← Book details Abdul Jalal Part 2 Complete Hausa Novel Local reading mode
CHAPTER 18 OF 61

   PART 2        

Abdul Jalal Part 2 Complete Hausa Novel · about 13 min read

                          _PAGE  1️⃣8️⃣71

Bismillahirrahmanirrahim, da sunan Allah me rahama me jinkai, Allah yakara tsira da aminci ga shugabanmu Annabi muhammadu salallahu alaihi wassalam.
Bayan haka bazan gajiba da mika gaisuwata da godiya ga yan uwa da abokan arziki ba, bayan haka
Banyarda a juyamin littafi ba ko amfani da wani bangare ba tareda izinina ba.
Domin gyara, shawara ko sharhi, za a iya tuntubata akan what's app number dina
07063065680
Or email address @ [email protected]

     
        _MY FIRST NOVEL_

Haka khadija tacigaba da wasa da hankalin Saudat ba tareda ita Saudat din tasan me khadija take shiryawa ba.
Khadija ta karbi kudade dayawa agurin Kabir da sauran kudaden data damfara a gurin samarinta tafara business na atamfofi da kayan sawa, gurin manyan masu kudi, saboda tace in Allah yasa lokacin bikinta kece raini zatayi bazata barima azo ayi wani abu  a wannan gidan nasuba, biki za'ayi kaman na diyar sarakuna, dan jikinta yana bata zatayi galaba akan Habib saboda alamun sun nuna yanada saukin kai da tausayi.

Ranar da habib yadawo Nigeria me gadinsa yakira khadija a waya yasanar mata, taimasa godiya take ta turamasa katin 5k saboda albishir din dayayi mata, shi habib har yamanta da batun me turomasa messages, se bayan kwana biyu yamaida layinsa na Nigeria messages din khadija yafara cin karodasu ba adadi, tsaki yayi ya aje wayar yashiga sabgoginsa, kwanan sa uku da dawowa yakoma gurin aikinsa, yana zaune a office aka kirashi a waya, bakuwar lamba ne dan haka beyi tunanin komai ba ya daga wayar, tana sallama ya gane wacece, amma yarasa meyasa duk lokacin dazata kirashi baya iyayimata rashin mutunci. Yana cikin wannan tunanin yaji muryarta tana cewa "Rayuwata, barka da dawowa kasa Nigeria, ina maka barka da zuwa nayi kewarka matuka, nayi rashin lafiya sosai bayan tafiyarka, ina fatan kundawo lafiya" Abun mamaki taji yace "ya jikin naki?" seda tayi murmushi ta wani lumshe ido "Jiki ina samun sauki Alhamdilillah"
"me yake damunki?" takuma kashe murya "hayatee komaima yana damuna, nikaina narasa meke damuna, amma jigon rashin lafiyata soyayya ce, at least zansamu relief tunda ka dawo, bari in barka ka huta, I love you hayatee" ta kashe wayarta, tunda habib ya dawo Nigeria tafara shawo kansa saboda koyace katta kara kiransa bata fushi, kullum cikin nuna masa soyayya take, ta lura ya dan damu akan maganar rashin lafiyarta, hakan yasa tafara ji ajikinta burinta yana daf da cika. Tacigaba da kokari tana dauke hankalin Saudat daga kokarin zuwa gidan habib.
Seda khadija ta lura habib yafara bata kulawa, seta dena tura masa message ta kashe wayar da take kiransa da ita domin ta tabattar da ko yafara sonta, haka ta danne zuciyarta tsawon sati biyu bata kirashi ba kuma bata turamasa message ba.
Ranar da sati biyu ta cika khadija ta kunna wayarta, messages ne suka shigo wayarta, data bude duk na habib ne sekuma kamfanin layi, dayake shikadai take kira da layin, duk messages din yana tambayarta ina tashigane layinta baya shiga Allah yasa lafiya, bata san lokacin datayi wani tsalle ba tayi ihu a daki, mamanta ta shigo dakin da sauri "ke lafiya meyasameki?"
"bakomai mama bansan nayibane"
"to Allah ya shiryeki auta" mama ta fice khadija ta mike tsaye hada rawa a cikin daki. Bayan sallar magariba kabir ya tura yaro yace yayi masa sallama da khadija, tace yaron yace tana zuwa, ta shirya zata fita gurin kabir sega kiran Habib. Nan da nan ta tashi ta kulle kofa tazo tanemi guri ta zauna akan gado ta daga wayar cikin sanyin murya tai masa sallama, kafin ya amsa sallamar yace "ina kikashiga haka tsayin wannan lokacin?"
"hayatee bani da lafiya ne fa"
Cikin sauri yace "subhanallah jikinne har yanzu? Yanzu kina inane?"
"ina gida naji sauki"
"dagaske kinji sauki kokuma wasa kike?"
"Am serious, yau naci Abinci sosai nayi wanka nayi kwalliya, i wish kaga kwalliya nan hayatee" murmushi yayi yace "dagaske?" "Eh mana nayi kyau sosai, sedai ciwon so duk ya ramar dani"
"yaushe zan ganki?"
"Duk sanda kakeso, a shiryenake"
"kiyi fixing time, seki gayamin zanzo mugaisa"
"masha Allah, hayateee harnaji na warke gaba daya"
"to Allah yakara afuwa, bari zan shiga gida" cikin sauri cikin shagwaba khadija tace "haba hayatee ni wallahi bangaji dajin muryarka ba, kalli tsayin lokacin daka dauka bana jin muryarka fa" haka khadija ta dinga hilartasa suka shantake suna waya, tana masa hira me dadi har gurin goma da rabi na dare sannan sukayi sallama, Kabir yagaji da jira gashi lokacin sanyi amma khadija taki fitowa maganar duniya tayi banza taki bude kofa tacigaba da wayarta, daga baya tace ace masa yacigaba da jira inyaga ze iya tana da abunyi me mahimmanci datakeyi.
Seda ta gama wayarta tace ace masa ya tafi bazatazoba. Saudat ta shigo dakinta tace "khadija wai dan Allah wani zazzafan kika samune haka kusan awa uku kina waya, naga duk saurayin dakikayi bakya yiwa Kabir wulakanci amma yau kin shuka masa dayawa fa" khadija tayi wani shu'umin murmushi tace "ai ke bar gara kawai, najefa fatsata a ruwa kuma da alamu nakamo kifi me nauyin gaske, ba kama kifinne matsalar ba, sedai zanyi gwagwarmaya kafin kifin yazama mallakina saboda akwai masu farautar wannna kifin dayawa abakin ruwan" ta kuma kallon Saudat tace "kodayake kince ranar biyan bukata rai ba abakin komai yakeba yar uwa, dan haka zan jure gwagwarmaya da kubale in mallaki kifin nan"
Saudat tace "kinga ni kiyimin hausar dazan gane, se wani kwana2 kikemin, nibangane mekike nufi ba"
"karki damu zaki gane very soon yar uwa"
Bangaren habib kuwa, Salma ta damu matuka baya kaiwa tsawon wannan lokacin a waje, amma yau ya kai, tayi2 yagayamata dalili yace bakomai wani abune ya rikeshi haka ta hakura.
Wasa2 taga ya maida hakan dabi'arsa baya shigowa gida se bayan goma, dataga bashida niyyar denawa itama ta watsar dashi tacigaba da sha'aninta, seta ajiye masa abincin sa akan dining tayi kwanciyar ta, hakan yakara bashi damar sakewa suyi waya da khadija.
Ranar juma'a da yamma suka shirya zasu hadu a wani gurin shakatawa, saboda khadija bataso yazo da rana gidansu Saudat ta ganshi, yarigata zuwa gurin yana zaune yanata duba agogo har yafara fidda ran kozatazo, yana kokarin kiran layinta ne, yaji kamshi me dadi yacika masa hanci, dukda yajuya baya, amma tana kallonsa tabaya tasan shine, a hankali ta tako tazo bayan kujerar dayake ta tsaya, ta durkuso da kanta a hankali tace "Hayateee barka da zuwa" ya dago kai ya kalleta daga sama har kasa, doguwar mace ce, sannan tana da dan kiba kadan, baza akirata da fara tas ba amma tanada hasken fata sosai, tabbas khadija tana da kyau dai dai2 gwargwado, murmushi yayi mata "sannu da zuwa masoyiyar boye" murmushi tayi ta zagaya ta zauna akan kujerar datake facing dinsa, suka gaisa sun sha hira sosai sannan ya dauketa ya kaita har bakin layinsu shikuma ya tafi.
Khadija tayi nasara samun zuciyar habib tana nunamasa soyayya iyayinta, haka habib yasake da khadija suke soyayya ba tareda Salma tasani ba, yakanzo gurin khadija tadi, Saudat ta fusakanci yan kwanakin nan khadija tana cikin farinciki. Bayan sun gama cin Abinci khadija ta tafi daki ta shafe kusan awa uku tana waya, a iya sanin Saudat datayiwa khadija tasan bata son doguwar waya, amma ya akayi kwanan nan take waya haka, mikewa tayi tabi khadija daki, taje ta tarar da ita tanata zuba shagwaba a waya, tana ganin Saudat ta shigo dakin tai maza tayiwa habib sallama ta mike zaune
"Saudat lafiya kuwa na ganki haka ba zato babu tsammani"
"hmm dole kice haka mana almost 3hrs kina waya, ba'a kojin mekike fada, shikam wani me nasarar ne haka? Kodai kin hadu da dream hubbyn nakine" wani kasaitaccen murmushi khadija tayi "kwarai kuwa kedai kiyitamin Addu'a"
"shine babu ko Labari balle a gabatarmin dashi"
'mekikeci na baka na zuba, shida zezama sirinkinku sekin gaji da ganinsa "Saudat tace" Allah sarki Kabir yanata tsuma ze aureki "
Tsaki khadija tayi
" ke dalla kidenamin zancen wannan wawan, nifa badan ina tausayinsa ba da tuni na dade masa wulakanci, kodayake wulakanci na nawa, bashida zuciya ne"
"Mhmmm nikam nace khadija waime ake ciki game danawa damuwar ne, wallahi khadija ko baccin kirki bana iyayi" Ajiyar zuciya khadija tayi tace
"gaskiya Saudat ina tausaya miki, abun nada matukar tausayi, nikaina na kagu inga kinshiga wannan daula amma semunbi komai a sannu, bakisan iya kokarin danakeyi miki ba, yanzu haka nabada cigiyar in yadawo a sanar dani, naje har layin gidansa dakaina, amma ance an hana shiga layin ba tareda wanda zakaje gurinsa yasaniba, amma inata miki kokari "
" to khadija Allah yasa adace"
"zama adace kakri damu Saudat".

Duk ranar da Habib zezo gurin khadija tadi sedai su hadu a gidan kanin mahaifiyarta acan suke zancen, soyayya ce me karfi tashiga tsakanunsu, duk kasar dayatafi A gaggauce yake ya dawo domin ya hadu da ita, baya jure dogon lokaci basu hadu ba.
Habib da kansa yacewa khadija ze turo iyayensa ayi maganar aure, amma zeje maiduguri tukuna in yadawo seya turo, tayi murna ranar kamar ta zauce bata taba zaton a abubuwa zasu mata da sauki haka ba.
Gefe guda habib yanata tunanin, yadsa ze sanarwa da Salma batun auren dayakeso yayi, dan yasanta da matukar kishi, dan haka ya yanke shawarar zefara zuwa maiduguri in magana tayi nisa yagayawa Salma.
Koda Habib yajewa mahifiyarsa da zancem Aure bata bashi goyon bayaba hasalima faada takama yimasa "haba habib, yaushe kayi auren fari da har zakace zaka kara aure, yarinyar nan yar uwarkace fa, mahifinka da mahifiyarta uwa daya uba daya, hakan ze iya shafar zumuncinku, gaskiya ka hakura kozakayi aure ba yanzu ba" yakada yaraya amma mahaifiyarsa taki yarda, Habib tunda yake betaba yiwa mahaifiyarsa musuba se wannan karon, yaita mata magiya, karshe seda yaje yagayawa yayanta yazo yasa baki, badan tasoba haka ta amince, amma tace kafin aje neman auren se anyi bincike, akayi bincike amma bincike ya nuna khadija ba mutuniyar kirki bace, batada aibu, sedai rashin kunyarta da iya fitsara, yan uwan mahifin habib suka gayawa mahaifiyarsa nan ma ta dage tace baze yuwi ayi auren nan ba.
Khadija yagayawa khadija halin da akeciki ta damu sosai nan ta shiga addu'a ba dare ba rana, ta sanarda mahifiyarta komai sukacigaba da addu'a habib yanakin baze iya rabuwa da itaba dan haka yacigaba da lallaba mahaifiyarsa.
Habib ya canza gida, yakoma wani dankareren gida daya Gina a gadon kaya, gidane na alfarma matuka, anan ya tsara inya auri khadija ze hadasu da Salma. Bayan khadija ta tabattar da Habib ya tashi daga gidansa, taje ta samu dansandan dayake gadin rukunin quaters din dasu Habib suka tashi, tabashi kudi, ta shiryamasa abunda takeso yayi mata, sannan ta dauki Saudat sukaje tsohuwar unguwarsu Habib da nufin suje sugani yadda zasuyi kozasu samu Habib, suna zuwa dansanda dayake gadin rukunin quaters din yace musu "wakuke nemane?" khadija tace "gidan Habib kamal mukazo"
Nan yagaya musu "Ai yabar quaters din nan, tunda yadawo daga Dubai bezoba"
Da sauri Saudat tace "ina suka koma?"
"kamarya ina sukakoma dokace, da sun yadda daku dakunsan inda suka koma dan haka kubar nan gurin" khadija tai kokarin yagaya musu amma yai musu korar kare tare da barazanar ze kullesu, khadija ta kashe masa ido alamar aikinsa yayi kyau.
Habib yasha wahala sosai sannan mahaifiyarsa ta amince da maganar Aurensa da khadija, dangin mahifinsa ciki harda mahifin Salma, sukazo nema masa auren khadija gurin wan mahaifinta, sannan mahifin Salma yajawa mahifiyarta kunne kan be yadda wani yagayawa Salma Habib zekara Aure ba shida kansa ze gaya mata, dangin mahifin Habib suka kai kudin Auren Habib akasaka wata shida.
Khadija jitake kaman ba itaba, habib yagaya mata ansaka wata shida ji take yamata nisa wata shidan nan, se murna take ta tafi dakinsu Saudat cikin zumudi tana kiran sunan Saudat, tana zuwa ta tarar da Saudat tana kuka, da sauri ta karasa inda take tadafata "Saudat meyasameki haka?" Saudat ta share hawayenta ta girgigiza kai tace "bakomai khadija"
"A'a da komai gayamin menene?" Saudat ta dan gyara zama tace "khadija har yanzu burina becikaba, gashi ke zakiyi aurenki amma ni se gararamba nake, ba wani tsayayye wanda nake hangen yakasa samuwa, yanzu zakiyi aurenki ki barni" khadija ta riko hanun Saudat sannaan tace "Saudat dan adam be isa yasamu abunda ba rabonsa ba, indai habib rabonkime sekin aureshi, inba rabonkibane ba ba yadda zakiyi, shawarata agareki shine karki tsaya jiran Habib, ki bata lokacin ki, tun wuri kinemawa kanki mafita"
"khadija kina nufin in hakura gaskiya bazan iyaba kome zefaru, kedai kiyi aurenki ni zancigaba da fafatukata, sena auri Habib wallahi" murmushi khadija tayi "to shikenan Allah yabawa me rabo sa'a" daga nan ta tashi ta fice.
Habib da kansa ya shirya ya dauki Salma suka je maiduguri, yakaita gidansu da nufin tayi musu yan kwanaki, mahaifin salma yasa aka kiramasa ita dakinsa, ya zaunar da ita yayi mata nasiha sosai sannan ya sanarmata Habib ze kara Aure, ji tayi kaman mahifinnata ya watsa mata wuta, take idonta yayi jawur ta kalleshi "Aabba kan nufin Habib dinane zeyimin kishiya, kuma kake gayamin innalillahi wa inna ilaihi raji un, dan Allah Abba kacemin da wasa kake, wallahi bazan iyazamabda wata a matsayin kishiyata ba"
"Ke meye hakane? Akanki aka fara, to ki nutsu, akanme mijinki yanada halin daze auri mata hudu ya kuma iya rike su danme zakice baze aure ba, karki kuskura inji kin daga masa hankali shiyasa nace nizan gaya miki da kaina, dan haka kiyi hakuri, daba a aure dakema baze aureki ba, yakamata kija girmanki tunda kece uwargida, dan haka kiyi hakuri tashi kije Allah yayi miki Albarka " da kyar ta mike tsaye tana tafe tana hada hanya ta tafi dakin mahaifiyarsu, tana zuwa ta zube a jikin mamansu takama kuka
" mama dama habib ze iya yimin kishiya, ko shekara biyu bamuyi da aure ba shine ze auri wata, mama anyimin adalci kenan" ajiyar zuciya mama tayi tana dan dukan bayan Salma alamun rarrashi
"kiyi hakuri Salma kinji, kuma bazamu kira abunda habib yayi da rashin kyautatawa ba tunda shima danmune, ni macece salma masan meye kishi abune me ciwo amma kiyi hakuri zakiga ribar hakurin, kiyi masa fatan alkhairi sannan karki nuna masa kin damu"
"A'a Mama bazan iyaba, wallahi zuciyata zata fashe, mama bakisan menakeji ba, bantaba mafarkin Habib zemun kishiya ba, in hakanema yabari sena kwana biyu a gidansa mana, amma yaushe mukayi auren zemun haka, toni na hakura da aurennasa yaje ya zauna da wadda yakeso" nan mama taita rarrashinta tana nunamata illar cewa zata kashe aurenta. Kwanan salma biyu a gida sannan habib yazo daukar ta, iyayen salma sam basu canza masa ba, sedai Salma fuskarta sam babu walwala zakayi zaton jinya takeyi, harsukazo kano batace masa uffan ba.
Bayan sunkoma gidama ta tattara tayi watsi dashi, bata cin Abinci sosai kullum cikin kuka take abun yafara damun habib sosai dan haka yaje ya sameta a dakinta yanzuma idonta jawur da alama tasha kuka sosai. A hankali ya karasa ya zauna kusa da ita yayi kokarin janyo ta jikinsa amma ta kwace, ya kalleta "habibty dan Allah kiyi hakuri, bazanyi Auren nan dan in wulakanta kiba, matsayinki yana nan a zuciyata kaman yadda kika sani, dan Allah badanniba kidena azabtarmin da kanki, kidinga cin Abinci kin rame sosai kindena bani kulawar da duk kike bani, please my Salma calm down" kuka takuma saki me ban tausayi, ya rungumeta ya dinga mata nasiha yana rarrashinta a irin kishi na salma be taba tunanin ze iya rarrashinta ta hakura ba, kusan kullum se iyayenta sun kirata a waya anmata nasiha da addu'oi hakan yasa tasamu raguwar radadin da take ji a zuciyarta.
Biki nata karatowa anata shirye2 amma har yanzu yan gidansu khadija basu taba ganin Habib ba, sunyi mitar sunyi harsun gaji amma taki yadda aganshi, yayyenta sunyi fada sosai dasukaji cewar ba Kabir ne yakawo kudin auren khadija ba, amma aka barshi yana wahala, amma mahaifiyarta ta goyamata baya, hatta yan anguwa bakowa yasan khadija zatayi aure ba saboda tace ba kowane garane zezo mata gurin biki ba, mussaman ma yan unguwarsu yan bakin ciki, Habib yana sakarwa khadija kudi yadda yakamata anata shirin biki. Babban abun mamakin yadda haryanzu kabir besan khadija zatayi Aure ba yana zuwa gurinta tadi, kuma yanabata abu takarba, yauma suna tsaye tagama hira da Kabir wani makocinsu yagansu, sungama tadi ya dakko uwar leda cike da kaya yabata, nan ya jinjina kai lallai wannan yarinyar tacika yar banza, aikuwa sena gayawa yaron nan, kokuma inje har gida ina sanarwa da uwarsa dan watakila idan nagaya masa wannan makirar yarinyar tace karya nake babarsa zanje ingayawa

Tirkashi

Share please
I want comments not stickers or just thanks
Daga alkalamin Aysher cool
🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️
What's app only 07063065680
🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹

              _ABDUL JALAL (2020)_

       _Story and written by_
      AISHA HUMAIRA (daddy's girl)
        
Chapter 18 · 0% Book details