Sashe 5
Matar Habibi Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Suma sallar suka wuce bayan sun rufe shagon, da yake akwai masallaci a nan gefensu. Ana idarwa Baffa ya fadawa Usman akwai inda zashi, in dai wani abin ya taso sai su kirashi a waya, ya dauki mashin dinshi bayan ya turawa Aziza sakon cewa yana hanya, sai lokacin ma ya kula da cajin wayarshi saura 2%. Tunda yaje shago da safe bai sakata a caji ba, daman kuma jiyama haka bacci ya dauke shi da dare suna chatting da Aziza bayan wayar da suka sha, wayar da itace ma tasa shi ya barowa Jamila dakin nashi ya dawo falo. Addu'a yakeyi kar wani ya kirashi wayar ta mutu kafin ya karasa, dan bayason saiya nemi wanda zai aika a kira masa Aziza, gara dai ya kirata a waya.
A ranshi ya dinga zabga tsaki, shifa abinda ya tsana da unguwar nan ta Rijiyar Lemo kenan, musamman wannan layin 'yan chanan, kamar babu layin daya kaishi yawan kwatoci, jiyan nan ya bada aka wanke masa mashin dinshi tas, wani lokacin har mamakin yanda za'ace yarinya kamar Aziza tana irin wannan unguwar yakeyi. Ko a cikin layin nasu ma gidansu ne kadai mai katoton gate. Sai dai bayan ya karasa, ya samu waje a gefe yayi parking din mashin dinshi yana kara kallon unguwar tasu, cike da mutane anata hada-hada, ga masu awara nan da dankali waje-waje, an zagaye su layi danqam. Baiyi mintina uku ba Aziza ta fito, kamshin da take zabgawa ya wanke masa duk wani takaicin bata mashin dinshi da yayi.
Daya kalleta kuwa saida ya tsinci kanshi da rokon Allaah daya hore masa halin karasa gininshi ko zai samu ya mallaki Aziza kafin wani yazo yayi masa shigar sauri, bakinta daya sha jambaki ja ya kara fito masa da hasken fatarta tar da kwan lantarki ya haske masa kamar don shi aka bar wuta
"Kinyi kyau"
Ya fadi yana mata murmushi, ta danyi far da ido kafin ta saukesu cikin kunya
"Zaka fara ko Habibi?"
Yanayin yanda tayi maganar yaji duk ya susuce, shifa wannan abubuwan, yanayin yanda take lankwasa murya in zatayi magana, 'yar shagwabar da takeyi masa, kwarkwasar nan, sai yaita kallon Jamila yana tunanin yanda akayi tun farko bai taba kula bata da wannan abubuwan ba, ya dinga zurfafa tunani, daman ko lokacin kafin suyi aure haka take? Ko kuma daga bayane ta canza tunda tanajin aita same shi bata bukatar ta dinga yi masa irin wannan abubuwan
"Kazo mu karasa ciki"
Cewar Aziza, bai kuma yi mata musu ba, yau ma kamar duk zuwan da zaiyi, ya shiga tunanin yanda za'ayi a shiga da mota gidan nasu Aziza. Inka shiga karamar kofar jikin gate din, baifi kayi taku hudu ba zaka samu katanga data raba gate din da cikin gidan nasu, sai kuma wata kofa da ba'a sakawa kyaure bama, nan zaka shiga, wani dan surkukin soro ne da su biyu ma in suka tsaya shi da Aziza a ciki tsaf yan hisba zasu samu sabon case, sai dai suji ana tambayar lambar wayar iyayensu, don da wahala jikinsu ba zai gogi na juna ba saboda kankantar shi, a gefe kofa ce da take a rufe, bai taba ganinta a bude ba, sai kuma dayar kofar da zata sadaka da wadataccen falon da suke zama suna zance a ciki.
Aziza ce a gaba yana biye da ita, tun daga bakin kofar kamshin turaren wuta yayi masa sallama kamar ya shiga Maiduguri. Yaji wani sanyi na ratsa shi, kasala da gajiya duk suka rufar masa, suna kara tuna masa da ya kamata shima yasa AC a gidanshi, ko da iya dakinshi ne kuwa. Ya zauna a daya daga cikin kujerun dakin da sallama a bakinshi yana ba Aziza dariya duk da ta amsa, ta dora da
"Ina wuni, an sha ruwa lafiya? Ya aiki?"
Ya sauke numfashi yana amsawa, hankalin shi yana kan kwanonin da aka shirya a tsakar dakin, bawai abinda ke ciki yake hasashe ba, kwanonin ne sukayi masa kyau matuka, dan bai taba ganin irinsu ba. Aziza ta sauko ta fara budewa, kamshi ya cika hancin shi, saida ta mike ta dauko wata darduma mai kyau, tukunna ta shimfida masa tana fadin
"Ka sauko Habibi, nasan bakaci komai ba"
Saukowar yayi ya zauna, yana kallon fararen yatsunta da jan lalle a jikin faratan, yayi saurin maida idanuwanshi kan farantin yana jan Istigfari saboda tunanin da yake neman kutso masa cikin kai
"Kice mun ba wahalar da kanki kikayi ba kika sake shirya wani abin, ai nace jiya ki sakamun a firij"
Saboda shifa wannan tortilla din data kirane a ranshi har yanzun, so yake kawai yaga daga inda zata bullo
"Ya zanyi dakai tunda baka zo ba? Kuma kasan Mummy ma zatayi mun fada tace ya za'ayi in baka abincin jiya"
Ta fara mika masa wani dan karamin kwano da wani abu a cikin narkakke da dan barbadin wani ganye-ganye a ciki. Ya karba yana kura masa ido na dan sakanni kafin ya duba sauran tarkacen da take ta kiciniyar dibar masa, shi dai baiga biredi ba, abinda yake hannun shi kuma yayi masa kama da butter
"Nasanka da son dankali, gashi anci maiko tunda azumi ne shine nace gara inyi maka mashed..."
Yaji kalmar, kuma yasan turanci ne, a dan abinda yakeji dai ya kasa fassara shi balle hadinshi da abinda yake hannunshi, ya dai karbi cokalin da ta mika masa ya dibo yana kaiwa bakinshi da Bismillah, ba don korar shaidan ba, don neman sa'a kar bakinshi ya kunyata shi yaki karbar wannan abin. Hakan kuwa ya faru, shi dai yaji galmi-galmi, amman baiyi masa yanayi da abinda zai iya ci ba. A yunwar da yakeji ai gara ma ta bashi kunu akan wannan mashed abin. Gudun karya bada kanshi ya dinga turawa yana hadiyewa yana rokon Allaah Ya kiyaye shi da bacin ciki, saboda cikinshi bai cika son bakon abu ba. Har wani numfashi ya sauke lokacin daya ajiye dan kwanon ta bashi filet
"Bari inzo Habibi, dan Allaah ka cinye komai"
Cewar Aziza tana tashi, yaji dadin bashi wajen da tayi, tana ficewa kan tsiren da yake ciki ya fara, yayi masa dadi sosai, yaso ace shine yafi komai yawa, sai kuma yaci samosa da spring rolls, shima sunyi masa fiye ma da tsiren, kamar ya bude sauran kwanonin ya kara haka yakeji, ya dauki lemon data tsiyaya masa ya kurba, akwai sanyi, amman dai bai gane ma dandanon lemon ba, yayi masa wani daci-daci saiya ajiye
"Sufa 'yan gayu harshensu ma kamar daban yake dana sauran mutane"
Ya raya ma ranshi, yanata barin abinda yake tunanin yamballs ne daga karshe saboda soyayyar da take tsakaninsu, idan Jamila tayi wuni yake yana ci, ya kudurce a ranshi zai siyi doya gobe tunda ta fada masa sauranta ne ta soya musu jiya, ya dan ajiye filet din yana, daya dauka dai sai yaji shi sakat a hannunshi, gashi da girma, amman baiyi masa nauyi kamar yanda ya sani ba. Sannan daya kalla da kyau ma, bayan abin kamar ba kwai bane ba, yadai yi kyan suya, sai kawai ya jefa shi a baki duka yana taunawa. Sai yaji kamar kubewa ce a tsakiyar, gabaki daya komai da yaci ya nemi dawo masa, ba arziki ya fito dashi daga bakinshi, sai kuma tunanin inda zai saka shi ya dinga masa yawo, cikin hanzari ya mike kamar zai kifa yana ficewa ya tura kyauren gidan ya jefa shi ya dawo ya zauna, lemon daya ajiye ya dauka ya kwankwade saboda zuciyarshi da taketa hargitsawa
Gabaki daya ba haka ya hango yau din ba, sai yakejin inama jiyan yazo, ya tabbata abinda ta shirya masa jiya yafi na yau nesa ba kusa ba, kawai dai ita din da kuma kwalliyarta ne suka danne masa rabin disappointment din, sai gata ta dawo dakin da sallamarta tana dorawa da
"Afuwan Habibi, kasan Matar Officer na gidan, yau nan tayi buda baki, nasan yanzun mijinta zaizo daukarta, akwai ajiyarta a wajena"
Matar Officer kamar yanda Aziza take kiran Yayarta Jalila dashi, daga Jalilar sai ita, tazarar shekaru biyu ce a tsakaninsu, sai dai Jalilar tayi aure da wuri, dan yanzun haka ma yaranta uku. Kuma daga yanda Aziza take yawan maganarta, akwai shakuwa mai karfi a tsakaninsu
"Haba ni da kin gama cikamun cikina, ga aiki na baro a shago, anya ma zan iya asham yau?"
Sai tayi dariya ta karasa cikin dakin sosai tana zama a gefenshi
"Baka cinye ba, ga cheese balls dinma baka cinye ba, kuma saboda kai nayi"
Ta karasa cike da rashin jin dadi a muryarta
"Cikina ya cikane sosai, naci daya dan yayimun kyau a ido"
Sai ta dan saki fuska
"Aikam sai in juye maka ka tafi dashi"
Baiyi musu ba, wannan ai mai sauki ne saiya cillar dashi a hanya koya samu wani almajiri ya bashi. Koma wanne abu dai, hira suka dingayi cikin nishadi. Ana fara kiran sallah yace mata
"An kiramu"
Ta turo baki
"Bangaji da ganinka ba"
Murmushi yayi
"Ni akace na gaji da ganinki ne? Gashi da wahala in sake samun damar zuwa kafin sallah idan Allaah Ya kaimu"
Aikuwa tayi kwal-kwal da idanuwa har yana hango kyallin hawaye a cikinsu, duk yaji ya susuce
"Kar muyi haka dake Babe, ga waya fa, ga video call"
Hawayen ta bari suka zubo
"Wanne video call? Abinda daka shiga gida baka yarda muyi saboda matarka, bayan nima yanzun ina da hakki akanka tunda ai aurena zakayi..."
Da sauri yace
"Inji wa ya gaya miki saboda ita ne? Nifa na isa da gidana, abinda nake so shi zanyi"
Aziza taja hanci tana kara narke masa
"To me yasa idan na kiraka baka dagawa? Aiko ba zakayi magana ba saika daga in ganka"
Ya jinjina kai
"Zan dauka, shikenan? Dan Allaah ki share hawayen nan bana sonsu"
A ranshi ya dinga zabga tsaki, shifa abinda ya tsana da unguwar nan ta Rijiyar Lemo kenan, musamman wannan layin 'yan chanan, kamar babu layin daya kaishi yawan kwatoci, jiyan nan ya bada aka wanke masa mashin dinshi tas, wani lokacin har mamakin yanda za'ace yarinya kamar Aziza tana irin wannan unguwar yakeyi. Ko a cikin layin nasu ma gidansu ne kadai mai katoton gate. Sai dai bayan ya karasa, ya samu waje a gefe yayi parking din mashin dinshi yana kara kallon unguwar tasu, cike da mutane anata hada-hada, ga masu awara nan da dankali waje-waje, an zagaye su layi danqam. Baiyi mintina uku ba Aziza ta fito, kamshin da take zabgawa ya wanke masa duk wani takaicin bata mashin dinshi da yayi.
Daya kalleta kuwa saida ya tsinci kanshi da rokon Allaah daya hore masa halin karasa gininshi ko zai samu ya mallaki Aziza kafin wani yazo yayi masa shigar sauri, bakinta daya sha jambaki ja ya kara fito masa da hasken fatarta tar da kwan lantarki ya haske masa kamar don shi aka bar wuta
"Kinyi kyau"
Ya fadi yana mata murmushi, ta danyi far da ido kafin ta saukesu cikin kunya
"Zaka fara ko Habibi?"
Yanayin yanda tayi maganar yaji duk ya susuce, shifa wannan abubuwan, yanayin yanda take lankwasa murya in zatayi magana, 'yar shagwabar da takeyi masa, kwarkwasar nan, sai yaita kallon Jamila yana tunanin yanda akayi tun farko bai taba kula bata da wannan abubuwan ba, ya dinga zurfafa tunani, daman ko lokacin kafin suyi aure haka take? Ko kuma daga bayane ta canza tunda tanajin aita same shi bata bukatar ta dinga yi masa irin wannan abubuwan
"Kazo mu karasa ciki"
Cewar Aziza, bai kuma yi mata musu ba, yau ma kamar duk zuwan da zaiyi, ya shiga tunanin yanda za'ayi a shiga da mota gidan nasu Aziza. Inka shiga karamar kofar jikin gate din, baifi kayi taku hudu ba zaka samu katanga data raba gate din da cikin gidan nasu, sai kuma wata kofa da ba'a sakawa kyaure bama, nan zaka shiga, wani dan surkukin soro ne da su biyu ma in suka tsaya shi da Aziza a ciki tsaf yan hisba zasu samu sabon case, sai dai suji ana tambayar lambar wayar iyayensu, don da wahala jikinsu ba zai gogi na juna ba saboda kankantar shi, a gefe kofa ce da take a rufe, bai taba ganinta a bude ba, sai kuma dayar kofar da zata sadaka da wadataccen falon da suke zama suna zance a ciki.
Aziza ce a gaba yana biye da ita, tun daga bakin kofar kamshin turaren wuta yayi masa sallama kamar ya shiga Maiduguri. Yaji wani sanyi na ratsa shi, kasala da gajiya duk suka rufar masa, suna kara tuna masa da ya kamata shima yasa AC a gidanshi, ko da iya dakinshi ne kuwa. Ya zauna a daya daga cikin kujerun dakin da sallama a bakinshi yana ba Aziza dariya duk da ta amsa, ta dora da
"Ina wuni, an sha ruwa lafiya? Ya aiki?"
Ya sauke numfashi yana amsawa, hankalin shi yana kan kwanonin da aka shirya a tsakar dakin, bawai abinda ke ciki yake hasashe ba, kwanonin ne sukayi masa kyau matuka, dan bai taba ganin irinsu ba. Aziza ta sauko ta fara budewa, kamshi ya cika hancin shi, saida ta mike ta dauko wata darduma mai kyau, tukunna ta shimfida masa tana fadin
"Ka sauko Habibi, nasan bakaci komai ba"
Saukowar yayi ya zauna, yana kallon fararen yatsunta da jan lalle a jikin faratan, yayi saurin maida idanuwanshi kan farantin yana jan Istigfari saboda tunanin da yake neman kutso masa cikin kai
"Kice mun ba wahalar da kanki kikayi ba kika sake shirya wani abin, ai nace jiya ki sakamun a firij"
Saboda shifa wannan tortilla din data kirane a ranshi har yanzun, so yake kawai yaga daga inda zata bullo
"Ya zanyi dakai tunda baka zo ba? Kuma kasan Mummy ma zatayi mun fada tace ya za'ayi in baka abincin jiya"
Ta fara mika masa wani dan karamin kwano da wani abu a cikin narkakke da dan barbadin wani ganye-ganye a ciki. Ya karba yana kura masa ido na dan sakanni kafin ya duba sauran tarkacen da take ta kiciniyar dibar masa, shi dai baiga biredi ba, abinda yake hannun shi kuma yayi masa kama da butter
"Nasanka da son dankali, gashi anci maiko tunda azumi ne shine nace gara inyi maka mashed..."
Yaji kalmar, kuma yasan turanci ne, a dan abinda yakeji dai ya kasa fassara shi balle hadinshi da abinda yake hannunshi, ya dai karbi cokalin da ta mika masa ya dibo yana kaiwa bakinshi da Bismillah, ba don korar shaidan ba, don neman sa'a kar bakinshi ya kunyata shi yaki karbar wannan abin. Hakan kuwa ya faru, shi dai yaji galmi-galmi, amman baiyi masa yanayi da abinda zai iya ci ba. A yunwar da yakeji ai gara ma ta bashi kunu akan wannan mashed abin. Gudun karya bada kanshi ya dinga turawa yana hadiyewa yana rokon Allaah Ya kiyaye shi da bacin ciki, saboda cikinshi bai cika son bakon abu ba. Har wani numfashi ya sauke lokacin daya ajiye dan kwanon ta bashi filet
"Bari inzo Habibi, dan Allaah ka cinye komai"
Cewar Aziza tana tashi, yaji dadin bashi wajen da tayi, tana ficewa kan tsiren da yake ciki ya fara, yayi masa dadi sosai, yaso ace shine yafi komai yawa, sai kuma yaci samosa da spring rolls, shima sunyi masa fiye ma da tsiren, kamar ya bude sauran kwanonin ya kara haka yakeji, ya dauki lemon data tsiyaya masa ya kurba, akwai sanyi, amman dai bai gane ma dandanon lemon ba, yayi masa wani daci-daci saiya ajiye
"Sufa 'yan gayu harshensu ma kamar daban yake dana sauran mutane"
Ya raya ma ranshi, yanata barin abinda yake tunanin yamballs ne daga karshe saboda soyayyar da take tsakaninsu, idan Jamila tayi wuni yake yana ci, ya kudurce a ranshi zai siyi doya gobe tunda ta fada masa sauranta ne ta soya musu jiya, ya dan ajiye filet din yana, daya dauka dai sai yaji shi sakat a hannunshi, gashi da girma, amman baiyi masa nauyi kamar yanda ya sani ba. Sannan daya kalla da kyau ma, bayan abin kamar ba kwai bane ba, yadai yi kyan suya, sai kawai ya jefa shi a baki duka yana taunawa. Sai yaji kamar kubewa ce a tsakiyar, gabaki daya komai da yaci ya nemi dawo masa, ba arziki ya fito dashi daga bakinshi, sai kuma tunanin inda zai saka shi ya dinga masa yawo, cikin hanzari ya mike kamar zai kifa yana ficewa ya tura kyauren gidan ya jefa shi ya dawo ya zauna, lemon daya ajiye ya dauka ya kwankwade saboda zuciyarshi da taketa hargitsawa
Gabaki daya ba haka ya hango yau din ba, sai yakejin inama jiyan yazo, ya tabbata abinda ta shirya masa jiya yafi na yau nesa ba kusa ba, kawai dai ita din da kuma kwalliyarta ne suka danne masa rabin disappointment din, sai gata ta dawo dakin da sallamarta tana dorawa da
"Afuwan Habibi, kasan Matar Officer na gidan, yau nan tayi buda baki, nasan yanzun mijinta zaizo daukarta, akwai ajiyarta a wajena"
Matar Officer kamar yanda Aziza take kiran Yayarta Jalila dashi, daga Jalilar sai ita, tazarar shekaru biyu ce a tsakaninsu, sai dai Jalilar tayi aure da wuri, dan yanzun haka ma yaranta uku. Kuma daga yanda Aziza take yawan maganarta, akwai shakuwa mai karfi a tsakaninsu
"Haba ni da kin gama cikamun cikina, ga aiki na baro a shago, anya ma zan iya asham yau?"
Sai tayi dariya ta karasa cikin dakin sosai tana zama a gefenshi
"Baka cinye ba, ga cheese balls dinma baka cinye ba, kuma saboda kai nayi"
Ta karasa cike da rashin jin dadi a muryarta
"Cikina ya cikane sosai, naci daya dan yayimun kyau a ido"
Sai ta dan saki fuska
"Aikam sai in juye maka ka tafi dashi"
Baiyi musu ba, wannan ai mai sauki ne saiya cillar dashi a hanya koya samu wani almajiri ya bashi. Koma wanne abu dai, hira suka dingayi cikin nishadi. Ana fara kiran sallah yace mata
"An kiramu"
Ta turo baki
"Bangaji da ganinka ba"
Murmushi yayi
"Ni akace na gaji da ganinki ne? Gashi da wahala in sake samun damar zuwa kafin sallah idan Allaah Ya kaimu"
Aikuwa tayi kwal-kwal da idanuwa har yana hango kyallin hawaye a cikinsu, duk yaji ya susuce
"Kar muyi haka dake Babe, ga waya fa, ga video call"
Hawayen ta bari suka zubo
"Wanne video call? Abinda daka shiga gida baka yarda muyi saboda matarka, bayan nima yanzun ina da hakki akanka tunda ai aurena zakayi..."
Da sauri yace
"Inji wa ya gaya miki saboda ita ne? Nifa na isa da gidana, abinda nake so shi zanyi"
Aziza taja hanci tana kara narke masa
"To me yasa idan na kiraka baka dagawa? Aiko ba zakayi magana ba saika daga in ganka"
Ya jinjina kai
"Zan dauka, shikenan? Dan Allaah ki share hawayen nan bana sonsu"