PART 2
Abdul Jalal Part 2 Complete Hausa Novel · about 16 min read
_PAGE 5️⃣1️⃣ 104
Bismillahirrahmanirrahim, da sunan Allah me rahama me jinkai, Allah yakara tsira da aminci ga shugabanmu Annabi muhammadu salallahu alaihi wassalam.
Bayan haka bazan gajiba da mika gaisuwata da godiya ga yan uwa da abokan arziki ba, bayan haka
Banyarda a juyamin littafi ba ko amfani da wani bangare ba tareda izinina ba.
Domin gyara, shawara ko sharhi, za a iya tuntubata akan what's app number dina
07063065680
Or email address @ [email protected]
Watpad @Ayshercool7724
_MY FIRST NOVEL _
Tunda aka gama biki Maama bata dawo ba, seda takuma kwana goma a Bauchi, taji dadin zaman garin sosai, gashi mutane ne masu karamci da son 'yan uwa, Abba ne yazo ya dauketa suka koma gida kanon dabo.
Bangaren Angwaye da Amare da sukayi Auren soyayya Se shan soyayya da kauna suke, tsakanin su banda Jalila da Jalal da babu wanda yake neman wani a tsakanin su,
Jalila ita wannan zaman hutun ya isheta, ita dama kano suka batta tayi zamanta a gurin Maama ya fiye mata wanna zaman.
Tana ta zancen zuci ne Husna 'yar gidan Anty ta shigo da waya ta mikowa Jalila, Jalila tasa hannu ta karba, video Call ne ta ďaga wayar tana ďagawa taga fuskar Jawwad cikin sauri ta mike zaune
"Yaya Jawwad kaine?"
"Nine Baby, yaya borno yasu Anty?"
"lafiya kalau Yaya Jawwad, kayi kiba sosai kaman ba kaiba, ina Hanan?"
"tana kitchen tana girki, kema gaki nan kinyi kibar ai, ya mijin naki?"
Tabe baki Jalila tayi tace "yana can lagos" Hanan ce ta taho da gudu ta haye kan cinyar Jawwad tace
"Hi queen, ya kike?"
"Wow Hanan, wannan kwalliya haka, masha Allah, naji dadin ganinku wallahi nayi farinciki, Allah ya albarkaci rayuwar aurenku, yara muku kaunar juna"
Tausayinta yakama su Jawwad, Hanan tace "Jalila kunyi waya da Nana kuwa?"
"Eh munyi waya da su, ya Abuja ya zaman kadaici?"
Jawwad yace
"muba ma zaman kadaici ko My sugar, masu zaman kadaici suna Azabtar da zukatansu sun san kansu" yai maganar yana kallon Hanan, Hanan tace "Sosai makuwa, ba wani kadaici, kullum muna tare, kema kice akaiki gidan mijinki kigani in zakiji wani kadaici"
"Allah ya kiyaye" Jalila ta fada tana harar Hanan. Wayar Jawwad ta fara ringing, Jalal ne yake kiransa, Jawwad yace
"Baby mijinki ke kirana, bari inje in amsa" Hanan ta zauna akan kujera tace "Jalila wai yaushe zaku sauke wannan taurin kan ke dashi ku fuskanci juna?"
"Hanan ya kikeso inyi ne? Nagaya muku Jalal ba sona yake ba, kawai an lika masa ni ne, tun lokacin biki nake rashin lafiya be nemeni ba, ko ta kaina bayabi, se ranar da ze tafiya ya ajiyemin takadda, sam be damu dani ba, Hanan ku kukayi dacen Auren soyayya amma bani ba, nasan da Ahmad na Aura baze watsi da lamarina ba" kan Jalila ta gama maganar har hawaye ya wanke mata fuska. Cikin taushin murya Hanan tace
"Jalila, kina da Aure yanzu be kamata kidinga ambaton wani namijin ba, Sannan Jalila kinsan halin mijinki tun kafin kuyi Aure, bashida shiga sabagar mutane, dukda ke matarsa ce yanzu, Amma kiyi hakuri, komai ze wuce Jalila, kalli yadda kikayi kyau kamar a saceki a gudu, i wish yana nan yaga wannan kwalliyar taki se ya rude, waima me suke bakine kikayi wannan kyan"
Murmushin takaici Jalila tayi tace
"Hanan kenan, kina tunanin zanyi wani abu daze gani ya yabane? Ko ya burgeshi, shi ba sona yake ba kawai an aura masa ni, be damu da yasan a halin da nake ba balle ya yaba kwalliya ta, se an jima ki gaida Yaya Jawwad.
Jalila ta ajiye wayar ta dora sabon kuka me sauti.
ji tayi an dafata, ta dago ta kalli wanda ya dafata Husna ce fuskarta dauke da damuwa tace
"Sorry dear, please stop crying, kidena kuka ko tunanin broz Jalal baya sonki, is not like that, ina kula da yadda kuke share juna kedashi, which is total bad, an riga an daura Aurenku, kamata yayi ku manta da abunda ya wuce, Jalal has a social disabilities at times, tun lokacin da yakoma drunker, mutane suke kyamarsa he decided to isolate himself from the people, he dint interact with people as before, believe me he loves you bazaki gane hakan ba sekin zauna da shi, yanada kirki sosai, ki dena yawan kukan nan please "
Jinjina mata kai Jalila tayi Husna tace
" Yawwa mrs Jalal, Jalal bashi da matsala bayan ta shaye2, zaki maida shi yadda kikeso, yana sonki ne shiyasa yakeyin abunda kike so, ba dan haka ba a duniya akwai abunda ba wanda ya isa Jalal yayi wani abun yayi. Husnah ta cigaba da rarrashin Jalila, a lokacin take gayawa Jalila Tanada Aure, mijinta baya gari ne, shiyasa itama tazo tayi zamanta a gida.
Ilham takasa zaune takasa tsaye, kwanata kusan shida a gidansu suna sakawa da warwara akan yadda zasu bullowa lamarin ita da umanta, yanzunma zancen da suke kenan
"Umma kin san kashinmu ya bushe idan yarinyar nan ta tare da Jalal, aikin ze lalace ne fa, zamu rasa komai, jiran da mukayi tsawon shekaru mu dauki fansa ze tashi a banza ne, indai yana tareda yarinyar nanmun rasa komai, daular da muke hange bazamu sameta ba"
Umman Ilham taja numfashi ta hura hanci tace
"Bazan taba yadda tsawon wannan lokacin daukar fansa ta ya tsaya akan lalacewar Jalal ba, dole in wulakanta khadija in mallake dukiyar da take takama da ita, sena ga ta wulakanta daga ita har Habib din"
Ilham tace "Umma to tayaya?"
"ki kylaeni kawai, nasan abunda zanyi, tunda ke kinkasa abunda ya kaiki gidan tsawon lokaci"
"Umma kenan, ba kasawa nayi ba, nayi iya yina, ba daban wannan Jalilan ba da tuni an wuce gurin, Amma ni hankalina a tashe yake umma, kin san abunda Aure ga Jalal yake nufi fa a shirin mu, so soyayya da wata mace bayanni ga Jalal kim san barazana ce a garemu, wallahi ko bacci bana iyayi"
"ni nace ki bar komai a hannuna, nasan me zanyi"
"Shikenan Umma"
Mummy har gidansu Jawwad taje da kanta, ta tarar da Maama tana ta fama da aikin gida. Cikin fara'a Maama ta tareta tana mata sannu da zuwa
Aikuwa a fusace mummy tace
"kinga niba yashe bakinki nazo gani ba, ba hakoranki nazo ki nunamin ba, baban su Jawwad na nan ne?
" A'a baya nan lafiya kuwa? "
" ina fa lafiya, saboda tsabar munafunci a haďa kai da ke a cuceni, a Aurawa Jalal wannan yarinyar dake kanki kinsam bata da cikakken Asali, meyasa baki yadda an
An aurawa ďanki ba se nawa ďan, wannan yarinyar mara mutunci akan me? Sumi2 da ita kamar ta Allah amma tana bin ďana"
Maama tace
"Subhanallah ni kaina ban san da batun ďaurin aurensu ba se ana i gobe ďaurin Aure, kuma iyayensu mazane suka yanke wannan hukuncin baniba, da amincewar mahaifinsa aka aura masa ita"
"ke kikasani koma suwaye suka amince, saboda tayi kwantai tarasa miji se abawa ďana, Allah kadai yasan abunda aka dukunkune aka bashi"
"Mummy Jalila ba kwantai tayi ba, tanada masoya, Allah ne yayi matarsa, Sannan be kamata kidinga wannan maganganun ba karkizo kiji kunya wataran kamar yadda naji kunya nima, Ni data zauna taredani tayi zaman hakuri dani na tabattar Alkhairi ce ga rayuwar Jalal, a irin zamanbda tayi a hannuna nasan halinta"
"kinga dan Allah ki sauraramin bana bukatar jin wa'azinki, tunda baya nan, ki gaya masa ya shirya karbar karamar bazawara, dan sena kashe Auren nan, ban ga dacewar Jalal da wannan yarinyar ba"
Maama tace "Shikenan duk yadda kika gani, komai ya samu bawa mukaddarine, dadinta ma ďan naki ba wani kintsatse bane balle aji haushi dan an rabu da shi, naga ke kanki baki isa da shi ba, temaka masa akayi aka bashi yarinyar nan, kuma duniya da gaskiya baki isa ki biya Jalila da mahifiyarta abunda tayiwa ďanki ba"
Maama takarasa maganar tareda shigewa ta bar Mummy a gurin.
Mummy ta dawo gida tana cizon ya tsa, tana tunani iri2 a ranta.
Jalila hankalin ta ya ďan kwanta, Husna na debe mata kewa suna hira lokaci zuwa lokaci, sannan duk lokacin da ta keso zata ari waya takira wanda takeso, Mijin Antyn Jalal professor Aliyu Ishaq yana koyar da darasin turanci a saudiyya, be fiye zama ba, yana da tarin Ilimi, gashi mutumin kirki ne, yana da barkwanci da raha, Girmama shin da Jalila da take da yadda yaga tana gudanar da Al'amuranta yasa take burgeshi, yayiwa Jalal murnanr samun yarinya me kwazo da tarbiyya kamar Jalila. Be kara sarewa da lamarin Jalila ba seda Antyn ta bashi labarin irin Abubuwan da Jalila ta dingayi da kokarinta akan rayuwar Jalal, ya zamana Jalila tana sakewa da shi fiye da kowa a gidan, kamar yadda Ake kiransa Abee haka take kiransa, Jalila tana son mu'amala da mutane masu ilimi dazata Amfana dasu, indai Abee ze fito parlour Jalila zata zauna Suyita hira tana masa tambayoyi akan abubuwa da dama, shikansa duk lokacin da be ganta ba ya dinga tambaya tana ina kenan, yana mamakin kaifin hankalin ta da basirarta, gata da ilimin Addini "
Yauma na gama dinner, Amma Jalila tanata hira da Abee tana bashi labarin irin fituntunun data dingayi lokacin kuruciya suna ta mata dariya, Hajiya Salma tace
"Nikam Alhaji Aliyu me kayiwa Jalila haka take sakewa da kai hada hira, mu kaman tsoronmu ma takeji"
Jalila tayi murmushi tace "Bahaka bane ba, Jalila Aliyu Imam, shine cikakken sunana, kuma Kafin Babana ya rasu Abee nake ce masa"
Anty tace "Haba shiyasa wannan shakuwa haka, Ashe ya da uba ne"
Abee yace "Eh ya ranku, yata kuma sirikata kuma malamata"
Zare ido Jalila tayi tace "Wace ni, se dai in durkusa a koyamin, Seda safenku" Jalila ta fada tana mikewa tsaye, sukayi Sallama ta tafi dakinta.
Bayan tafiyarta Abee yace "Kuna ganin raba yaran nan yanada wata fa'ida ne? Yana can matar tana nan"
Anty tace "Eh mana, muna so mugane dagaske yana sonta ne kokuwa?"
Abee yayi murmushi yace "Lallai kun manta waye ďan naku ne, shikenan Allah ya tabattar da alkhairi, Amma nayiwa Jalal murna samun yarinyar kirki kamar ta, tanada hankali sosai"
Haka dai suka cigaba da tattaunawa.
Jalalila kamar kullum ta gama wannan wankan turaren, ta shirya a cikin wata doguwar riga, dayake Anty sunyiwa Jalila sayayyar kayan sawa dana kwalliya tana kan wani karamin kujera tana gyara gashin ta.
Husnah ce ta shigo dakin tana murmushi tace
"Maigidanki yana hanya, broz Jalal zezo ba sanarwa ba komai, kuma nasan badan ke ba bazamu ganshi ba, tashi muje ayi masa girki, Anyiwa me kitso waya tana hanya, ki taso muje"
Hade rai Jalila tayi tace "ba wani girki da zanyi, kuma ni ku kyalemin kaina a haka"
Husnah tace
"Haba Sister meyasa haka ne?" (nikam nace baki san halin Jalila da taurin kai ba)
Jalila tace "wai meye Amfanin inta bawa kaina wahala akan wanda be damu dani ba? Watana daya da kwana Goma a gidan nan ko ta waya baya kira balle yaji ya nake, seni zan ta faman wahala akansa"
Ajiyar Zuciya Husnah tayi tace
"Kina da gaskiya Jalila Amma hakurin dazakiyi yanzu baze kai na baya ba, ki bari ki kama shi a hannu, daga nan seki rama, taso muje su Mummy suna parlour"
Jalila bata da zabi sena ta mike tabi bayan Husnah, suna zuwa parlour Hajiya Salma tace
"Yawwa Jalila, Jalal yayi waya yakusa isowa maiduguri, me kitso tana hanya, dama lallanki jiya akayi shi, in an gama kitson kafin ya karaso ayi masa girkin.
Jalila ta samu guri ta zauna ba tareda tace komai ba, Husnah ta zauna a kusa da ita tana mata magana kasa2
"please sister idan yazo karki hade masa rai haka, karki biye masa dan Allah, ki bawa mara ďa kunya"
Ita dai Jalila jinsu kawai take.
Tunda Daddy ya tafi be kara dawowa Nigeria ba, Mummy tarasa me yake mata daďi, in dai Jalal ya zauna da yarinyar nan to zata kwace mata shine gaba daya, dan tun kafin ya aureta ma yana sonta tunda yanajin maganar ta, tarasa ta inda zata bullowa lamarin, gashi a yanzu tasan bata isa taje maiduguri tayi musu tijara ba.
Kafin Jalal ya karaso har angama yiwa Jalila kitso, kitso akayi mata kanana sosai, gashi hannunta ya sha lalle, duk inda ta gifta kamshi take, ga fatarta ta kara kyau se sheki take.
Anty tace " Jalila me yakamata ki girkawa Jalal ne? Mara nauyi sosai tunda naga alamar shigowar dare zeyi"
Dan zumbura baki Jalila tayi tace "befiye cin Abinci da daddare ba yafi shan tea ko fruit, wani lokacin koya ci Abinci seya sha tea da daddare" ta fada tana dan tura baki cikin ko in kula
Boye dairiyar su sukayi, banda Husna da seda ta dara, tace "Ya akayi kika san haka?"
"Nike musu girki shida Yaya Jawwad a gida" tabata amsa
Anty tace "Ke Husnah ina ruwanki ne? Jalila ki dafa masa abunda kika ga ya dace kawai"
Jinjina kai tayi ta tafi ďakinta.
.
Seda ta tafi sukayi dariya, Hajiya Salma tace "Kai lamarin yaran nan sesu, ni ban san wanda yafi wani taurin kai a cikin su ba, ana so ana kaiwa kasuwa"
Anty tace "Jalal yafita taurin kai, bafa yanzu yafara sonta ba shi, Jalal ya dade yana sonta, nasan komai, Dan yaga ya samu yanzu shine yake basarwa kaman be damu da ita ba"
Hajiya Salma tace
"Aike ta hannun damansa ce kinsan komai akansa, Allah ya daidaita tsakani"
Suka Amsa da Ameen
Lokacin sallar magariba Jalal ya iso gidan, ya sha tafiya dan a mota yazo ya gaji sosai, Jalila bata san ya karaso ba, har bayan sallar isha'i tana palourn Abee yana mata bayani akan wani littafi da yake son wallafawa, Husnah tana gefe tana dan tsoma musu baki lokaci zuwa lokaci, zaman da Jalila tayi da su tafara gane yarensu kadan2, kaman gaisuwa da yaren.
Suna hira kai kace 'ya da ubane, Anty ta shigo palourn tace
"Jalila kina nan, tun dazu Jalal ya iso fa, nazata kina can kina shiryawa ne, kije ki shirya ki kaimasa Abincin"
Jalila ta dan langabe kai tana kallon Anty. A ranta tace "Sekace wani mijin kirki ko wadda zata biki anata in shirya, bayan nasan ko kallo ban isheshi ba"
Abee ya kalli Anty yace "Madam jeki zamuyi magana da' yar auta ta"
"to shikenan nidai ayi Sauri, in ba sokuke yayi zuciya ba ya tafi" ta fada tana shirin barin palourn tareda yin murmushi, Ameera tana zaune bata fita ba.
Abee yace
"Jalila tambayar ki zanyi, ki gayamin tsakani da Allah, in dai kin baban dani ki gayamin kina kuwa son Jalal?"
Taji ya mata tambayar ba tareda ta shirya jin hakan ba.
Hade fuska ta danyi tace "Ni dai ban sani ba ko ina sonshi, shima fa baya sona" ta karasa maganar kaman tana shagwaba
Fuskarta ya kalla, Akwai alamar kuruciya sosai a tareda ita, yarinya ce me tunani irin na manya, Amm lokuta da dama kuruciya tana dawainiya da ita.
Yace "Shikenan daughter Allah ya daidaita ku, ki cigaba da hakuri zaki fara sonsa, Mijin kine yanzu, ki manta da halinsa kinemi Aljannar ki, kuma insha Allah komai ze wuce"
Jalila tace "to Abee nagode" harzata fita Husnah tace "Jirani muje in miki kwalliya, nasan idan na kyaleki ba zakiyi ba"
Ta tasa Jalila a gaba zuwa ďaki, ta ďakko mata wani material baki da adon jan flowers, riga da skirt ta mikawa Jalila ta karba tana zumbura baki ta saka, tayi kyau sosai, Husnah ta bata turaruka ta shafa, kamshi dai kam ya riga yagama kama jikin Jalila a gidan nan, Husnah tace
"bari in miki kwalliya"
"ni ba wata kwalliya daza'a yimin"
"Jalila ya hakane? To sa kwalli da jan baki mana"
Jalila ta saka kwalli se jan baki Ja, tasaka kwalli, tayi kyau sosai, Husnah ta bata karamin gyale Ja akanta, Jalila ta kalli kanta a mudubi, kayan nan sun kamata sosai ta kalli Husnah tace "Nikam gyalen nan yayi min karami gaskiya, ki bari in saka babba"
"Haba Jalila, gurin mijinki zaki fa, Mijinki ne ba wani ba, in kuma kinki in barki da su Mummy"
Husnah tasata gaba zuwa Kitchen ta shirya mata kayan Abincin a tray ta rakata har kofar palourn da Jalal yake tace
"please Jalila don't mess up, karki bani kunya dan Allah"
Jalila ba tace komai ba ta shiga gabanta se faduwa yake yi, Sallama tayi sannan ta shiga, bata tabaccin ya amsa sallamar nan tata. da farko dakin kamshin turarensa yakeyi, Jalila na shigowa kuwa temperature dakin ta canza zuwa kamshin turaren jikinta, kallo daya tayi masa ta dauke kanta, kanan kayane a jikinsa amma yayi kyau sosai sumarsa se kyalli take, duk ya dena saka wannan kalar dayake wa gashinsa, ya dora kafarsa akan center table, ko a ina zata ajiye tray din oho, ta gefen ido ya dan saci kallonta, tana zuwa bata kula shi ba ta ajiye tray din a kasa, ta juya zataje ta zauna hakan ya bashi damar kare mata kallo, tubarkallah she has a very beautiful heart and body structure, Jalila tana da kyau ga kyakywan surar jiki, ga zuciyarta me matukar tausayi, matsalarta taurin kai da Izza wani lokacin.
Taje ta nemi guri ta zauna a kujerar da take kallonsa ta dora kafa daya kan daya tana kada kafa tareda dauke kanta gefe tana wasa da yatsun hannunta.
Jalal a ransa yace 'Tsabar wulakanci ko ta gaisheni kota ce min ya hanya ba ruwan ta dani, hakan na nufin dagaske bata sona ne? Ko kuma tsabar rigima da taurin kaine? " Jalal ya gaza gano amsoshin tambayoyin sa, to bata kulashi da sannu da zuwa ba ma balle yasa ran zata zuba masa Abincin.
Kallon ta ya kumayi, kayanta cif jikinta ga mayafin iyakarsa wuyanta, hanun nan yayi kyau da lalle, kanta ba dan kwali dan haka yana iya ganin tsagar kanan kitso dake kanta.
Itama Jalila a ranta mita take "tsabar wulakanci koma ya tambayeni ya nake, bayan tafiyar sa ya na karke, ya tafi ya barni ba lafiya koya bugo waya yaji ya jikina, ya sani a gaba da kallo yaki cin Abincin in baze ci ba ni in tafi, mtseww ta danyi tsaki, tsakin ya fito fili ba tareda sanin ta ba.
Saurin dagowa yayi suka haďa ido ta basar.
Mikewa yayi ba tareda ya kalli inda Abincin yake ba ya mike ze fice, itama ta mike da sauri tasha gabansa suka tsaya suna kallon Juna, lokaci na farko da suka kasance tare tun bayan daura Auren su
"lafiya meye haka?" ya tambayeta
"ya zan kawo Abinci ka tashi baka ciba? Salon in koma ayita tuhuma ta"
"in sun tuhumeki kice su koya miki yadda ake kula da miji, dan baki iya ba" Ta dan yatsina fuska ta kalleshi
"Waye mijin? Aini banga miji anan ba, kaima yakamata a koya maka yadda ake kula da mace dan..... Se kuma tayi shiru ganin yadda ya kura mata ido, Ashe fa yanzu mijinta ne, ba kowace magana yakamata ta gaya masa ba
"Ni kike cewa bakiga Miji anan ba ko?, Nagode sosai, matsa kibani guri in wuce"
Hanya ta bashi ya fice daga dakin, bata bi ta kan kayan ba itama tayi waje abunta.
Washegari ma da Safe Aka sa Jalila ta kai masa Abinci, haushin taki kulashi jiya yasa beci Abincin ba yakuma barinsa.
Yana fita ya tafi gurin Abee, bayan sun gaisa Abee yanata tsokanarsa, Jalal yace
"Abee so nake kasa baki su kaimin matata, ko in dauketa mu tafi basu sani ba"
Abee yace "A'a baza'ayi haka ba ai, kwantar da hankalinka, ko gobe kake so za'a kaimaka ita zan saka baki suba ka ita, na goyi bayanka tunda Daddynka yana jin nauyinsu, ina dalili kanada Aure amma sun barka kana ta fama sun rike maka mata" haka Abee ya lallaba Jalal ya tafi.
Yaje yasamu Anty yace mata "kinga tun wuri kubawa yaron nan matarsa yana son abarsa, yamuku kawaici amma kunki ganewa"
Anty tace "Abee Akwai dalilin da yasa muka riketa anan ne"
"A'a Ku bashi matarsa kawai, in baso kike kiga tafara miki laulayi a gidan nan ba, sannan ku kwasheta ku kaita"
Zare ido Anty tayi "Haba dai"
"Eh mana, yanzu da muka rabu da shi yake gayamin insa baki ku bashi matarsa"
Aimin hakuri fa rashin posting akan lokaci, abubuwa sunyimin yawa, adinga min uzuri nagode da kulawarku
Vote and
Share please
I want comments not stickers or just thanks
Daga alkalamin Aysher cool
🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️
What's app only 07063065680.
Follow me onWatpad @Ayshercool7724
🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹 🌹
*ABDUL JALAL*
_Story, writing and edited _
By
AISHA HUMAIRA
( _Daddy's girl_)
*PERFECT WRITER'S*
*ASSOCIATION*🌞
(𝕎𝔼 𝔸𝕀ℕ'𝕋 ℙ𝔼ℝ𝔽𝔼ℂ𝕋 𝔹𝕌𝕋 𝕎𝔼'ℝ𝔼 𝔸𝕃𝕎𝔸𝕐𝕊, 𝕋ℝ𝕐𝕀ℕ𝔾 𝕆𝕌ℝ 𝔹𝔼𝕊𝕋 𝕋𝕆 𝕄𝕆𝕋𝕀𝕍𝔸𝕋𝔼 𝔸ℕ𝔻 𝔼ℕ𝕋𝔼ℝ𝕋𝔸𝕀ℕ 𝕆𝕌ℝ ℝ𝔼𝔸𝔻𝔼ℝ𝕊💪)
/https://www.facebook.com/Perfect-writers-association-100452275039839/
*P.W.A*✍️
Bismillahirrahmanirrahim, da sunan Allah me rahama me jinkai, Allah yakara tsira da aminci ga shugabanmu Annabi muhammadu salallahu alaihi wassalam.
Bayan haka bazan gajiba da mika gaisuwata da godiya ga yan uwa da abokan arziki ba, bayan haka
Banyarda a juyamin littafi ba ko amfani da wani bangare ba tareda izinina ba.
Domin gyara, shawara ko sharhi, za a iya tuntubata akan what's app number dina
07063065680
Or email address @ [email protected]
Watpad @Ayshercool7724
_MY FIRST NOVEL _
Tunda aka gama biki Maama bata dawo ba, seda takuma kwana goma a Bauchi, taji dadin zaman garin sosai, gashi mutane ne masu karamci da son 'yan uwa, Abba ne yazo ya dauketa suka koma gida kanon dabo.
Bangaren Angwaye da Amare da sukayi Auren soyayya Se shan soyayya da kauna suke, tsakanin su banda Jalila da Jalal da babu wanda yake neman wani a tsakanin su,
Jalila ita wannan zaman hutun ya isheta, ita dama kano suka batta tayi zamanta a gurin Maama ya fiye mata wanna zaman.
Tana ta zancen zuci ne Husna 'yar gidan Anty ta shigo da waya ta mikowa Jalila, Jalila tasa hannu ta karba, video Call ne ta ďaga wayar tana ďagawa taga fuskar Jawwad cikin sauri ta mike zaune
"Yaya Jawwad kaine?"
"Nine Baby, yaya borno yasu Anty?"
"lafiya kalau Yaya Jawwad, kayi kiba sosai kaman ba kaiba, ina Hanan?"
"tana kitchen tana girki, kema gaki nan kinyi kibar ai, ya mijin naki?"
Tabe baki Jalila tayi tace "yana can lagos" Hanan ce ta taho da gudu ta haye kan cinyar Jawwad tace
"Hi queen, ya kike?"
"Wow Hanan, wannan kwalliya haka, masha Allah, naji dadin ganinku wallahi nayi farinciki, Allah ya albarkaci rayuwar aurenku, yara muku kaunar juna"
Tausayinta yakama su Jawwad, Hanan tace "Jalila kunyi waya da Nana kuwa?"
"Eh munyi waya da su, ya Abuja ya zaman kadaici?"
Jawwad yace
"muba ma zaman kadaici ko My sugar, masu zaman kadaici suna Azabtar da zukatansu sun san kansu" yai maganar yana kallon Hanan, Hanan tace "Sosai makuwa, ba wani kadaici, kullum muna tare, kema kice akaiki gidan mijinki kigani in zakiji wani kadaici"
"Allah ya kiyaye" Jalila ta fada tana harar Hanan. Wayar Jawwad ta fara ringing, Jalal ne yake kiransa, Jawwad yace
"Baby mijinki ke kirana, bari inje in amsa" Hanan ta zauna akan kujera tace "Jalila wai yaushe zaku sauke wannan taurin kan ke dashi ku fuskanci juna?"
"Hanan ya kikeso inyi ne? Nagaya muku Jalal ba sona yake ba, kawai an lika masa ni ne, tun lokacin biki nake rashin lafiya be nemeni ba, ko ta kaina bayabi, se ranar da ze tafiya ya ajiyemin takadda, sam be damu dani ba, Hanan ku kukayi dacen Auren soyayya amma bani ba, nasan da Ahmad na Aura baze watsi da lamarina ba" kan Jalila ta gama maganar har hawaye ya wanke mata fuska. Cikin taushin murya Hanan tace
"Jalila, kina da Aure yanzu be kamata kidinga ambaton wani namijin ba, Sannan Jalila kinsan halin mijinki tun kafin kuyi Aure, bashida shiga sabagar mutane, dukda ke matarsa ce yanzu, Amma kiyi hakuri, komai ze wuce Jalila, kalli yadda kikayi kyau kamar a saceki a gudu, i wish yana nan yaga wannan kwalliyar taki se ya rude, waima me suke bakine kikayi wannan kyan"
Murmushin takaici Jalila tayi tace
"Hanan kenan, kina tunanin zanyi wani abu daze gani ya yabane? Ko ya burgeshi, shi ba sona yake ba kawai an aura masa ni, be damu da yasan a halin da nake ba balle ya yaba kwalliya ta, se an jima ki gaida Yaya Jawwad.
Jalila ta ajiye wayar ta dora sabon kuka me sauti.
ji tayi an dafata, ta dago ta kalli wanda ya dafata Husna ce fuskarta dauke da damuwa tace
"Sorry dear, please stop crying, kidena kuka ko tunanin broz Jalal baya sonki, is not like that, ina kula da yadda kuke share juna kedashi, which is total bad, an riga an daura Aurenku, kamata yayi ku manta da abunda ya wuce, Jalal has a social disabilities at times, tun lokacin da yakoma drunker, mutane suke kyamarsa he decided to isolate himself from the people, he dint interact with people as before, believe me he loves you bazaki gane hakan ba sekin zauna da shi, yanada kirki sosai, ki dena yawan kukan nan please "
Jinjina mata kai Jalila tayi Husna tace
" Yawwa mrs Jalal, Jalal bashi da matsala bayan ta shaye2, zaki maida shi yadda kikeso, yana sonki ne shiyasa yakeyin abunda kike so, ba dan haka ba a duniya akwai abunda ba wanda ya isa Jalal yayi wani abun yayi. Husnah ta cigaba da rarrashin Jalila, a lokacin take gayawa Jalila Tanada Aure, mijinta baya gari ne, shiyasa itama tazo tayi zamanta a gida.
Ilham takasa zaune takasa tsaye, kwanata kusan shida a gidansu suna sakawa da warwara akan yadda zasu bullowa lamarin ita da umanta, yanzunma zancen da suke kenan
"Umma kin san kashinmu ya bushe idan yarinyar nan ta tare da Jalal, aikin ze lalace ne fa, zamu rasa komai, jiran da mukayi tsawon shekaru mu dauki fansa ze tashi a banza ne, indai yana tareda yarinyar nanmun rasa komai, daular da muke hange bazamu sameta ba"
Umman Ilham taja numfashi ta hura hanci tace
"Bazan taba yadda tsawon wannan lokacin daukar fansa ta ya tsaya akan lalacewar Jalal ba, dole in wulakanta khadija in mallake dukiyar da take takama da ita, sena ga ta wulakanta daga ita har Habib din"
Ilham tace "Umma to tayaya?"
"ki kylaeni kawai, nasan abunda zanyi, tunda ke kinkasa abunda ya kaiki gidan tsawon lokaci"
"Umma kenan, ba kasawa nayi ba, nayi iya yina, ba daban wannan Jalilan ba da tuni an wuce gurin, Amma ni hankalina a tashe yake umma, kin san abunda Aure ga Jalal yake nufi fa a shirin mu, so soyayya da wata mace bayanni ga Jalal kim san barazana ce a garemu, wallahi ko bacci bana iyayi"
"ni nace ki bar komai a hannuna, nasan me zanyi"
"Shikenan Umma"
Mummy har gidansu Jawwad taje da kanta, ta tarar da Maama tana ta fama da aikin gida. Cikin fara'a Maama ta tareta tana mata sannu da zuwa
Aikuwa a fusace mummy tace
"kinga niba yashe bakinki nazo gani ba, ba hakoranki nazo ki nunamin ba, baban su Jawwad na nan ne?
" A'a baya nan lafiya kuwa? "
" ina fa lafiya, saboda tsabar munafunci a haďa kai da ke a cuceni, a Aurawa Jalal wannan yarinyar dake kanki kinsam bata da cikakken Asali, meyasa baki yadda an
An aurawa ďanki ba se nawa ďan, wannan yarinyar mara mutunci akan me? Sumi2 da ita kamar ta Allah amma tana bin ďana"
Maama tace
"Subhanallah ni kaina ban san da batun ďaurin aurensu ba se ana i gobe ďaurin Aure, kuma iyayensu mazane suka yanke wannan hukuncin baniba, da amincewar mahaifinsa aka aura masa ita"
"ke kikasani koma suwaye suka amince, saboda tayi kwantai tarasa miji se abawa ďana, Allah kadai yasan abunda aka dukunkune aka bashi"
"Mummy Jalila ba kwantai tayi ba, tanada masoya, Allah ne yayi matarsa, Sannan be kamata kidinga wannan maganganun ba karkizo kiji kunya wataran kamar yadda naji kunya nima, Ni data zauna taredani tayi zaman hakuri dani na tabattar Alkhairi ce ga rayuwar Jalal, a irin zamanbda tayi a hannuna nasan halinta"
"kinga dan Allah ki sauraramin bana bukatar jin wa'azinki, tunda baya nan, ki gaya masa ya shirya karbar karamar bazawara, dan sena kashe Auren nan, ban ga dacewar Jalal da wannan yarinyar ba"
Maama tace "Shikenan duk yadda kika gani, komai ya samu bawa mukaddarine, dadinta ma ďan naki ba wani kintsatse bane balle aji haushi dan an rabu da shi, naga ke kanki baki isa da shi ba, temaka masa akayi aka bashi yarinyar nan, kuma duniya da gaskiya baki isa ki biya Jalila da mahifiyarta abunda tayiwa ďanki ba"
Maama takarasa maganar tareda shigewa ta bar Mummy a gurin.
Mummy ta dawo gida tana cizon ya tsa, tana tunani iri2 a ranta.
Jalila hankalin ta ya ďan kwanta, Husna na debe mata kewa suna hira lokaci zuwa lokaci, sannan duk lokacin da ta keso zata ari waya takira wanda takeso, Mijin Antyn Jalal professor Aliyu Ishaq yana koyar da darasin turanci a saudiyya, be fiye zama ba, yana da tarin Ilimi, gashi mutumin kirki ne, yana da barkwanci da raha, Girmama shin da Jalila da take da yadda yaga tana gudanar da Al'amuranta yasa take burgeshi, yayiwa Jalal murnanr samun yarinya me kwazo da tarbiyya kamar Jalila. Be kara sarewa da lamarin Jalila ba seda Antyn ta bashi labarin irin Abubuwan da Jalila ta dingayi da kokarinta akan rayuwar Jalal, ya zamana Jalila tana sakewa da shi fiye da kowa a gidan, kamar yadda Ake kiransa Abee haka take kiransa, Jalila tana son mu'amala da mutane masu ilimi dazata Amfana dasu, indai Abee ze fito parlour Jalila zata zauna Suyita hira tana masa tambayoyi akan abubuwa da dama, shikansa duk lokacin da be ganta ba ya dinga tambaya tana ina kenan, yana mamakin kaifin hankalin ta da basirarta, gata da ilimin Addini "
Yauma na gama dinner, Amma Jalila tanata hira da Abee tana bashi labarin irin fituntunun data dingayi lokacin kuruciya suna ta mata dariya, Hajiya Salma tace
"Nikam Alhaji Aliyu me kayiwa Jalila haka take sakewa da kai hada hira, mu kaman tsoronmu ma takeji"
Jalila tayi murmushi tace "Bahaka bane ba, Jalila Aliyu Imam, shine cikakken sunana, kuma Kafin Babana ya rasu Abee nake ce masa"
Anty tace "Haba shiyasa wannan shakuwa haka, Ashe ya da uba ne"
Abee yace "Eh ya ranku, yata kuma sirikata kuma malamata"
Zare ido Jalila tayi tace "Wace ni, se dai in durkusa a koyamin, Seda safenku" Jalila ta fada tana mikewa tsaye, sukayi Sallama ta tafi dakinta.
Bayan tafiyarta Abee yace "Kuna ganin raba yaran nan yanada wata fa'ida ne? Yana can matar tana nan"
Anty tace "Eh mana, muna so mugane dagaske yana sonta ne kokuwa?"
Abee yayi murmushi yace "Lallai kun manta waye ďan naku ne, shikenan Allah ya tabattar da alkhairi, Amma nayiwa Jalal murna samun yarinyar kirki kamar ta, tanada hankali sosai"
Haka dai suka cigaba da tattaunawa.
Jalalila kamar kullum ta gama wannan wankan turaren, ta shirya a cikin wata doguwar riga, dayake Anty sunyiwa Jalila sayayyar kayan sawa dana kwalliya tana kan wani karamin kujera tana gyara gashin ta.
Husnah ce ta shigo dakin tana murmushi tace
"Maigidanki yana hanya, broz Jalal zezo ba sanarwa ba komai, kuma nasan badan ke ba bazamu ganshi ba, tashi muje ayi masa girki, Anyiwa me kitso waya tana hanya, ki taso muje"
Hade rai Jalila tayi tace "ba wani girki da zanyi, kuma ni ku kyalemin kaina a haka"
Husnah tace
"Haba Sister meyasa haka ne?" (nikam nace baki san halin Jalila da taurin kai ba)
Jalila tace "wai meye Amfanin inta bawa kaina wahala akan wanda be damu dani ba? Watana daya da kwana Goma a gidan nan ko ta waya baya kira balle yaji ya nake, seni zan ta faman wahala akansa"
Ajiyar Zuciya Husnah tayi tace
"Kina da gaskiya Jalila Amma hakurin dazakiyi yanzu baze kai na baya ba, ki bari ki kama shi a hannu, daga nan seki rama, taso muje su Mummy suna parlour"
Jalila bata da zabi sena ta mike tabi bayan Husnah, suna zuwa parlour Hajiya Salma tace
"Yawwa Jalila, Jalal yayi waya yakusa isowa maiduguri, me kitso tana hanya, dama lallanki jiya akayi shi, in an gama kitson kafin ya karaso ayi masa girkin.
Jalila ta samu guri ta zauna ba tareda tace komai ba, Husnah ta zauna a kusa da ita tana mata magana kasa2
"please sister idan yazo karki hade masa rai haka, karki biye masa dan Allah, ki bawa mara ďa kunya"
Ita dai Jalila jinsu kawai take.
Tunda Daddy ya tafi be kara dawowa Nigeria ba, Mummy tarasa me yake mata daďi, in dai Jalal ya zauna da yarinyar nan to zata kwace mata shine gaba daya, dan tun kafin ya aureta ma yana sonta tunda yanajin maganar ta, tarasa ta inda zata bullowa lamarin, gashi a yanzu tasan bata isa taje maiduguri tayi musu tijara ba.
Kafin Jalal ya karaso har angama yiwa Jalila kitso, kitso akayi mata kanana sosai, gashi hannunta ya sha lalle, duk inda ta gifta kamshi take, ga fatarta ta kara kyau se sheki take.
Anty tace " Jalila me yakamata ki girkawa Jalal ne? Mara nauyi sosai tunda naga alamar shigowar dare zeyi"
Dan zumbura baki Jalila tayi tace "befiye cin Abinci da daddare ba yafi shan tea ko fruit, wani lokacin koya ci Abinci seya sha tea da daddare" ta fada tana dan tura baki cikin ko in kula
Boye dairiyar su sukayi, banda Husna da seda ta dara, tace "Ya akayi kika san haka?"
"Nike musu girki shida Yaya Jawwad a gida" tabata amsa
Anty tace "Ke Husnah ina ruwanki ne? Jalila ki dafa masa abunda kika ga ya dace kawai"
Jinjina kai tayi ta tafi ďakinta.
.
Seda ta tafi sukayi dariya, Hajiya Salma tace "Kai lamarin yaran nan sesu, ni ban san wanda yafi wani taurin kai a cikin su ba, ana so ana kaiwa kasuwa"
Anty tace "Jalal yafita taurin kai, bafa yanzu yafara sonta ba shi, Jalal ya dade yana sonta, nasan komai, Dan yaga ya samu yanzu shine yake basarwa kaman be damu da ita ba"
Hajiya Salma tace
"Aike ta hannun damansa ce kinsan komai akansa, Allah ya daidaita tsakani"
Suka Amsa da Ameen
Lokacin sallar magariba Jalal ya iso gidan, ya sha tafiya dan a mota yazo ya gaji sosai, Jalila bata san ya karaso ba, har bayan sallar isha'i tana palourn Abee yana mata bayani akan wani littafi da yake son wallafawa, Husnah tana gefe tana dan tsoma musu baki lokaci zuwa lokaci, zaman da Jalila tayi da su tafara gane yarensu kadan2, kaman gaisuwa da yaren.
Suna hira kai kace 'ya da ubane, Anty ta shigo palourn tace
"Jalila kina nan, tun dazu Jalal ya iso fa, nazata kina can kina shiryawa ne, kije ki shirya ki kaimasa Abincin"
Jalila ta dan langabe kai tana kallon Anty. A ranta tace "Sekace wani mijin kirki ko wadda zata biki anata in shirya, bayan nasan ko kallo ban isheshi ba"
Abee ya kalli Anty yace "Madam jeki zamuyi magana da' yar auta ta"
"to shikenan nidai ayi Sauri, in ba sokuke yayi zuciya ba ya tafi" ta fada tana shirin barin palourn tareda yin murmushi, Ameera tana zaune bata fita ba.
Abee yace
"Jalila tambayar ki zanyi, ki gayamin tsakani da Allah, in dai kin baban dani ki gayamin kina kuwa son Jalal?"
Taji ya mata tambayar ba tareda ta shirya jin hakan ba.
Hade fuska ta danyi tace "Ni dai ban sani ba ko ina sonshi, shima fa baya sona" ta karasa maganar kaman tana shagwaba
Fuskarta ya kalla, Akwai alamar kuruciya sosai a tareda ita, yarinya ce me tunani irin na manya, Amm lokuta da dama kuruciya tana dawainiya da ita.
Yace "Shikenan daughter Allah ya daidaita ku, ki cigaba da hakuri zaki fara sonsa, Mijin kine yanzu, ki manta da halinsa kinemi Aljannar ki, kuma insha Allah komai ze wuce"
Jalila tace "to Abee nagode" harzata fita Husnah tace "Jirani muje in miki kwalliya, nasan idan na kyaleki ba zakiyi ba"
Ta tasa Jalila a gaba zuwa ďaki, ta ďakko mata wani material baki da adon jan flowers, riga da skirt ta mikawa Jalila ta karba tana zumbura baki ta saka, tayi kyau sosai, Husnah ta bata turaruka ta shafa, kamshi dai kam ya riga yagama kama jikin Jalila a gidan nan, Husnah tace
"bari in miki kwalliya"
"ni ba wata kwalliya daza'a yimin"
"Jalila ya hakane? To sa kwalli da jan baki mana"
Jalila ta saka kwalli se jan baki Ja, tasaka kwalli, tayi kyau sosai, Husnah ta bata karamin gyale Ja akanta, Jalila ta kalli kanta a mudubi, kayan nan sun kamata sosai ta kalli Husnah tace "Nikam gyalen nan yayi min karami gaskiya, ki bari in saka babba"
"Haba Jalila, gurin mijinki zaki fa, Mijinki ne ba wani ba, in kuma kinki in barki da su Mummy"
Husnah tasata gaba zuwa Kitchen ta shirya mata kayan Abincin a tray ta rakata har kofar palourn da Jalal yake tace
"please Jalila don't mess up, karki bani kunya dan Allah"
Jalila ba tace komai ba ta shiga gabanta se faduwa yake yi, Sallama tayi sannan ta shiga, bata tabaccin ya amsa sallamar nan tata. da farko dakin kamshin turarensa yakeyi, Jalila na shigowa kuwa temperature dakin ta canza zuwa kamshin turaren jikinta, kallo daya tayi masa ta dauke kanta, kanan kayane a jikinsa amma yayi kyau sosai sumarsa se kyalli take, duk ya dena saka wannan kalar dayake wa gashinsa, ya dora kafarsa akan center table, ko a ina zata ajiye tray din oho, ta gefen ido ya dan saci kallonta, tana zuwa bata kula shi ba ta ajiye tray din a kasa, ta juya zataje ta zauna hakan ya bashi damar kare mata kallo, tubarkallah she has a very beautiful heart and body structure, Jalila tana da kyau ga kyakywan surar jiki, ga zuciyarta me matukar tausayi, matsalarta taurin kai da Izza wani lokacin.
Taje ta nemi guri ta zauna a kujerar da take kallonsa ta dora kafa daya kan daya tana kada kafa tareda dauke kanta gefe tana wasa da yatsun hannunta.
Jalal a ransa yace 'Tsabar wulakanci ko ta gaisheni kota ce min ya hanya ba ruwan ta dani, hakan na nufin dagaske bata sona ne? Ko kuma tsabar rigima da taurin kaine? " Jalal ya gaza gano amsoshin tambayoyin sa, to bata kulashi da sannu da zuwa ba ma balle yasa ran zata zuba masa Abincin.
Kallon ta ya kumayi, kayanta cif jikinta ga mayafin iyakarsa wuyanta, hanun nan yayi kyau da lalle, kanta ba dan kwali dan haka yana iya ganin tsagar kanan kitso dake kanta.
Itama Jalila a ranta mita take "tsabar wulakanci koma ya tambayeni ya nake, bayan tafiyar sa ya na karke, ya tafi ya barni ba lafiya koya bugo waya yaji ya jikina, ya sani a gaba da kallo yaki cin Abincin in baze ci ba ni in tafi, mtseww ta danyi tsaki, tsakin ya fito fili ba tareda sanin ta ba.
Saurin dagowa yayi suka haďa ido ta basar.
Mikewa yayi ba tareda ya kalli inda Abincin yake ba ya mike ze fice, itama ta mike da sauri tasha gabansa suka tsaya suna kallon Juna, lokaci na farko da suka kasance tare tun bayan daura Auren su
"lafiya meye haka?" ya tambayeta
"ya zan kawo Abinci ka tashi baka ciba? Salon in koma ayita tuhuma ta"
"in sun tuhumeki kice su koya miki yadda ake kula da miji, dan baki iya ba" Ta dan yatsina fuska ta kalleshi
"Waye mijin? Aini banga miji anan ba, kaima yakamata a koya maka yadda ake kula da mace dan..... Se kuma tayi shiru ganin yadda ya kura mata ido, Ashe fa yanzu mijinta ne, ba kowace magana yakamata ta gaya masa ba
"Ni kike cewa bakiga Miji anan ba ko?, Nagode sosai, matsa kibani guri in wuce"
Hanya ta bashi ya fice daga dakin, bata bi ta kan kayan ba itama tayi waje abunta.
Washegari ma da Safe Aka sa Jalila ta kai masa Abinci, haushin taki kulashi jiya yasa beci Abincin ba yakuma barinsa.
Yana fita ya tafi gurin Abee, bayan sun gaisa Abee yanata tsokanarsa, Jalal yace
"Abee so nake kasa baki su kaimin matata, ko in dauketa mu tafi basu sani ba"
Abee yace "A'a baza'ayi haka ba ai, kwantar da hankalinka, ko gobe kake so za'a kaimaka ita zan saka baki suba ka ita, na goyi bayanka tunda Daddynka yana jin nauyinsu, ina dalili kanada Aure amma sun barka kana ta fama sun rike maka mata" haka Abee ya lallaba Jalal ya tafi.
Yaje yasamu Anty yace mata "kinga tun wuri kubawa yaron nan matarsa yana son abarsa, yamuku kawaici amma kunki ganewa"
Anty tace "Abee Akwai dalilin da yasa muka riketa anan ne"
"A'a Ku bashi matarsa kawai, in baso kike kiga tafara miki laulayi a gidan nan ba, sannan ku kwasheta ku kaita"
Zare ido Anty tayi "Haba dai"
"Eh mana, yanzu da muka rabu da shi yake gayamin insa baki ku bashi matarsa"
Aimin hakuri fa rashin posting akan lokaci, abubuwa sunyimin yawa, adinga min uzuri nagode da kulawarku
Vote and
Share please
I want comments not stickers or just thanks
Daga alkalamin Aysher cool
🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️🖊️
What's app only 07063065680.
Follow me onWatpad @Ayshercool7724
🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹 🌹
*ABDUL JALAL*
_Story, writing and edited _
By
AISHA HUMAIRA
( _Daddy's girl_)
*PERFECT WRITER'S*
*ASSOCIATION*🌞
(𝕎𝔼 𝔸𝕀ℕ'𝕋 ℙ𝔼ℝ𝔽𝔼ℂ𝕋 𝔹𝕌𝕋 𝕎𝔼'ℝ𝔼 𝔸𝕃𝕎𝔸𝕐𝕊, 𝕋ℝ𝕐𝕀ℕ𝔾 𝕆𝕌ℝ 𝔹𝔼𝕊𝕋 𝕋𝕆 𝕄𝕆𝕋𝕀𝕍𝔸𝕋𝔼 𝔸ℕ𝔻 𝔼ℕ𝕋𝔼ℝ𝕋𝔸𝕀ℕ 𝕆𝕌ℝ ℝ𝔼𝔸𝔻𝔼ℝ𝕊💪)
/https://www.facebook.com/Perfect-writers-association-100452275039839/
*P.W.A*✍️