← Book details Masarautar Jondan Part 3 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 8 OF 9

Sashe 8

Masarautar Jondan Part 3 Complete Hausa Novel · about 8 min read

A gigice ya shigo d'akin ina ganin shi, na kalli su Batul fita suka yi, nake inda yake tsaye na riko hannunshi, na zaunar dashi, sannan na zauna tare da daura kanshi a kafad'ana.
"Sun mai dakai matsayin ka ba! Shine kake jin tashin hankalin ko"

"Toh meye a ciki da kake damuwa zab'in Allah ne, dan haka ka amshi tayin su tun kafin su ma na karfi."
Na maida abin wasa, sannan na nuna mishi girman abinda suka yi da ya dace, sannan na kuma bashi goyan baya.

Ranar da akayi addu'o'in a ranar aka mai dashi kujeran shi, na dindindin.

Sai dai wannan karon anga tsarin matashin Basaraken, dan komai sai da aka zamanantar dashi, aka mai dashi boko zalla. Amma batun abinda ya shafi addini yana nan, bisa tsari.

Bayan shekara biyar, kwance nake a jikinshi bani da lafiya, amma dan bakin jaraba sai da ya cinye ni (🤣😂) sannan ya dawo yana tausayin gulma.
"Anya SAFINAH ba ciki ne dake ba kuwa? Dan naji kin kara armashi"

Make hannunshi nayi wanda yake kan shafafeffen cikina, kamar ban juyen yara ba, kodan banda jikine yasa haka oho, amma a kwana biyu nan nayi kina har idanuna irin na yan Chinese ya koma ciki.

Tabbas nima ina zargin cikin ne dani, sabida kuwa robar bakin mahaifa suka saka min, kuma ba.
Kafe shi nayi da ido, nace.
"Please Dr Fu'ad zaka kira."

"Toh muje muyi wanka."

Kamar na saka kuka haka nake ji, dakyar na mike ya tallabe Ni, muka je wanka muna fitowa yakira Dr Fu'ad, yazo duba Ni sosai.

Sannan ya tabbatar ina dauke da cikin wata uku (🤣shashanci irin na SAFINAH ba ita daya ba mata dayawa haka suke fama dashi sai ayi tsarin iyali da zaran rabo yazo Alkur'an sai dai wata taji haihuwa kawai, sabida Ni naga haka da idona)

Kamar mara gaskiya haka nake ji, dan Ni nasaka a raina na gama haihuwa, shi kam murna zai sake samun haihuwa a gidan shi,

Ablah zan iya cewa shekarunta bakwai, sai Amir me Shekara shida, sai Artah me shekara biyar, kuma kana ganin su kasan yaran kwakwa ne, koma nace kunika.
Kuma mazan basu da Fitina kamar Ablah, wallahi bata ji ga shegen taurin kai da kafiyar bala'i, idan tayi haka zaneta nake muyita rigima da Ubansa har yace nice na lalata mishi Y'a da rashin ji. Sai dai fatar shirya.

★★★
Kwanci tashi aran me rai, har za ayi bikin Khalilah, Ni ban samu zuwa ba Amma Ashraf ya tafi, harsu Ghaniyu nice dai Ashraf ya hana.

Kwanansu uku suka dawo dama abokin Dudu ta aura Dr Muhsin.

Sun dawo suka same Ni nayita fushi dasu, da zasu zo ne aka tawo da Hajja nace shikenan Aljanun batsa sun zo naga takaina.
........ Sha'anin rayuwa sosai Nannah ta zubawa alamarin mu ido, har cikin ya shiga wata tara wannan karon zan haifu yan wata tara.

Wasa wasa sai da na shige wata tara, sannan na haifo yan mata na biyu, masu mabanbantar kama, dan mun rasa da suwaye suke kama, a ranar da na haihu nasaka aka juya mahaifar,

Har muka dawo gida kallon Yaran yake, sannan yace..
"Wani sunaye ya kamata su ci"

Juya idanuna nayi nace.
"Me ban purple sunanta Amatul Islam Me ban pink Amatullah"

Da haka yayi musu hudubar, ranar da yaran suka cika bakwai aka fadi sunan sai da naga rashin jin dadi Nannah a fili dan taso a mata takwara Ni kuma naki yarda dan tun kafin na haihu nake tanadin sunan yaran.

...
Watanmu biyar muka zo naija har da tazuje na, wato Ashraf kai jama'a ina ganin bibiko yoh ko jela sai haka.
Munyi yawon cikin yan uwa da dangi sannan muka dire Maiduguri dan maida Hajja,

A jirgi muka hadu da Dr inda ya nemi yafiyata baki kula shi sai da Ashraf yasaka baki sannan na yafe mishi, munyi kwanaki sannan muka baro Abuja zuwa jordan, tunda Allah ya nufa a can zanen Kaddararmu take.

....
Ina samu Amatullah tayi barci na gungurata can gefe nace.
"Zo na baka labari me dad'i."
Daga nan muka lalace a duniyarmu.......

★★★
Ina zaune muna hira da Batul, sai gashi ya shigo yace.
"Kizo munyi baki"

Mik'ewa nayi ina mamakin suwaye bakin haka.

Har Palourn bakin shi naje nasame su anata hira wajen maza da ban mata daban cikin shiga irinta Alfarmar, duk cikin biyu ne muke kusan shekaru d'aya dasu.

Da sallama na shiga, matan suka zuba min ido.
K'asa-k'asa naji wata me ƙaranci shakaru a cikin su tace.
" Itace Sarauniya SAFINAH?"

"Eh ita ce."

"Assalamu alaikum! Yan uwan ga SAFINATA nan itace mata ta, kuma Sarauniyata"
Juyawa yayi zuwa gare Ni sannan yace.
"Tawa! Wancan me rawanin buzayen Shine Maude amma sunan shi Asadullah Aliyu Haidar, Na cikin Zanen kaddarata, ga matar shi can WEEHIDAN, sai wancan dan gayen Sadiq ga matar shi can Amrah na ciki da ciwo a rayuwata, sai Wancan dan Sanda, Mansoor ga matar shi can Muwaddah, na cikin ina da Buri, sai Babban Yayanmu Yunus me nasara na cikin matar so tare da MariamSajidah, ga Soja Aliyu Indimi mijin meenarsin na cikin Abadan Da'iman, sai Wancan dan kwallon golf Abu turab, mijin Aleeshbah, sai kuma Amiduddawlah mijin Jal Parih dan kwallon Real Madrid ne, sai Likitan can da matar shi Khadijah, Dr Maheer na cikin Yar gidan Yaddiko. Me gayya me aiki Yaya Malam na cikin Matar Malam tare da Matar shi Neeha. Yawwa ban gabatar miki da babban abokin Sadiq ba Wato Imran da matar sa Sarauniya Zuljah amma dukkan sai dai jinsin Aljanun ne, bismillah ku."

Haka Imran da Zuljah suka bayyana, sannan aka, dariya suka saka yan matasan masu jini a jika Imamu da Mai Nasara murmushi suka yi, Ya Man ya mike yace.
"Wai don Allah ya akayi muka zo nan ɗin nan"

Tab'e baki Ya Abu Turab yayi sannan yace.
"Mai Dambu itace ta hado mu nan tun zuwa na naganta a bayana labule fito kafin mu baki mamaki"

Haka na fito tsamo tsamo, ina zare idanuna, Haidar ya fidda bindiga yace.
"Daga nan ina zaki nufa"
Kallon buzayen nan nayi Asadullah da matar shi Weehidan, sannan na koma kan Jan Parih nace.
"Ita Soja Damagaran da Bauchi zan tsaya bayan nan nayi muku alqawarin bani sake gulmar kowa"

Murmushi Suka yi Imamu yace.
"Ya sunan labarinsu, Zanen Kaddarata shine labarin Weehidan da Asadullah, sai Mrs Amiduddawlah, kuruciyar Jan Parih, suke nan ai akwai TSUNTSUN DA YAJA Ruwa. Labarin Mahnoor"

"Toh ina take?"
Wata budurwa ce ta shigo, sannan na nuna musu ita.

Alhamdulillah Alhamdulillah mungodewa Allah da ya bani ikon gama wannan labarin cikin kwanciyar hankali da nutsuwa Inda nayi kuskure Allah ya yafe mana, inda nayi dai dai Allah yasa muyi tarayyar akan dai-dai.....

Da wannan nake muka fatan Alkhairi sannan anan nake ajiye alkalamina, zan tafi hutu, Insha Allah sai Bayan sallah, idan labari na ya iso muku toh ina niman yafiyar ku, domin Ni yafe muku.

Ana nake cewa duk wanda na mishi ba dai dai ba yayi hakuri Ajizanci ne na dan Adam, wanda ya cuce Ni da kalma d'aya Allah zai bi min hakkina.

Fatan Alkhairi

Idan da nisan kwana
Mrs Amdud
ZANEN QADDARATA
TSUNTSUN DA YAJA....
Insha Allah... Allah ya kawo mana karshe wannan Annoban

Nagode taku har kullum

Mai_Dambu
Oum Muwaddah....
[3/26, 2:54 PM] +234 806 222 4030: number da xaku mata magana idan kuna son Book ɗin Wanda yake a 500fs  +227 96 51 58 05 Maman Fareesah*
   *Ga masu son biyan Book 2-3 zasu iya turo kuɗinsu sai nasakasu a Paid grp idan ta bank ne 150₦ ne idan kuma Kati ne Transfer 200₦ ne, Mtn, ga number bankinaAcct: 0472282105...*
*Gtbnk Ramlat Abdulrahman Manga. Ga number da za asame ni 08130269641 nagode Masha Allah*

MJ3
9️⃣

   Lokacin da aka fito da Babyn, aka kawo musu k'in karb'a yayi yana kallon Nurse din da ta kawo babyn, dakyar ya bud'e baki yace.
"Ina mata ta?!"
      Sunkuyar da kanta tayi cikin sanyin jiki tace.
"Tana ciki sai dai muna kokuwar dawo da numfashita ne, dan yana kwacewa."

          Kamar wacce zai bugata da kasa yayo kanta.
"Ina mata ta nace."
"Kayi hakuri sir! Muna bakin kokarin mu akanta."
          Shigewa tayi ta barshi a gurin, sai Safa da marwa yake. Ko kallon yaron dake hannun Ghaniyu bai yi ba, suna tsaye Nurse din ta kuma fitowa ta amshi yaron ta shiga dashi, sannan ta koma, ciki bayan mintuna goma sha biyu ta kuma fitowa da sauri, ga baki daya sun birkitawa Ashraf lissafi. Dan kaiwa da komowar da suke kad'ai ya isa ya tabbatar maka SAFINAH tana cikin wani hali.

          Zama yayi ya cusa hannunshi cikin gashin kan shi, yana jin tashin hankalin da ya ci kaniyar wanda suke ciki.

      Kuma abin takaici duk yadda Bilal yaso su mishi bayani basu kula shi ba, haka suka zuba musu ido har suka gama abinda zasu yi. Sannan suka fito daga d'akin kowanne su fuskar shi a cike da alhini suka fito.
   Dafa kafad'arshi likitan yayi yace.
"Kayi hakuri!"
    Ya wucce shi jikin shi ne ya dauki rawa, yace.
"A'ah!!! Wallahi bazata mutu yanzun ba, karku ce min haka"

   D'akin ya shiga, cikin d'imuwar da damuwa, ya isa gaban gadonta. Ya kura mata ido cikin tashin hankali ya rike hannunta, sannan yace.
"Me yasa bana jin komai akan abinda idanuna suke nuna min, wallahi na kasa gasgatawa wai kece a kwance ba rai! Kinsan yadda nake jinki kuwa? SAFINAH ta ba haka ta shirya mana rayuwarmu ba, don Allah tashi kinji Safinatu na, don Allah ki rufa min asiri karki tafi ki barni Ni d'aya ina bukatar ki a rayuwata."

  Ya jima a kanta yana magana, sannan yayi shiru yana kallonta, a hankali ya juya zai bar d'akin dan sai lokacin hawaye Masu zafi suka biyo fuskar shi yace.
"Na yafe miki!"

       Rike hannunsa yaji anyi da sauri ya juya, sannan nace mishi.
"Gawa ta tashi."
     Murmushi yayi tare da jan kumatuna, ya dawo ya rungume Ni, tare da sake dariya yace.
"Me yasa?!"
            Kwantar da kaina nayi a kirjinshi nace.
"Sabida ina matuƙa sonka! Fushin da kake yi dani ne yaja nayi haka, amma kayi hakuri."
Chapter 8 · 0% Book details