← Book details Mai Daki Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 9 OF 10

Sashe 9

Mai Daki Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

111
Idan har akwai abinda nake tunawa
da Ishak da ke sake sani kin shi to bai
wuce dukan rashin tausayi da yake yi
mun ba.
To sai na auri Ahmad, mutumin da
ya an yanci na walwala. Nayi
rayuwar aure irin wacce ban taba
mafarkin ana yin irinta ba a gidan
aure.
Saboda irin sona da tattalina da
mijina yake yi. Ya nuna mun cewa ni
din ina da matukar muhimmanci a
wurinshi.
Ya kuma so ni so na hakika, ya
mutunta iyayena da yan uwana, ya
guje mun bacin raina, ya tattali farin
cikina.
Amma sai gashi 'ya'yanshi da
mahaifiyarshi sun ki yarda su bar ni

112
na zauna da shi duk da hakuri da
halinsu da nake yi.
Idan har ina da laifi ko kuma wani
ganganci da na aikata a lokacin da
aurena na fari ya mutu, to a wannan
karon kam nasan ba ni da wani laifi.
Sai dai na kasa hakura, fatana bai
wuce da ni da shi mu samu maslaha
kan al'amarin aurenmu ba.
Tunda dai an yi sa'a saki daya ne a
tsakaninmu.
An kwaso kayana tas daga gidan
Ahmad, ba wai don na hakura da
zama da shi ba.
Sai dai kawai don jiran shawarar da
shi da kanshi zai zartar a kan maganr.
Sakon da ya turo mun kenan a waya
daren da na dawo gida.

113
Cewa na saurare shi kan shawarar
da zai yanke na neman mana mafita
nan da kwanaki uku.
Sai kuma kudi da suka shigo
account dina masu auki.
Ta bangaren Babana dai abin ba a
cewa komai, don kuwa bakin cikinshi
ba ya' misaltuwa.
Umma kam har a wannan karon ba
ta ce komai ba, harkokinta take yi.
Nayi matukar kokarin ganin ban
takura kaina da tunane-tunane ba, ta
hanyar shiga duk wani hidima na gida
da ake yi.
Har girki na karba ni nake yi da
sassafe kan bakwai zuwa bakwai da
rabi na kammala abin karyawa.
Idan na gama kumana zauna taya
Umma saye da sayarwanta, muna
kulla na kullawa.

114
Babbar matsalata ba ta wuce na
rashin barciba. Sai nayi matukar sa'a
ne kwarai nake samu na dan runtsa.
Al'amurana ne kawai za su yi ta
dawo mun rayuwar da nayi da Ahmad
mu'amallarshi da kuma yadda yake
harkokinshi a cikin gidanshi.
Daga manya zuwa yara da kuma
masu yi mishi hidima bisa sassauci da
ganin mutuncin kowa.
Ranar shi da farin cikinshi dakuma
fushin shi da kuma wasu abubuwa
masu dama.
Me yasa mutane ba su da tausayi
ne, babu sassauci a cikin al'amura
amma kuma mu sai muce muna
neman sassauci a wurin Ubangijinmu.
Bayan mun san shi ne ya yi umurni
da mu yi wa na kasa damu sassauci da
adalci.

115
Duk da abin da Hajiya tasa danta
ya yi mun zama dashi bai fita a kaina
ba, har yanzu kuma jiran shi nake yi
naji abinda zai ce.
Satina uku cif a gida Ahmad yazo
sai da ya gaisa da Babana da Umma
sannan na same shi a zauren gidanmu,
bayan Babana ya aiko Tasi'u cewa
naje na same shi.
Cikin kyakkyawar shiga na dogon
hijabi da na dora akan kayan dake
jikina dinkin atamfa riga da zani na
same shi.
Nayi matukar kokarin daurewa ta
ganin bai fahimci wani abu game da
halin da na shiga ba.
Kaina na sunkuye na gaishe shi
bayan na zauna akan shimfidar
tabarmar da aka yi mishi.

116
Ya amsa cikin yanayin shi kadaran
kadahan. Ban kalle shi ba na ce, "Ya
su Hajiya?"
Ya dan yi jim bai amsa ba kafin ya
ce, "Suna nan kalau." Abinda a sani
kuma shi ne kallona yake yi duk da
kin yarda mu hada ido da nayi ta
hanyar kallon 'yan yatsun hannuna da
na yi wa lalle a safiyar yau.
"Nayi tafiya ne Hauwa'u, shi ne
abinda yasa ba ki ganni ba, tafiyar ta
dauke ni tsawon kwanaki goma sha
takwas, sai a daren jiya na dawo. Don
haka kiyi hakuri."
Shi dai mai yawan bada hakuri ne,
abinda zuciyata ta ke fada mun kenan.
To amma hakurin da ya bani a yanzu
menene ma'anarshi?

117
Nayi hakuri ne a kan sakin da ya ya
mun, ba zai iya sake zama da ni ba ko
kuwa nayi hakuri ne na koma dakina?
A yanzu ne nasan na daga kaina na
kalle shi muka hada ido alamar ya
dade yana kallona hakan bai sa na
daina kallon shi ba babu abinda ya
canza a tare da shi.
Komai nashi yadda yake illa
idanunshi da launin su ya dan surka.
"Kiyi hakuri Hauwa'u." Abinda ya
sake fada kenan a lokacin da na
sunkuyar da kaina na hadiye wani abu
mai tsanani da ya rike mun wuya.
"Ina so ki san kowa da irin
jarrabawarshi a rayuwa ni tawa
jarrabawar kenan.
A tafiyar da nayi nasa mutane
daban-daban sun je don su taushi
zuciyarta har sau úku.

118
A tunanina idan na dawo zan samu
wani dan sauyi daga gareta a game da
maganarmu wanda har da hakan ne
yasa na kara jan kwanakina na
dawowa.
Amma da na iso gida sai ban ga
hakan ba, don haka ne nayi
sammakon zuwa Kano a yau na gana
da kanin Mahaifina da a gobe nake sa
ran zai zo don ya samu Hajiyan."
Wani irin tunani ne ya yi gaggawan
shiga zuciyata da kwakwalwata, duk
da irin kwabata da zuciyata take yi sai
da bakina ya furta na ce.
"Idan a kaina ne ka ke tura mutane
wajen Hajiya to na roke ka ka daina
saboda kai da kanka ka gaya mun
cewa baka taba saba mata ba.

119
Kenan kana so ka tilastata ta
hakura ta barka ka zauna da ni ba bisa
son ranta ba.
Wanda hakan ba zai sa ta yi
sassauci a kan kiyayyar da take yi
mun ba."
"Ba a kanki nake turawa ba, a
kaina ne saboda halin da na shiga,
barin ki gidan da kuma dawowan da
nayi ba kya cikin shi.
Gaskiya ki ka fada, ban taba yin
makamancin hakan ba sai a yanzu
wanda nasan ko ta sassauto ta hakura
to akwai wani tsanani da za ki iya
fuskanta.
Amma ina so nayi miki alkawarin
ba zai yiwu na barki haka ba.
Har a yanzu ina da niyyar dauke ki
a gidan zuwa Kano. A karo na biyu na

120
dago kai na kalli Ahmad da har yanzu
yake kallona.
"Ba zan jagoranci batawarka da
Mahaifiyarka ba. Burina bai wuce
naga mun daidaita matsalolinmu sun
kare mun maida aurenmu ba.
Amma sai dai dama matsalar ba
tamu ba ce a inda matsalar take kuma
banga alamar wani sauki ba.
Ina rokonka kada ka tilasta
Mahaifiyarka zama da ni, don Allah.
Yadda a yanzu zuciyata ta hakura
ina rokonka kaima ka sakawa taka
Zuciyar sassauci.
Ina kaiwa nan na mike na shiga
gida, na fada kan katifata, kuka nake
yi irin wanda na dade ban yi ba.
Duk yadda na kai da son zama da
Ahmad abin ba zai yiwu ba.

121
Ya zama dole na taushi zuciyata na
danganaa na fawwalawa Ubangiji
lamarinshi, don ya isar mun ya bani
abin yi.
Kwana nayi cikin wani yanayi da
ba zan iya kwatantawa ba, don saukin
abin ma nayi alwala nayi ta nafilfili
ina rokon Ubangiji sauki, da
kyakkyawan zabi.
A cikin satin ne aka kai sadakin
Yaya Auwalu abin da muka dauka shi
ne za su saka ranar auren da nisa.
Sai kawai muka ji sun saka sati
hudu kacal.
Muna zaune da Umma a tsakar
gida muna kullin kukar da Baba Ladi
ta aikowa Umma na siyarwa.
Na ce, "Amma Umma gaskiya
auren nan da suka saka ya yi kusa da
yawa."

122
Ta ce, ""To ai na Allah ne, sannan
shi Babanku jiya ya same shi yayi
mishi bayanin komai.
Ya ce, Babu damuwa, don yana da
dan abin da ya dade yana tanadawa
don shirin auren.
Na ce "To ai shi kenan."
Umma ta ce, "To sannan kin san
shi hidima irin wannan ba ka shirya
mata nemi taimako kawai a wurin
Ubangiji idan tazo maka."
Na ce Haka ne, Allah yasa mu
gani lafiya." Ta ce, To amin.
Ke kuma Ubangiji ya baki mafita
kan wannan matsala da ta same ki na
mutuwar aure, ya ba ki miji nagari da
zai zauna da ke bisa adalci da
kyautatawa.
Ya kuma zaunar da ke a dakinki ba
tare da kin sake fitowa ba."

123
Ban iya amsawa Umma ba, don
kuwa babu abin da nake so naji irina
ce Allah ya sassauta zuciyar Hajiya ta
bar ni na koma dakina.
Gidan Alhaji Ahmad Rufa'i, don
kuwa har a yanzu dinnan burina
kenan ko zuciyata tayi kamar ta
hakura sai kuma ta kara harzukowva.
Idan na tuna da irin rayuwar da
nayi tare da shi, daurewa kawai nake
yi nake rokon zabin alkairi a wurin
Ubangiji a lokacin da nayi sallah.
Amma idan da da hali to da rokon
komawa kawai na rinka yi ko da
hakan yana nufin batawar Ahmad da
Mahaifiyarshi.
To amma abinda na sani shi ne,
idan nayi haka ban yi mishi adalci ba,
don kuwa da kanshi ya gaya mun

124
cewar ta sadaukar da farin cikin
rayuwarta domin shi.
Da kuma Yarshi da har a yau din
nan ban ma santa ba.
Sannan shi din ko ba don haka ba
mahaifiyarshi ce da Aljannarshi take
karkashinta.
Hakan da na sani shi ne yasa na
danne zuciyata na kara ba shi
shawarar cewa mu hakura har a jiya
da ya kira ni.
Don na tabbatar da ban zalunce shi
ba. Idan yaso ni kuma Allah sai yayi
mun kyakkyawan sakamako.
Shiri sosai muke yina shirin bukin
Yaya Auwalu. Ya hada lefenshi rigijif
gwanin sha'awa.
Samun Umma nayi na ce mata ina
so na kwashe kayan dakinta na zuba
mata nawa na gidan Ahmad.

125
Chapter 9 · 0% Book details