut me sanyi, yace "Bismillah"
Ta kalli kazar ta kalleshi tace "Ni na koshi"
"me kika ci da kika koshi?"
"bakomai" ta bashi amsa, ya lura gaba daya a firgice take, har hakan yaso ya bashi dariya amma ya maze ya ďan bata fuska yace
"in baki ci ba, zan kwana da yunwa ne, kuma ni inajin yunwa sosai, tunda aka fara biki bana samun cin Abinci fa, se Ulcer ta kamani ko?"
Yai maganar a ďan shagwabe, dariya ya bata tace
"in Ulcer ta kamaka ba rabin zamce ai, Dama haka ka iya shagwaba, wallahi tayi maka kyau"
tai maganar tana dariya, cikin hikima yanayi ya namata hira ya dinga bata kazar tana ci, seda suka kammala, Jawwad ya jagorance su sukayi Sallar nafila, domin nuna godiyarsu ga Allah da kuma fatan zaman lafiya me dorewa a cikin Rayuwar Aurensu.
Se Hamma take tana lumshe ido, da alamun gajiya da kuma bacci a tareda ita, Jawwad ya kalleta yace
"Wannan hammar da kike karki hadiyeni mana"
Tayi dariya ta Mike, tana cewa "gara in hadiyaka in huta ai"
fita Jawwad yayi domin rufe kofofin gidan, da kuma tabattar da komai lafiya.
Hanan ta canza kaya, ta nemi guri ta kwanta, wani nannauyan bacci yayi awon gaba da ita.
Cikin baccin nata ne tana kokarin yin juyi ta jita a jikin mutum, a hankali ta bude ido tace "Haidar"
"My love" ya amsa mata
"bakayi bacci ba?"
"Banyi ba"
"meyasa?"
"ina tunani ne"
"Nasan me kake tunani, be wuce su Jalila ba, ni na gaya maka komai ze wuce, zasu koma normal, Jalila tana son Jalal, kawai dai kasan ta da taurin kai"
A jiyar zuciya yayi, ya kuma kwantar da kansa a jikin ta yace "Naikaina na san Jalal yana sonta sosai, daga baya na yadda da maganar ki soyayyar 'yan uwatanka ne tsakanina da ita, hankalinta akan rayuwar Jalal take, a tunanin ta tausayinsa take ji, amma da haka sonshi yayi mata illa bata sani ba, kaman yadda ban fargaba naki son yakusa karasani"
Ya kai bakinsa kunnenta ya rada mata
"I Love you my Hanan"
Makalkale shi tayi tace "I love you too Haidar"
Daga nan hirar kuma ta canza salo zuwa wani abu na daban, tun Hanan tana daurewa tana biye masa, taji abun ya wuce tunanin ta, ta fara neman taimako, 'yan gidan su ba wanda be sha kira ba dama an hadu da uwar shagwaba, A wanna daren Jawwad ya saukewa Hanan wannan rawan kan nata.
(nima me rahoto naga abun yafi karfina dan haka na dawo da baya, na fito 😜😜😂😂😂)
Gaba daya Nana ta takurawa Jalila da waya, har sha biyun dare tana manne a waya seka ce wata mara aikinyi, haushi duk ya ishi Jalila tana ganin ta fiye zakewa, ji ta ke kaman suna karama ta takaicin da take ciki, ta ja bargo ta rufe har kanta dan ta dena jin abunda Nana take fada.
Washegari tunda safe Su Nana suka fara haramar tafiya.
Wayar Nana Jalila ta karba sukayi waya da Maama, har daki aka kawowa su Jalila breakfast, Nana kanta ba ta sake taci ba, saboda gaba daya ji take ba dadi, zata daga tabar kasarta ta haihuwa Aure kenan.
Karfe sha dayan safe su Nana suka gama shirinsu, suka shirya domin tafiya airport, nan ma seda aka sha daru Da Jalila saboda kuka, haka sukayi Sallama Nana da Mahmud suka tafi.
Hajiya Salma bata bisu ba ita seda ga baya zata koma.
Bayan tafiyar Nana Jalila dakin ta koma ta kwanta gaba daya ji take duniyar tayi mata fadi, ba abokin hira an kawota inda ba wanda ta sani. Ta lura nan gidan Antyn Jalal ne, tana da yara 'yan mata guda biyu, daya zata girmi Jalila, Husnah da Amal, Amma sam basa san mutane basa shiga harkar mutane, dan haka ko sannu bata hadasu da Jalila, sedai sukan gaishe ta.
Hajiya Salma ta shigo ta samu Jalila a kwance tace "Jalila har yanzu jikin ne?"
Jalila tace "A' a naji sauki kaina ne kawai be dena ciwon ba"
"ko dai likita za'a kira"
"A'a Anty naji sauki"
"to shikenan, Amma Jalila ki kwantar da hankalinki, ki cire duk wata damuwa a ranki, Kicigaba da raguwarki kaman yadda kike yi a da kinji"
Jinjina mata kai kawai Jalila tayi.
Koda Hajiya Salma ta fita dakin da Jalal yake taje, yana zaune yana kallon labarai a tashar CNN.
"Sannu Jalal kana nan kana kallo, kai ko tambaya matarka bakayi, ka sameta a sauki, dan haka baka damu da ita ba ko?"
"to me zance? Kokuma me zanyi? Nima ai bata nemana"
"Au hakama zakace ai shikenan, yaushe zaka koma?"
"gobe insha Allah"
"zakaje kano ne kokuwa?"
Jalal ya dan yamutsa fuska yace "daga nan gurin aiki zan koma, bazanje Mummy ta hargitsa min kai ba, lagos zan wuce"
"Shikenan Allah ya kaimu goben" Jalal yace "Ameen Amma, se yaushe Zaku bani ita mu koma kano"?
Hajiya Salma tace
"ita wa kenan?"
"Matata mana" ya bata amsa
Hajiya Salma tace "au ashe matarka ce, baka da kunya Jalal, se lokacin dana shirya yayi tukuna, ashe dai ka damu da ita"
Dan dage kafada yayi irin i don't care din nan.
Jalal idan ya tuna yadda Jalila ta ce bata sonsa a gaban kowa da kowa, yana tunanin wani irin zaman Aure zasuyi? Tsawon lokacin nan dama bata taba sonsa ba kenan? To meze sa ya cigaba da bibiyar ta tunda tace bata sonsa.
Bayan Hanan tayi sallar Asuba komawa tayi kan gado, wani wahalallen bacci ya kuma dauketa. Koda Jawwad ya dawo ya tarar ta koma bacci, ya hau kan gadon ya ďan tsira mata ido, baccin ta take hankali kwance, tuno darun da tayi jiya yayi, ya danyi murmushi ya janyo ta jikinsa ya kwanta shima baccin ya dauke shi.
Wajen karfe tara Jawwad ya tashi, Amma Hanan bata farka ba, ya je ya dafa musu tea ya fita, ya fita ba dadewa Hanan ta tashi daga baccin, taje tai brush tai wanka ta saka wata doguwar riga mara nauyi, ta fito parlour amma bata ga Jawwad ba, ta nemi guri ta zauna a kan kujera, befi mintuna goma da fitowarta ba se gashi ya dawo hannunsa dauke da kaya, yayi sallama ta juyo ta amsa suna hada ido ya kashe mata ido, hakan yasata sunkuyar da kai tana murmushi, ya karaso ya ajiye kayan yace
"good morning dear, kin tashi lafiya?"
"lafiya kalau, kaima ka tashi lafiya?" tai maganar tana kokarin kaucewa hada ido da shi
"lafiya kalau na tashi lafiya, How was your night?" ya kuma jefo mata tambayar.
Pillow ta dauka ta rufe fuska tana murmushi haka Jawwad ya cigaba tsokanarta yana bata kunya.
Ya dakko cups yana kokarin hada musu tea tace "Haidar waye ya dafa tea din nan?"
"ni na dafa" ya bata amsa
"Allah yasa dai baka bari yayi kanzo ba, dan na san baka iya girki ba"
Dariya ta bashi sosai
"Ai nafi ki iya girki in gaya miki, zaki kuma gani"
"to ai shikenan hada min yunwa nakeji"
"Ai wannan tea din nawane ni kadai, bazaki sha ba ke kazarki zaki warming a oven ki cinye"
Zare ido tayi tace
"gaskiya bazan ciba na koshi"
Jawwad yayi dariya yace
"se kin cinye ta kuwa"
"aikuwa bazan ci ba, tsaya in baka a baki" ta dinga bawa Jawwad Abinci a baka, yana bata haka sukayi breakfast cike da kulawa da kaunar juna.
Wunin ranar yau Jalila ji tayi duniyar ta kara mata fadi, ga har yanzu Bata kuma sa Jalal a idonta ba balle ta sa ran karbar wayarta.
Bangaren Jalila ma tunanin ta yaza'ayi tayi zaman Aure da Jalal be damu da kansa ba balle ita, tana ganin shima an cusa masa ita ne kawai baya sonta, banda haka kwanan su nawa da zuwa be nemeta ba ga rashin lafiya tanayi amma ko keyarsa bata gani ba balle tasa ran ze mata sannu.
Ko parlour bata fita tana ďaki, Hajiya Salma da Antyn Jalal suna monitoring din Jalal da Jalila domin ganin actions dinsu, Amma abun mamaki kowannensu yana nuna be damu da ďan uwansa ba, tunda sukazo kwana uku ba wanda ya nemi wani a cikinsu.
Antyn Jalal tana zaune suna hira a parlour su Husnah suna cin Abinci Jalal ya shigo, su Amal suka gaisheshi a ciki ya amsa, dan sun fidda ran ze amsa musu, suka cigaba da cin Abincin su.
Anty tace "Jalal ina zuwa haka?"
"Zan koma lagos ne"
Anty sukayi ido hudu da Hajiya Salma.
Hajiya Salma tace "to wannaan tafiya haka kaman wanda ake kora? Ka gayawa matarka yau zaka koma?"
Cikin ko in kula yace "in kun ganta ku gaya mata"
Anty tace "dan kaniyarka mu zamu gaya mata ka tafi, Anya Jalal ka shirya rike yarinyar nan?"
A ransa yace "ita zaku tambaya in ta shirya zaman Aure dani?"
Hajiya Salma tace "nima dai haka nagani, tunda muka taho bata da lafiya, Amma yaron na ko ta kanta bebi ba, balle in sa ran ya duba ta, ya mata sannu" da sauri yace "bata da lafiya kuma? Me yasa me ta?"
Hajiya Salma tace "ban sani ba" mikewa yayi ya kalli Husna yace
"ina ne dakinta"?
"tana upstairs kusa da ďakina" ta bashi amsa, be kuma bi takansu Anty ba ya haura saman.
Kai tsaye ya bude dakin ya shiga, ya sameta ta dukunkune a cikin bargo, a hankali ya karasa gaban gadon nata ya kai hannu ya janye bargon.
Wata sleeping dress a jikinta blue me matukar kyau, kanta babu dan kwali, dukda tayi parking din gashin nata amma gashin ya hargitse, bacci takeyi sosai, Amma tayi rama a baccin ma se ajiyar zuciya take.
Ya kura mata ido fatarta se sheki take, a hankali ta motsa ta mike hannyen ta wajen kirjinsa, hannayenta sun sha ado da jan lalle, hannunsa yasa a nataa ya rike yana kuma kallon fuskarta, bacci take amma tayi kyau sosai. Ya bata lokaci sosai yana kallon ta. A hankali ya saki hannunta
Ya dakko wata 'yar takarda a Aljihinsa da biro yayi rubutu ya ajiye mata akar kashin pillow dinta, ya mayar mata da hannun ta kan gado ya lullube ta ya fice.
Koda ya sakko bekuma ce musu uffan ba yayi waje abunsa.
Anty tace "kinga danki ko?"
Hajiya Salma tace "ai bari kawai, Jalal Akwai taurin kai, suna son juna amma taurin kai neke damun su, se nunawa suke kaman basu damu da juna ba, Allah shi yabarwa kansa sanin dalilin dayasa ya hadasu, Amma wannan zaman Auren nasu da kallo"
"hakane amma zamu cigaba da yi musu Addu'a, zasu dai daita, bari kiga sukoma gidansu da zama, bazaki sake jin kansu ba"
"hakane Allah ya tabattar da alkhairi, Amma bazata koma kano yanzu ba, sonake hankalin ta ya kwanta ta sake nustuwa, daga nan ma waccan jarababbiyar watakila ta sakko"
Anty tace "tab haba sister Salma, kin manta wacece khadija kenan, ai babu batun ta sakko yanzu, kawai dai mu tayasu da Addu'a" haka suka cigaba da hirarakin su.
Koda Jalila ta tashi ji tayi gaba daya dakin ya gauraye da kamshin Jalal, dan tabe baki tayi ta shiga toilet tayi wanka ta sa kaya, tazo tana kokarin gyara gadon tana cire bedsheet din taga takadda ta fado, ta dauka ta bude, wani tsararren handwriting tagani a jiki.
Am going back to lagos, get well soon
ABDUL JALAL se signing dinsa da date
Juya takaddar tayi ta jefar da ita a gurin tayi tsaki, "kwana nawa bani da lafiya, tunda aka daura auren ko ta kaina bebi ba, se yanzu ze wani rubuta min wata banzar takadda, ya tafi abunda yafi lagos ma ni be shafe ni ba, kuma maimakon ya ajiyemin wayata amma yakuma tafiya da ita sekace tasa.
Haka Jalila ta cigaba da mita, har ta gama gyaran gadon.
Parlour ta fito dan ta gaji da zaman dakin ga shi ba waya a hannunta balle ta debe mata kewa.
Anty na ganin Jalila tayi murmushi tace "Jalila kin fito? Ya jikin naki kuwa?"
"naji sauki Anty"
"to Allah yakara sauki, dazu Mijinki ya shiga dubaki ai"
Dan tabe baki Jalila tayi tai shiru.
Tundaga Ranar kullum cikin turara Jalila suke da samfurin turaruka daban2, a rana se ayiwa kayan sawa turare kusan sau hudu, banda wanda ake tuarar mata jikinta, hatta ruwan wankan Jalila akwai turaren da'ake zubawa, sabulun wankan ta ma na musamman ne aka hada mata, ga mayukan shafawa dana kai, nan da nan Jalila jikin Jalila yara canzawa, duk inda ta gifta kamshi take, duk rashin son kitson Jalila wani na tsufa me kitso take zuwa tayi mata wani, hakama lalle, gaba ďaya wannan gidan sun maida Amfani da turaruka kamar ibada, babu wani aiki da takeyi sedai taci ta kwanta, ko ta yunkura zatayi aiki se a hanata, ga kyan gyra da'ake bata dan haka har wani kiba tayi abunta tai kalau da ita. Jalila idan tana son yin waya sedai ta ari ta Anty tayi, ta mata magana akan wayarta tace tabari Jalal yazo.
Tunda Jalal yazo ko a waya be kuma neman inda Jalila take ba itama ba ta nemi jin inda yake ba.
Mummy ta cigaba da tayarwa da Daddy hankali akan maganar Auren Jalal, amma sam yaki saurararta, ya tattara ya koma Dubai, duk abun nan da ake Ilham bata sani ba.
Daddare Ilham na kwance tana chatting, ta shiga Twitter kamar wadda aka saka ta shiga profile din Jalal Alhamdilillah got married to Jalila Aliyu Imam shine abunda Ilham ta gani zumbur ta tashi Zaune tana kuma mutsukke ido, Amma still taga ba mafarki take ba.
Da sauri ta kira layin Nana, Amma bata shiga, se lokacin ta tuna ai Nana Mahmud ta aura, a England zasu zauna.
Fitowa tayi da sauri ta tafi ďakin Mummy tana kwala mata kira
"ke lafiya kuwa kike min wannan kiram, meya faru ne?"
Nunawa Mummy wayar tayi, mummy tace "me zan gani?"
"Mummy wai dagaske ne Jalal yayi Aure"
Ajiyar zuciya Mummy tayi tace "tun satin da Daddy yaje daurin auren Jawwad, ya hada baki da 'yan uwansa suka masa Aure, nayi2 ya gayamin wacece yaki"
Innalillahi wa inna ilaihi raji un, Mummy kin san wacece kuwa? Jalila ce fa, kalli Abunda ya rubuta ita ya aura Mummy, na shiga uku, Mummy ki kashe Auren nan kafin sun tare, Wallahi idan suka tare na kade, zan rasa komai, komai nawa ya rushe"
Gaba ďaya Mummy tsayawa tayi tana kallon Ilham
"dolene in kashe Auren nan, baze yuwu ba, wallahi ko yana so koba ya so sena kashe auren nan, ni Hajiya zainab zata munafunta, a hada kai da ita a Aurawa ďana wannan makirar yarinyar, in abun gaskiyane ta aurawa nata ďan mana, indai nina haifi Jalal seya saketa, a ďaura masa Aure ko ya nemi inda nake, rabona da shi wata biyar kenan, baze yuwu ba wallahi"
Share please
I want comments not stickers or just thanks
Daga alkalamin Aysher cool
🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️
What's app only 07063065680.
Follow me onWatpad @Ayshercool7724
🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹 🌹
*ABDUL JALAL*
_Story, writing and edited _
By
AISHA HUMAIRA
( _Daddy's girl_)
*PERFECT WRITER'S*
*ASSOCIATION*🌞
(𝕎𝔼 𝔸𝕀ℕ'𝕋 ℙ𝔼ℝ𝔽𝔼ℂ𝕋 𝔹𝕌𝕋 𝕎𝔼'ℝ𝔼 𝔸𝕃𝕎𝔸𝕐𝕊, 𝕋ℝ𝕐𝕀ℕ𝔾 𝕆𝕌ℝ 𝔹𝔼𝕊𝕋 𝕋𝕆 𝕄𝕆𝕋𝕀𝕍𝔸𝕋𝔼 𝔸ℕ𝔻 𝔼ℕ𝕋𝔼ℝ𝕋𝔸𝕀ℕ 𝕆𝕌ℝ ℝ𝔼𝔸𝔻𝔼ℝ𝕊💪)
/https://www.facebook.com/Perfect-writers-association-100452275039839/
*P.W.A*✍️