← Book details Zafin Wuta Part Two Complete Hausa Novel Local reading mode
CHAPTER 9 OF 16

CHAPTER 9

Zafin Wuta Part Two Complete Hausa Novel · about 19 min read

بسم الله الرحمن الرحيم.
Da ƙyar na kawar da tunanin Mama na wajen ya ɗauka da haka har muka gama karyawa a tsanake cikin tsari da burgewa.

Bayan kowa ya gama ne muka ɗunguma zuwa wajen duba jikin Fauzan, sai da kowa ya gama shiga sannan na shiga daga ƙarshe ina ɓuya bayan Hajjo.

Idanuwansa a kulle suke amma jin wannan sanyin me saka ma shi nutsuwa ya saka shi saurin buɗe rinannun idanuwanshi, haƙiƙa wannan sanyi rahama ne a gareshi, wannan sanyi ya na taka muhimmiyar rawa cikin rayuwarshi, sannan bugu da ƙari tun daga jiya bai huta ba koda na second ɗaya daga tunanin tsari da zubin halitar wacce ta taryeshi hannu biyu a matsayin mijin aurenta wanda ya ke a mawuyacin hali, haƙiƙa ya yabawa jarumta, haƙuri gami da tawassali irin nata, a halin da yake ciki yanzu haka shi yasan ba kowa zai so shi ba sai dai aji tausayinshi.

Ɗaya bayan ɗaya suka shiga gaisheshi su na yi ma shi ya jiki, ya na amsa su da kai, da haka har aka zo kaina, yayinda a sanyaye na matsa kusa da shi ina kin wani abu da ba daidai ba a wajen, cikin sanyin murya na buɗe baki na ba tare da na kalleshi ba na ce.

"Barka da safiya, ya ƙarfin jikin, Allah ya bada lafiya."

Bai amsa ba kuma bai daina kallona ba, a hankali na yi niyyar matsawa, amma sai naji saukar hannu me ɗumi ya riƙo nawa hannun, wani irin tsale duka ƙirjina ya yi, yayinda na ɗaga idona ahankali na sauke akan na shi hannun wanda babu komi sai ƙasusuwa da fata, amma sosai na yi mamakin yanda ya riƙe ni da ƙarfi sosai.

"Kai Fauzan cika ma ta hannu manah, baka ganin aikin zuba maka magani za ta yi." Mommy ta faɗi ganin yanda nike ta kiciniyar janye hannuna amma na kasa.

Da wani irin sauri na juya tare da sakin baki galala, ba ni kaɗai ba harsa su Hajjo sun cika da mamakin jin abin da na ji.

"Uhumm, Mommy ina son ɗumin jikinta, pleasw ki ce ma ta karta tafi ta barni."Fauzan ya faɗi cikin wata iriyar haɗaɗiyar murya me daɗin amo, nutsuwa, kamala gami da shagwaɓa duka muryar tasa ta haɗa, nan take na ji wani abu ya tsaga ta cikin jinin jikina, yayinda sautin bugun zuciyata ya sauya ta koma dokawa a hankali cikin sanyi.

Da sauri Mommy ta taso tazo gabana ta kama hannuna tare da matsawa kusa da Fauzan idonta na tsiyayarda hawayen farin ciki ta damƙa hannuna a cikin nashi ta na faɗin.

"My lovely son🥹, indai har zaka samu lafiya ka dawo cikin farin ciki kamar yanda muke a baya, to ga Mubaraka nan na damƙa ma ka ita amana, ka ƙarfafa zuciya da gangar jikinka wajen hana ciwo yin galaba akanka, ga kwarara zuciyarka ta hanyar sakawa wannan baiwar Allar me zuciyar zinare da mafificin alkairi kamar yanda ta sadaukar da farin ciki da ƙuruciyarta ta amince da aurenka sannan ta amince da jinyarka alhalin ko mu da muke makusantanka bamuyi maka wannan sadaukarwar ba, tabar ƴan uwanta da danginta harma da rayuwarda ta saba ta zo cikinmu ta zauna dan kawai ta faranta mana rai ta hanyar kulawa da kai, ga Mubaraka nan na damƙa maka ita ɗin matarka ce kuma amana a wajenka da mu baki ɗaya."

Mommy ba ta ƙarashe faɗin abin da za ta faɗa ba wani irin raunananen kuka ya ci ƙarfinta, wanda hakan ya saka ta ƙanƙame hannuna da nashi wajen ɗaya hawayenta na sauka akan hannuwan namu, Phapha ne ya taso cikin sanyi jiki ya janyeta daga wajen tare da rungumeta ya fice fuskarshi da damuwa, Hajjo ma jan hannun Sulaima da bakinta ya mutu murus dan tsabar murna ta yi suka bar wajen, ficewa sukai suka barni daga ni sai Fauzan wanda ke ƙanƙame da hannuna kamar wani zai kwace ma sa ni.

Cikin sassanyan sauti me taushi na kalleshi tare da falin.
"Ammm,,, ɗan cika min hannu zan haɗa magani."
Na faɗi ina ƙifta manyan idanuwana dan kuka ne ke neman kwace min.

"Ni bazan cika ki ba gaskiya😩."Fauzan ya faɗi a shagwaɓe ya na janyo ni gaba ɗaya, saura kaɗan in faɗa jikinsa amma na hana hakan faruwa ta hanyar dafe ƙasa da hannunawa, fuskata na fuskantar ta shi fuskar wacce tai baƙi saboda maganin da na shafa masa jiya.

Bazan iya banbance halitar fuskarshi ba amma yanayin yanda naga gashin kanshi ya kwanta luf baƙi wuluk sai hakan ya saka nike tunanin ko yayane zai kasance cikin sahum maza ƴan kwalisa.

Sauke fararena na yi a cikin nasa, wani irin abu me ƙarfi ne ya ke haɗuwa a cikin idanuwanmu, saurin sauke kaina ƙasa ƙirjina na luguden duka.

Zare jikina na yi na ja baya tare da tashi cikin rashin kwarin jiki, tashi na yi tare da zuwa wajenda aka ajiye waɗannan ledojin da baƙin jiya suka kawo jayan dubiya, raɗau nike ganin shatin yatsun wanda ya riƙe ledar na fitar da baƙin hayaƙi, sannan wani irin wari marar daɗi na tashi, gabana na faɗuwa haka na buɗe ledar ina leƙen abin da ke ciki, sai naga kayan fruit ne wasu duk sun ruɓe wasu kuma nunanun sai walƙiya suke da ɗaukar ido, waɗanda suka ruɓe kuma sai wari suke fitarwa tare da wannan baƙin hayaki, saurin ɗaukar ledar na yi na fitar da ita daga ɗakin, a bakin ƙofa na ajiye ta ina jin tsikar jikina na tashi, juyowa na yi na koma ɗakin sai naji yanzu yamin daidai, ajiyar zuciya na sauke sannan na shiga gyara ɗakin duk da ba wani datti yai ba, kuma yau da sauƙin ƙarnin ba kamar jiya ba, bayan na gama na koma wajen Fauzan ɗauke da ruwan magani wanda Phapha ya bani akan agoge ma shi jiki da shi, ruwa na haɗa masu sanyi sannan na ɗauki tsaftatacen towel fari ƙar na saka a cikin ruwan maganin, ba tare da na ce da shi komi ba na matsa kusa da shi na fara aikina, idonshi ƙur a kaina ya na kallona kamar wanda zai haddace kamanin fuskata, bayan na gama goge ma shi fuska da hannuwa na koma kan wuyanshi zuwa cikinshi, duk inda na ɗaura towel ɗin sai wajen ya kwalje amma banji komi ba haka na ci gaba sa goge ma shi jiki, yau ba kamar jiya ba dan yau ko ina sai da na goge ma shi a jikinshi da maganin sannan na na barbaɗa wanda na barbaɗa ma shi jiya, abin gwanin ban tausayi dan kuda fatar jikinshi ta saɓule tai jajir, ban gaji ba na sake kaɗa ma shi na sha, nai bisimilla tare da kaina saikin bakinshi, kamar me jira haka ya buɗe bakin na shiga zuba ma shi maganin, sai da ya shanye tas sannan ya lumshe ido, ina tsaka da tattare kayan wajen zan tashi naji ya riƙo hannuna da ƙarfi, kafin inyi wani yunƙuri tuni ya shiga kelaya amai kamar dai jiya, sai dai na yau harda jini da wani abu kamar saɓa, duk dauriyata sai da nai kuka dan ba kaɗanba ya bani tausayi, a hankali na dafa kafaɗarshi gudun kar in fama ma shi ƙunar na samu na kwantar da kanshi akan pillow sannan na zare hannuna ina jera ma shi sannu, lumshe ido kawai ya yi tare da sake min hannu, a hankali na tashi daga wajen tare da kwashe kayan sannan na gyara wajen tsaf, bayan na gama ne na koma gefe na rakuɓe nai shiru ina tunanin duniya da irin ƙalubalen da ke cikinta, haka wani kalar nannauyan barci yai gaba da ni.

Sarauniya Zubudiyya ce zaune akan bango ta na kallon dukanin abin da muke yi, yayinda tausayina da na Fauzan ya sake kamata, ita ɗin hallita ce me tsananin tausayi, sam bata son zalinci kuma bata shiri da duk wani me aikatashi, daga inda take ta na ganin inda Zuka yayi ajiya a jikin Fauzan, wanda hakan ke taimakawa wajen sake tsananta ciwon na shi, daga inda take zaune ta ziro hannu ta tattaro ajiyar kakaf, hakan yayi daidai da lokacinda na bashi maganin sha, shine ya amayar da sukanin ajiyar, sai ya ji wasai cikin cikinshi kamar an ɗauke ma shi wani nannauyan dutse, cikin sanyin da ta saka min ta huro ma shi iska wace ta saka shi barcin rahama da salama.


ABUJA NG.
MAITAMA.

Tsaye ya ke agaban makeken frem ɗin da ke ɗauke da hotunan kyawawan ƴan mata guda biyu masu tsananin kama, babbar ba zata wuce shekaru huɗu ba alokacin da akai hoton, ɗayar kuma jinjirace fara sol kyakkyawar gaske.
Idonshi na zubda ruwan hawaye ya ke kewaye daidai fuskar jinjirar ya na shafawa.

Wa ta kyakkyawar ma ta ce me kama da laraba ta shigo ɗakin inda mutumin ya ke, taɗan jima a bayanshi ta na kallonshi, fuskarta ɗauke da matsananciyar damuwa irin wacce tafi ƙarfin a bayyanata a baki, tabbas ta na cikin matsananciyar damuwa, amma hakan bai hana ta yi tawassali da Allah ba, domin tasan dukan abin da ya samu bawa to yana rubuce a jikin littafin ƙaddararsa, kuma babu me gujewa ƙaddara face ta biyo shi da mugun gudu, irin gudun da idan har ta cimma masa to kuwa sai ta Allah kawai, ita ɗin mahaifiyace kuma me rauni, akwai raunin da yakai a raɓa uwa da ƴarta tun bata gama tantance iskar duniya ba, akwai raunin da yakai a raba uwa da ƴarta lokacinda ta gama wahalar shayarwa da reno, ita tasan me rauni ce gaba da baya, amma batabawa zuciyarta damar raunana har ta kaita ga samun matsala ba, ta riga da ta dangana, ta bar komi a wajen Allah, mudin rana na fitowa ta na faɗuwa tasan wannan ranar za ta zo, ranar da duk wani ƙulli zai warware kansa da ƙarfin ƙudurar ubangiji, ko da bata raye tasan ta yi babban tanadin zuwan wannan ranar, abu ɗaya kawai take jira, shine wanzuwar ikon ubangiji ta hanyar bankaɗo duk wa ta ajiya da aka bizne a cikin baƙin duhu.

Cike da ƙwarin gwuiwa ta taka zuwa inda mutumin yake tsaye ya na ta faman sharɓar kuka tare da shafar fuskokin jikin photon.

"Bansan har zuwa yaushe gwarzon jarumina zai yi tawassali da ƙadararda ta daɗe da yanke wannan damɓarariyar ƙaunarba, ha isa hakan, ya isa!! yanzu ba lokacin yin kuka ko nuna damuwa bane akan zarenda ƙaddara ta daɗe da yankewa ba, yanzu lokacin farin ciki ne da nuna godiya ga Allah da akan manya-manyan kyaututtukan da ya bamu, zo muje muyi tafiyar da za ta sada mu da farin ciki madawwani wanda bazai yanke ba da izinin Ubangiji."
Ta ƙarashe maganar ta na janyo hannuwanshi duka biyu kamar ƙaramin yaro me koyon tafiya, haka ta dinga janshi ta na tafiya da baya-baya harta cimma ƙofar wani ɗaki, buɗe ƙofar ta yi da ƙafarta sannan ta shiga har lokacin bata saki hannuwanshi ba, a gaban baby bed guda biyu ta tsaya tare da dafo kafaɗunshi ta juyar da fuskarshi ta na faɗin.

"Yanzu lokacin farin ciki da godiyar Allah ne da ya azurta mu da wannan gagarumar kyautar wacce muka daɗe muna jira, ga makwafin yaranmu da muka rasa Allah ya dawo manah da su, MUBARAKA da MARYAM sun dawo gare mu, kallah!!! kallafa!, kalesu Alhaji."

Ta yi maganar ta na ɗago da jariran yaran ɗaya bayan ɗaya ta na nuna ma shi, fuskarta faɗaɗe da yalwatacen farin ciki, wanda ya kasance na gidoya ga Allah da ya ake azurtata da ƴaƴa mata waɗanda ta ke fatan su kasance ma ta sanyin idaniya, kuma su mamaye wawakeken ramin da ke zuciyarta na rashin ƴaƴanta da ta yi, waɗanda ba mutuwa sukai ba, kawai ƙaddarace da jarabawa ta Ubangiji ta nesanta tsakaninsu.
LITTAFIN ZAFIN WUTA🔥🔥🔥 PAID BOOK NE, ZA KI BIYA 500 KACAL DOMIN KI MALLAKI NAKI.

9136291920
MARYAM UMAR
OPAY

TAKU HAR KULLUM ME SON GANIN FARIN CIKINKU.
MARYAM STAR⭐⭐⭐ KE MUKU FATAN ALKIRI🙏🙏🙏.

🔥𝐙𝐀𝐅𝐈𝐍 𝐖𝐔𝐓𝐀🔥

LABARI ME CIKE DA

BAN TAUSAYI,😩MATSANANCIYAR DAMUWA,😭
KUNCIN CUZIYA,💔
SADAUKARWA,💌
ZAZZAFAR SOYAYYA ME TSAYAWA A RUHI.💋💘


WRITING BY
MARYAM STAR ⭐⭐
YAR BAIWAR JJRT.


MARUBUCIYAR📒✍️
RAYUWAR SAMHAD
DAFIN MACIJI
A DAREN AURENA
AND NOW
ZAFIN WUTA🔥


💪 *JAJIRTATTU WRITER'S ASSOCIATION*💪 ✍️
*(J.W.A)*

🦚🦋THE NOBLE WRITER'S TEAM🦋🦚


PAID BOOK 500 ONLY👌
BOOK TWO
CHARTER 10
بسم الله الرحمن الرحيم

Durƙushewa ya yi akan gwuiyoyinsa, yayinda kuka da dariya suka haɗe ma sa lokaci ɗaya, sai kuma yakai hannayensa cikin bed ɗin ya tattaro yaran waɗanda keta sharar barci abinsu, ya haɗa su a ƙirjinsa ya rungume kamar wani zai ƙwace ma shi su, sai kuma ya shiga jero addu'o'i ya na tofesu, sannan ya shiga sumbatarsu kamar zai cinye su, bai tsagaita ba sai da ɗaya ya motsa ta na yamutse fuska kamar za ta yi kuka, sai ya yi saurin mayarda su ya kwantar shi kuma ya kwanta akan lallausan carpet ɗin da ke shimfiɗe a ƙasa ya na sakin ajiyar zuciya a jere kamar wanda ya kubto daga hannun abin cutarwa.

Alhaji Umar kenan, shararen gogagen ɗan kasuwa wanda manya-manyan ƴan kasuwa, gwamnati da al'umaa ke ji da shi, Alhaji Umar sanannen mutumne wanda tauraruwarsa ke haskawa da tsananin haske, haskenda ke tattare a cikin tarin ƙaddarorin da ya shallake kafin haskakuwarshi a sararin samaniyar duniyar kasuwanci, Alhaji Umar mutum ne wanda rayuwarshi ke cike da tari ƙaddararo mabanbanta, tun tasowarshi ƙaddara ke walagigi d rayuwarsa, amma bai sare ba wajen yin tawassali da kuma rungumar ƙaddarar a duk sa'ilin da ta dumfaro rayuwarshi, yakan tsaya tsayin daka wajen ƙasƙantar da kanshi a wajen Mahalicci me kowa kuma me komi, wanda ke aika dukkan abin da ya so ba tare da shamaki ba, manzon Allah ya yi gaskiya da ya ce a cikin wani hadisi, "Allah ya na son bawa me tsoronshi, me wadata".
Tsoron Allah da kuma ƙarfin iymani irinna Alhaji Umar sune suka taimaka ma shi wajen samun ɗaukaka a duniya, Allah ya azurtashi da tarin dukiya wacce shi kanshi bai san iya adadinta ba, sannan kuma Allah ya albarkace shi da farin jini a cikin mutane.

Ƙaddara ɗaya ce Alhaji Umar ya kasa haƙuri da dangana da ita, wacce ta ke neman zautar da shi, ya rasa ƴaƴansa mata har karo biyu, ba rasuwa sukai ba rasa su ya yi ta hanyar son zuciya da kwadayi irin na makusantanshi.

A hankali Hajiya Sadiya ta dire tray ɗin da ta ɗauko goran ruwa gami da cup a ƙasa, sai kuma ta buɗe wa ta ƴar jaka ta ɗauko kwalin magunguna guda biyu, ta buɗe tare da ballawa ta saka a cup ɗin, haka sauran suma ta saka a cikin cup ɗin sannan ta zuba ruka kaɗan ta dama kamar yanda ake bawa yara magani, bayan ta gama ta aje a gefe tare da gyara zamanta ta ɗauki kan Alhaji Umar ta ɗaura akan cinyarta tare da share ma shi hawayen da ke ta faman silalowa daga kwarmin idonshi, a hankali ta janyo cup ɗin tare da bisimilla sannan ta kafashi akan busashen bakinshi wanda laɓɓan suka bushe kamar wanda yai sati ɗaya ya na tafiya ba tare da ya sha ruwa ba, buɗe bakin ya yi ta juye ma shi maganin ya shanye tas, sannan ta kora mashi da ruwa me rangwamen sanyi ta gyara ma shi kwanciya akan cinyarta ta na shafa sumar kanshi a hankali, sai da ta tabbatar da barci me nauyi ya yi awon gaba da shi, sannan ta ja shi da ƙarfin zuciyarta ta ɗaura shi akan makeken bed ɗin da ke ɗakin ta gyara ma shi kanciya sannan ta fice daga ɗakin.

Wajen photon ta je ta tsaya ita ma ta na kuka me ciwo ta na shafa fuskokin yaran ta na sambatu, ta jima a wajen ta na kuka kamin daga bisani ta rarrashi kanta ta tashi ta koma wajen ƴaƴanta da ke kuka ta rarrashe su tare da shayar da su, kwantar da su ta yi a tsakanin ita da mijinta Alhaji Umar, ta jima a kwance ta na tunanin rayuwa, kafin daga bisani barci me nauyi ya yi awon gaba da ita.

A cikin barcinta ta yi mafarki kamar yanda ta saba aduk lokacin da takai kafaɗarta ƙasa da sunan yin barci, yauma kamar kullum.
Zaune suke a waje ɗaya, cikin wani faffaɗan fili me yalwar bishiyu da ciyayi, fuskokinsu na kallon juna a zahiri, amma a baɗini ba junansu suke kalloba ko wacensu na kallon wani abu daban, su na matuƙar kama da junansu sosai, sai de ɗaya ta kasance fara tas ɗayar kuma me matsakaicin haske, amma baza'a kirata da baƙa ba ko wankan tarwaɗa saboda tana da haske dande ba can sosaiba, Yau kuma ba kamar yanda ta saba ganinsu su kaɗai ba, yau su biyu ne sannan kuma mazaje guda biyu na gefen kowace.

Da Salati ta farka kamar kullum idan ta yi mafarki, sosai yau zuciyarta ta tsinke da lamarin, sai ta ji yau kaɗai ta na so ta tattauna lamarin da wani, to amma kuma wani wah, waye zai dubeta da idon basira ya fuskanci abin da ta ke nufi ba tare da ya yi ma ta kallon mahaukaciya ba, amma kuma ya dace a duba lamarinan gaskiya, wannan mafarkin ta jima ta na yinshi tun shekarun baya, kuma kullum duniya ta kwanta barci sai ta yi mafarkin, ya kamata ace tasan mi wannan mafarkin nata ya ke nufi.

Ita kaɗai ta ci gaba da zancen zucin, ta na lalubawa kanta mafita, kamin daga bisani ta tsaida tunani da nazarin wacce ta dace da tayi shawara da ita, tasan za ta fuskanceta kuma ta fahimceta, ba kowa ba ce face ƴar uwarta Asma'u.


LEGOS.
MUBEENAH.

Yau satina biyu cif a gidan Alhaji Abdallah me gwalagwala, na murje na yi ɓulɓul abina na ƙara zama cikakkiyar budurwa duda kasancewata me ƙaramim jiki da siranta, haske da sheƙin fatata ya sake daɗuwa, ni kaina nakan zauna ina taɓa fatata ina jin daɗin yanda tai laushi gwanin kyau, baƙin gashin kaina wanda daƙyar Mama ke gyara min shi dan sam bana son kitso, yanzu ya sake linka tsayi da baƙi saboda musamman Sulaima ke ware lokaci duk bayan kwana biyu ta gyara min shi tsab, haka nike fitowa kamar budurwar ba'indiya irin masu tashen kyawunan, yanzu kullum zaka same ni cikin ado da kwalliya, ga ƙamshin tsadadun turaruka wanda Pahpah da kanshi ya bani kyautarsu, sannan yanzu na yi wani irin sabo da ƴan gidan, na saki jikina da su sosai, su kuma kullum cikin yaba min suke da godiya akan yanda nike jajircewa akan Fauzan, wanda yanzu jikin na shi yai sauƙi sosai, wannan zafin jikin duk babu shi, kasancewar an canza mashi ɗaki yanzu, da wannan damar na yi amfani wajen saka matakin tsaro daga dukanin abin cutarwa mutum ko aljan, ƙira'a nike sakawa cikin ƙaramin sauti a makeken plasma da aka jingine a bangon ɗaki, sannan da lokacin azkar ya yi da kaina nike canza channel, hakan ya taka rawa sosai wajen dawo da hankalin su Mommy suma suka shiga neman kariyar jiki da neman tsari daga dukkanin abin halitta, duk maricen duniya zaka same su a ɗakin Fauzan su na bin ƙira'ar azkar ɗin da ake yi a Sunnah TV, haka za ka ga kowa ya zauna yana bin ƙira'ar cikin ƙaramin sauti, hatta Pahpah yakan zauna idan ya na gida shima ayi da shi, bayan angama kuma abawa ƴan aiki umurnin cike wajen da kayan ciye-ciye mu zauna ana fira ana ciye-ciye abin gwanin burgewa.

A duk lokacin da na tsinci kaina cikin farin ciki nakan tuno rayuwata ta baya wacce da ni da dabba bamu da bancin, haƙiƙa na yi rayuwa me cike da rashin ƴanci, kyara da rashin samun sakewa a cikin gidanmu, a rayuwata ta baya babu ranar da za ta zo ta wuce ba tare da Abba ya lakaɗa min shege duka ba, sannan ya bini da mugayen kalamai masu kama da ZAFIN WUTA, bani da iko da kaina sai abin da aka gindayamin, ba ni sa zaɓin kaina sai wanda aka zaɓamin, a wajen mutum ɗaya nike samun rangwame har in samu rarrashi da tarairayar da na rasa samu a wajen mahaifina ita ce Mama ita kaɗai ce ke nuna min zallar soyayya wacce babu surki, takan zauna da ni domin ta ji matsalata, takan tayani ɓakin ciki ko damuwa idan wani abu ya same ni, shi yasa har gobe na kasa cire tunaninta, kasa mancewa da ita, kullum sai na yi hawayen kewarta.

A hankali na saukar da kaina daga kallon jikin miron da nike, cikin nutsuwa na sagala mayafin kayan da na saka, sannan na zira takalmina ina sake daidaita fuskata na fice.

Har yanzu na kasa sabawa da bugun zuciyarda nike tsintar kaina aduk lokacin da na tunkari ɗakin Fauzan, abu ɗaya ne na kasa sabawa da shi tun zuwana gidan shine, kaifafa idanuwan Fauzan bana sakewa idan ya kafe ni da su ya na kallona, shikuma muddin idanuwansa biyu to ya dinga kallona kenan kamar sabon maye, yanzu haka da nike ƙoƙarin shiga ɗakin sai da naɗanyi jimmm a bakin ƙofar tare da ɗaure fuska sannan na yi sallama cikin ƙaramin sauti na tura kaina cikin ɗakin.

Tun sanda na tsaya jikin ƙofar ƙamshin turarena ya riga ni shigowa ɗakin, da sauri ya buɗe idanuwanshi ya na jiran ƙarasowata, da yake yau tun safe da na bashi magani ban sake bi takanshi ba sai yanzu d nasan kowa na gidan na daf da hallara dan mu zauna kamar yanda muka saba dan gudanar da azkar.

Daddaɗar sautin muryata ne ya ratsa can cikin ƙoƙon kan majiyar sautin kunnuwansa, a hankali ya sauke nannauyan ajiyar zuciya, wata iriyar kewar sanyin jikina na baibayeshi, sanyin da ke tattare da ni wanda ke samar ma shi da nutsuwa na mamaye ɗakin.

Kamar kullum wai ma bai amsa sallamar a fili ba, amma naga lokacin da jajayen laɓɓansa suka yi motsi kaɗan, da sauri na sauke kaina ƙasa tare da ƙarasawa wajen shi, ba tare da na kalleshi ba na hau haɗa ma shi maganin marice, bayan na gama na gyara zamana tare da fuskantar inda ya ke kwance amma fuskata na kallon gefe, na wani maze sannan na ce.

"Magana nike so inyi da kai, amma dan hasken musulinci ka daina kallona hakanan, idan kana kallona bazan iya faɗin abin da nike so imfaɗi ba."
Nai maganar ina cuɗanya ƴan yatsuna, amma koda kuskure ban kalli inda yake ba.

"Ki na da kyau me fizgar hankali, bazan iya janye idanuwana akan ki ba muddin zamu kasance waje ɗaya, kallonki na rage min zugi da raɗaɗin ZAFIN WUTAR da bai gama hucewa a jikina ba, please ki yarjemin kallonki a koda yaushe."

Yai maganar cikin salon da ke saka ni jin wani abu ya tsarga tun daga tafin ƙafata har zuwa ƙoƙon kaina, mazewa na yi na daure na hana idanuwa da ke ƙoƙarin bani kunya akan satar kallonshi, sannan na ce.

"Ban san iya adadin watannin daka shafe a kwance cikin halin ciwo ba, amma kai nasan za ka iya tuna lokacin, ina so in tunatar da kai yanzu Alhamdulillah ka samu sauƙi sosai, sai nike ganin ya kamata ace ka fara ramakon sallolin da aka biyoka, ba dole sai ka yi kamar yanda ka saba yi abaya ba, zaka iya yi a kwance ta hanyar ayyanawa a zuciyarka, sai kaga sanadiyar sallar Allah ya sake baka lafiya mawadaciya."

Tun da na fara magana ya kafe ɗan mitsitsin bakina da kaifafan idanuwansa, ya na kallon yanda nike zaro magana cikin amon da ke saukar ma shi da kasala, da wani yanayi me wuyar fassarawa.
Bai ce komi ba amma na jiyo sautin fitar murmushinshi, sai na tsinci kaina da jin haushin shirun da ya yi min, dan harga Allah da wannan kallo da yake min gwara ya dinga yimin magana, saboda ina jin daɗin amon muryarsa, sannan ina tsintar kaina cikin matsanancin farin ciki aduk lokacinda ya yi min magana.
🔥𝐙𝐀𝐅𝐈𝐍 𝐖𝐔𝐓𝐀🔥

LABARI ME CIKE DA

BAN TAUSAYI,😩MATSANANCIYAR DAMUWA,😭
KUNCIN CUZIYA,💔
SADAUKARWA,💌
ZAZZAFAR SOYAYYA ME TSAYAWA A RUHI.💋💘


WRITING BY
MARYAM STAR ⭐⭐
YAR BAIWAR JJRT.


MARUBUCIYAR📒✍️
RAYUWAR SAMHAD
DAFIN MACIJI
A DAREN AURENA
AND NOW
ZAFIN WUTA🔥


💪 *JAJIRTATTU WRITER'S ASSOCIATION*💪 ✍️
*(J.W.A)*

🦚🦋THE NOBLE WRITER'S TEAM🦋🦚


PAID BOOK 500 ONLY👌
BOOK TWO
Chapter 9 · 0% Book details