← Book details Matar Shege Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 12 OF 21

Sashe 12

Matar Shege Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Bayan na gama kuka na sai tunanin sharad'in Junaina ya dawo min,a gaskiya ina son Salim kuma ko da na ke ganin zan iya yin komai a kansa abun bai kai na aikata zina ba,to na saida mutunci na don ya aure ni,na je masa fanko kuma na saka ran zan yi wata daraja a idonsa? Ai idan na yi hakan na yaudari kaina,kamar an ba ni umarni na d'akko wayata na dubo lambar Junaina na doka mata kira

Ta d'aga da sallama ta na kiran sunana,ban amsa ba na fara magana"Junaina wannan sharad'in ya yi min girma,gaskiya ba zan iya ba,idan akwai wani ki fad'a".

"Za ki yarda da romance? Ina nufin ki yarda ya biya buk'atarsa ba tare da ya kusance ki ba". Ta fad'a kai tsaye kamar me bani shawarar na yi azumi ko sallah

Na yi shiru,ina tunani duk zina ai sunan ta d'aya ne,ko ta ido ma an ce ana zina bare kuma wannan babban abun

"Idan fa kin ga ba za ki iya ba,babu dole" Muryarta ta katse ni.

Mu na cikin wayar kiran Baby ya shigo,na yi saurin ce mata"zan kira ki anjima".

Na katse kiran,na d'auki na Baby na k'irk'iri murmushi me sauti na yi mata sallama.

Ta amsa sannan ta ce"da fatan kina lafiya matar Yaya Salim"

Na ji zuciyata ta motsa,na yi y'ar dariya na ce"Baby kenan,to Allah ya tabbatar".

Ta ce "Amin".
Sannan ta yi jim ta ce" amm...Zinatu ina son ganin ki gobe,akwai magana me muhimmanci da za mu yi da ke akan Salim,ina tunanin na samo mafitar da za ta shigar da ke wurin shi ta hanya me sauk'i".

"Da gaske kike!?" Na fad'a da d'an k'arfi,farinciki ya mamaye zuciyata

Ta ce"e,goben ki zo shagon gyaran jikina da yamma"

Na yi mata godiya na ce zan zo mu ka yi sallama.Tun kafin na ajiye wayar na ji muryar Baba ya na k'wala min kira

Gabana ya fad'i,don na san yau dama tara ni ya ke yi,na saka hijjabi na fita kaina a k'asa kamar malama,na je na tsugunna nesa da shi a tsakar gida na ce"Baba ga ni".

Ya ce"Zinatu da gaske dai ban isa da ke ba ko?"

Muryata na rawa na ce"a'a,wallahi ka isa da ni Baba".

Ya ce"to indai kin yarda ni ne na haifeki,daga yau kada ki sake fita ko k'ofar gida sai da izinina!"

Ban ce komai ba,sai gyad'a kai da na yi alamar na amince,na tashi na koma d'ak'i na fashe da kuka.

HABIB😥
Babu me son Habib don Allah?
*MATAR SHIGE...!*
_(Ba ta daraja)_

BY
*SADIYA ABDUL*
_(Maizafafa)_

*☀️FIRST CLASS WRITER'S ASSOCIATION☀️*

Page 13

Bacci kad'an na samu a daren,ina ta tunanin yanda zan yi na yiwa Baba biyayya,ba na son b'ata masa rai,amma kuma Baby ta buk'aci gani na goben,kuma na san ba zai yiwu na ce ita ta zo ba,tunda k'aruwa ta ce ba tata ba,na so ma na ce ta fad'a min ta waya sai kuma na ga rashin dacewar hakan,ta na ta k'ok'ari a kaina,ai sai ta ga kamar ma ban damu ba,itama ta janye jikinta.Ga tunanin yanayin da na saka Habib a ciki,watak'il ya na can a cikin damuwa ta dalili na.Ita dai Junaina na ajiye buk'atar su a gefe,don ta yi kad'an ta saka ni aikata zina,ta dad'e ba ta bani bayanan Salim d'in ba don uwarta!.

Washegari da ciwon kai na tashi,ina d'aki tun safe,na kira Salim har sau biyar bai d'aga ba,na tura masa sak'on fatan alkhairi,ina nan kwance ina ta juye-juye da sak'a da warwara na ji sallamar yayata anti Na'ima,na yi farinciki da zuwanta sosai kuwa,na fito tsakar gida inda suke zaune da Mama Saude ni ma na zauna mu ka shiga shan fira,don babu laifi anti Na'ima su na shiri da Mama,cikin firar take fad'a min alfarma ta zo nema a wurin Baba

Da mamaki na ce"alfarma kuma anti?"

Ta ce"e mana,so na ke ya bani ke mu tafi gidana,na fara yi miki gyaran jiki".

"Kuma tun yanzu ake yi?" Na tambaye ta.

Ta ce"to Zinatu sai yaushe? Sati biyar ne fa ya rage,sai na miki na sati hud'u,ki dawo idan bikin ya rage sati d'aya".

Jikina ya d'an yi sanyi na ce"to Allah yasa ya yarda".

Mama ta ce"zai ma yarda,ai ko ni sai na saka baki ya amince,to wa ya k'i gyara?"

Anti ta ce"a to! Idan ma Habib d'in kike ji ai ya san hanyar gidana,sai ya dinga zuwa kuna gaisawa".

"Uhm!" Kawai na ce,don ni fa ganin lamarin aurena da Habib na ke kamar almara.Na rasa ta yanda zan sanar da su na fasa,kowa na kalla sai na ga ya yi min kwarjinin da ban isa na tunkare sa da wannan batun ba,to amma fa na ga hakan ba mafita bace,tunda abu ya na ta k'ara matsowa,ya zama dole na samu mafita kafin sati biyun.

Bayan la'asar ta koma gidan Ummi, ta ce idan Baba ya dawo na kira ta a waya,kuma na shirya idan ya amince a yau za mu tafi Hotoro,k'arfe hud'u da rabi Baby ta yi min waya ta na tambayar zan shigo kuwa? Na ce mata ina nan tafe.

Da na gama shiri ma na jima ina nuk'u-nuk'u a d'aki,don ina shakkar taka umarnin Baba yau d'in,sai da na ga Mama ta shiga band'aki,sannan na zo na fice sad'af-sad'af,ba tare da na rufe k'ofar d'akina ba,na je na hau adaidaita,sai Sharad'a.

Muka gaisa da Baby cikin fara'a,ta bani wurin zama ta na tsokana ta da matar Yaya,ni kuwa sai murmushi nake ina jin kamar ya tabbata.

"Zinatu kin je wurin Junaina?" Ta tambaye ni

Kamar na yi mata k'aryar ban je ba sai na ga rashin dacewar hakan, "e na je" Na bata amsa

Ta gyad'a kai ta ce"to ya ku ka yi? "
Na yi jimm! Don ba na jin zan fad'a mata irin sharad'in da Junaina ta bani,don haka kawai na ce"cewa ta yi na je na tambaye shi,shi ya san dalilin da yasa ya ke son ta".

Baby ta tab'e baki ta ce"ai dama na fad'a miki kar ki je".

"Kin san mafitar da na samo miki?" Ta tambaye ni,na girgiza kai alamar ban sani ba

Ta ce"kin ganni nan! Duk gidanmu an fi so na,ana ji da ni,kuma ana gudun b'acin raina sosai, musamman Yaya,don ni kad'ai Allah ya jarabta da ciwon zuciya,idan ya tashi ina shan wahala sosai,su na mugun lallab'a ni don kar ciwon ya tashi,to kin ga kuwa idan na so za ki iya shigowa rayuwar Salim ta dalilin ciwona".

Na yi jim! Na y'an sakanni,kafin na ce"amma Baby ki na ganin hakan zai yiwu? Kuma ke d'in tada ciwon naki za ki yi saboda ni?"

Ta yi murmushi ta ce"Zinatu,ina son Yayana sosai,ina yi masa sha'awar ya auri macen da take mugun son shi kamar ke,saboda ban San lokacin da zai daina shaye-shaye ba,kuma kin San zama da me shaye-shaye sai wanda ya jure,sai mace me mugun hak'uri, ko kuma wadda take bala'in k'aunar mijin".

Na jinjina kai alamar gamsuwa,ina dai sauraron ta,amma ni har mantawa nake da shaye-shayen Salim,don a ganina ba komai bane,wannan k'aramar matsala ce.Hmmm! Ashe na yi kuskuren fahimtar da ya kusa jefa ni a rijiya gaba dubu,nan gaba dai za ku ji...

Baby ta d'ora da fad'in"zan nuna masa kawai indai yana son farinciki na to ya aure ki,idan ya k'i amincewa sai na fara nuna ina cikin damuwa,na daina walwala a gaban kowa,hakan zai tashi hankalin kowa na gidan,har su nemi jin ba'asi,to a sannan ne zan sanar musu da na zab'a mishi ke kuma idan bai aureki ba mutuwa zan yi..."

Ta na kawowa nan na tuntsure da dariya,ta saki baki ta na kallo na,sai da na yi me isa ta sannan ta rik'e hab'a ta ce"mene ya sa ki dariya?"

Na ce"haba Baby! Na ji ki na zance ne sai kace a shirin films, yanzu kawai sai ki cewa iyayenku kin yiwa Salim zab'in matar aure? Kuma don kin ce za ki mutu idan bai amince ba sai su yi masa dole?"

Baby ta yi murmushi ta ce"ki na mamaki ne? Da ace yau zan bawa Abba da Ammi labarin ki,na ce musu na yi k'awa ina son ta sosai,wallahi gobe idan ki ka zo gidanmu sai kin yi mamakin yanda za su karb'e ki,don har Abba ba zai fita aiki ba saboda ku gaisa".

Na jinjina kai na ce"a lallai na yarda ke y'ar gata ce".

Ta yi dariya ta ce"yanzu kin san yanda za a yi? Zan cewa Ammi na samu k'awa,na san za ta yi farinciki sosai"

Na katse ta da fad'in"to wai ke d'in ba ki da k'awaye?"

Ta yi wani murmushi ta ce"yanzu ba ni da k'awa ko d'aya,da dai ina da k'awa,sai ta ci amanata, na yarda da ita sosai ina son ta,amma ta cuceni,ta raba ni da wanda na ke masifar so,da tuni shi zan aura,yanzu haka har an yi auren su.Tun daga lokacin ban kuma sha'awar yin wata k'awa ba,kowa sai dai mu gaisa sama-sama,amma banda k'awance".

Cikin tausaya mata na ce"Allah sarki,Allah ya saka miki cin amanar da suka yi miki".

Ta yi murmushi ta ce"manta da su kawai.Za ki fara zuwa gidanmu as mun shak'u da juna,ni ma zan dinga zuwa gidanku,to daga nan sai na fara nuna wa Ammi kyaun halinki,idan na ga ba ta gane inda na dosa ba,sai na yiwa Salim zancen kai tsaye,tunda ya san komai,idan bai amince ba sai na yi plan d'in da na shirya"

Na ce"amma ki na ganin hakan zai yiwu kuwa?"

Ta ce"yes! Abu me sauk'i,amma fa gaskiya sai nan da sati uku".

Gabana ya fad'i da na tuna saura sati biyar bikina,ga shi ta ce sai nan da sati uku za a fara wasan,kuma ban san sati nawa game d'in zai d'auke mu ba.

"Me yasa sai nan da sati uku?" Na tambaye ta

Ta ce"e,saboda nan da sati uku Salim zai yi birthday, ya na girmama birthday d'insa,shi ya sa ba na son rage masa farinciki kafin zuwan ranar,don indai ina cikin damuwa shi ma ba ya tab'a walwala".

Hmmm! Na sauke ajiyar zuciya na ce"to shikenan Baby,na gode sosai da kulawarki".

Ta ce"kar ki damu,ai yi wa kai ne".
Chapter 12 · 0% Book details