Sashe 4
Matar Habibi Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Dan jim Jamila tayi tana tauna maganganun Rufaida din, wata irin shakuwa ce ta shiga tsakaninsu kamar sunyi shekaru tare, dan Jamila zatace ita dai a yanzun bata da kawa kamar Rufaida, kuma sukan tattauna matsalolin da ba'a rasa duk wata mace dashi, musamman ta maza, su ba juna shawara
"Hmmm..."
Jamila ta iya fadi, kuma yanayinta yasa Rufaida ta fahimci cewa tana da damuwar da bataso ta fito fili ta fadi
"Karki yarda ki bar mijinki a hannun wata, musamman ma yarinyar da duk wani feleqe da takeyi kokarinta ta taddoki ne, kibari inta shigo sai kiyi lokacinta, amman yanzun kam ki kara rike mijinki"
Haka Rufaida ta dinga bata shawarwari kala-kala har saida taga tana aminta da maganganunta, ta kuma kira Arif tace ya bita ya karbo mata gumbar. Rufaida na fita bata jima ba, dan dawowar Arif kenan shima ya ruga daki dan ya cigaba da kallon shi, taji wayarta na ringing, ta dauka tunda tana nan ajiye a kusa da ita. Baffa ne, ta daga tasa a kunne hadi dayin sallama
"Mamin yara"
Ya fadi daga dayan bangaren yanasa tayi murmushi, kafin kuma ta amsa ya dora da
"Daman zanji ya kuka wuni ne? Ina yaran? Kinata aiki halan?"
Sai taji wani sanyi ya ratsa zuciyarta, akace abubuwan da mata suke so daga wajen mazajensu ba masu yawa bane ba, kulawa komin kankantarta na daga cikin wannan abubuwan, ta manta rabon da haka kawai Baffa ya kirata a waya. In kuwa ya kira to sako zai bata, ayi masa wani abin, ko ita ta kirashi suna bukatar wani abu, da takan kira inya tafi dan taji ya ya isa shagon sai yace mata
"Daman shikenan abinda zaki fada? Kai kema dai kina da rigima, sai kace wanda zai bace a hanya"
Irin wannan sage gwiwar da yakeyi mata kan abubuwa da yawa yasa ta hakura ta yakicewa kanta yi masa su tunda basa burgeshi. Ko kuma ita dince ta daina burgeshi ba zata iya cewa ba
"Bama aikin da nakeyi, dankali ne nake ferewa"
Ta fadi muryarta cike da annashuwa
"Akwai saura ne har yanzun? Ko in bada a karo sai a kawo muku?"
Kai ta girgiza tanata murmushi
"Akwai fa, kasan shi saurin lalacewa yakeyi, kuma azumin ma yazo gangara"
Tunda ita dankalinma baya cikin abubuwan da suke burgeta, saita soya shi sau nawa bataci ba
"To shikenan, kinga dinkunan nan da yawa, daman ince miki karki wahalar da kanki yau ba zan dawo gida da wuri ba, mun nemi wani abin muci anan. Kiyi abinci mai sauki kawai na sahur"
Lokaci daya taji wani abu ya haska cikin kanta
"Me kake so a dafa maka?"
Dariya yayi
"Kome kika dafa ai kinsan zanci"
Saita jinjina kai
"Zan dan fita anjima to tunda ba zaka dawo da wuri ba"
Dariyar ya sakeyi
"Kafarki ce take kaikayi daman, Allaah Ya tsare, ki dauki dubu biyu a dakina inda nake ajiye kudi saikiyi kudin mota..."
Ta fara jera masa godiya
"Wai ina ma zakije matar nan?"
Saita kama dariya
"Badai kace kabarni ba?"
Shima dariyar yakeyi
"Bazan biye miki ba, bari inyi aikina koma ina ne a dawo lafiya. Ki kula da kanki dai, kar kuma ki dade"
Ta jinjina kai, saida tasa hannu tana share wata yar kwallar farin ciki, yaushe rabon data jita cikin nishadi haka? Yaushe rabon da Baffa ya biye mata suyi hira cike da kulawa irin wannan? Harta manta, waya kuwa ko history ta duba na shekara daya basuyi wayar data wuce yan sakanni ba dashi, tunda yana gama fadar abinda zai fada yake kashewa batare ma daya jira tace wani abu ba, hira kuwa tunda ya gane mayi da 'yan matanshi inya dawo ta yanke a tsakaninsu, saita kirga magana nawa take hadasu inya dawo gidan kafin su kwanta.
"Asaad ajiye tsintar waken nan haka..."
Tace tana tsame hannunta daga cikin dankalik ta tafi ta dibo cefane ta hau gyarawa, bayan ta wankesu, ta dauko wani kwali da busashen kifi yake a ciki, Yayanta Kabiru ne ya kawo musu tsarabar shi daga Jos inda yake aiki, da yawa ta diba ta zuba a wata tukunya ta yanka albasa ta zuba citta da tafarnuwa, dan Allaah Yayita da jin karni matuqa, in zatayi amfani da kifin saita fara tafasa shi haka ta zubar da ruwan, tukunna ta zauna ta gyara shi ta cire kan da kaya. Cikin wani lokaci sai gashi ta gama miyarta mai yawa. Yau kam yanda ya faranta mata rai, itama saita faranta mishi.
Zata bashi mamaki, kayan buda baki zataje ta kai masa har shago, yaran shagon nashi ma sai bakinsu ya canza yau, ba zata bari yanda baiyi sahur ba, yayi buda baki a wahale. Shinkafa da miyar kifin zatayi, ta soya dankalin da wainar kwai, sai ta hada musu lemon citta, ta sauko wasu kulolinta da bata taba amfani dasu ba, a ciki zata shirya komai, haka wasu filet dinta masu kyau ta dauraye, ta fiddo robobin da taketa boyo don irin haka, Rufaida ce ta bata su guda goma, design dinsu yayi kyau matuka, shisa ma ta adana, yau ga ranar amfani dasu tazo, shawarwarin Rufaida na dazun suka dinga mata shawagi
Haka kawai da zata biyewa zuciyarta da bakin kishi taje ta illata mijinta, a yanzun dai in wani abin ya same shi ai ita da yaranta sune da asara ba AZ din ba
Sai dai a lokacin da Jamila take aikinta cike da nishadi da son farantawa Baffa
Haka a gefe daya Baffa yake cikin nishadi da dokin ganin Magriba tayi dan yaje yaga abinda Aziza take ta fadin ta tanadar masa...!
#LubnaSufyan ✨
#WomenOfWords
#09035723778
Littafin nan na kudine akan #1k kacal, zaizo a manhajar Telegram 10/12/2024 In Shaa Allaah, bayan mun kammala shafukan dandano.
9035723778
Opay
Lubabatu Sufyan
Saika turo shaidar biya ta lambar da take sama. Nagode da addu'a'inku, nagode kuma da kwarin gwiwar da bakwa gajiya da bani
*
Duka littafin nan sadaukarwa ne ga Marubuciya Aisha Shafi'i, idan kunci karo da littafin nan, kun nishadantu, kun karu ta kowacce irin fuska, ku rokawa mijinta Isma'il Rahmar Allaah, ku roka mata sauki da juriyar rashin shi, ku rokawa yarinyarta rayuwa mai albarka. Nagode
********************** **************************
********** Ai Hausa Novels ****************
************************* **********************
DOWNLOAD More complete Hausa Novels, Education Books, Adventure, Drama, Mystery, Religion, Fiction, Non-Fiction, Romance, Meimor, True Life Stories & Others from our blog.
Visit > https://www.aihausanovels.com.ng
Ka tura mana sako ta adireshinmu na email, domin tuntubarmu ko turo mana hausa novel ko kuma post.
Email > [email protected]
******* FOLLOW US ******
Facebook: Ai Hausa Novels
Twitter: Ai Hausa Novels
Telegram Channel: https://t.me/Aihausanovels
WhatsApp Number: 08138873799
Haka kuma domin shiga kowanne daga cikinsu za ku iya ziyartar shafinmu ku yi search na AI HAUSA NOVELS, hatta facebook group dinmu ma za ku samu.
********************** **************************
*************** Ai Hausa Novels ****************
********************** **************************
MATAR HABIBI
3
(Free page)
Wannan shagon na yanzun, guda biyu ne ya siya, da 'yar karamar plaza ce, akace mai ita ya rasu, to cikin yaran bayan an raba gado sai wasu suka siyar da nasu kason, wajene mai kyau, kuma a bakin hanya. Bayan ya siya a hankali saiya rushe katangar data raba shagunan, aiki yayi masa sosai, kusan duk wani tari daya dingayi da nufin siyan mota a wajen gyaran shagon suka tafi. Aka fadada shi, akayi musu dan karamin bandaki a ciki, saboda yaran shagon nashi idan aiki ya kacame musu, sukan kwana, da yake Baffa mutum ne mai tsantsani, bayason amfani da bandakunan plaza din sam.
Har yar doguwar kujera aka saka a cikin shagon daga gefe. Da shigar kananun kaya ya fito daga gida, sai kawai cikin yaran shagon nashi, Isma'il da yanzun zaice ma yana neman finshi kwarewa a harkar dinkin nasu na maza, gashi shi harda na mata ma yakeyi, ya dauko masa yadin daya manta ya siye shi yana fadin
"Oga Baffa nafa gama maka dinkin nan"
Ya karba, yadine ruwan toka mai duhu, irin masu laushin nan, ba wani abu akayi a jikin dinkin ba, amman yayi kyau matuqa, hannun dogo mai links, sai maballai a jiki, yasha guga, sai kamshin turaren sa Isma'il din yake amfani dasu a jikin duk wani kaya da zai dinka sukeyi, sai yaji ai wannan kayan sune ma yakamata ace ya saka anjima in zaije wajen Aziza. Haka kuwa akayi, yana ganin shida tayi ya shiga bandakin nan, yayi amfani da soso da sabulun da suke dashi ya kara wanke kafafuwanshi da babu abinda sukayi, har fuska ya wanke, inda ace shi din ba kumama bane ba wanka zai karayi, to komin zafin da akeyi saiya sirka ruwa yake iya wanka. Haka ya dauki mai da yake ajiye a saman wata yar shelf din katako da akayi, ya murza a hannuwanshi da kuma kafafuwa, sauran ya murza fuska, ya daura alwala, tukunna ya dauki kayan ya saka a cikin bayin
Yana fitowa ana fara kiran sallar magriba, Usman ya mika masa ruwa mai sanyi da dabino, yayi Bismillah ya fara cin dabinon tukunna yasha ruwan
"Oga Allaah dai yasa ba zance zakaje ba, irin wannan shan wanka da magribar nan"
Cewar Rabi'u dayake mikewa daga kan kekenshi
"Kaga wani sa'ido ko?"
Baffa ya fadi yana murmushi
"Da gaskiyarshi fa Oga, ba zamu bari a hada baki damu ayiwa Maman Arif haka ba, kai Isma'il kaine kayi dinkin nan, kamar a kunnenta"
Dariya Isma'il yayi yana daga hannuwa sama alamar saranda
"Ku rufamun asiri, ni na dauka ma cikin kayan sallah ne wallahi"
Kai kawai Baffa ya jinjina
"Wato dai in na lura daku, kamar bayan Jamila zakubi"
A tare suka hada baki suka amsa, ciki kuwa harda Abbati da bai cika magana ba, dan shi saida ya dora da
"Nan Madam take shaqaro kuloli da abinci ana aiko mana, so kakeyi a janye mana tallafi?"
Maganar taba Baffa dariya sosai
"Ni sallah zanje, ku kuka sani"
"Hmmm..."
Jamila ta iya fadi, kuma yanayinta yasa Rufaida ta fahimci cewa tana da damuwar da bataso ta fito fili ta fadi
"Karki yarda ki bar mijinki a hannun wata, musamman ma yarinyar da duk wani feleqe da takeyi kokarinta ta taddoki ne, kibari inta shigo sai kiyi lokacinta, amman yanzun kam ki kara rike mijinki"
Haka Rufaida ta dinga bata shawarwari kala-kala har saida taga tana aminta da maganganunta, ta kuma kira Arif tace ya bita ya karbo mata gumbar. Rufaida na fita bata jima ba, dan dawowar Arif kenan shima ya ruga daki dan ya cigaba da kallon shi, taji wayarta na ringing, ta dauka tunda tana nan ajiye a kusa da ita. Baffa ne, ta daga tasa a kunne hadi dayin sallama
"Mamin yara"
Ya fadi daga dayan bangaren yanasa tayi murmushi, kafin kuma ta amsa ya dora da
"Daman zanji ya kuka wuni ne? Ina yaran? Kinata aiki halan?"
Sai taji wani sanyi ya ratsa zuciyarta, akace abubuwan da mata suke so daga wajen mazajensu ba masu yawa bane ba, kulawa komin kankantarta na daga cikin wannan abubuwan, ta manta rabon da haka kawai Baffa ya kirata a waya. In kuwa ya kira to sako zai bata, ayi masa wani abin, ko ita ta kirashi suna bukatar wani abu, da takan kira inya tafi dan taji ya ya isa shagon sai yace mata
"Daman shikenan abinda zaki fada? Kai kema dai kina da rigima, sai kace wanda zai bace a hanya"
Irin wannan sage gwiwar da yakeyi mata kan abubuwa da yawa yasa ta hakura ta yakicewa kanta yi masa su tunda basa burgeshi. Ko kuma ita dince ta daina burgeshi ba zata iya cewa ba
"Bama aikin da nakeyi, dankali ne nake ferewa"
Ta fadi muryarta cike da annashuwa
"Akwai saura ne har yanzun? Ko in bada a karo sai a kawo muku?"
Kai ta girgiza tanata murmushi
"Akwai fa, kasan shi saurin lalacewa yakeyi, kuma azumin ma yazo gangara"
Tunda ita dankalinma baya cikin abubuwan da suke burgeta, saita soya shi sau nawa bataci ba
"To shikenan, kinga dinkunan nan da yawa, daman ince miki karki wahalar da kanki yau ba zan dawo gida da wuri ba, mun nemi wani abin muci anan. Kiyi abinci mai sauki kawai na sahur"
Lokaci daya taji wani abu ya haska cikin kanta
"Me kake so a dafa maka?"
Dariya yayi
"Kome kika dafa ai kinsan zanci"
Saita jinjina kai
"Zan dan fita anjima to tunda ba zaka dawo da wuri ba"
Dariyar ya sakeyi
"Kafarki ce take kaikayi daman, Allaah Ya tsare, ki dauki dubu biyu a dakina inda nake ajiye kudi saikiyi kudin mota..."
Ta fara jera masa godiya
"Wai ina ma zakije matar nan?"
Saita kama dariya
"Badai kace kabarni ba?"
Shima dariyar yakeyi
"Bazan biye miki ba, bari inyi aikina koma ina ne a dawo lafiya. Ki kula da kanki dai, kar kuma ki dade"
Ta jinjina kai, saida tasa hannu tana share wata yar kwallar farin ciki, yaushe rabon data jita cikin nishadi haka? Yaushe rabon da Baffa ya biye mata suyi hira cike da kulawa irin wannan? Harta manta, waya kuwa ko history ta duba na shekara daya basuyi wayar data wuce yan sakanni ba dashi, tunda yana gama fadar abinda zai fada yake kashewa batare ma daya jira tace wani abu ba, hira kuwa tunda ya gane mayi da 'yan matanshi inya dawo ta yanke a tsakaninsu, saita kirga magana nawa take hadasu inya dawo gidan kafin su kwanta.
"Asaad ajiye tsintar waken nan haka..."
Tace tana tsame hannunta daga cikin dankalik ta tafi ta dibo cefane ta hau gyarawa, bayan ta wankesu, ta dauko wani kwali da busashen kifi yake a ciki, Yayanta Kabiru ne ya kawo musu tsarabar shi daga Jos inda yake aiki, da yawa ta diba ta zuba a wata tukunya ta yanka albasa ta zuba citta da tafarnuwa, dan Allaah Yayita da jin karni matuqa, in zatayi amfani da kifin saita fara tafasa shi haka ta zubar da ruwan, tukunna ta zauna ta gyara shi ta cire kan da kaya. Cikin wani lokaci sai gashi ta gama miyarta mai yawa. Yau kam yanda ya faranta mata rai, itama saita faranta mishi.
Zata bashi mamaki, kayan buda baki zataje ta kai masa har shago, yaran shagon nashi ma sai bakinsu ya canza yau, ba zata bari yanda baiyi sahur ba, yayi buda baki a wahale. Shinkafa da miyar kifin zatayi, ta soya dankalin da wainar kwai, sai ta hada musu lemon citta, ta sauko wasu kulolinta da bata taba amfani dasu ba, a ciki zata shirya komai, haka wasu filet dinta masu kyau ta dauraye, ta fiddo robobin da taketa boyo don irin haka, Rufaida ce ta bata su guda goma, design dinsu yayi kyau matuka, shisa ma ta adana, yau ga ranar amfani dasu tazo, shawarwarin Rufaida na dazun suka dinga mata shawagi
Haka kawai da zata biyewa zuciyarta da bakin kishi taje ta illata mijinta, a yanzun dai in wani abin ya same shi ai ita da yaranta sune da asara ba AZ din ba
Sai dai a lokacin da Jamila take aikinta cike da nishadi da son farantawa Baffa
Haka a gefe daya Baffa yake cikin nishadi da dokin ganin Magriba tayi dan yaje yaga abinda Aziza take ta fadin ta tanadar masa...!
#LubnaSufyan ✨
#WomenOfWords
#09035723778
Littafin nan na kudine akan #1k kacal, zaizo a manhajar Telegram 10/12/2024 In Shaa Allaah, bayan mun kammala shafukan dandano.
9035723778
Opay
Lubabatu Sufyan
Saika turo shaidar biya ta lambar da take sama. Nagode da addu'a'inku, nagode kuma da kwarin gwiwar da bakwa gajiya da bani
*
Duka littafin nan sadaukarwa ne ga Marubuciya Aisha Shafi'i, idan kunci karo da littafin nan, kun nishadantu, kun karu ta kowacce irin fuska, ku rokawa mijinta Isma'il Rahmar Allaah, ku roka mata sauki da juriyar rashin shi, ku rokawa yarinyarta rayuwa mai albarka. Nagode
********************** **************************
********** Ai Hausa Novels ****************
************************* **********************
DOWNLOAD More complete Hausa Novels, Education Books, Adventure, Drama, Mystery, Religion, Fiction, Non-Fiction, Romance, Meimor, True Life Stories & Others from our blog.
Visit > https://www.aihausanovels.com.ng
Ka tura mana sako ta adireshinmu na email, domin tuntubarmu ko turo mana hausa novel ko kuma post.
Email > [email protected]
******* FOLLOW US ******
Facebook: Ai Hausa Novels
Twitter: Ai Hausa Novels
Telegram Channel: https://t.me/Aihausanovels
WhatsApp Number: 08138873799
Haka kuma domin shiga kowanne daga cikinsu za ku iya ziyartar shafinmu ku yi search na AI HAUSA NOVELS, hatta facebook group dinmu ma za ku samu.
********************** **************************
*************** Ai Hausa Novels ****************
********************** **************************
MATAR HABIBI
3
(Free page)
Wannan shagon na yanzun, guda biyu ne ya siya, da 'yar karamar plaza ce, akace mai ita ya rasu, to cikin yaran bayan an raba gado sai wasu suka siyar da nasu kason, wajene mai kyau, kuma a bakin hanya. Bayan ya siya a hankali saiya rushe katangar data raba shagunan, aiki yayi masa sosai, kusan duk wani tari daya dingayi da nufin siyan mota a wajen gyaran shagon suka tafi. Aka fadada shi, akayi musu dan karamin bandaki a ciki, saboda yaran shagon nashi idan aiki ya kacame musu, sukan kwana, da yake Baffa mutum ne mai tsantsani, bayason amfani da bandakunan plaza din sam.
Har yar doguwar kujera aka saka a cikin shagon daga gefe. Da shigar kananun kaya ya fito daga gida, sai kawai cikin yaran shagon nashi, Isma'il da yanzun zaice ma yana neman finshi kwarewa a harkar dinkin nasu na maza, gashi shi harda na mata ma yakeyi, ya dauko masa yadin daya manta ya siye shi yana fadin
"Oga Baffa nafa gama maka dinkin nan"
Ya karba, yadine ruwan toka mai duhu, irin masu laushin nan, ba wani abu akayi a jikin dinkin ba, amman yayi kyau matuqa, hannun dogo mai links, sai maballai a jiki, yasha guga, sai kamshin turaren sa Isma'il din yake amfani dasu a jikin duk wani kaya da zai dinka sukeyi, sai yaji ai wannan kayan sune ma yakamata ace ya saka anjima in zaije wajen Aziza. Haka kuwa akayi, yana ganin shida tayi ya shiga bandakin nan, yayi amfani da soso da sabulun da suke dashi ya kara wanke kafafuwanshi da babu abinda sukayi, har fuska ya wanke, inda ace shi din ba kumama bane ba wanka zai karayi, to komin zafin da akeyi saiya sirka ruwa yake iya wanka. Haka ya dauki mai da yake ajiye a saman wata yar shelf din katako da akayi, ya murza a hannuwanshi da kuma kafafuwa, sauran ya murza fuska, ya daura alwala, tukunna ya dauki kayan ya saka a cikin bayin
Yana fitowa ana fara kiran sallar magriba, Usman ya mika masa ruwa mai sanyi da dabino, yayi Bismillah ya fara cin dabinon tukunna yasha ruwan
"Oga Allaah dai yasa ba zance zakaje ba, irin wannan shan wanka da magribar nan"
Cewar Rabi'u dayake mikewa daga kan kekenshi
"Kaga wani sa'ido ko?"
Baffa ya fadi yana murmushi
"Da gaskiyarshi fa Oga, ba zamu bari a hada baki damu ayiwa Maman Arif haka ba, kai Isma'il kaine kayi dinkin nan, kamar a kunnenta"
Dariya Isma'il yayi yana daga hannuwa sama alamar saranda
"Ku rufamun asiri, ni na dauka ma cikin kayan sallah ne wallahi"
Kai kawai Baffa ya jinjina
"Wato dai in na lura daku, kamar bayan Jamila zakubi"
A tare suka hada baki suka amsa, ciki kuwa harda Abbati da bai cika magana ba, dan shi saida ya dora da
"Nan Madam take shaqaro kuloli da abinci ana aiko mana, so kakeyi a janye mana tallafi?"
Maganar taba Baffa dariya sosai
"Ni sallah zanje, ku kuka sani"