← Book details Abdul Jalal Part 2 Complete Hausa Novel Local reading mode
CHAPTER 51 OF 61

            PART 2        

Abdul Jalal Part 2 Complete Hausa Novel · about 16 min read

                          _PAGE 5️⃣2️⃣ 105

Bismillahirrahmanirrahim, da sunan Allah me rahama me jinkai, Allah yakara tsira da aminci ga shugabanmu Annabi muhammadu salallahu alaihi wassalam.
Bayan haka bazan gajiba da mika gaisuwata da godiya ga yan uwa da abokan arziki ba, bayan haka
Banyarda a juyamin littafi ba ko amfani da wani bangare ba tareda izinina ba.
Domin gyara, shawara ko sharhi, za a iya tuntubata akan what's app number dina
07063065680
Or email address @ [email protected]
Watpad @Ayshercool7724

     

             _MY FIRST NOVEL _


Zare ido Anty tayi tace "gaskiyane Abee, tunda ya iya budar baki yace a bashi matarsa he mean it, zanyiwa Anty Salma magana gaskiya, a bashi iga suje can su karata, tunda be san abun Arziki ba"

Abee yace "gara dai kuyi tunani, wannan ba mafita bace ku bashi matarsa kawai"


Tunda Abee ya bashi goyon baya A ranar Jalal ya shirya ya tafi kano ko sallama basuyi da Jalila ba, dan in dai suka hadu fada zasuyi.
Yayi waya da Daddy ya gaya masa yana son zeyi magana dashi, Daddy yayi masa Alkawarin zezo Nigeria su hadu a kano.


Ba zato ba tsammani Ilham ta dawo taga motar Jalal a harabar gidan, ai a guje takarasa cikin gidan ta nufi dakin  Mummy tana kwala mata kira,
"Mummy Kinsan Jalal ya dawo kuwa?"
Mikewa Mummy tayi "dagaske ko wasa"?
"Wallahi dagaske nake, ga motarsa can"
Jinjina kai Mummy tayi tace "Shikenan rabu dashi, nasan tunda yazo Akwai abunda ya kawo shi, kyleni da shi kawai"

Ilham ta koma dakinta tana cigaba da tunanin wani mataki Ummanta ke shirin dauka akan wannan lamarin, Itakuma me yakamata tayi?
Wasa2 kwanan Jalal uku da dawowa amma sam Mummy bata sa Jalal a idonta ba, da kanta taje dakin Jalal amma baya nan.
Ilham ma duk yadda taso taga Jalal bata ganshi ba, ko ina yake tafiya oho?.


Bangaren Jalila kuwa sekuma shan gyara takeyi, basu gaya mata Jalal yace zasu koma kano ba.


Kwanan Jalal hudu a kano sannan Daddy ya dawo, koda ya dawo babu wata tarbar Arziki daya samu daga Mummy se mita da masifa, Bebi takanta ba ya cigaba da sha'anin sa, babban abunda yake kular da ita kenan, tasa shi agaba taita masifa Amma ya kyaleta yaki kulata.

Ranar da Daddy ya dawo da daddare Jalal ya shigo, ba kowa a palourn dan haka ya wuce part din Daddy, shikansa Daddy yaji dadin ganin Jalal,

Daddy yace "Ango, Ango se wani kyau ka keyi, alamu hankalin ka a kwance"

Jalal ya dan bata fuska yace

"Ina wani hankalina a kwance yake, Kawai su Anty sunje sun rike ta a can gurinsu ko mene amfanin hakan oho?"

Daddy yai murmushi yace "Tunda sukayi haka Akwai dalili"

Jalal ya dan hade fuska yace
"koma meye dalilin nasu ni munyi magana da Abee zan dakkota tazo ta tare"

"Jalal meyasa kai haka? Zasu ga kaman bakayi musu kara ba"

"Daddy sati guda da komawa makaranta yakamata ace ta koma itama, sannan kasan in dai da Auren nan idan nazo kano bani da masauki, bani kwanciyar hankali saboda masifar Mummy indai nazo gidan nan, nasan bata son Auren nan, nikuma inason abuna, kaga ko nazo Kano a gidana zan sauka baseta ganni ba bazan zo mata gida ba"

Murmushi Daddy yayi yace "koma dai meye she's your Mum, yakamata ka dinga mata uzuri sannan ka dinga hakuri da ita"

Jalal yace
"Daddy maganar gidan da zan zauna ne yasa nazo Kano fa"

"to wane gidan zaka zauna, gadon kayan zaka koma kokuma yaya?"

"No bazan koma gadon kaya ba, zamana a gidan nan zena tunamin abubuwan da suka wuce masu batamin rai"

"to ya kake so ayi?" daddy ya tambayar yana bawa Jalal attention dinsa

"gida zan siya a tarauni, a can zan zauna in danyi nesa daku, bana son yawan fitina ko hayaniya, Gobe in Allah ya kaimu se muje ka tayani zaban gidan"

"hmm Jalal kenan, to ai tunda bani zan zauna ba, kai da ita matar taka yakamata ku zabi gidan da kuke so"

"Kyaleta kawai duk gidan dana zaba baza tace beyi ba"

"to shikenan ina fatan kun daidai ta kanku babu matsala"

"karka damu Daddy, in Allah ya kaimu gobe muje a siyi gidan, ka gayawa Abba, next week Insha Allah in basu kawo ta ba, zanje in dakko ta"

Daddy kallon Jalal kawai yake, jalal din maganar sa yake kansa tsaye kuma hankali kwance ba wata kunya ko makamancin haka a tare da shi.
Suna ta hirarsu ba zato ba tsammani sega Mummy ta shigo ďakin, seda ta danyi turus ta tsaya, ganin Jalal da tayi kanan kayane a jikin Jalal kaman yadda yasaba sakawa, Amma abun mamaki dogon wandone har kasa a jikinsa, da riga me dogon hannu, wuyansa babu sarka, sannan babu wannan askin banzan da yakeyi kuma ya sawa kan color duk babu, yayi kiba abunsa kuma fuskarsa ba laifi a sake yana murmushi, sabanin da da kullum fusakarsa a murtuke.

Idan lissafinta dai2 ne kimanin watanni shida bata ganshi ba ko a waya baya kiranta, dama ina ta kai matsayin da Jalal ze aje lambarta balle ya kirata.

Jalal yace "Daddy in aka siyi gidan se a sai furnitures ma in saka, kayan kitchen ban san kansu ba maybe su Anty sa saimata, kokuma muje da ita ta siya"

Wannan statement din data ji yafi kowanne bata mata rai, su Jalal basu san ta shigo ba, dan sun bawa kofar baya, nan Take ta shakunu ta karasa shigowa dakin fuskarta babu walwala ta zo ta tsaya.

Jalal na ganinta ya maze ya jingina da jikin kujera ya dora kafa daya kan daya
Ta kalli Jalal tace

"Sannu mara mutunci wanda be san ciwon kansa ba, Jalal saboda ba ka maidani komai ba tsawon watanni shida ban saka a idona ba, kuma saboda kai ba dan mutunci bane har a hada kai ai maka Aire ba tareda izinina ba, saboda munafunci baka tuntubeni ba tunda akayi Auren nan ka hada kai da dangin ubanka kayi tafiyarka inda ta zaba maka, se yau ka dawo kana zaka saimata gida da furnitures, kudin na ubanta ne? Ko shi ya tara maka? Wallahi Jalal se an kashe Auren nan, ban yadda ka zauna da yarinyar nan ba, seka saketa kuma seka baro wannan tsinan nan aikin data samo maka a lagosa, tunda ba ita ta haifamin kai ba"

cikin masifa Mummy take wannan hakilon Masifar, har Daddy ya fusata zeyi magana Jalal yace

"No Daddy yi hakuri, ban sanka da fada ba, kayi shiru kawai, bari zanje in dawo" Jalal ya mike ze fita, Mummy ta kuma fusata tace
"Nizaka mayar 'yar Iska ina maka magana, Wallahi Jalal in baka saki yarinyar nan ba sena maka baki" cak Jalal ya tsaya ya waigo yana kallonta.
Daddy dafe kai yayi, dan shi a rayuwarsa sam baya son tashin hankali.
Jalal yazo gaban Mummy ya kalleta yace

"Mummy idan kikamin baki akan na wasu zaki ďora, inkin min baki baze dameni ba, tunda wanda yake dawainiya dani be ishekiba, baki da wata cikakkiyar hujja na kin Aure na, bazan saki Jalila ba saboda ina sonta, kema soyayya ce tasaki zama da mahaifina, nima na Auri wadda na rayu da sonta, baze yuwu amin Auren dole ba, tunda kema bashi aka miki ba"
"Jalal ni kake gayawa haka?"

Kai tsaye yace

"Yau na fara gaya miki gaskiya? Bazan Auri macen da bana so ba saboda san zuciyarki, da in saki mata ta gara kimin bakin, dama can a lalace nake, in kika min baki kinga dorawa zanyi"
Yana gama maganar ya fice.

"Innalillahi wa inna ilaihi raji un, nashiga uku, dan dana haifa ya tsaya a gabana yana gaya min wannan maganganun, Habib Jalal ua zabi mace akaina da na haifeshi, ban taba zaton haka ba, tunanina Jalal shaye2 kawai yake, yaushe Jalal ya fara son Jalila da har yake gayamin wannan maganar akanta, tun yanzu, wallahi na tsani yarinyar nan"

Daddy yace "Khadija be kamata kiyi wannan maganar ba, bari in tuna miki wani abu, Soyayyar da nake miki tasa na zauna dake tsawon shekaru, na fifita ki fiye da Ahalina, kika rabani da kowa nawa, Ashe ba dadi, na fuskanci Soyayya bazata yiwa Jalal da wasa ba, dan haka ki shirya sa hannu ki karbi irin abunda kika aikata kema"
Mummy cigaba da rusa kuka tayi tama fadin

"Wallahi baze yuwu ba, ni na haifi dana ba'a isa amin iko da shiba, babu wadda ta isa ta juyamin yaro, nasan wannan makircin Salma ne, zata ďau fansa a kan ďana, tana tunanin zata mallake min ďa saboda wannan banzan shirin nata? Wallahi bata isa ba" tuni Idon Mummy yayi jawur tana kuka tana masifa, Daddy ba shi da zabin da ya wuce yabar mata ďakin, dukda yadda yakejin kukan nata a zuciyarsa, Amma wannan faďan rashin gaskiyane kawai take yi.


Ilham kuwa tana kitchen tana hada abunda zata ci, sama bata san Jalal ya shigo part din ba, tana daga kai ta window taga shigar Jalal part dinsa, gabanta ne ya fadi, ya wani kara kiba, wani tunani ne yazo mata, hakan yasa ta fito da sauri ta tafi part din nasa, tana zuwa ta tarar baya palourn dan haka kai tsaye itama ta bishi bedroom din nasa, Amma tana zuwa ta tarar har ya shiga toilet, gefen gadonsa ta samu ta zauna ba tare da fargabar komai ba, tayi a kalla mintuna Ashirin sannan ya fito sanye da gajeren wando jikinsa babu riga se karamin towel yana goge ruwan jikinsa, Sam Jalal be kula da Ilham ba, yayinda Ilham ta daskare a zaune tana karewa surar Jikin Jalal kallo,
Gaskiya Jalal ya kai a so shi koba dan dukiyar sa ba, ko ina na jikinsa kwance yake da gashi tun daga kansa har kafafunsa, dogone jikin sa a murde yake, dama ga jikinsa yana cin karfe, kallo daya zaka masa kasan namiji ne me matukar kwarjini, yana ďaga kai yayi ido hudu da Ilham zaune akan gadonsa, a fusace yace "Ke meye haka? Uban me yakawo ki dakina a daren nan? Ta shi kifita ki barmin daki"

Mikewa Ilham tayi ta tako gaban sa ta tsaya tana kuma kare masa kallo, "Jalal dagaske kayi Aure ko?"

"Tambayata ma kike? Ban sani ba, fita ki barmin daki"

Towel din hannunsa ta karba, ta ajiye ta zuba masa ido, Hawaye ne ya fara bin idonta

"Jalal namaka son da ban taba yiwa wani namiji makamancin sa ba, Jalal why? Ina sonka Jalal, meyasa zaka Auri wata bani ba, Wallahi ina sonka, Jalal ka shmmace ni, ka Auri yarinyar da nafi tsana a rayuwata, Haba Jalal meyasa kamin hakan?"

"kina son Jalal ko kina son cutar da shi? Kina sona nikuma na rayu da son yarinyar da kika fi tsana, saboda a duniya a yanzu babu wanda ya gwada min so kamar yadda tayi, I love Jalila with all my heart, ba abunda bazan sadaukar akanta ba, i am sorry, kema Allah yabaki me sonki"

Wani kululun takaici ne ya tokare kirjin Ilham, Amma ta maze, hannu ta mika kirjin Jalal zata shafa kirjinsa amma ya rike hannunta, ya girgiza mata kai,

Ya dan lumshe ido ya bude yace

"Abunda yasa nake kara Son Jalila kenan, ba ruwanta da abunda ba nata ba, karki tsallake iyakar ki, karki taba mata miji kin san halin ta dai base na gaya miki ba, Abunda kike hari tsawon lokaci ya zama nata, a gaskiya ta miki ba dadi, ta rusa shirinki gaba ďay" ya karasa maganar yana ďanyin murmushin mugunta, sekuma ya haďe rai yace

"malama get out from my room"
Ilham tace "Amma Jalal"
"ki fitar min daga ďaki malama, ko ba kya banbance abunda ya dace da wanda be dace ba? Kifita bana son ganinki" Jalal ya katseta

"Yaya Jalal..."

"kifita nace ko in miki Illa, natsaneki bama son ganinki, ki fita ki bar min daki ko in kakkarya ki"

Yadda yakoma yana maganar a fusace ya sa Ilham ta fita da sauri ta bar dakin. Wani dogon tsaki Jalal ya ja ya saka doguwar Jallabiya ya kwanta.

Ilham kwana tayi tana juyi ta kasa bacci, Jalal da ba ruwansa da mata yaushe ya fara Soyayya? Har yake gaya mata yana son Jalila fiye da komai, yadda taga rana haka taga dare zuciyarta kamar zata fito,tana karajin tsanar Jalila a ranta.

Kamar yadda suka tsara, Jalal da Daddy sukaje suka sai gida a tarauni, gidan yayi matukar kyau da tsaruwa, yanada girma sosai gidan, palour biyu, bedroom uku kowanne da toilet se kitchen biyi da store da katuwar harabar gida.
Daddy ya samu Abba akan, an sai gidan dasu Jalal zasu zauna, Jalal ze sai furnitures, Abba yace be yadda ba shi zewa Jalila kayan daki, Jalal ba dan yaso ba ya hakura, Abba da Maama sukaje suka ga gidan sun yaba gidan sosai, Abba seda ya cikawa Jalila ko ina da kaya, gidan ta yayi kyau ya tsaru matuka.


Sam Jalila bata san abunda ake ba, ita dai taga su Hajiya Salma sunata kara shiryata, Hajiya Salma taje ta samu Jalila a daki tace "Jalila ki ware gashinki, me kitso zatazo ayi miki kunshi da kitso, ranar Asabar zaki tare"
Zare ido Jalila tayi tace "Wai Asabar me zuwa?"
"Eh mana, mijinki yace; se kin tare ya gaji da wannan sintirin"
Shiru Jalila tayi ta sunkuyar da kai, Hajiya Salma tace

"Haba Jalila meye kuma na damuwa? Allah ya baku zaman lafiya, karki damu kinji" jinjina mata kai kawai Jalila tayi ba tareda tace komai ba.


Yau weekends ne, Hanan sun gama cin Abincin Rana da Jawwad, tana ta zuba shagwabarta yana biye mata, dan ba karamin birge shi wannan shagwabar take ba, yace
" Habibty Inaga ranar Saturday fa sister dinki zata tare"

"Wai Jalila?"

Jawwad yace

"eh ita, munyi waya da shi dazu da safe kina bacci, ya gayamin ya sai gida, an gama zuba komai ranar Saturday zata tare, inkuma sunki zeje ya dauketa ne kawai"
Dariya Hanan ta kama yi, Jawwad yace
"ya dai, ya naga kina dariya?"

"Akwai kura ne"

"Kura kuma? Meyasa kikace haka?"

"Hmm bakomai, gaskiya yakamata muje kano, zanso inyi kallon yadda wannan rayuwar masoyan zata kasance"
Jawwad yai murmushi yace "lafiya kalau zasu zauna"

"Hakane wuyatta su zauna guri daya, bari a jima in kirata, naga har yanzu bata da waya, se dai kabani taka in kirata"

Jawwad yace "Shikenan naga be bata wayarba har yanzu"

"nasan ze bata insha Allah"
Hanan ta mike ta tafi bedroom dinta.


Jalila tarasa meya kema ta dadi, wai ita ce zata tare a gidan Jalal, a matsayin matarsa, tanata tunane2, Amal tayi sallama, Jalila ta amsa, Amal tace "Anty Jalila, Mummy tace in kawomiki phone, your sister wants to talk to you"
Jalila a ranta tace ;kai yaran gidan nan sunfiye iyayi, ji yadda take magana kamar me koyon hausa
Jalila tasa hannu ta karbi wayar tareda cewa "Nagode"
Wayar aka sake kira Jalila ta daga wayar tareda fadin
"Salamu Alaikum"

Yanayin muryarta ze gaya maka tana cikin damuwa, Hanan tace

"Amaryar Yaya Jalal, ke ko kirana ba kyayi se idan nina kiraki ko?"
Cikin sanyin jiki Jalila tace

" kinsan bani da waya tun ranar dinner da ya karba be baniba, bana son yawan takura musu da karbar waya"

Hanan tace "hakane ya kike ya shirye2"

"shirye2 me?" Jalila ta tambaya

Hanan tace

"Ahhh Haidar yacemin ranar Saturday In Allah ya kaimu zaki tare"
Dan karamin tsaki Jalila tayi

"shine wani ya shirye2, ba wani shirye2 ni abun duniya ya dameni, ina tunanin irin zaman da zanyi a gidan nan"

"meye wani abun damuwa kuma? Karki dorawa kanki ciwo mana, Allah yabaku zaman lafiya yasa kina zuwa kiyi karo da shi"

Jalila tace "inyi karo dame?"

"ďan baba mana, nan da wata tara muzo suna" hanan ta bata amsa

Wani uban tsaki Jalila tayi "Ke kinfiye shirme wallahi"

"bawani shirme, Addu'a nai miki tagari"

"rike addu'ar ki bana so, ni ba haka naje yi ba"

Dariya Hanan ta dinga yi "Wallahi karya kike, abunda kikaje yi kenan, sekin cika masa gida da 'ya' ya duk shekara zaki dinga haihuwa"
Kashe wayar Jalila tayi, tareda yin dogon tsaki, inta biyewa Hanan bata mata rai zata cigaba da yi.


Shirye2 sunyi nisa, Hajiya Salma da Anty sun tsaya an gyara Jalila yadda yakamata, sun hada mata kayan turaruka daban2, Suka shirya mata kayanta a trolley. Ta wani bangaren Jalila tanata murna zata koma garinsu, ta cigaba da zuwa makaranta,


Anty tace "Jalila na cika alkawarin dana taba yi miki, ga turaruka nan, in sun kare ma kiyi magana se in hado miki wasu"
"to Anty na gode"
Abee yayiwa Jalila nasiha sosai, tareda yi mata fatan Alkhairi, yabata kyautuka na litattafan Addini dana zamani, sekuma kyautar system yace taje taita karatu. Jalila tai tayi masa godiya.

Hajiya Salma sunyi waya da Jalal, cewar zasu taho da Jalila gobe zasu tsaya a gidan su Jalila, sannan su kaita gurin Mummy daga nan akaita gidanta.
Jalal yace "gaskiya bana son ku kaita gidan Mummy, dan seta bata muku rai, kawai ku kyale ta"

"A'a Jalal baza'ayi haka ba, Mahaifiyarka ce akwai bukatar a sauke hakkinta na uwa, yakamata ta sawa Aurenka Albarka"

Jalal yace "Shikenan yadda kuka gani, Amma ni a gurina babu bukatar hakan.


Ilham bata taba sanin tana kaunar Jalal ba kamar yanzu, gaba daya kishi ya hanata sukuni ko Abinci bata iya ci, ita a tunanin ta tana so tayi soyayya da Jalal ne dan cika burin mahaifiyarta, Amma yanzu ta gane kaunar Jalal tayi mata illa, bata bacci sam, yadda taga rana haka taga dare, wai Jalal ke gaya mata shidin mallakin Wata mace ne, macen da ta dade tana cusa masa miyagun maganganu da cin mutunci amma saboda bashi da zuciya yake fadin shi mallakin ta ne, hawaye ne ya gangaro daga idon Ilham tace "Wallahi Jalal muddin baka Aureni ba sena fitini rayuwar Auren ka, sena uzzurawa rayuwarku, se Gidan Auren ka yazama kurku ta fishi 'yanci, idan har kuka ji dadin Aure ba Saudatu ce ta haifeni" ta cigaba da kuka da surutai a daki.


Jalila se murna take zata koma Kano, koba komai zata dinga zuwa makaranta ta rage kadaici, karfe goma sha daya na safe suka shirya, Anty, Hajiya Salma, Husna, da wasu daga danginsu Jalal suka taho yiwa Jalila rakiya Kano,
Se kusan karfe hudu na yamma suka iso, Maama ta san da zuwansu dan haka ta riga ta shirya komai, har 'yan uwanta da makwabta ta sanar, bayan sallar magariba za'a raka Jalila gidanta.
Jalila tayi murna ganinta a gida, Abba yayi murna yadda yaga Jalila tayi kalau da ita tayi fes kaman wata matar hamshaki. Dakinsu taje komai yana nan yadda ta barshi, kewar Nana ta dinga ji a ranta, tana tuno abubuwa da dama da ya faru a wannan dakin, wasu ma farinciki wasu na bakinciki. Maama tazo ta sameta tace

"Jalila ki debi duka abunda kike so akayanki, wanda zakiyi Amfani da shi nan kusa se a tafi miki dashi"
"to Maama zan diba Insha Allah"
Sukaci Abinci sukayi Sallolin da ake binsu.
Anty tace "Jalila yakamata ki shirya muje a kaiki gurin uwar mijinki, kar dare yayi sosai"
Ras gaban Jalila ya fadi! Jikinta yafara Rawa, ta shiga duniyar tunanin wace irin karba Mummy zatayi mata.

Kamar wadda kwai ya fashewa a ciki ta Amsa, seda takuma wanka ta canza kaya, suka nadeta a cikin lafaya, se kamshi takeyi Maama ta kama hannunta ta kaita gurin Abba, ya dinga mata nasiha da Addu'a, Jalila se kuka take, yadda Abba yaji rabuwa da Jalila beji haka akan Nana da Jawwad ba, yana matukar tausayinta. Bayan ya gama ne Maama tayi mata 'yan nasihohi da Addu'a, dan sosai take jin kunyar abubuwan da ta aikatawa Jalila.
Wasu daga cikin' yan rakiyar amarya sunyi gaba dan suje suga ďaki, Yayinda Hajiya Salma da Antyn Jalal suka nufi gidan su Jalal Da Amarya Jalila.


Vote, Comment and
Share please
I want comments not stickers or just thanks
Daga alkalamin Aysher cool
🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️

What's app only 07063065680.
Follow me onWatpad @Ayshercool7724
        

🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹 🌹

*ABDUL JALAL*

_Story, writing and edited _

By
AISHA HUMAIRA
( _Daddy's girl_)

*PERFECT WRITER'S*
*ASSOCIATION*🌞

(𝕎𝔼 𝔸𝕀ℕ'𝕋 ℙ𝔼ℝ𝔽𝔼ℂ𝕋 𝔹𝕌𝕋 𝕎𝔼'ℝ𝔼 𝔸𝕃𝕎𝔸𝕐𝕊, 𝕋ℝ𝕐𝕀ℕ𝔾 𝕆𝕌ℝ 𝔹𝔼𝕊𝕋 𝕋𝕆 𝕄𝕆𝕋𝕀𝕍𝔸𝕋𝔼 𝔸ℕ𝔻 𝔼ℕ𝕋𝔼ℝ𝕋𝔸𝕀ℕ 𝕆𝕌ℝ ℝ𝔼𝔸𝔻𝔼ℝ𝕊💪)

/https://www.facebook.com/Perfect-writers-association-100452275039839/

*P.W.A*✍️
Chapter 51 · 0% Book details