← Book details Rijiya Gaba Dubu Part 2 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 3 OF 6

Sashe 3

Rijiya Gaba Dubu Part 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read

TO JAMA'A ZAN CIGABA IDAN NA HUTA
RIJIYA GABA DUBU2 CIGABA 6
Al'amarin su marwatu kuwa,wadan da suka hawo wani jirgin tare da mugayen karnuka kimanin guda arba'in sai suka nemi jirgin su Imhal suka rasa a cikin tekun domin ya bace musu sakamakon iskar da ta ie kadawa mai karfin gaske ce gami da hazon da ake yi mai duhun gaske,amma sai suka cigaba da tuka jirgin nasu a haka,sai da suka kwana uku suna tafiya a cikin teku sannan suka iso bakin gaba a wata sakaliyar safiya,ai kuwa suna isowa suka yi kicibis da jrgin su Imhal a gefen tekun,cikin hanzari murwatu yasa aka saki wadan nan karnuka suka ruga izuwa cikin jirgin Imhal suna nemansa suna shinshine-shinshine,A lokacin ne murwatu da dakarunsa suka iso gaban jirgin suka caje cikinsa kaf amma basu ga Imhal ba sai alamar jinin zauwadu da ya zuba a kasa wanda har ya bushe,Kawai sai marwatu ya dago kai ya dubi dakarunsa yace Duk yanda akayi Imhal yana nan cikin dajin nan bai yi nisa ba amma abokinsa zauwadu ya mutu domin babu mutumin da zai zubar da jini mai yawa haka ya rayu,yanzuzamu bazama cikin wannan daji duk inda Imhal yake sai mun riske shi mun kashe shi,sai na cire kansa na tafi dashi izuwa darul maut domin sauran fursunonin gaba daya su gani ya zama gargadi a gare su don kada wani yace zai kara yunkurin gudu anan gaba,kuma nasan cewa sai sarki Gurzalu ya daukaka ni ya bani dukiya mai yawan gaske sakamakon wannan gagarumin aiki da zanyi kai inda hali ma a araye nake so na kamo Imhal domin na mayar dashi cikin darul maut mu sake tsare shi sabo da sarki ya fi son su sake haduwa a gasar jarumtaka wacce za ayi a birnin misra nan da cikar kwana goma sha daya,maza ku saki karnukan nan subi sawun Imhal domin suna iya jin kamshin mutum komai tazarar da ya basu kuma suna da karfin gudun da bai isa ya tsere musu ba.Koda jin wannan umarni sai dakarun dake rike da karnukan suka sake su suka sake rugawa izuwa cikin dajin suna masu haushi da falfala azababben gudu su marwatu suka bi bayan karnukan da gudu.Marwatu na cikin yin gudu sai raunin da ke gefen cikinsa ya motsa yaji wani azababben zafi da zugi ya shige shi,bai san sanda ya fadi a kasa ba,nan da na dakaru suka yanyame shi,koda ya kwaye rigarsa sai yaga ashe dinkin raunin ne ya farke,cikin tsananin takaici marwatu ya kwarara uban ihu ya dubi dakarun yace Maza ku tafi farautar Imhal kada ku dawo nan sai tare dashi,nan take kuwa suka bi bayan karnukansu da gudu shi kuwa marwatu sai ya bude jakar guzurinsa ya dauko zare da allura gami da garin magani domin ya sake gyara rauninsa.

Al,amarin Imhal kuwa,a ranar da jirgin ya kawo shi gabar teku sai ya dauko gawar zauwadu ya fito da ita daga cikin jirgin ya nausa da ita izuwa cikin daji,sai da yayi tafiya mai nisa ya iso gaban wani katon dutse sannan ya sauke gawar ya haka kabari ya binne ta.A sannan ne ya kurawa kabarin idanu yana tuno duk abubuwan da suka faru a baya tsakaninsa da zauwadu a cikin darul maut,kawai sai hawaye ya fara zubo masa,yana cikin wannan hali ne ya jiyo sautin haushin karnukan nan na darul maut,da yake yasan irin haushin nasu kuma ya san tsananin gudunsu da irin mugun horon da aka basu sai hankalinsa ya dugunzuma ainun,kawai sai ya mike tsaye zumbur! ya falfala da azababben gudu izuwa cikin dajin.

Imhal ya dage iya karfinsa da iyawarsa har yana tashi sama yana shallake duwatsu da karyayyun bishiyoyi da suka fadi kasa amma koda ya waigo sai ya hango wadan nan karnukan suna neman cimmasa sai kawai ya kara kaimin gudun,Ba zato ba tsammani sai yaga wani katon rami mai tsananin zurfi a gabansa,kafin ya iya sarrafa kansa ya cije sai karfin gudun nasa ya rinjaye shi ya fada cikin ramin yana mai kurma uban ihu.

TO AYI MIN AFUWA IDAN NA HUTA ZAN CIGABA
RIJIYA GABA DUBU2 CIGABA 7
Sa'ar da yayi kawai kawai kasan ramin cibiya ce ta ruwan teku amma yana tsunduma a cikin ruwan sai kansa ya bugu da wani dutse ya sume.

Su kuwa karnukan suna isowa bakin ramin sukayi tirjiya suka fara haushi,sautin haushin nasu ya cika dajin gaba daya,wanda hakan ne ya janyo hankalin dakarun Marwatu suka rugo sashin da suke jin haushin cikin matsanancin gudu,suna cikin gudun ne suka hango karnukan sun kewaye wani rami suna ta haushi,don haka suka kara azama don nufar inda ramin yake.

Lokacin da dakarun marwatu suka iso bakin ramin wanda Imhal ya fada sai suka iske karnuka a tsaye a wajen suna ta haushi sai suka leka kasan ramin,ai kuwa sai suka hango Imhal a kwance akan ruwa kuma ruwan yana tafiya dashi ko motsi bayayi kamar gawa.

Cikin gaggawa wasu daga cikinsu suka gangara kasan ramin suka shiga cikin ruwan suka tsamo Imhal,suna fitowa dashi sai suka ga yana numfashi don haka sai suka yi sauri suka turmushe shi suka daure hannayensa da kafafunsa da sarkoki sabo da sun san cewa in har ya farfado baza su iya kamashi ba.

Nan take suka daure shi suka kai shi can inda Marwatu yake zaune,da zuwan su suka iske Marwatu a kishingide ya gama dinke raunin dake cikinsa ya saka magani,koda Marwatu yaga dakarunsa sun dawo dauke da Imhal a daure cikin sarka sai ya kamu da tsananin farin ciki mara misaltuwa ya mike tsaye zumbur!ya kwarara uban ihu irin wanda manyan barade ke yi afilin yaki yayinda suka samu nasara akan abokin gabar su,kawai sai yasa aka warbar da Imhal gefe daya a kasa aka kyale shi har sai da ya farfado daga suman da yayi.

Koda Imhal ya bude idon sa yayi arbuna da marwatu zaune a gabansa yana yi masa murmushin mugunta sai hankalinsa ya dugunzuma ainun ya yunkura da nufin ya gudu amma sai ya kasa sakamakon sarkokin da suka daure kafafuwansa da hannayensa
AYIMIN AFUWA ZAN CIGABA
TO AYIMIN AFUWA ZA CIGABA IDAN NA HUTA
RIJIYA GABA DUBU2 CIGABA8
Nan take yaji wani irin bakin ciki ya lullube shi,ya ayyana a ransa cewar da ma ya mutu a kokarin wannan guduwa da yayi daga kurkukun Darul maut da ya fiye masa alheri.

Kawai sai yaji marwatu ya bushe da dariyar mugunta yana mai nuna shi da yatsa,daga can sai marwatu ya fara yiwa kansa kirari yana cewa Nine sa gudu maganin ki gudu,kuma nine sarkin darul maut mai RIJIYA GABA DUBU,ya kai wannan takadarin jarumi,kayi Sani cewa inda ba muyi nasarar kamoka ba da sai Na kashe kaina sabo da Kaine kadai jarumin da ya karya alkadarina,ya sami nasarar guduwa daga kurkukun darul maut Wanda Na shafe shekara da shekaru INA gadinsa,ban taba samun rauni ba a rayuwata sai wannan karon don haka idan muka koma darul maut sai Na dandana maka azabar da bantaba dandanawa wani fursuna ba sai Na shigar da kai RIJIYA ta azaba mai GABA DUBU.Koda gama fadin haka sai marwatu ya mike tsaye yaje inda jarumi Imhal yake zaune ya shammace shi ya gabza masa wawan naushi a fuska ,nan take Imhal ya sulale a kasa sumamme.
lokacin da Imhal ya farfado sai ya tsinci kansa a cikin jirgin ruwa ga marwatu da dakarunsa sun kewaye shi,yana daga kansa sama ya dubi gabas sai ya hango kurkukun Darul maut a nesa da su kadan,jirgin Na tafiya acikin teku,al'amarin da ya jefa Imhal acikin bakin ciki kenan a cikin zuciyarsa yace Yanzu mene ne amfanin wannan yunkurin guduwar da nayi?wai shin menene dalilin da yasa bai kashe kansa ba ya huta da wannan bakin ciki?yana cikin wannan tunanin zuci ne jirgin nasu ya I so kofar kurkukun Darul maut,nan take aka tsaida jirgi ya tsaya cak! sannan dakaru suka kama Imhal suka tashe shi tsaye aka fitar dashi daga cikin jirgin ,shi kuwa marwatu bai fita daga cikin jirgin ruwan ba sai ya dubi dakarun da suke rike da Imhal yace dasu Kada Ku kaishi bangaren dakin fursunoni Ku kaishi dakin RIJIYA GABA DUBU Ku daure shi a jikin bango da sarkoki Ku barshi a haka,kuma kada a bashi ruwa ko abinci har sai Na dawo,
Zanci GABA in Na huta
RIJIYA GABA DUBU2 CIGABA9
Na tafi gidan Sarki domin inyi masa albishir bisa nasarar kamo Imhal da mukayi,koda gama fadin haka sai marwatu ya juya ya umarci masu tukin jirgin da su juya akalar jirgin su nufi cikin gari,ba tare da gardamar komai ba kuwa suka bi umarninsa suka juya jirgin suka kama hanya akan ruwa.

Su kuwa dakaru sai suka shigar da jarumi Imhal cikin kurkukun,suna shigewa aka mai da kofar Gidan aka rufe,tayi kara mai karfi tamkar an kulle kofar birnin gaba daya,yayin da aka zo wucewa da jarumi Imhal ta bangaren dakunan fursunoni suka kyalla I do suka hango shi sai suka kama ihu da shewa suna yi masa tafi da jinjina sabo da kasancewarshi fursuna Na farko da ya taba samun nasarar guduwa kuma ya tsira da rayuwarsa.Koda fursunoni suka ga an nufi dakin RIJIYA GABA DUBU da Imhal sai gaba dayan su jikin su yayi sanyi suka kamu da tsananin tausayinsa,ba komaine ya haddasa hakan ba face sanin cewar duk mutumin da aka shigar dashi cikin
ayya frnds ayimin afuwa wlh fefar littafin ta tsakiya banganta ba amma bari nayi wani postn din Na cigaba yanzu
RIJIYA GABA DUBU2 CIGABA 11
Koda Imhal yazo nan a zancensa sa aljani Sautil makatur ya bushe da dariyar mugunta a karo Na biyu yace, Sai kayi kokari ka fita daga nan din cikin hayyacinka yadda zaka iya bude idanunka ka kalli maharbi Imzanu.
Chapter 3 · 0% Book details