Sashe 14
Matar Shege Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Na yi saurin kallon shi,sai na ga fuskarsa sam babu walwala,na ja k'afa,na k'arasa inda ya ke tsaye a k'ofar gida.
Ya kalleni da kyau ya ce "kukan me ki ke yi?"
Oho! Ni ban ma san ina hawaye ba sai da ya fad'a, na kai hannu na share na ce"babu komai".
Ya ce"ban yarda ba! Waye wannan d'in Zinatu?"
Na ce"yayan k'awata ne fa,ya zo ya ke fad'a min ta rasu tun wancen satin".
"Kuma kun shak'u da k'awar sosai ko?" Ya tambaye ni,ya na maida fuskarsa kalar tausayi
Na share wasu hawayen,ina shirin yin magana ya rigani
"K'aryar ki ba ta samu shiga ba.Me ya had'a ki da J.S har ya zo wurinki? Ba ma wannan ba,me ya fad'a miki da ya saka ki kuka?"
Na ce"a ina ka san shi?"
Ya ce"fara ba ni amsa,kafin ki tambaye ni".
Haka kawai na ji na yiwa Nazifi yardar da zan ba shi labarin gaskiyar abin da ya had'ani da Salim.Ashe rabon ayi ne ya ja ni...
Mu ka shiga ciki,a tsakar gida mu ka zauna kamar an jona min batir haka na zayyane wa Nazifi tun had'uwata da Salim har izuwa abin da ya kawo shi wurina yanzu.Ya sauke ajiyar zuciya ya na murmushi ya ce"lallai ke ma Zinatu sai a barki! Yanzu ana ta shirye-shiryen aurenki,ke ashe ki na can ki na naki d'an bikin? To wallahi ki na ruwa!" Ya kwashe da dariya
Takaici ya rufeni,na ji dama ban sanar masa ba,na ce"dama don ka yi min dariya ka so jin sirrina?"
Ya daina dariyar ya ce"to ai ki na bada labarin tun kafin ki k'arasa,mafita ta zo min raina,wannan dariyar da kika ga ina yi,har da ta mugunta"
"Mugunta kuma?" Na tambaye shi,ina had'e gira.
Ya ce"yes! Salim na ke yiwa dariya,don kuwa muddin ki ka yarda da sharad'ina to fa ki sa a ranki kawai kin zama matar Salim,ko da za a kira ki da MATAR SHIGE...
*MATAR SHIGE...!*
_(Ba ta daraja)_
BY
*SADIYA ABDUL*
_(Maizafafa)_
*☀️FIRST CLASS WRITER'S ASSOCIATION☀️*
Page 15
"Zan amince da sharad'in ka kowane iri ne,muddin babu sab'awa Allah a ciki" Na fad'a jikina na d'an yin sanyi,don na tsorata da jin kalmar sharad'i,tunda ga dai yanda mu ka yi da Junaina
Nazifi ya yi murmushi ya ce"babu wani sab'on Allah a ciki,zance ake yi na kud'i muddin ki na da kud'i to kuwa ni zan shige miki gaba har sai kin samu shiga.Ke ni fa ban ga laifinki ba,wallahi yaron ya had'u ga kyau ga kud'i".
Na d'an fara fargaba,don ban san ko nawa zai buk'ata ba,kuma ni yanzu kud'in hannuna ba su haura dubu takwas ba,na ce"kamar nawa kenan?"
Ya ce"ki tanadi dubu hamsin,kafin nan da kwana takwas".
"Dubu hamsin!?" Na fad'a ina zare ido,saboda na yi mamaki,kuma uwa-uba ban ga ta inda zan samu dubu hamsin ba.
Ya yi y'ar dariya ya ce"e,dubu hamsin kuma a hakan ma fa bai zama lallai ta isa ba,kin ga ba ni kad'ai zan yi aikin ba,dole sai mun siyi wani na kusa da Salim,wanda zai taimaka mu samu damar gudanar da komai cikin sauk'i,sannan dole na sai get fast..."
Na yi saurin katse shi da fad'in"dakata! Wai wane irin aiki ka ke magana akai? Kuma get fas na meye?"
Ya ce"aiki ne mai wahala kuma me hatsari,amma muddin aka yi sa'a ya wakana babu tangard'a,to ni na tattabar miki kin samu Salim kin gama,sai dai idan ba ki so ba.Shi kuma get fas na shiga wurin da zai yi birthday na ke nufi,nan da sati d'aya ne,haka na ji a bakin wani abokin sa".
Na jinjina kai na ce"na san da maganar birthday d'in,amma ban san ya kusa ba,zan yi wa Baby zancen na ji ko zan samu get fas d'in".
Ya ce"to indai za ta ba ki,kawai idan ki ka karb'a ki bani saboda ke ba sai kin shiga wurin ba".
"Kamar ya!?" Na fad'a ina b'ata rai.
Ya ce"kin ga dai yanzu ki fara tanadin kud'in kafin mu gama tsara komai,amma in sha Allah komai zai zo da sauk'i".
Na ce"Allah yasa".
Jikina duk ya yi sanyi, ina tunanin ta inda zan samu dubu hamsin,ya fita daga gidan ni kuma na shiga sashen Anti
A falo na tadda ita ta na kallo,ta kalle ni ta ce"har ya tafi?"
Ni sai yanzu ma na tuna da k'aryar da na yi kafin na fita,na ce"e ya tafi"
Ta ce "ai da ya shigo mun gaisa,yaushe za a bugo invitation?"
Ina shegewa d'akin da aka bani a gidan na ce"kai Anti,ai da saura".
Zama na yi na kira lambar Baby,ta d'auka,bayan mun gaisa na ke ce mata"ashe birthday d'in mutumin nawa ya zo,ko gayyata ko?"
Ta yi dariya ta ce"ya ma zama naki ko? Ai ban yi zaton za ki je ba,in dai za ki je gobe ki zo ki karb'i katin,jiya ya bani guda uku"
Na ce"me zai hana ni zuwa? Wani ma ya yi rawa bare d'an makad'a? To amma sauran biyun na waye?"
Ta ce"a'a,ai dama ya bani ne kawai ko da wanda zan gayyata,tunda kin ga ni ba sai da get fas ba,tare za mu shiga da shi".
Na ce"kuma Junaina ta na zuwa?"
Ta yi guntun tsaki ta ce"wai ke meye damuwarki da wannan banzar? Me zai kawo ta?"
Na yi dariya na ce"ke dai kawai ba kya son ta,abu nasu me zai hana ta zuwa?"
Ta ce"ai sai ta zo mu gani".
Na ce"to suwa za ki bawa? Guda biyu nake so,ina son gayyatar wata k'awata ne".
Ta ce"ok! Ba matsala,ko gobe sai ki zo ki karb'a ai,don dai yau yamma ta yi ne ma".
Daga haka na yi mata godiya muka yi sallama.
Washegari da safe Nazifi ya kira ni a waya,ya ce min sun riga sun shirya komai da yanda abun zai kasance,amma fa babu yanda za a yi dubu hamsin ta isa,don haka dole na samo hanyar da kud'i za su shigo.
Gabana ya fad'i cikin sauri na ce "yanzu kana ina?"
Ya ce"ina d'akina,amma yanzu zan fita".
Na ce"to idan ka fita ka jirani a k'ofar gida,sai na fito mu yi magana".
Haka kuwa aka yi,ya na fita ni ma na fita,na yi sa'a ma Anti ba ta falo. "Wai Nazifi dubu hamsin d'in ma ka san da yanda zan samu,da har ake neman k'ari?"
Ya ce"to Zinatu me zai hana a hak'ura? Tunda babu dole, wai ni dama taimakon ki zan yi,ganin halin da kike ciki,kuma da ina da kud'i wallahi ni me iya biya ne ayi miki komai ba tare da ko sisinki ba".
Na sauke ajiyar zuciya na ce"to yanzu nawa ake buk'ata?"
"Dubu d'ari biyu" Ya fad'a kai tsaye.
Na dafe k'irji tare da zaro ido na ce"haba Nazifi! Ko sata na fara ai ba na jin zan had'a dubu d'ari biyu nan da kwana bakwai".
Ya yi dariya ya ce"wa ma zai aike ki sata? Ki na mace,macen ma buduruwa,buruwar ma me kyaun suffa irinki Zinatu amma ki dinga tunanin ta inda za ki samu dubu d'ari biyu acikin kwana bakwai? Wallahi sai dai rashin niyya!"
Cikin son gano inda zancen sa ya dosa na ce"ban fa gane ba,ka yi min dalla-dalla".
Bai yi magana ba ya d'akko wayarsa a aljihu,kafin na ankara ya k'yasta min hoto,sannan ya ce"ba ni minti biyar ki gani".
Ya cigaba da danne-danne a waya,kafin ya kalle ni ya ce"na fad'a miki ba ni kad'ai zan yi aikin ba,dole sai mun had'a da direban sa,duk da ma na ji ance bai fiya son tafiya da direban ba,sai in mahaifinsa ya matsa masa.Sannan wanda zai kula da abinci da kuma abun sha a wurin,shi ma dole sai mun biya shi,ke megadin gidansu ma sai mun biya shi,sannan shi ma abokina da za a yi aikin tare da shi sai an biya shi,ni kuma na yafe, na miki saboda Allah".
Na ce"ni fa duk ba wannan ba,so na ke na fara jin yanda aikin zai wakana,idan na ji ba mai yiwuwa bane gwara na hak'ura kawai".
Sai ya duba wayarsa da na ji shigowar sak'o ya ce"kin gani ko!? Dama na fad'a miki ai ki na da kadara" Ya yi maganar ya na murmushi
Cikin rashin fahimta na ce"wai mene?"
Ya ce"yanzu na turawa wani gaye hotonki,na ce masa haja ce sabuwa dal,nawa zai siya? Shi ne ya ce ya siya dubu d'ari biyar kwana biyu".
"Nazifi ni ce hajar!?" Na fad'a da k'arfi,zuciyata na zafi
Ya yi shiru ya na kallo na. Na d'ora"tun farko sai da na fad'a maka zan yarda da sharad'in ka ne kawai idan babu sab'on Allah a ciki..."
Ya katse ni"wannan ba ya cikin sharad'i ai,idan ki na da hanyar samun kud'in an wuce wurin".
Na ce"Nazifi,ban tab'a Zina ba,kuma ba zan fara ta ba saboda Salim,idan na bada kaina ka na da tabbacin abun da za mu shirya d'in zai yiwu? Idan ba mu yi nasara ba fa? Na yi biyu babu kenan fa,ko kud'in za su siyo min wani mutuncin? Idan ma aikin ya yi kyau,da wane ido zan kalli Salim bayan ya aureni? Me zan fad'a masa?"
"Gaskiya ne!" Ya fad'a da d'an rauni a muryarsa
Sannan ya ce"ni dama na yi tunanin ba ki da hanyar samun kud'in ne,shi ya sa na yi hakan".
Na yi huci me zafi na ce"tabbas! Ba ni da wata hanya da zan samu dubu d'ari biyu,amma hakan ba zai sa ni aikata zina ba.Mutuncina na mijina ne in sha Allah, ba ma Salim ba,duk wani namiji da ya aureni ko da ba na son shi shi kawai zan mallakawa kaina.Zan dai nemi wata hanyar ba wannan ba,zan yi shawara".
Ya ce"to,amma ki yi da wuri,kin ga lokaci ya na k'urewa"
Na ce"in sha Allah! Sannan maganar get fas,na samu guda biyu, anjima zan k'arb'o a wurin Baby".
Ya ce"yawwa! Ya yi kyau,idan na dawo da daddare sai ki taho min da shi sashenmu".
Ya kalleni da kyau ya ce "kukan me ki ke yi?"
Oho! Ni ban ma san ina hawaye ba sai da ya fad'a, na kai hannu na share na ce"babu komai".
Ya ce"ban yarda ba! Waye wannan d'in Zinatu?"
Na ce"yayan k'awata ne fa,ya zo ya ke fad'a min ta rasu tun wancen satin".
"Kuma kun shak'u da k'awar sosai ko?" Ya tambaye ni,ya na maida fuskarsa kalar tausayi
Na share wasu hawayen,ina shirin yin magana ya rigani
"K'aryar ki ba ta samu shiga ba.Me ya had'a ki da J.S har ya zo wurinki? Ba ma wannan ba,me ya fad'a miki da ya saka ki kuka?"
Na ce"a ina ka san shi?"
Ya ce"fara ba ni amsa,kafin ki tambaye ni".
Haka kawai na ji na yiwa Nazifi yardar da zan ba shi labarin gaskiyar abin da ya had'ani da Salim.Ashe rabon ayi ne ya ja ni...
Mu ka shiga ciki,a tsakar gida mu ka zauna kamar an jona min batir haka na zayyane wa Nazifi tun had'uwata da Salim har izuwa abin da ya kawo shi wurina yanzu.Ya sauke ajiyar zuciya ya na murmushi ya ce"lallai ke ma Zinatu sai a barki! Yanzu ana ta shirye-shiryen aurenki,ke ashe ki na can ki na naki d'an bikin? To wallahi ki na ruwa!" Ya kwashe da dariya
Takaici ya rufeni,na ji dama ban sanar masa ba,na ce"dama don ka yi min dariya ka so jin sirrina?"
Ya daina dariyar ya ce"to ai ki na bada labarin tun kafin ki k'arasa,mafita ta zo min raina,wannan dariyar da kika ga ina yi,har da ta mugunta"
"Mugunta kuma?" Na tambaye shi,ina had'e gira.
Ya ce"yes! Salim na ke yiwa dariya,don kuwa muddin ki ka yarda da sharad'ina to fa ki sa a ranki kawai kin zama matar Salim,ko da za a kira ki da MATAR SHIGE...
*MATAR SHIGE...!*
_(Ba ta daraja)_
BY
*SADIYA ABDUL*
_(Maizafafa)_
*☀️FIRST CLASS WRITER'S ASSOCIATION☀️*
Page 15
"Zan amince da sharad'in ka kowane iri ne,muddin babu sab'awa Allah a ciki" Na fad'a jikina na d'an yin sanyi,don na tsorata da jin kalmar sharad'i,tunda ga dai yanda mu ka yi da Junaina
Nazifi ya yi murmushi ya ce"babu wani sab'on Allah a ciki,zance ake yi na kud'i muddin ki na da kud'i to kuwa ni zan shige miki gaba har sai kin samu shiga.Ke ni fa ban ga laifinki ba,wallahi yaron ya had'u ga kyau ga kud'i".
Na d'an fara fargaba,don ban san ko nawa zai buk'ata ba,kuma ni yanzu kud'in hannuna ba su haura dubu takwas ba,na ce"kamar nawa kenan?"
Ya ce"ki tanadi dubu hamsin,kafin nan da kwana takwas".
"Dubu hamsin!?" Na fad'a ina zare ido,saboda na yi mamaki,kuma uwa-uba ban ga ta inda zan samu dubu hamsin ba.
Ya yi y'ar dariya ya ce"e,dubu hamsin kuma a hakan ma fa bai zama lallai ta isa ba,kin ga ba ni kad'ai zan yi aikin ba,dole sai mun siyi wani na kusa da Salim,wanda zai taimaka mu samu damar gudanar da komai cikin sauk'i,sannan dole na sai get fast..."
Na yi saurin katse shi da fad'in"dakata! Wai wane irin aiki ka ke magana akai? Kuma get fas na meye?"
Ya ce"aiki ne mai wahala kuma me hatsari,amma muddin aka yi sa'a ya wakana babu tangard'a,to ni na tattabar miki kin samu Salim kin gama,sai dai idan ba ki so ba.Shi kuma get fas na shiga wurin da zai yi birthday na ke nufi,nan da sati d'aya ne,haka na ji a bakin wani abokin sa".
Na jinjina kai na ce"na san da maganar birthday d'in,amma ban san ya kusa ba,zan yi wa Baby zancen na ji ko zan samu get fas d'in".
Ya ce"to indai za ta ba ki,kawai idan ki ka karb'a ki bani saboda ke ba sai kin shiga wurin ba".
"Kamar ya!?" Na fad'a ina b'ata rai.
Ya ce"kin ga dai yanzu ki fara tanadin kud'in kafin mu gama tsara komai,amma in sha Allah komai zai zo da sauk'i".
Na ce"Allah yasa".
Jikina duk ya yi sanyi, ina tunanin ta inda zan samu dubu hamsin,ya fita daga gidan ni kuma na shiga sashen Anti
A falo na tadda ita ta na kallo,ta kalle ni ta ce"har ya tafi?"
Ni sai yanzu ma na tuna da k'aryar da na yi kafin na fita,na ce"e ya tafi"
Ta ce "ai da ya shigo mun gaisa,yaushe za a bugo invitation?"
Ina shegewa d'akin da aka bani a gidan na ce"kai Anti,ai da saura".
Zama na yi na kira lambar Baby,ta d'auka,bayan mun gaisa na ke ce mata"ashe birthday d'in mutumin nawa ya zo,ko gayyata ko?"
Ta yi dariya ta ce"ya ma zama naki ko? Ai ban yi zaton za ki je ba,in dai za ki je gobe ki zo ki karb'i katin,jiya ya bani guda uku"
Na ce"me zai hana ni zuwa? Wani ma ya yi rawa bare d'an makad'a? To amma sauran biyun na waye?"
Ta ce"a'a,ai dama ya bani ne kawai ko da wanda zan gayyata,tunda kin ga ni ba sai da get fas ba,tare za mu shiga da shi".
Na ce"kuma Junaina ta na zuwa?"
Ta yi guntun tsaki ta ce"wai ke meye damuwarki da wannan banzar? Me zai kawo ta?"
Na yi dariya na ce"ke dai kawai ba kya son ta,abu nasu me zai hana ta zuwa?"
Ta ce"ai sai ta zo mu gani".
Na ce"to suwa za ki bawa? Guda biyu nake so,ina son gayyatar wata k'awata ne".
Ta ce"ok! Ba matsala,ko gobe sai ki zo ki karb'a ai,don dai yau yamma ta yi ne ma".
Daga haka na yi mata godiya muka yi sallama.
Washegari da safe Nazifi ya kira ni a waya,ya ce min sun riga sun shirya komai da yanda abun zai kasance,amma fa babu yanda za a yi dubu hamsin ta isa,don haka dole na samo hanyar da kud'i za su shigo.
Gabana ya fad'i cikin sauri na ce "yanzu kana ina?"
Ya ce"ina d'akina,amma yanzu zan fita".
Na ce"to idan ka fita ka jirani a k'ofar gida,sai na fito mu yi magana".
Haka kuwa aka yi,ya na fita ni ma na fita,na yi sa'a ma Anti ba ta falo. "Wai Nazifi dubu hamsin d'in ma ka san da yanda zan samu,da har ake neman k'ari?"
Ya ce"to Zinatu me zai hana a hak'ura? Tunda babu dole, wai ni dama taimakon ki zan yi,ganin halin da kike ciki,kuma da ina da kud'i wallahi ni me iya biya ne ayi miki komai ba tare da ko sisinki ba".
Na sauke ajiyar zuciya na ce"to yanzu nawa ake buk'ata?"
"Dubu d'ari biyu" Ya fad'a kai tsaye.
Na dafe k'irji tare da zaro ido na ce"haba Nazifi! Ko sata na fara ai ba na jin zan had'a dubu d'ari biyu nan da kwana bakwai".
Ya yi dariya ya ce"wa ma zai aike ki sata? Ki na mace,macen ma buduruwa,buruwar ma me kyaun suffa irinki Zinatu amma ki dinga tunanin ta inda za ki samu dubu d'ari biyu acikin kwana bakwai? Wallahi sai dai rashin niyya!"
Cikin son gano inda zancen sa ya dosa na ce"ban fa gane ba,ka yi min dalla-dalla".
Bai yi magana ba ya d'akko wayarsa a aljihu,kafin na ankara ya k'yasta min hoto,sannan ya ce"ba ni minti biyar ki gani".
Ya cigaba da danne-danne a waya,kafin ya kalle ni ya ce"na fad'a miki ba ni kad'ai zan yi aikin ba,dole sai mun had'a da direban sa,duk da ma na ji ance bai fiya son tafiya da direban ba,sai in mahaifinsa ya matsa masa.Sannan wanda zai kula da abinci da kuma abun sha a wurin,shi ma dole sai mun biya shi,ke megadin gidansu ma sai mun biya shi,sannan shi ma abokina da za a yi aikin tare da shi sai an biya shi,ni kuma na yafe, na miki saboda Allah".
Na ce"ni fa duk ba wannan ba,so na ke na fara jin yanda aikin zai wakana,idan na ji ba mai yiwuwa bane gwara na hak'ura kawai".
Sai ya duba wayarsa da na ji shigowar sak'o ya ce"kin gani ko!? Dama na fad'a miki ai ki na da kadara" Ya yi maganar ya na murmushi
Cikin rashin fahimta na ce"wai mene?"
Ya ce"yanzu na turawa wani gaye hotonki,na ce masa haja ce sabuwa dal,nawa zai siya? Shi ne ya ce ya siya dubu d'ari biyar kwana biyu".
"Nazifi ni ce hajar!?" Na fad'a da k'arfi,zuciyata na zafi
Ya yi shiru ya na kallo na. Na d'ora"tun farko sai da na fad'a maka zan yarda da sharad'in ka ne kawai idan babu sab'on Allah a ciki..."
Ya katse ni"wannan ba ya cikin sharad'i ai,idan ki na da hanyar samun kud'in an wuce wurin".
Na ce"Nazifi,ban tab'a Zina ba,kuma ba zan fara ta ba saboda Salim,idan na bada kaina ka na da tabbacin abun da za mu shirya d'in zai yiwu? Idan ba mu yi nasara ba fa? Na yi biyu babu kenan fa,ko kud'in za su siyo min wani mutuncin? Idan ma aikin ya yi kyau,da wane ido zan kalli Salim bayan ya aureni? Me zan fad'a masa?"
"Gaskiya ne!" Ya fad'a da d'an rauni a muryarsa
Sannan ya ce"ni dama na yi tunanin ba ki da hanyar samun kud'in ne,shi ya sa na yi hakan".
Na yi huci me zafi na ce"tabbas! Ba ni da wata hanya da zan samu dubu d'ari biyu,amma hakan ba zai sa ni aikata zina ba.Mutuncina na mijina ne in sha Allah, ba ma Salim ba,duk wani namiji da ya aureni ko da ba na son shi shi kawai zan mallakawa kaina.Zan dai nemi wata hanyar ba wannan ba,zan yi shawara".
Ya ce"to,amma ki yi da wuri,kin ga lokaci ya na k'urewa"
Na ce"in sha Allah! Sannan maganar get fas,na samu guda biyu, anjima zan k'arb'o a wurin Baby".
Ya ce"yawwa! Ya yi kyau,idan na dawo da daddare sai ki taho min da shi sashenmu".