Sashe 18
Matar Shege Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Na kalli Baby,na ga sai share hawaye take yi,na kalli Ammi na ga ta rik'e k'ugu,fuskar nan murtuk kamar kunun kanwa,na kai duba ga gogan nawa,shi ma ni ya ke kallo kamar idanunsa za su fito
Sai kawai na maida kaina k'asa,gabana na tsananta fad'uwa.
Ammi ta ce"tambayarki fa ake yi!"
Sai da na yi wasu huci masu zafi har uku a jere sannan na ce"Fyad'e ya yi min".
"Innalillahi wa inna ilaihi raji'un!" Duka suka d'auki salati,har da Salim d'in.
#Team Salim
#Team Zinatu
Waye abin tausayi wai?😥
*MATAR SHIGE...!*
_(Ba ta daraja)_
BY
*SADIYA ABDUL*
_(Maizafafa)_
*☀️FIRST CLASS WRITER'S ASSOCIATION☀️*
Page 18
"K'arya take,wallahi ban yarda ba!" Cewar Ammi ta na nuna ni da yatsa.
K'irjina ya dinga lugude,tuni nadama ta rufe ni, kai gaskiya ranar na yi danasani,na ji haushin kaina sosai. Salim ya kalle ni ya ce"Zinatu ki ji tsoron Allah! Yanzu saboda na k'i karbar soyayyarki sai ki saka min da wannan?"
"Kai!" Abba ya daka tsawa ya kalli Salim ya ce"Salim! Ka san ni dai ba sa'anka bane,bare ka tsaya yin wasan kwaikwayo a gabana,don haka ka fad'a min gaskiyar yanda abin ya kasance".
Salim ya cije leb'e da alama dai ya na jin zafi a zuciyarsa,ya ce"wallahi tallahi Abba ban yi mata komai ba,sharri ta yi min kawai!".
Ammi ta ce"amma lallai yarinyar nan ke makira ce! Kenan saboda ya ce ba ya son ki sai ki nemi jifansa da sharri? To plan d'inki bai samu shiga ba!".
Abba ya d'aga mata hannu ya ce"kin ga Rahma! Ba a shaidar d'an yau,kuma ki yi tunani idan Khadija aka yiwa haka ya za ki ji? To wallahi ba zan bar maganar nan haka ba,dole na tabbatar da adalci a ciki".
Ni dai hawaye kawai nake sharewa,yanzu kam na fi tausayin Salim fiye da kaina.Baby dai har yanzu ba ta ce komai ba,ban kuma san abin da shurunta ya ke nufi ba,jikina ya mutu murus nadama ta haifar min da kasala sosai.
"Don Allah Abba ka yi bincike,wallahi wannan yarinyar sharri ta yi min, ban san wanda ya kawo ta d'akina ba,kuma tun farko fargabar yanda za ku d'auki zancen ne yasa na kasa fad'a muku,na yi yunk'urin fitar da ita daga gidan nan". Salim ya fad'a murya na rawa.
Abba ya ce"alfarma d'aya zan yi maka! Gobe za mu je asibiti da yarinyar nan,likitoci su duba ta muddin aka tabbatar an yi mata fyad'e to na yarda da zancen ta,na watsar da naka,don kai ne ka yi kenan. Idan kuma aka tabbatar da babu wani fyad'e da aka yi mata,to zan yarda da zancen ka,kuma ba zan bar duk wani me hannu a sharrin da aka k'ulla maka ba".
Salim ya ce"amma Abba..."
"Na gama magana,kuma ban buk'aci jin komai daga bakin kowa ba". Ya katse shi da fad'in haka.
Gabana ya fad'i da jin furucinsa,nan take na fara tunanin anya kuwa na yiwa Salim adalci? Ni dai a halin yanzu ban san a wane hali nake ciki ba,an yi min fyad'e? Ba a yi min? Wallahi ba ni da masaniya,idan aka je asibiti ya tabbata anyi min,shikenan fa na had'a Salim da mahaifinsa,kuma bani da tabbacin hukuncin da zai yanke min zai yi daidai da burina,hukuncin tilastawa Salim aurena na ke nufi.Idan kuma ba a yi min fyad'en ba duk cikin plan d'in su Nazifi ne fa? Wane irin hukunci zai yanke akan mu,bayan asiri ya tono? Na dinga jero salati a zuciyata, da na tuna yanzu duk inda hankalin Anti Na'ima ya ke ya tashi,na rashin dawowa ta,watak'il har Ummi da Baba duk sun ji.
Abba ya kalli Baby da ke share hawaye ya ce" Khadija,je ki bata d'akin da za ta kwanta kafin goben".
"Ki biyo ni" Baby ta fad'a, ba tare da ta kalli inda nake ba.Shi kuma Salim har yanzu ya na nan a durk'ushe kamar me neman gafara,kodayake kusan hakan ne ma ai
Na tashi jiki ba k'wari na bi bayan Baby,tun ban yi nisa ba na ji Abba ya saki salati,na yi saurin juyowa sai ya juyar da kai ya ce"sannu kin ji? Khadija ki bata kayanki ta canza wad'annan".
"Salim ka na da imani kuwa? Da har ciwo ka ji mata haka,amma shi ne za ka fita da ita a haka?" Na ji muryar Abba, hakan ya tabbatar min ya ga jinin jikin rigata ne.
Ban ji amsar da Salim ya ba shi ba na shiga d'akin da na ga Baby ta shiga,ta kunna haske sannan ta fita.Na bi d'akin da kallo,fess yake,babu wani shirgi daga katifa madaidaiciya,sai mudubi lik'e a jikin bango,na samu gefen katifar na rab'a,sanyi ya na ratsa sassan jikina
Ba a jima ba Babyn ta dawo,da sallama na amsa ina son ganin cikin idonta,amma ba ta bani dama ba,ta ajiye min riga da sket na atamfa,ta juya ta na shirin fita na ce"zan samu hijjabi don Allah? "
Ba ta juyo ba ta fice kamar ba ta ji ni ba,amma kuma ba ta dad'e ba ta dawo ta jefo min hijjabin ta koma
Na tashi na shiga band'akin cikin d'akin,don dama fitsari nake ji sosai ya d'aure min mara.Sai dai na yi mamakin rashin ganin jini a jikina,don a iya rigar kawai ya tsaya,na jima a tsugunne ina son na gano halin da nake ciki,da gaske anyi min fyad'e ko a'a? Amma na kasa ganewa,don haka na hak'ura na tashi na yi wankan tsarki,tunda ban gama yarda da kaina ba,na wanke farar rigar,ko nace na d'auraye ta tunda ban ga clean ba,haka dai na cukuikuye ta na barta a band'akin,na fito na saka kayan da ta kawo min na saka hijjabin na tada sallah,margiba da isha'i na yi don su ake bi na,haka na zauna na yi ta istigfari tun kafin na san yanda za ta kaya goben.Wata yunwa ma nake ji sosai,amma sanin a yanzu ba ni da gatan samun abinci na kwanta a haka na lullab'a da hijjabi,tuni bacci ya kwashe ni.
Washegari da na farka har an idar da sallar asuba,gari ya fara haske,kuma a hakan ma fa baccin bai isheni ba,na tashi na yi sallah na kwanta a kafet d'in ina jin yanda babban yatsana na k'afa yake zugi,wani baccin ya sake kwasa ta.
"Zinatu,Zinatu" Na ji muryar Baby cikin baccin nawa
Na farka na ganta tsaye a bakin k'ofa. "Ki fito inji Abba" Ta fad'a, sannan ta fice
Na tashi,na saka hijjabin na fito cikin jin kunya,kaina a k'asa,a falo na tadda su duka har da Salim d'in,na saci kallonsa ta gefen ido,sanye ya ke da bak'ar shadda da kofin shayi a hannunsa,ya na juyawa da cokali,sai na ga ya yi min kyau sosai.
Na k'arasa na duk'a na gaida Abba,ya amsa ya na yi min ya jiki,ban amsa ba saboda kunya,na juya wurin Ammi na gaisheta,ita kam ba ta ma nuna ta san da halitta ta a wurin ba,na juyo kan gogan nawa na ga ni ya ke kallo, na ce "ina kwana?"
"Lafiya lau" Ya amsa min,ban yi zato ba. Na koma gefe na rakub'e kamar yajin k'osai
Habiba y'ar aikin gidan ta shigo falo ta kalleni ta ce"ki zo ki karya".
Na tashi na bi bayanta da d'an d'ingishi,don har na fara zaton na yi targad'e ne a jefoni da ya yi,daga cikin bahon wanka.A nan dinning d'in na tadda Baby ta na karyawa,na kalle ta na ga hankalinta na kan farantin dankalin dake gabanta
"Baby,an tashi lafiya?" Na fad'a ina k'irk'iro murmushi.
Sai ta yi kamar ba ta ji ba, ta tashi ta bar wurin.Cikin d'ari-d'ari na had'a shayi,don ba dan ina jin yunwa ba ma ba zan ci komai ba,na zuba dankalin kad'an na karya,sai na yi zama na a wurin,don duka kunyar su nake ji wallahi, na dinga tunanin halin da gidanmu yake ciki a yanzu,watak'il ana can ana ta nema na,na fara fargabar kada Habib ya ji labari,tunda shi ne kawai ya ga lokacin da aka d'aukeni a mota,kuma babbar matsalar ma ya ga wanda ya d'auke ni d'in.
Ina nan zaune Baby ta dawo cikin shirinta,har da hijjabi,ta kalle ni ta ce"ki taso muje asibiti.Kuma ki sani ko kin auri Salim ba za ki tab'a samun wani farincikin rayuwar aure ba,saboda Ammi ba za ta tab'a k'aunarki ba,ta san tsakaninku da Salim,tun ranar da kuka gaisa a gidan nan,na bata labarinki duka.Sannan ko da kin yi nasarar shigowa dangin mu,za ki yi rayuwa ne ke da mijinki kawai,saboda har ni ma ba na tare da ke!". Ba ta jira cewata ba ta bar wurin
Ba ni da zab'in da ya wuce na bi bayanta,don haka na tashi jikina duk ya yi sanyi,na nufi falon,har Abba ya so bani tausayi,yanda yake kallo na cikin kulawa da tausayi a idonsa,na fita kamar yanda na ga sun yi.
Muka shiga mota,Salim ne a mazaunin direba,Abba a gaba,sai ni da Baby muka shiga baya,sai da na ga an tada motar na gane banda Ammi za a je.
"Ina ne gidanku?" Abba ya tambaye ni.
"Hotoro ne" Na fad'a a sanyaye.
"Wace unguwa?" Ya sake tambaya ta.
"Abba na fa san gidan" Ya fad'a da murya ciki-ciki.
Abba ya ce"to ka ga Salim,in har ka san da gaske ka yaudari yarinyar nan ka fad'a min,ba sai mun je asibiti mun tonawa kanmu asiri ba".
Salim ya ce"wallahi Abba gaskiya na fad'a maka,ni ban yi mata komai ba".
"To amma ta ya ka san gidansu?" Ya tambaye shi.
Salim ya yi shiru,kamar bai ji shi ba.Motar ta yi shiru,har muka k'arasa k'ofar gidan Anti Na'ima,bugun zuciyata fa sai ya k'ara tsananta,Abba ya ce na shiga na yi masa sallama da Babana,na yi masa bayanin nan d'in gidan Yayata ne,sai ya ce na kira yayar tawa,ko mijinta.
Na fito daga motar jiki a sanyaye na shiga gidan,ina shiga na tadda Anti a falo,ta tashi tsaye ta ce"Zinatu a ina ki ka kwana? Hankalinmu duka ya tashi muna ta nemanki,kuma kin bar wayarki a gida!"
"Ina wayar tawa?" Na tambaye ta.
Ta ce"ban sani ba! Na ce a ina ki ka kwana?"
Na sunkuyar da kai ban bata amsa ba na ce"ana sallama da ke a waje".
Cikin mamaki ta ce"sallama kuma? Waye?"
"Mahaifin Salim ne" Na bata amsa.
Ta ce"waye kuma Salim?"
"Anti suna jiranki,ba fa k'ananun mutane bane" Na fad'a cikin k'osawa da tambayoyin ta.
Sai kawai na maida kaina k'asa,gabana na tsananta fad'uwa.
Ammi ta ce"tambayarki fa ake yi!"
Sai da na yi wasu huci masu zafi har uku a jere sannan na ce"Fyad'e ya yi min".
"Innalillahi wa inna ilaihi raji'un!" Duka suka d'auki salati,har da Salim d'in.
#Team Salim
#Team Zinatu
Waye abin tausayi wai?😥
*MATAR SHIGE...!*
_(Ba ta daraja)_
BY
*SADIYA ABDUL*
_(Maizafafa)_
*☀️FIRST CLASS WRITER'S ASSOCIATION☀️*
Page 18
"K'arya take,wallahi ban yarda ba!" Cewar Ammi ta na nuna ni da yatsa.
K'irjina ya dinga lugude,tuni nadama ta rufe ni, kai gaskiya ranar na yi danasani,na ji haushin kaina sosai. Salim ya kalle ni ya ce"Zinatu ki ji tsoron Allah! Yanzu saboda na k'i karbar soyayyarki sai ki saka min da wannan?"
"Kai!" Abba ya daka tsawa ya kalli Salim ya ce"Salim! Ka san ni dai ba sa'anka bane,bare ka tsaya yin wasan kwaikwayo a gabana,don haka ka fad'a min gaskiyar yanda abin ya kasance".
Salim ya cije leb'e da alama dai ya na jin zafi a zuciyarsa,ya ce"wallahi tallahi Abba ban yi mata komai ba,sharri ta yi min kawai!".
Ammi ta ce"amma lallai yarinyar nan ke makira ce! Kenan saboda ya ce ba ya son ki sai ki nemi jifansa da sharri? To plan d'inki bai samu shiga ba!".
Abba ya d'aga mata hannu ya ce"kin ga Rahma! Ba a shaidar d'an yau,kuma ki yi tunani idan Khadija aka yiwa haka ya za ki ji? To wallahi ba zan bar maganar nan haka ba,dole na tabbatar da adalci a ciki".
Ni dai hawaye kawai nake sharewa,yanzu kam na fi tausayin Salim fiye da kaina.Baby dai har yanzu ba ta ce komai ba,ban kuma san abin da shurunta ya ke nufi ba,jikina ya mutu murus nadama ta haifar min da kasala sosai.
"Don Allah Abba ka yi bincike,wallahi wannan yarinyar sharri ta yi min, ban san wanda ya kawo ta d'akina ba,kuma tun farko fargabar yanda za ku d'auki zancen ne yasa na kasa fad'a muku,na yi yunk'urin fitar da ita daga gidan nan". Salim ya fad'a murya na rawa.
Abba ya ce"alfarma d'aya zan yi maka! Gobe za mu je asibiti da yarinyar nan,likitoci su duba ta muddin aka tabbatar an yi mata fyad'e to na yarda da zancen ta,na watsar da naka,don kai ne ka yi kenan. Idan kuma aka tabbatar da babu wani fyad'e da aka yi mata,to zan yarda da zancen ka,kuma ba zan bar duk wani me hannu a sharrin da aka k'ulla maka ba".
Salim ya ce"amma Abba..."
"Na gama magana,kuma ban buk'aci jin komai daga bakin kowa ba". Ya katse shi da fad'in haka.
Gabana ya fad'i da jin furucinsa,nan take na fara tunanin anya kuwa na yiwa Salim adalci? Ni dai a halin yanzu ban san a wane hali nake ciki ba,an yi min fyad'e? Ba a yi min? Wallahi ba ni da masaniya,idan aka je asibiti ya tabbata anyi min,shikenan fa na had'a Salim da mahaifinsa,kuma bani da tabbacin hukuncin da zai yanke min zai yi daidai da burina,hukuncin tilastawa Salim aurena na ke nufi.Idan kuma ba a yi min fyad'en ba duk cikin plan d'in su Nazifi ne fa? Wane irin hukunci zai yanke akan mu,bayan asiri ya tono? Na dinga jero salati a zuciyata, da na tuna yanzu duk inda hankalin Anti Na'ima ya ke ya tashi,na rashin dawowa ta,watak'il har Ummi da Baba duk sun ji.
Abba ya kalli Baby da ke share hawaye ya ce" Khadija,je ki bata d'akin da za ta kwanta kafin goben".
"Ki biyo ni" Baby ta fad'a, ba tare da ta kalli inda nake ba.Shi kuma Salim har yanzu ya na nan a durk'ushe kamar me neman gafara,kodayake kusan hakan ne ma ai
Na tashi jiki ba k'wari na bi bayan Baby,tun ban yi nisa ba na ji Abba ya saki salati,na yi saurin juyowa sai ya juyar da kai ya ce"sannu kin ji? Khadija ki bata kayanki ta canza wad'annan".
"Salim ka na da imani kuwa? Da har ciwo ka ji mata haka,amma shi ne za ka fita da ita a haka?" Na ji muryar Abba, hakan ya tabbatar min ya ga jinin jikin rigata ne.
Ban ji amsar da Salim ya ba shi ba na shiga d'akin da na ga Baby ta shiga,ta kunna haske sannan ta fita.Na bi d'akin da kallo,fess yake,babu wani shirgi daga katifa madaidaiciya,sai mudubi lik'e a jikin bango,na samu gefen katifar na rab'a,sanyi ya na ratsa sassan jikina
Ba a jima ba Babyn ta dawo,da sallama na amsa ina son ganin cikin idonta,amma ba ta bani dama ba,ta ajiye min riga da sket na atamfa,ta juya ta na shirin fita na ce"zan samu hijjabi don Allah? "
Ba ta juyo ba ta fice kamar ba ta ji ni ba,amma kuma ba ta dad'e ba ta dawo ta jefo min hijjabin ta koma
Na tashi na shiga band'akin cikin d'akin,don dama fitsari nake ji sosai ya d'aure min mara.Sai dai na yi mamakin rashin ganin jini a jikina,don a iya rigar kawai ya tsaya,na jima a tsugunne ina son na gano halin da nake ciki,da gaske anyi min fyad'e ko a'a? Amma na kasa ganewa,don haka na hak'ura na tashi na yi wankan tsarki,tunda ban gama yarda da kaina ba,na wanke farar rigar,ko nace na d'auraye ta tunda ban ga clean ba,haka dai na cukuikuye ta na barta a band'akin,na fito na saka kayan da ta kawo min na saka hijjabin na tada sallah,margiba da isha'i na yi don su ake bi na,haka na zauna na yi ta istigfari tun kafin na san yanda za ta kaya goben.Wata yunwa ma nake ji sosai,amma sanin a yanzu ba ni da gatan samun abinci na kwanta a haka na lullab'a da hijjabi,tuni bacci ya kwashe ni.
Washegari da na farka har an idar da sallar asuba,gari ya fara haske,kuma a hakan ma fa baccin bai isheni ba,na tashi na yi sallah na kwanta a kafet d'in ina jin yanda babban yatsana na k'afa yake zugi,wani baccin ya sake kwasa ta.
"Zinatu,Zinatu" Na ji muryar Baby cikin baccin nawa
Na farka na ganta tsaye a bakin k'ofa. "Ki fito inji Abba" Ta fad'a, sannan ta fice
Na tashi,na saka hijjabin na fito cikin jin kunya,kaina a k'asa,a falo na tadda su duka har da Salim d'in,na saci kallonsa ta gefen ido,sanye ya ke da bak'ar shadda da kofin shayi a hannunsa,ya na juyawa da cokali,sai na ga ya yi min kyau sosai.
Na k'arasa na duk'a na gaida Abba,ya amsa ya na yi min ya jiki,ban amsa ba saboda kunya,na juya wurin Ammi na gaisheta,ita kam ba ta ma nuna ta san da halitta ta a wurin ba,na juyo kan gogan nawa na ga ni ya ke kallo, na ce "ina kwana?"
"Lafiya lau" Ya amsa min,ban yi zato ba. Na koma gefe na rakub'e kamar yajin k'osai
Habiba y'ar aikin gidan ta shigo falo ta kalleni ta ce"ki zo ki karya".
Na tashi na bi bayanta da d'an d'ingishi,don har na fara zaton na yi targad'e ne a jefoni da ya yi,daga cikin bahon wanka.A nan dinning d'in na tadda Baby ta na karyawa,na kalle ta na ga hankalinta na kan farantin dankalin dake gabanta
"Baby,an tashi lafiya?" Na fad'a ina k'irk'iro murmushi.
Sai ta yi kamar ba ta ji ba, ta tashi ta bar wurin.Cikin d'ari-d'ari na had'a shayi,don ba dan ina jin yunwa ba ma ba zan ci komai ba,na zuba dankalin kad'an na karya,sai na yi zama na a wurin,don duka kunyar su nake ji wallahi, na dinga tunanin halin da gidanmu yake ciki a yanzu,watak'il ana can ana ta nema na,na fara fargabar kada Habib ya ji labari,tunda shi ne kawai ya ga lokacin da aka d'aukeni a mota,kuma babbar matsalar ma ya ga wanda ya d'auke ni d'in.
Ina nan zaune Baby ta dawo cikin shirinta,har da hijjabi,ta kalle ni ta ce"ki taso muje asibiti.Kuma ki sani ko kin auri Salim ba za ki tab'a samun wani farincikin rayuwar aure ba,saboda Ammi ba za ta tab'a k'aunarki ba,ta san tsakaninku da Salim,tun ranar da kuka gaisa a gidan nan,na bata labarinki duka.Sannan ko da kin yi nasarar shigowa dangin mu,za ki yi rayuwa ne ke da mijinki kawai,saboda har ni ma ba na tare da ke!". Ba ta jira cewata ba ta bar wurin
Ba ni da zab'in da ya wuce na bi bayanta,don haka na tashi jikina duk ya yi sanyi,na nufi falon,har Abba ya so bani tausayi,yanda yake kallo na cikin kulawa da tausayi a idonsa,na fita kamar yanda na ga sun yi.
Muka shiga mota,Salim ne a mazaunin direba,Abba a gaba,sai ni da Baby muka shiga baya,sai da na ga an tada motar na gane banda Ammi za a je.
"Ina ne gidanku?" Abba ya tambaye ni.
"Hotoro ne" Na fad'a a sanyaye.
"Wace unguwa?" Ya sake tambaya ta.
"Abba na fa san gidan" Ya fad'a da murya ciki-ciki.
Abba ya ce"to ka ga Salim,in har ka san da gaske ka yaudari yarinyar nan ka fad'a min,ba sai mun je asibiti mun tonawa kanmu asiri ba".
Salim ya ce"wallahi Abba gaskiya na fad'a maka,ni ban yi mata komai ba".
"To amma ta ya ka san gidansu?" Ya tambaye shi.
Salim ya yi shiru,kamar bai ji shi ba.Motar ta yi shiru,har muka k'arasa k'ofar gidan Anti Na'ima,bugun zuciyata fa sai ya k'ara tsananta,Abba ya ce na shiga na yi masa sallama da Babana,na yi masa bayanin nan d'in gidan Yayata ne,sai ya ce na kira yayar tawa,ko mijinta.
Na fito daga motar jiki a sanyaye na shiga gidan,ina shiga na tadda Anti a falo,ta tashi tsaye ta ce"Zinatu a ina ki ka kwana? Hankalinmu duka ya tashi muna ta nemanki,kuma kin bar wayarki a gida!"
"Ina wayar tawa?" Na tambaye ta.
Ta ce"ban sani ba! Na ce a ina ki ka kwana?"
Na sunkuyar da kai ban bata amsa ba na ce"ana sallama da ke a waje".
Cikin mamaki ta ce"sallama kuma? Waye?"
"Mahaifin Salim ne" Na bata amsa.
Ta ce"waye kuma Salim?"
"Anti suna jiranki,ba fa k'ananun mutane bane" Na fad'a cikin k'osawa da tambayoyin ta.