Sashe 3
Matar Habibi Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
"Amman ai mun makara sahur ko? Kinsan irin wahalar da na sha jiya kuwa Jamila? Gaskiya kisa alarm a wayarki yau"
Kai ta jinjina masa
"Kaje karka makara sallah"
Kamar ba zai tafi ba sai kuma ya wuce, ta tabe baki, jiya bayan ta kwantar da Nana tayi mata addu'a sosai, da batayi niyyar zuwa dakinshi bama, sai kuma ta sake kayan jikinta zuwa doguwar rigar bacci da ta wuce har kwaurinta, ta kara goga humra, ta nemi hula ta saka a kanta sannan ta tafi, a kwance ta sameshi yana danna waya, da yake wutar dakin a kunne take saita kashe, tabi hasken wayarshi har zuwa kan gadon, kafin ma ta gyara kwanciyarta yace
"Nifa a gajiye nake ba wani abu zan iya yi miki ba"
Maganar tayi mata bambarakwai, a lokaci daya kuma wani abu yazo yayi mata tsaye a makoshi, tasan shi din ba wani mabukaci bane ta wannan fannin, saboda kaso tamanin cikin dari na lokutta itace take binshi, kuma tasan tana iya kokarinta wajen yin gyara, shi ba ma'abocin bada kudi bane ba, sai ayi watanni kyautar kudi bata gifta a tsakaninsu ba, ko roka tayi kuwa bako da yaushe yake bata ba, saima kaji yana mitar
"Kin cika kashe kudi Jamila, meye zaki siya da baki dashi a gida?"
Amman kyautar da 'yan uwanta suke mata lokaci zuwa lokaci tunda sun san ba sana'a takeyi ba, a ciki take dauka tana siyan magungunan mata, maganin sanyi kam wannan baya yanke mata sam ko dan yanda ake kara jaddada amfanin yawan shanshi ga mace ko da bata da aure balle kuma mai aure. Da kanta a WhatsApp ta fice daga cikin groups da dama na matan aure saboda yanda in an samu wata mai maganin matan, suka siya aka gwada za'azo ayita sharhi, kaji wasu suna bada labarin yanda miji ya manne musu, wata ma zatace
"Nifa da niyyar kwana biyu yazo, amman kinganshi nan yana maganar ya kamata ace wannan komawar dani ya koma"
To ita kuwa duk wani doki da rawar kai a wannan harkar Baffa yayi mata itane a cikin watanni ukunsu na farkon aure kafin ta fara laulayin cikin Arif da yazo mata da zafi, daga baya kuma sai taga kamar abin koya fita daga ranshine, yanayin wannan hirar da take gani tsakanin mata, ita kuma inta siya tayi amfani dashi sai taga dai babu wani canji ta bangaren Baffa, saima ita da wasu magungunan zata ga kyansu, wasu kuma inta sha idan sun cika bauri ta wuni cikinta na murdawa. Sai kuma takeji kamar ta daina burgeshi yanzun, wannan soyayyar duk ta disashe. Amman duk da haka kai tsaye bai taba bude baki ya fada mata magana mai zafin ta yau ba. Idan ma gajiyar yayi to zai kyaleta ne ta shige jikinshi sosai ta kwanta.
Yanda gwiwoyinta sukayi mata sanyi yasa ta kasa tashi tabar masa dakin, zuciyarta ta dinga mata zafi, musmaman ma data ga ya juya kwanciyar shi yana matsawa ya bada tazara a tsakaninsu. Ta rufe idanuwanta da sukeyi mata yaji-yaji, bata kasance cikin mata masu saurin kuka ba, asalima abinda zai saka hawayenta zuba ba karami bane ba, ta dinga jero duk wata addu'a da tazo bakinta ko zata samu saukin zafin da kirjinta yakeyi, ashe bacci ne ya dauketa a haka, bata sani ba sai data fitsari ya tasheta tunda ta daddaki zobon da tayi babu laifi. Bataga alamar Baffa a kusa da ita ba, saita dauka ya shiga bayi, shisa ta nufi kofa ta bude da nufin tafiya dakinta, kuma har zata wuce saita dinga juyo karar kiran wayarshi daga falo.
Da mamaki ta nufi falon, yana kwance kan doguwar kujera yana bacci, ga wayar nan a kasa da alama subuce masa tayi bai sani ba, daman Baffa da bacci, sau nawa ko kiranshi akayi ita kiran saiya tasheta shi yana baccinshi. Ta karasa ta dauki wayar, sai dai tana dauka kiran na yankewa, zata ajiye masa a gefenshi sako ya shigo, kuma da yake ko a mukulli take zaka iya karanta sakon ta saman inka dan taba, haka kawai taji tanaso ta karanta, anyi saving din lambar da "AZ" kawai.
"Habibi bacci kayi ko? To bari in tashi inyi sallah in rokar mana Allaah Yasa next azumi kana gefena zakayi baccin nan"
Wani duhu-duhu ya nemi rufe mata ido, musamman da wani sakon ya kara shigowa
"Ina sonka sosai. Allaah Ya kulamun da kai Habibi Na, sai anjima In Shaa Allaah dan yau gara na kwana a zaune da in bari kayi dorere"
Daman haka kishin yake? Duk wanda take zato tanaji a baya karya ne, yanzun ne tasan yanda yake. To taya mata suke iya danne shi? Ya suke kallon mijinsu ya ketare ya tafi dakin wata matar batare da zuciyarsu ta kama da wuta ta kone ba? Ita gata, sako kawai tagani amman zuciyarta kamar tana gab da zama toka saboda yanda takejin tana ci da wuta. Sai gashi tanajin alamar hawaye suna neman zubo mata, ta ajiye masa wayarshi inda ta ganta a kasa, ta wuce dakinta da kudiri daya. In Shaa Allaah har a karasa azumi nan da kwanaki bakwai ko takwas ta gama tashin shi Sahur, ita AZ din saita tashe shi kafin azumi na gaba din da zasuyi tare saita dora daga inda ta tsaya a wannan din.
Yau ko dar bataji bama, dan daya shigo dakinta bankan-bankan lokacin ma da hijabinta a hannu
"Ke Jamila wai wanne irin abune ya sameki yau ma?"
Ya fadi bayan ya turo kofar
"Kasan goman karshen nan, sallah jima inayi, sai na dan kishingida sai yanzun na tashi naji anata kiraye-kirayen sallah, to alwala nayi ma yanzun nake shirin zuwa in tasheka"
Taji ranta yayi mata sanyi-sanyi ganin nashi ran a bace, a nutse tayi sallarta ta idar tana zaman Azkar. Tana idarwa ta koma tayi kwanciyarta.
*
Wajen Azahar tana zaune tana firar dankali, Nana kuma ta gama kukan faduwar da tayi da keken Arif ta buge bakinta har saida yayi jini, shine ta samu take baccin wahala, tayi mata shimfida anan tsakar gidan. Da yake gidan inka shigo gate, akwai wata yar haraba da har mota ma za'a iya parking dinta kuma a samu waje, sai ka kara shigowa wata kofa da zata hadaka da cikin gidan, daka shigo kofar akwai dan filin tsakar gida da ba wani girma ne dashi ba, daga gefe kitchen ne wadatacce anyi masa kanta mai kyau daga ciki, da yake itama ba wani tarkace ne da ita ba sai tsarin kitchen din yayi kyau. Akwai karamin bandaki a tsakar gidan, sai kuma wata kofa da inka shiga itace zata sadaka da falon Jamila, a cikin falon akwai daki daga hannun dama, inda ta mayar dashi dakin yaran, sai kuma daga hannun haggu dan dogon corridor ne da zai sadaka da dakuna guda biyu da suke kallon juna, daya na Jamila, dayan kuma na Baffa, kowanne daki kuma da bayi a ciki.
Tsarin gidan yayi kyau, dai-dai na masu rufin asiri. Sai dai yanda Baffa yake gaya mata tsarin saman ne yasa taji son wajen ya kara kamata, tunda yace a falon har wajen dining za'a fitar, sannan kuma kitchen a ciki za'ayi shi shima, ba kamar na kasan da yake a waje ba. Irin dai tsarin gidajen 'yan gayu. Abinda kawai take so da kasan shine tsakar gida, dan ita tanaso ta fito taga sararin samaniya lokaci zuwa lokaci, bawai kullum kana cikin daki ba. Har mamakin irin gidajen da basu da tsakar gida kwata-kwata takeyi.
"Mami waken duka zan tsince? Akwai yawa fa"
Asaad ya fadi cike da kosawa, tayi 'yar dariya. Shi Arif in dai akwai kallo tofa bashi da lokacin komai tunda yarone marar hayaniya, komai nashi da sanyi-sanyi yakeyi. Asaad kuwa irin yaran nan ne masu kulafacin uwa. Baiki duk inda tasa kafarta ya mayar da tashi ba, gashi da son aiki, shisa bata rasa abinda zata bashi ya tayata ko danma ya zauna waje daya
"Duka zaka tsince dan albarka, kayi maza kagama in baka ka dakamun maggi"
Aikuwa saiya kara maida hankali, dan yanason ta bashi dakan abu a karamin turminta, kwankwasa gidan da akayi yasa ta ajiye firar dankalin taje ta bude, tun daga kofar suka fara gaisawa da Rufaida. Wata mata guda daya da tun ranar da suka dawo unguwar suka fara mutunci saboda kirkinta, itama tace basu fi shekara biyu da dawowa unguwar ba, tana da yaranta hudu
"Dan Allaah ki taimako mun da flavor in kina da milk zansa a kunun aya, ragowar Intee ta mungular mun dashi"
Cewar Rufaida bayan sun gaisa da Jamila
"Allaah Ya shirya mana yaran nan, gashi kai ba abin ka jibgi kudinka ba"
Kai Rufaida ta jinjina
"Inka biye musu ai karyasu zakayi 'yan albarkar"
Daki Jamila ta shiga tana barin Rufaida da Asaad da yake gaishe da ita, tunda dan karamin firij din nata a falo yake, data ajiye shi nan tsakar gida rana ta hanashi abin kirki, a kitchen kuma ya cike mata waje, saita mayar dashi falo tayi masa waje tunda falon wadatacce ne. Data fito ta kawo mata ne take ce mata
"Kinga wata gumba ce aka kawomun naji dadinta wallahi, kin aiko Arif ya karbar miki na manta dana fito miki da ita"
Tabe baki Jamila tayi
"Dan Allaah ki rabani da 'yan shaye-shayen nan ina azumina"
Hararta Rufaida tayi
"Wannan gumbar yanda kikasan kina shan madara da kantu haka zakijita, kefa mazan yanzun saida gyara"
Yanayin fuskar Jamila dai inka gani kasan yau zancen bai zauna mata ba sam, saima yake tuno mata da wulakancin da Baffa yayi mata jiya
"Wannan duk baya hanasu karo aurensu insun tashi"
Dariya Rufaida tayi sosai
"Allaah Ya shiryaki wallahi, to ke ina ruwanki da karo aurenshi? Daman ai bawai zaki gyara bane dan karya karo aure, a'a taki mafitar zaki duba, ki gyara dan ki samu naki matsayin a wajen shi, in kika tsaya wallahi 'yan matan nan na yanzun da suke da ido a tsakar kai sai su sa kwabarki tayi ruwa"
Kai ta jinjina masa
"Kaje karka makara sallah"
Kamar ba zai tafi ba sai kuma ya wuce, ta tabe baki, jiya bayan ta kwantar da Nana tayi mata addu'a sosai, da batayi niyyar zuwa dakinshi bama, sai kuma ta sake kayan jikinta zuwa doguwar rigar bacci da ta wuce har kwaurinta, ta kara goga humra, ta nemi hula ta saka a kanta sannan ta tafi, a kwance ta sameshi yana danna waya, da yake wutar dakin a kunne take saita kashe, tabi hasken wayarshi har zuwa kan gadon, kafin ma ta gyara kwanciyarta yace
"Nifa a gajiye nake ba wani abu zan iya yi miki ba"
Maganar tayi mata bambarakwai, a lokaci daya kuma wani abu yazo yayi mata tsaye a makoshi, tasan shi din ba wani mabukaci bane ta wannan fannin, saboda kaso tamanin cikin dari na lokutta itace take binshi, kuma tasan tana iya kokarinta wajen yin gyara, shi ba ma'abocin bada kudi bane ba, sai ayi watanni kyautar kudi bata gifta a tsakaninsu ba, ko roka tayi kuwa bako da yaushe yake bata ba, saima kaji yana mitar
"Kin cika kashe kudi Jamila, meye zaki siya da baki dashi a gida?"
Amman kyautar da 'yan uwanta suke mata lokaci zuwa lokaci tunda sun san ba sana'a takeyi ba, a ciki take dauka tana siyan magungunan mata, maganin sanyi kam wannan baya yanke mata sam ko dan yanda ake kara jaddada amfanin yawan shanshi ga mace ko da bata da aure balle kuma mai aure. Da kanta a WhatsApp ta fice daga cikin groups da dama na matan aure saboda yanda in an samu wata mai maganin matan, suka siya aka gwada za'azo ayita sharhi, kaji wasu suna bada labarin yanda miji ya manne musu, wata ma zatace
"Nifa da niyyar kwana biyu yazo, amman kinganshi nan yana maganar ya kamata ace wannan komawar dani ya koma"
To ita kuwa duk wani doki da rawar kai a wannan harkar Baffa yayi mata itane a cikin watanni ukunsu na farkon aure kafin ta fara laulayin cikin Arif da yazo mata da zafi, daga baya kuma sai taga kamar abin koya fita daga ranshine, yanayin wannan hirar da take gani tsakanin mata, ita kuma inta siya tayi amfani dashi sai taga dai babu wani canji ta bangaren Baffa, saima ita da wasu magungunan zata ga kyansu, wasu kuma inta sha idan sun cika bauri ta wuni cikinta na murdawa. Sai kuma takeji kamar ta daina burgeshi yanzun, wannan soyayyar duk ta disashe. Amman duk da haka kai tsaye bai taba bude baki ya fada mata magana mai zafin ta yau ba. Idan ma gajiyar yayi to zai kyaleta ne ta shige jikinshi sosai ta kwanta.
Yanda gwiwoyinta sukayi mata sanyi yasa ta kasa tashi tabar masa dakin, zuciyarta ta dinga mata zafi, musmaman ma data ga ya juya kwanciyar shi yana matsawa ya bada tazara a tsakaninsu. Ta rufe idanuwanta da sukeyi mata yaji-yaji, bata kasance cikin mata masu saurin kuka ba, asalima abinda zai saka hawayenta zuba ba karami bane ba, ta dinga jero duk wata addu'a da tazo bakinta ko zata samu saukin zafin da kirjinta yakeyi, ashe bacci ne ya dauketa a haka, bata sani ba sai data fitsari ya tasheta tunda ta daddaki zobon da tayi babu laifi. Bataga alamar Baffa a kusa da ita ba, saita dauka ya shiga bayi, shisa ta nufi kofa ta bude da nufin tafiya dakinta, kuma har zata wuce saita dinga juyo karar kiran wayarshi daga falo.
Da mamaki ta nufi falon, yana kwance kan doguwar kujera yana bacci, ga wayar nan a kasa da alama subuce masa tayi bai sani ba, daman Baffa da bacci, sau nawa ko kiranshi akayi ita kiran saiya tasheta shi yana baccinshi. Ta karasa ta dauki wayar, sai dai tana dauka kiran na yankewa, zata ajiye masa a gefenshi sako ya shigo, kuma da yake ko a mukulli take zaka iya karanta sakon ta saman inka dan taba, haka kawai taji tanaso ta karanta, anyi saving din lambar da "AZ" kawai.
"Habibi bacci kayi ko? To bari in tashi inyi sallah in rokar mana Allaah Yasa next azumi kana gefena zakayi baccin nan"
Wani duhu-duhu ya nemi rufe mata ido, musamman da wani sakon ya kara shigowa
"Ina sonka sosai. Allaah Ya kulamun da kai Habibi Na, sai anjima In Shaa Allaah dan yau gara na kwana a zaune da in bari kayi dorere"
Daman haka kishin yake? Duk wanda take zato tanaji a baya karya ne, yanzun ne tasan yanda yake. To taya mata suke iya danne shi? Ya suke kallon mijinsu ya ketare ya tafi dakin wata matar batare da zuciyarsu ta kama da wuta ta kone ba? Ita gata, sako kawai tagani amman zuciyarta kamar tana gab da zama toka saboda yanda takejin tana ci da wuta. Sai gashi tanajin alamar hawaye suna neman zubo mata, ta ajiye masa wayarshi inda ta ganta a kasa, ta wuce dakinta da kudiri daya. In Shaa Allaah har a karasa azumi nan da kwanaki bakwai ko takwas ta gama tashin shi Sahur, ita AZ din saita tashe shi kafin azumi na gaba din da zasuyi tare saita dora daga inda ta tsaya a wannan din.
Yau ko dar bataji bama, dan daya shigo dakinta bankan-bankan lokacin ma da hijabinta a hannu
"Ke Jamila wai wanne irin abune ya sameki yau ma?"
Ya fadi bayan ya turo kofar
"Kasan goman karshen nan, sallah jima inayi, sai na dan kishingida sai yanzun na tashi naji anata kiraye-kirayen sallah, to alwala nayi ma yanzun nake shirin zuwa in tasheka"
Taji ranta yayi mata sanyi-sanyi ganin nashi ran a bace, a nutse tayi sallarta ta idar tana zaman Azkar. Tana idarwa ta koma tayi kwanciyarta.
*
Wajen Azahar tana zaune tana firar dankali, Nana kuma ta gama kukan faduwar da tayi da keken Arif ta buge bakinta har saida yayi jini, shine ta samu take baccin wahala, tayi mata shimfida anan tsakar gidan. Da yake gidan inka shigo gate, akwai wata yar haraba da har mota ma za'a iya parking dinta kuma a samu waje, sai ka kara shigowa wata kofa da zata hadaka da cikin gidan, daka shigo kofar akwai dan filin tsakar gida da ba wani girma ne dashi ba, daga gefe kitchen ne wadatacce anyi masa kanta mai kyau daga ciki, da yake itama ba wani tarkace ne da ita ba sai tsarin kitchen din yayi kyau. Akwai karamin bandaki a tsakar gidan, sai kuma wata kofa da inka shiga itace zata sadaka da falon Jamila, a cikin falon akwai daki daga hannun dama, inda ta mayar dashi dakin yaran, sai kuma daga hannun haggu dan dogon corridor ne da zai sadaka da dakuna guda biyu da suke kallon juna, daya na Jamila, dayan kuma na Baffa, kowanne daki kuma da bayi a ciki.
Tsarin gidan yayi kyau, dai-dai na masu rufin asiri. Sai dai yanda Baffa yake gaya mata tsarin saman ne yasa taji son wajen ya kara kamata, tunda yace a falon har wajen dining za'a fitar, sannan kuma kitchen a ciki za'ayi shi shima, ba kamar na kasan da yake a waje ba. Irin dai tsarin gidajen 'yan gayu. Abinda kawai take so da kasan shine tsakar gida, dan ita tanaso ta fito taga sararin samaniya lokaci zuwa lokaci, bawai kullum kana cikin daki ba. Har mamakin irin gidajen da basu da tsakar gida kwata-kwata takeyi.
"Mami waken duka zan tsince? Akwai yawa fa"
Asaad ya fadi cike da kosawa, tayi 'yar dariya. Shi Arif in dai akwai kallo tofa bashi da lokacin komai tunda yarone marar hayaniya, komai nashi da sanyi-sanyi yakeyi. Asaad kuwa irin yaran nan ne masu kulafacin uwa. Baiki duk inda tasa kafarta ya mayar da tashi ba, gashi da son aiki, shisa bata rasa abinda zata bashi ya tayata ko danma ya zauna waje daya
"Duka zaka tsince dan albarka, kayi maza kagama in baka ka dakamun maggi"
Aikuwa saiya kara maida hankali, dan yanason ta bashi dakan abu a karamin turminta, kwankwasa gidan da akayi yasa ta ajiye firar dankalin taje ta bude, tun daga kofar suka fara gaisawa da Rufaida. Wata mata guda daya da tun ranar da suka dawo unguwar suka fara mutunci saboda kirkinta, itama tace basu fi shekara biyu da dawowa unguwar ba, tana da yaranta hudu
"Dan Allaah ki taimako mun da flavor in kina da milk zansa a kunun aya, ragowar Intee ta mungular mun dashi"
Cewar Rufaida bayan sun gaisa da Jamila
"Allaah Ya shirya mana yaran nan, gashi kai ba abin ka jibgi kudinka ba"
Kai Rufaida ta jinjina
"Inka biye musu ai karyasu zakayi 'yan albarkar"
Daki Jamila ta shiga tana barin Rufaida da Asaad da yake gaishe da ita, tunda dan karamin firij din nata a falo yake, data ajiye shi nan tsakar gida rana ta hanashi abin kirki, a kitchen kuma ya cike mata waje, saita mayar dashi falo tayi masa waje tunda falon wadatacce ne. Data fito ta kawo mata ne take ce mata
"Kinga wata gumba ce aka kawomun naji dadinta wallahi, kin aiko Arif ya karbar miki na manta dana fito miki da ita"
Tabe baki Jamila tayi
"Dan Allaah ki rabani da 'yan shaye-shayen nan ina azumina"
Hararta Rufaida tayi
"Wannan gumbar yanda kikasan kina shan madara da kantu haka zakijita, kefa mazan yanzun saida gyara"
Yanayin fuskar Jamila dai inka gani kasan yau zancen bai zauna mata ba sam, saima yake tuno mata da wulakancin da Baffa yayi mata jiya
"Wannan duk baya hanasu karo aurensu insun tashi"
Dariya Rufaida tayi sosai
"Allaah Ya shiryaki wallahi, to ke ina ruwanki da karo aurenshi? Daman ai bawai zaki gyara bane dan karya karo aure, a'a taki mafitar zaki duba, ki gyara dan ki samu naki matsayin a wajen shi, in kika tsaya wallahi 'yan matan nan na yanzun da suke da ido a tsakar kai sai su sa kwabarki tayi ruwa"