Sashe 19
Matar Shege Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Sai ta d'akko hijjabi ta saka ta ce na ce su shigo ciki kawai. Su ka shigo,amma banda Baby da ta zauna a motar,bayan sun gaisa Abba ya tsara mata yanda komai ya faru,sannan ya shaida mata yanzu wani nasu ya shirya aje asibitin tare.
Anti Na'ima ta dinga jera salati babu k'akk'autawa,sannan ta fara k'walla ta ce"wallahi Alhaji aurenta saura sati biyu,ashe ita yarinyar nan shirin ta da ban!"
Abba ya jinjina kai ya ce"duk abar maganar,aje asibitin kawai".
Anti ta ce ta na zuwa,ta shiga d'aki.Ba ta jima ba ta fito,ta mik'o min wayata,tana min wata kafirar harara, mu ka tafi. Hanyar asibitin Aminu Kano muka d'auka,Anti ta ce gwara aje Nasarawa akwai likitoci mata ta wannan fannin,Salim ya juya kan motar muka yi Nasarawa,ni dai gabana sai fad'uwa ya ke yi,shi kuwa Salim ban san abin da yake ransa ba.
Muka shiga asibitin,Anti ta ce ta san b'angaren da ya kamata mu je,kamar an san da zuwanmu mu na zuwa aka nuna mana inda za mu shiga,Anti ce ta yiwa wata nurse bayani a tak'aice,sai aka yankan min kati,babu jimawa aka nuna min d'akin da zan shiga a dubani.
K'irjina fa ya tsananta bugu,na dinga taku d'aya bayan d'aya kamar wahainiya,fargaba fal raina
Da na shiga d'akin kusan fad'uwa na yi,saboda wani tuntub'en bazata da na yi,sakamakon ganin Habib sanye cikin uniform d'insa na asibiti,ya hard'e hannu a k'irji,fuskar nan babu walwala,shi kad'ai ne a d'akin,da alama dai shi ne likitan da zai duba ni.
*MATAR SHIGE...!*
_(Ba ta daraja)_
BY
*SADIYA ABDUL*
_(Maizafafa)_
*☀️FIRST CLASS WRITER'S ASSOCIATION☀️*
Page 19
*Ni fa na san so,kuma na yarda k'addara ne.Don haka ina team d'in Zinatu,idan kuna zaginta Allah zan tafi hutun typing na sati biyu,kafin nan zuciyarku ta yi sanyi,sai mu d'ora😉*
Habib ya yi min wani firgitaccen kallo,da alama dai bai tsammaci gani na ba.Ni kuwa kusan mutuwar tsaye na yi,ganin wannan tonon sililin da ya tunkaro ni,ko kuma na ce na jefa kaina a ciki,amma sosai na yi mamakin ganin shi a b'angaren,don a iya sani na Habib likitan ido ne,to me zai kawo shi nan b'angaren? Ban gama raba d'ayan biyu ba na ji muryarsa
"Zinatu! Kar dai ki fad'a min ke ce wadda za a duba yanzu!" Ya yi maganar ya na k'ank'ance ido da alamun b'acin rai.
Na ji wata kunyarsa ta rufto min,na kasa magana,kawai sai na fara zub da hawaye ba tare da na shiya ba. Ya yi huci me zafi ya nemi kujera ya zauna,sannan ya d'akko wayarsa a aljihu ya yi danne-danne ya kara a kunne
Na yi shiru ina sauraron wayar tashi,ban san da wanda yake wayar ba,na dai ji ya na cewa"ka ga doctor, ka k'arasa a tsanake,ni ma na ari office d'in naka na y'an mintuna,idan na kammala zan kira ka".
Ya ajiye wayar ya kalle ni fuskar nan murtuk kamar ba shi ba ya ce"maganar fyad'en da ake tantama a kansa,ina so ki fad'a min gaskiya anyi miki,ko ba a yi miki ba?"
Na yi shiru,kaina a k'asa.Ya buga teburin da k'arfi ya ce"ke! Ina tamabayarki ne fa as your doctor, ba Habibun da kika sani ba,ki d'auka ban ma tab'a ganin ki ba sai yau,saboda haka idan kin shirya ganin likita sai ki bud'e bakinki,idan ba ki shirya ba ki fice min daga office!"
Na d'ago na kalle shi, sai na ga tabbas wannan ba Habib d'ina bane,da gaske ya ke yau a gaban doctor Habib nake,sai na saka a raina ban san shi ba d'in,don haka na ce"ni ma ban sani ba".
"Kamar ya ba ki sani ba? Shekarunki nawa?" Ya tambaye ni,idonsa a kaina
"Ashirin" Na ba shi amsa.
Ya ce"ko y'ar shekara biyar aka yi mata fyad'e dole ta sani,bare ke da kin isa zaman aure! Ki na kokwanton anyi miki fyad'e,ta ya ki ka tsaida wanda kike zargi?"
Na lura dai da gaske Habib ya ke son k'ure ni,gwara ni ma na dawo masa Zinatu,don ya na shirin canza min suna da wata banzar barazanar sa,wai shi likita!
Na had'e rai na gyara zama na ce"kafin na shigo wurin nan ce min aka yi likita zai duba ni,ba lauya ba,kuma a zatona da doctor Habib na ke magana,ba barrister Habib ba".
"E hakane,amma wannan tambayar duka cikin aikina ne". Ya fad'a ya na had'e gira.
Na ce"tunda ka ga har sun kawo ni nan,ai ka san an zo gab'ar raba gardama kenan.Idan za ka duba ni bismillah kawai". Na k'arasa maganar zuciyata na bugu,don ina fargaba da takaicin wani gardi ya ga tsaraicina,musamman ma Habib d'in,wannan rashin darajar ina zan kai shi? Amma a fili ba za ka tab'a kawo haka nake tunani a raina ba.
Ya yi shiru ya na kallo na,tsawon sakanni,sannan ya jinjina kai ya ce" bismillah! Ga gado can je ki hau".
Gabana ya fad'i,duk da har yanzu zuciyata ba ta amince da zai iya duba ni d'in ba,ban nuna ba na dake na tashi na yi inda gadon ya ke,sai dai zama na yi ba kwanciya ba
Na d'an jima da zama,har na fara k'aguwa sannan ya k'araso wurin,ya janyo kujera ya zauna ya fuskance ni,ni kuma na sunkuyar da kai, don ba na son ya kalli k'wayar idona.
Tun kafin ya fara magana wani likita ya shigo,wanda na ke kyautata zaton shi ne me office d'in.
"Doctor ka kammala?" Ya tambaye shi,idonsa a kaina
Habib ya yi wani huci ya dafe kansa da duka hannayensa biyu.
Likitan ya janyo wata kujerar ya zauna a kusa da shi,ya ce"na fa kasa fahimta,a iya sani na ba ka harka da mata,wacece wannan?"
Kamar ba zai ba shi amsa ba,sai can ya ce"ita ce Zinatu".
Ko idona ne oho! Sai na ga kamar lokaci d'aya yanayin likitan ya canza,zuwa ga b'acin rai,ya yi min wani kallon da na kasa fassra shi a lokacin,sai daga baya,sannan ya kalli Habib ya ce"to me ya kawo ta nan d'in?"
Habib ya tashi ya je kan teburin ya d'akko masa takarda ya ba shi.Ko me aka rubuta a takarda tawa oho! Na dai ga ya kalle ni da sauri,kuma da alamun b'acin rai
Ya kalli Habib ya ce"yanzu ka duba ta d'in?"
Ya girgiza masa kai alamar a'a.Sai ya ce"ok,ka je kawai zan saita komai".
Habib ya yi masa wani kallo me wuyar fassrawa ya ce"kai! Matar da zan aura d'in za ka duba!?"
"Ai cikin aikina ne" Ya ba shi amsa ya na d'age kafad'a.
Habib ya kalle ni ya ce"ke tashi ki fita! Sai dai ku canza wani asibitin wallahi,ta ya wanda na sani zai duba min mata?"
Likitan ya dafa kafad'arsa ya ce"ok! Na fahimce ka Habib,amma ka sani ko wani asibitin aka kai ta ba ka da tabbacin mace ce za ta duba ta.Na yi maka alk'awarin ba zan duba ta ba,zan lallab'a ta ta sanar da ni gaskiya".
Habib ya yi shiru kamar me nazari. "Ka yarda da ni abokina,ka je d'in".
Habib ya kalle ni,sannan ya maida facemask d'insa ya fice.Na sauke ajiyar zuciya a b'oye,har yanzu zaune nake a bakin gadon
Likitan ya kalle ni da kyau ya ce" ke anyi miki fyd'en ko ba a miki ba?"
"Ni ma na kasa tantancewa fa" Na fad'a, ina juyar da kai gefe
Sai ya tab'e baki ya ce"yanzu ya kike jin jikinki?"
Na ce"ya na yi min ciwo kad'an,sai bacci da nake ji".
"Tun yaushe abun ya faru?"
"Jiya da daddare" Na ba shi amsa.
"Waye wanda ake zargi" Ya tambaye ni.
"Wani ne" Na fad'a
Ya ce"ko Salim da na gani a waje?"
"Shi" Na fad'a a tak'aice.
Ya ce"ok! To yanzu zan canza miki d'aki,sai na saka miki drip,idan ya k'are za a sallame ki".
Ina shirin yin magana ya tashi,ya na cewa na biyo shi.
Ba ni da zab'in da ya wuce bin umarnin shi.Zazzaune muka tadda su Abba,da alama har sun k'osa da jira,na tsaya daga d'an nesa,yayinda likitan ya k'arasa wurin su,Abba ya tashi da sauri ya mik'a mishi hannu suka gaisa ya na tambayar sa ya ake ciki?
Likitan ya kalli Salim sannan ya maida duban shi wurin Abban ya ce"fyad'en dai ya tabbata,sai dai Allah ya rufa asiri".
"Ban yarda ba! Wallahi akwai k'ulla-k'ulla a wannan abun!" Muryar Salim ta karad'e kunnuwanmu.
Gabana ya fad'i. Likitan cikin nuna rashin damuwa ya ce"me ye ya ba ka tabbacin hakan?"
Salim ya ce"duba yarinya ba sai likitoci biyu ba,likitan farko da ya dace ya duba ta ya jima a ciki,sannan ya fito kuma ina kallon shi,sam ban yarda da yanayinsa ba,kai ma kuma da ka shiga ka jima a ciki,to meye dalilin dad'ewarku a duba mutum d'aya kawai?"
Likitan ya kalle shi na y'an sakanni,har na fara fargaba sai ji na yi ya ce"amma dai ina tunanin ka san irin b'arnar da ka yi mata ko?"
"Ban gane ba!" Salim ya fad'a a hasale.
Likitan ya ce"likitan farko da ka ga ya fita,shi ne ya fara duba ta,kuma ya ga b'arnar da ka yi mata,shi yasa ya kira ni saboda na fi shi k'warewa a fannin d'inki,yanzu dai an gama gyarata,za mu saka mata ruwa,idan ya k'are kuma sai a sallame ta.Akwai magungunan da zan rubuta".
"Dank'ari!" Na fad'a a zuciyata.Amma lallai wannan likitan idan ya shiga wasan kwaikawayo zai samu abinci sosai, na ji wani farinciki ya rufe ni,sai dai fa na yi mamakin abin da ya sa shi wannan k'aryar har haka,kuma na sa a raina ba sai na ji dalili ba,ko ma menene ni kam ya taimake ni.
Salim ya ce"kai ka ga! Kada ka sake danganta ni da wannan,can za ta nemi wanda ya yi mata b'arna ba...".
"Kai!" Abba ya daka masa tsawa,Salim ya koma ya zauna fuskar nan kamar bai tab'a murmushi ba.
Abba ya ja likitan gefe,ban san dai me suka tattauna ba,ni kuma wata nurse ta zo ta rik'e hannuna muka shiga wani d'akin. Aka bani gado,ta saka min drip,ta ba ni magani na sha,har da lulllub'e ni da bargo,aikuwa bacci ya ce min mu je.
Ba ni na tashi ba sai bayan azhar,na duba wayata dake kusa da ni,na ga k'arfe biyu da minti ashirin,na tashi zaune,yanzu kam na ji dad'in jikina sosai,babu wani sauran bacci a idona,na tashi na shiga band'aki na d'auro alwala.
Anti Na'ima ta dinga jera salati babu k'akk'autawa,sannan ta fara k'walla ta ce"wallahi Alhaji aurenta saura sati biyu,ashe ita yarinyar nan shirin ta da ban!"
Abba ya jinjina kai ya ce"duk abar maganar,aje asibitin kawai".
Anti ta ce ta na zuwa,ta shiga d'aki.Ba ta jima ba ta fito,ta mik'o min wayata,tana min wata kafirar harara, mu ka tafi. Hanyar asibitin Aminu Kano muka d'auka,Anti ta ce gwara aje Nasarawa akwai likitoci mata ta wannan fannin,Salim ya juya kan motar muka yi Nasarawa,ni dai gabana sai fad'uwa ya ke yi,shi kuwa Salim ban san abin da yake ransa ba.
Muka shiga asibitin,Anti ta ce ta san b'angaren da ya kamata mu je,kamar an san da zuwanmu mu na zuwa aka nuna mana inda za mu shiga,Anti ce ta yiwa wata nurse bayani a tak'aice,sai aka yankan min kati,babu jimawa aka nuna min d'akin da zan shiga a dubani.
K'irjina fa ya tsananta bugu,na dinga taku d'aya bayan d'aya kamar wahainiya,fargaba fal raina
Da na shiga d'akin kusan fad'uwa na yi,saboda wani tuntub'en bazata da na yi,sakamakon ganin Habib sanye cikin uniform d'insa na asibiti,ya hard'e hannu a k'irji,fuskar nan babu walwala,shi kad'ai ne a d'akin,da alama dai shi ne likitan da zai duba ni.
*MATAR SHIGE...!*
_(Ba ta daraja)_
BY
*SADIYA ABDUL*
_(Maizafafa)_
*☀️FIRST CLASS WRITER'S ASSOCIATION☀️*
Page 19
*Ni fa na san so,kuma na yarda k'addara ne.Don haka ina team d'in Zinatu,idan kuna zaginta Allah zan tafi hutun typing na sati biyu,kafin nan zuciyarku ta yi sanyi,sai mu d'ora😉*
Habib ya yi min wani firgitaccen kallo,da alama dai bai tsammaci gani na ba.Ni kuwa kusan mutuwar tsaye na yi,ganin wannan tonon sililin da ya tunkaro ni,ko kuma na ce na jefa kaina a ciki,amma sosai na yi mamakin ganin shi a b'angaren,don a iya sani na Habib likitan ido ne,to me zai kawo shi nan b'angaren? Ban gama raba d'ayan biyu ba na ji muryarsa
"Zinatu! Kar dai ki fad'a min ke ce wadda za a duba yanzu!" Ya yi maganar ya na k'ank'ance ido da alamun b'acin rai.
Na ji wata kunyarsa ta rufto min,na kasa magana,kawai sai na fara zub da hawaye ba tare da na shiya ba. Ya yi huci me zafi ya nemi kujera ya zauna,sannan ya d'akko wayarsa a aljihu ya yi danne-danne ya kara a kunne
Na yi shiru ina sauraron wayar tashi,ban san da wanda yake wayar ba,na dai ji ya na cewa"ka ga doctor, ka k'arasa a tsanake,ni ma na ari office d'in naka na y'an mintuna,idan na kammala zan kira ka".
Ya ajiye wayar ya kalle ni fuskar nan murtuk kamar ba shi ba ya ce"maganar fyad'en da ake tantama a kansa,ina so ki fad'a min gaskiya anyi miki,ko ba a yi miki ba?"
Na yi shiru,kaina a k'asa.Ya buga teburin da k'arfi ya ce"ke! Ina tamabayarki ne fa as your doctor, ba Habibun da kika sani ba,ki d'auka ban ma tab'a ganin ki ba sai yau,saboda haka idan kin shirya ganin likita sai ki bud'e bakinki,idan ba ki shirya ba ki fice min daga office!"
Na d'ago na kalle shi, sai na ga tabbas wannan ba Habib d'ina bane,da gaske ya ke yau a gaban doctor Habib nake,sai na saka a raina ban san shi ba d'in,don haka na ce"ni ma ban sani ba".
"Kamar ya ba ki sani ba? Shekarunki nawa?" Ya tambaye ni,idonsa a kaina
"Ashirin" Na ba shi amsa.
Ya ce"ko y'ar shekara biyar aka yi mata fyad'e dole ta sani,bare ke da kin isa zaman aure! Ki na kokwanton anyi miki fyad'e,ta ya ki ka tsaida wanda kike zargi?"
Na lura dai da gaske Habib ya ke son k'ure ni,gwara ni ma na dawo masa Zinatu,don ya na shirin canza min suna da wata banzar barazanar sa,wai shi likita!
Na had'e rai na gyara zama na ce"kafin na shigo wurin nan ce min aka yi likita zai duba ni,ba lauya ba,kuma a zatona da doctor Habib na ke magana,ba barrister Habib ba".
"E hakane,amma wannan tambayar duka cikin aikina ne". Ya fad'a ya na had'e gira.
Na ce"tunda ka ga har sun kawo ni nan,ai ka san an zo gab'ar raba gardama kenan.Idan za ka duba ni bismillah kawai". Na k'arasa maganar zuciyata na bugu,don ina fargaba da takaicin wani gardi ya ga tsaraicina,musamman ma Habib d'in,wannan rashin darajar ina zan kai shi? Amma a fili ba za ka tab'a kawo haka nake tunani a raina ba.
Ya yi shiru ya na kallo na,tsawon sakanni,sannan ya jinjina kai ya ce" bismillah! Ga gado can je ki hau".
Gabana ya fad'i,duk da har yanzu zuciyata ba ta amince da zai iya duba ni d'in ba,ban nuna ba na dake na tashi na yi inda gadon ya ke,sai dai zama na yi ba kwanciya ba
Na d'an jima da zama,har na fara k'aguwa sannan ya k'araso wurin,ya janyo kujera ya zauna ya fuskance ni,ni kuma na sunkuyar da kai, don ba na son ya kalli k'wayar idona.
Tun kafin ya fara magana wani likita ya shigo,wanda na ke kyautata zaton shi ne me office d'in.
"Doctor ka kammala?" Ya tambaye shi,idonsa a kaina
Habib ya yi wani huci ya dafe kansa da duka hannayensa biyu.
Likitan ya janyo wata kujerar ya zauna a kusa da shi,ya ce"na fa kasa fahimta,a iya sani na ba ka harka da mata,wacece wannan?"
Kamar ba zai ba shi amsa ba,sai can ya ce"ita ce Zinatu".
Ko idona ne oho! Sai na ga kamar lokaci d'aya yanayin likitan ya canza,zuwa ga b'acin rai,ya yi min wani kallon da na kasa fassra shi a lokacin,sai daga baya,sannan ya kalli Habib ya ce"to me ya kawo ta nan d'in?"
Habib ya tashi ya je kan teburin ya d'akko masa takarda ya ba shi.Ko me aka rubuta a takarda tawa oho! Na dai ga ya kalle ni da sauri,kuma da alamun b'acin rai
Ya kalli Habib ya ce"yanzu ka duba ta d'in?"
Ya girgiza masa kai alamar a'a.Sai ya ce"ok,ka je kawai zan saita komai".
Habib ya yi masa wani kallo me wuyar fassrawa ya ce"kai! Matar da zan aura d'in za ka duba!?"
"Ai cikin aikina ne" Ya ba shi amsa ya na d'age kafad'a.
Habib ya kalle ni ya ce"ke tashi ki fita! Sai dai ku canza wani asibitin wallahi,ta ya wanda na sani zai duba min mata?"
Likitan ya dafa kafad'arsa ya ce"ok! Na fahimce ka Habib,amma ka sani ko wani asibitin aka kai ta ba ka da tabbacin mace ce za ta duba ta.Na yi maka alk'awarin ba zan duba ta ba,zan lallab'a ta ta sanar da ni gaskiya".
Habib ya yi shiru kamar me nazari. "Ka yarda da ni abokina,ka je d'in".
Habib ya kalle ni,sannan ya maida facemask d'insa ya fice.Na sauke ajiyar zuciya a b'oye,har yanzu zaune nake a bakin gadon
Likitan ya kalle ni da kyau ya ce" ke anyi miki fyd'en ko ba a miki ba?"
"Ni ma na kasa tantancewa fa" Na fad'a, ina juyar da kai gefe
Sai ya tab'e baki ya ce"yanzu ya kike jin jikinki?"
Na ce"ya na yi min ciwo kad'an,sai bacci da nake ji".
"Tun yaushe abun ya faru?"
"Jiya da daddare" Na ba shi amsa.
"Waye wanda ake zargi" Ya tambaye ni.
"Wani ne" Na fad'a
Ya ce"ko Salim da na gani a waje?"
"Shi" Na fad'a a tak'aice.
Ya ce"ok! To yanzu zan canza miki d'aki,sai na saka miki drip,idan ya k'are za a sallame ki".
Ina shirin yin magana ya tashi,ya na cewa na biyo shi.
Ba ni da zab'in da ya wuce bin umarnin shi.Zazzaune muka tadda su Abba,da alama har sun k'osa da jira,na tsaya daga d'an nesa,yayinda likitan ya k'arasa wurin su,Abba ya tashi da sauri ya mik'a mishi hannu suka gaisa ya na tambayar sa ya ake ciki?
Likitan ya kalli Salim sannan ya maida duban shi wurin Abban ya ce"fyad'en dai ya tabbata,sai dai Allah ya rufa asiri".
"Ban yarda ba! Wallahi akwai k'ulla-k'ulla a wannan abun!" Muryar Salim ta karad'e kunnuwanmu.
Gabana ya fad'i. Likitan cikin nuna rashin damuwa ya ce"me ye ya ba ka tabbacin hakan?"
Salim ya ce"duba yarinya ba sai likitoci biyu ba,likitan farko da ya dace ya duba ta ya jima a ciki,sannan ya fito kuma ina kallon shi,sam ban yarda da yanayinsa ba,kai ma kuma da ka shiga ka jima a ciki,to meye dalilin dad'ewarku a duba mutum d'aya kawai?"
Likitan ya kalle shi na y'an sakanni,har na fara fargaba sai ji na yi ya ce"amma dai ina tunanin ka san irin b'arnar da ka yi mata ko?"
"Ban gane ba!" Salim ya fad'a a hasale.
Likitan ya ce"likitan farko da ka ga ya fita,shi ne ya fara duba ta,kuma ya ga b'arnar da ka yi mata,shi yasa ya kira ni saboda na fi shi k'warewa a fannin d'inki,yanzu dai an gama gyarata,za mu saka mata ruwa,idan ya k'are kuma sai a sallame ta.Akwai magungunan da zan rubuta".
"Dank'ari!" Na fad'a a zuciyata.Amma lallai wannan likitan idan ya shiga wasan kwaikawayo zai samu abinci sosai, na ji wani farinciki ya rufe ni,sai dai fa na yi mamakin abin da ya sa shi wannan k'aryar har haka,kuma na sa a raina ba sai na ji dalili ba,ko ma menene ni kam ya taimake ni.
Salim ya ce"kai ka ga! Kada ka sake danganta ni da wannan,can za ta nemi wanda ya yi mata b'arna ba...".
"Kai!" Abba ya daka masa tsawa,Salim ya koma ya zauna fuskar nan kamar bai tab'a murmushi ba.
Abba ya ja likitan gefe,ban san dai me suka tattauna ba,ni kuma wata nurse ta zo ta rik'e hannuna muka shiga wani d'akin. Aka bani gado,ta saka min drip,ta ba ni magani na sha,har da lulllub'e ni da bargo,aikuwa bacci ya ce min mu je.
Ba ni na tashi ba sai bayan azhar,na duba wayata dake kusa da ni,na ga k'arfe biyu da minti ashirin,na tashi zaune,yanzu kam na ji dad'in jikina sosai,babu wani sauran bacci a idona,na tashi na shiga band'aki na d'auro alwala.